Showing 24001 words to 27000 words out of 54100 words
wayar taja dogon tsaki tace shegiya Allah yakara!
Aeda sauranki tunda haryanzu ALI bai gane waye keba yamiki saki uku yakoreki daga gidansa ba, Allah yasa kafankin nan tarube kowama yahuta banza
Ae wlh baby nice tamun daidai dataki daga wayanki nima shegiya ce idan nasake daga kiranki nan gaba...
Abun duniya yataru yamata yawa gashi yanzu batada wasu kudi ahanunta balle tabawa Auntynta tamata sabon aiki, kiranda takema su Rukky dansu bata kudi ne idan tasamu gun ALI tabiyasu gashi suma sun juya mata baya!
Shikuwa bokanta takirasa awaya yafi sau dari cewa ake wayar akashe!
Jin Rukky takashe mata wayar ne yasata sakin sabon kuka maicin rai...
Nidai nace Allah shikaraπ€ͺ
Kamar kullun randa bata girki ALI yazo mata saida safe nan take tambayarsa yabata kudi akwai abunda zatayi dasu
Kallonta yayi kafin yace keda kike zaune me zakiyi dawasu kudi kuma?
Su Mama zanyima siyayyar kayan abinci tafada kanta tsaye
Mamaki ne yakamashi danko shekaran jiyar nan ne yakaimusu abinci wanda akalla zasuyi wata biyu suna amfani dashi basu kare ba banda kudinda yabasu kuma yanzu tazo masa da wanan zancen?
Dayake badan tayaba masa yayi ba yasa yace da ita kamar nawa kike bukata?
Jika dari tace!
Hmm shikenan zan turo miki jika hamsin kiyi maneji dashi!
Nifa kudin bazasu isheni ba, kawai kabani yanda nace, ALI meyasa kake mun hakane? Tunda nazauna rashin lafiyar nan kake wani shashareni kamun adalci kenan?
Tsaye yayi kanta yace Faridah karki maidani sakaren namiji mana!
Agidan nan kema kinsan ina iyakacin kokarina akanki ina baki kulawa yanda yakamata, karki manta fa ko wata uku ba ayiba nabaki million daya ina kika sakasu? Bafa abunda kika siya ina gani ban miki magana ba bai isheki ba harkin rokeni wasu kudin kuma bayan shekaran jiyar nan dakaina nakaima su Mama abinci banda kudin kashi dana basu kuma kice su zakima siyayya?
Kuka tasaka tace ALI yau harni zakama gori da iyayena?
Cikin takaici yace kema kin sani nafi karfin namiki gori Faridah! Yau shekara nawa muna tare dake irin haka ta taba faruwa tsakaninmu dake? Haba kimun adalci mana!
Yana gama fadin yabar dakin jim kadan yadawo rikeda kudi ahanunsa yazo gabanta ya ajiye mata yace gasu nan jika dari ne kamar yanda kika tambaya shikenan ?
Kin bashi ansa tayi ganin yajuya yafita abunsa yana fadin mukwana lfy.
Saida yafita tashare hawayenta tana murna afili tafurta zaga gane kurenka ne idan kashigo hannuna daga kai har shegiyar matarka Sajidah wlh dik saikun dandana kudarku!
Ransa abace yashiga dakinsa Sajidah na ganinsa ta taso ta taresa cikin salon jan hankali take takowa izuwa inda yake kafin takaraso yadakatarda ita yana fadin Sajidah ba yauba!
Raina abace yake kije ki kwanta kawai
Kayi hakuri tafada kafin takoma takwanta cikin sanyin jiki
Kashe wutar dakin yayi daman da shirin baccinsa yakwanta bayan yagama jero aduo'in bacci yashafa ajikinsa
Saidai yarufe ido amma bacci yaki zuwa
Haka itama Sajidah takasa bacci danya saba mata idan yana dakinta tana jikinsa zatayi bacci
Kasa hakura tayi ahankali tamatsa ta isa inda yake tamanne ajikinsa
Kamar jiranta ALI yake yajuyo tareda janta ajikinsa suka shiga duniyar ma'aurata kowane kokarin faranta ran dan uwansa yake tuni kuwa ALI yamanta da baccin randa Faridah tacusa mishi...
Washe gari tun wajen karfe goma na safe saiga Salimat da Shuraime agidan alokacin ALI yana bacci dan yau bayada aikin safe
Hayaniyarsu ce ta tasheshi daga bacci dan daman Salimat badai surutu ba Shuraieme yace yafita itakam HaYaT jefi jefi take saka musu baki cikin hirarsu da Sajidah
Jallabiyarsa yasaka yafito daga can yake musu magana
Wanan wane irin iskanci ne haka kun hana mutane bacci?
Dikansu dagowa sukayi suka kalleshi Salimat tace
Yaya ALI ina kwana
Bansani ba yace yakoma daki
Dikansu dariya suka saka suka cigaba da hirarsu Salimat nafadin ae wallahi Aunty Sajidah kina kokari da halin Yaya ALI, yacika takura fa abu kadan an masa laifi shi jifa inda muke shikuwa yana sama dakinsa amma dan son bala'i yace an hanasa bacci ae wlh gwarama yatashi mutum yayita bacci haryanzu ace bai tashi ba?
Nikam yau bayada aiki ne?
Bayada aikin safe yau shiyasa Sajidah tafada tana murmushi cigaba da hirarsu sukayi HaYaT kam tsam tamike tanufi dakinta ta kwanta abunta
Suna nan zaune mai aikin Faridah tazo tawuce bayan tagaidasu da wasu kunshin kaya ahanunta
Salimat tace gida zakije ne?
Eh kawai tace da ita tasakai ta fita cikin sauri sauri gudu gudu dikansu da kallo suka bita harta bacema ganinsu
Sajidah Sajidah Sajidah....
Sunan Sajidah Faridah take kira kamar tatsaga bakinta da gudu Sajidah dasu Salimat suka karasa dakinta sukayi cirko cirko danko azaune take ba kuma abunda yasameta azatonsu ko faduwa tayi take wanan uban kiran
Lafiya dai?
Sajidah ta tambaya dan kuwa yau ne karo nafarko dataji sunanta abakin Faridah wacce ko gaisuwarta bata ansawa
Faridah au munafukai daman nasan arina! Da hadin bakinku mai aikina tasace mun kudi da sarkokina tagudu
Toh wallahi kunsha karya bazaku karyani ba ni nan nafi karfinku harke munafuka da munafukan iyayenki tafada tana nuna Salimat
Banda munafunci meya kaki gidan nan bayan shekaranjiyar nan kukazo?
Wai meke damunki ne Farida ? Sajidah ta tambaya tana mata wani kallo nada sauranki
Hmm ae Aunty Sajidah halin Aunty Faridah ne baki sani ba?
Kiji fa zagin su Ammiey take agabana
Amma gaskia Faridah baki kyautawa aeko ba komai su Ammiey sun girmeki bai kamata kina zaginsu irin haka ba koda ace baki auri d'ansu ba!
Kuma yar aikin taki ni banda yau ba maganarda ta taba shiga tsakaninmu da ita saiyau dazata fita tagaidamu muka ansa
Bawani! Funafuka wallahi in nayi lafiya daga ke harsu Ammieyn gabadaya kashinku yabushe ahanuna kuma wallahi kudina sai anbiyani!
A'a a'a ya haka?
Dikansu juyowa sukayi suna kallonsa karasa shigowa dakin yayi yace kowa yafita yabasu waje
Ba musu suka fita Salimat sai kunkuni take kasa kasa tana fadin daman ba laifinta yake gani ba kome tayi mtswwww Allah ya waddan naka ya lalace!
Ita kanta Sajidah mai hakuri yau ranta yabace matuka taya Faridah zata d'aura musu alhakin yimata sata akansu? Meta tara? Me take dashi dahar za'a d'auka...?
Kisani naji dik abunda kika fada Faridah kedai bazaki canza halinki ba!
Kinje kin jajuboma kanki yarinya tamiki sata kirasa abun fad'a saiki d'aura alhakin hakan akansu?
Su Ammiey ma baki raga musu ba amatsayinsu na iyayena ba?
Meyasa ?
Agaskiya nayi dana sanin aurenki wallahi Faridah kisani izuwa yanzu nasan komai akanki nakuma san dalilin aurenki dani gameda sirrinki ba abunda ban sani ba wlh kawai nazuba miki ido ne naga iya gudun ruwanki!
Wayarsa yaciro yadanna wata dauka da yayi na muryan Rukky
Tun ranar haduwarsu har izuwa ranarda HaYaT tayi wanan haukan saida Rukky takwashe komai tagaya masa
Faridah taji da kunnenta banda zufa da kyarma ba abunda take kuka tafashe dashi tana rokon ALI ya yafe mata
Wallahi sonka da kaunarda nakema ne yasani aekata hakan agareka kuma tun ranarda nahadu dakai nadena karuwanci nadena kula kowane namiji saikai kayi hakuri kamanta da komai muyi zamanmu dagani saikai zan baka kulawa nabaka dik abunda kakeso arayuwa
Zaki bani komai kikace?
Nazauna dagani saike?
Zaki iya haifo mun yara da cikinki?
Ya kikeso nayi da Sajidah narabu da ita kenan kike nufi?
Eh eh tafada tana murmushi wlh kome kake bukata arayuwa zan baka shi ALI dan Allah karka rabu dani
Murmushi yayi yace kin manta kin lalata mahaifarki tun kafin kishigo gidan nan Faridah?
Dawacce mahaifar zaki haihu kamar yanda kikace?
Tsuru tayi da ido tarasa abun fada sai kuka take dan kam yau karyarta takare batada wata mafita ALI yasan komai akanta!
D'aura hannunta tayi aka tana fadin wayyo rayuwa ya zaki juya mun baya haka?
Ke kika cuci kanki Faridah idan na cuceki ina rokon Allah yafidda miki hakkinki akaina
Idan kece kika cuceni ni nayafe miki duniya da lahira!
Yana gama fadin haka yafita yabarta sai shirgar kuka take tanama kanta kaico da wanan sauyin rayuwarda yasameta...
Ke kuzo muje nabiya daku ALI yafada yayi gaba ransa abace
Da ido Sajidah tabishi ganin yau yanda ransa yabace gashi yafita balle tasan yanda zatayi ta mantar dashi ajiyar zuciya tasauke tana fadin
Salimat idan kinje ki gaisheda Ammiey zanzo nadubasu kwanan nan kinji?
Toh Aunty Sajidah sai anjima taja hannun Shuraime tafita ko HaYaT batama sallama ba...
Ammiey nagajida zama da Faridah wallahi ko ganinta banasonyi ayanzu zaman dole nake da ita tausayinta kawai nake ganin halinda take ciki idan nakorata kamar ban mata adalci ba shiyasa kawai nake daga mata kafa dikda nasan wacece ita
Ajiyar zuciya Ammiey tasauke ita kanta jin wacece Faridah yasa dikta fita ranta gabadaya daman can bata sonta saidai kawai tana dannewa ne
Saidai tabbas idan ALI yasaketa yanzu bai mata adalci ba kuma mutane dayawa zasu zagesa su zagesu amatsayinsu na iyayensa muddin yarabu da Faridah a irin halin nan datake ciki
ALI ba abunda zance dakai kawai kayi istikara idan alkhairi ce ita nan agaba Allah ya daidaita tsakaninku idan kuma akasin haka ne Allah yasan meya dace dakai
Karike Faridah karkashin kulawarka harta warware gabadaya in yaso dik matakinda kaga yadace da ita kadauka akanta amma ba yanzu ba kanajina ko?
Toh Ammiey yafada cikeda ladabi da kaunar Ammieyn tasa Uwa tagari kenan farin cikin 'Ya'yanta...
Wajen karfe tara taji wayarda Salimat tabata tana kara d'auka tayi taga sunan Sis Salimat yabayana tana d'auka takara akunnenta tareda sallama
Salimat ta ansa bayan sun gaisa tace Sis HaYaT kihau Wtspp naga haryanzu baki hau ba nasaki groupes kusan uku kihau kiga
Murmushi HaYaT tayi dan ita tama manta dawayar gabadaya banda yanzu datayi kara ta tuna da ita
Ok barina hau nagani!
Ok Salimat tace tareda kashe wayar
Kunna data HaYaT tayi nan kuwa taga messags hudu sun shigo mata uku na grp ne daya kuma na Salimat murmushi tayi aranta tashiga na salimat ta ansa mata sallamarta tace Sis Salimat
Ykk
Lfy kalau! ina fatan kema?
Nima haka!
Yasu Ammiey?
Suna lafiya!
Ya kadaici?
Alhmdllh...
Daga nan suka shiga hira kafin sukoma cikin wani grp mai suna MATA TUBALIN AL'UMMA nan HaYaT taga ana wani shirin INA MAFITA? wata mata ta turo wasikarta akan matslar mijinta mata sun dage kowace sai bada tata shawarar take
Aekuwa HaYaT taji grp din yakwanta mata sosai fiyeda sauran....
Yau tsawon wata daya kenan bayan fallasar wacece Faridah sosai taji sauki yanzu tana takawa saidai ahankali kamar mai koyan tafiya
Ganin tun ranar ALI baisake dauko mata maganar ba yasa take tunanin koya yafe mata ne yamanta da komai?
Shiyasa tasaki jikinta saboda dik ranar girkinta adakinta yake kwana saidai ba abunda yakara shiga tsakaninsu tun ranarda hatsarin nan yafaru da ita, saidai yana sakar mata fuska yana mata dik abunda takeso dan har tambayarta yake idan zai fita me takeso azo mata dashi?
Wani lokacin tafada wani lokacin kuma tace ba komai!
Alakarta da Sajidah kuwa haryanzu bata sauya zani !
Musamn ma HaYaT dako ganinta batasonyi arayuwa dan aganinta ita tajayo mata dik halinda take ciki yanzu
Ba alamar yin nadama atattare da ita, burinta tafara fita dakanta tanemi mafita yanda zata samu tajuya kan ALI yadawo mata kamar da suyi zamansu daga ita saishi agidansu!
Hmmm abunda Faridah bata saniba shine ALI yajima da sauwake mata jira kawai yake tayi sauki yabata takardarta yahuta!
Yau ranar asabar yace tashirya zasuje su gaida iyayenta dan tajima rabonta dasu sukuma ba zuwa gidanta suke ba saidai sukirata awaya
Da murnarta tashirya tafito ta tardashi kasa shida Sajidah gaisheda ita Sajidah tayi bata ansa ba saima wata uwar harara data watsa mata tareda jan wani uban tsaki
Dauke kanta tayi kamar ba ita akayima ba azuciyarta take fadin Allah yakyauta!
Kallonta yayi shigarsa cikin manyan kayan Malam bahaushe yayi wani uban kyau yasaka fula tazauna daf kansa sai uban kanshi yake tashi ajikinsa ALI cikakken namiji burin kowace mace arayuwa tasamu kamarsa
Kalar gezner dinsa fara tasha dinkin hannu da zare kalar bleu
Dan iya yi Faridah itama lesh tasaka fari mai adon bleu ita ala dole saitayi kala da agonta ALI sai wani shan kanshi take tana hura hanci ita ala dole gata uwar gida zata fita da miji kuma ranar girkin Sajidah ne sai wani jiji dakanta take batasan me ALI yashirya mata baπ
Nikam Faridah bakiji gaisuwar bane?
Yatsina fuska tayi tace
Naji mana!
Banyi niyar ansawa ba banson raini shiyasa
Yanda take magana tana kwarkwasa yabawa Sajidah mamaki da dariya gashi kome tayi bakyua take ba dan haryanzu akwai tabon ciyo agoshinta bai bace ba kwana biyu kuma tayi baki fuskarta yakoma iri daya da jikinta tazama kamar wata dodaniya ahaka kuma bata ganin kamarta!
Allah yakyauta ALI yace kafin yajuya kan Sajidah yace
Natafi saina dawo!
Adawo lafiya tafada tana sakar masa murmushi
Shima murmushin yasakar mata yafita Faridah tabi bayansa
Dakyer take daga kafarta dan tazama kamar gurguwa gabadaya tafiyarta tacanza harda wani dukawa take kafin ta taka kafar tazama delu cogal cogalπ ance Malam kabiru makaho...
Agaban mota takame abunta sai murmushi take tana karawa ranta fal farin ciki yau abunta batasan meke jiranta ba...
Da sallama suka shiga Mamanta tashinfida musu tabarma ALI yazauna yana gaidasu cikin girmamawa da farin cikinta take ansawa
Kallon Faridah Maman tayi tace ke bazaki zauna bane Faridah ?
Girgiza kai tayi tace
Mama bazan iya zama akan tabarman nan ba!
Ina wancan dana siya muku kwanaki? Dama ita kika d'auko ae wanan sai kayana su lalace!
Tana dakin mahaifinki shi yadauketa yake amfani da ita kuma yanzu baya nan balle nadauko dakin akulle yake
Kiyi hakuri ki zauna yar nan
Kallonta ALI yayi yana mamakin hali irina Faridah shikam sai yanzu yake ganin rashin nutsuwarta da rashin tarbiyarta da rashin dacewarta tazama mata agareshi
Girgiza kai kawai yayi yana mikewa yace Mama daman kawota nayi danta jima bata ganku ba ku bazuwa kuke ba shiyasa!
Allah sarki ka kyauta kuwa!
Ni zan tafi yafada yana zura hannu cikin aljuhunsa yaciro wata takarda yamikama Faridah tawashe hakora tana kashe masa ido ita azatonta check ce ta kudi yabata danta bawa iyayenta farin ciki bakinta har kunne
Dakanta tarakashi har bakin motarsa tana fadin bazan jiraka ba gaskia anjima zan koma dan haka karma kabiyo dan batardani zakayi ba!
Murmushi kawai yamata yace sai wani lokacin Faridah yana fadin haka yaja motarsa yabarta nan tsaye
Maganarsa takarshe ce tadan bata mamaki saikuma dai tabasar tashige cikin gida da zumudinta kudi sun samu burinta zai cika
Tana zuwa tanemi guri can nesa da Mamanta tazauna tabude enveloppe din takarda biyu taga sun fado lokaci daya tasa hannu tadaukesu
Cheick din tafara karantawa taga kudi ne yarubuta har jika dari biyar cas ganinsu ne yasa tasaki murmushi afili tafurta ALI bawan Allah baka biyar mutum da halinsa dan aljana kenan!
Daya takardar tabude tafara karantawa kamar haka
_Ni ALI na saki Faridah saki uku ba igiyar aurenta kodaya akaina itama haka, idan kinsamu miji kiyi aurenki bazan iya cigaba da zama dake ba har abada tun bayan sanin wacece ke naji natsaneki Faridah dan haka na sauwake miki dan karna shiga hakkinki nayafe miki dik abunda kika mun wanda nasani da wanda ban sani ba! Wanan kudin nabaki ne saboda kitaimaki kanki da iyayenki kinemi sana'a mai kwari kidingayi gudun fadawa halinda kika fito aciki abaya kafin haduwarmu, ina fatan wanan abun zai zame miki aya kituba ki canza halinki ma'assallam. *ALI GADANGA*_
Tana kai karshen karanta takardar tafasa wani uban ihu tareda zubewa kasa sumamiya....
βπ»
[8/1, 7:01 AM] Hayat: πππππππππ
πππππππππ
*AyNuL HaYaTπ*
_MATAR ALI GADANGA_
πππππππππ
πππππππππ
*-_-_-_-_-_-_-_-_-_-*
*LaBaRi Da RuBuTaWaβπ»*
*-_-_-_-_-_-_-_-_-_-_*
*NeEnA_CoOlπ©π»βπ¦±*
*-_-_-_-_-_-_-_-_-_*
*_______________________*
*π³πͺNiGeR Ma FiErTΓ©π€π»*
*Ψ§ΩΩΩΩ
Ψ₯ΩΩ Ψ£Ψ³Ψ£ΩΩ ΨΨ¨Ω ΩΨΨ¨ ΩΩ Ω
Ω ΩΨΨ¨ΩΨ ΩΨΨ¨ ΩΨ¨ΩΩ Ω
ΨΩ
Ψ― Ψ΅ΩΩ Ψ§ΩΩΩ ΨΉΩΩΩ ΩΨ³ΩΩ
.*
*ΩΨΨ¨ ΩΩ ΨΉΩ
Ω ΩΩΨ±Ψ¨ΩΩ Ψ₯ΩΩ ΨΨ¨Ω ΩΨ§Ψ±Ψ¨ Ψ§ΩΨΉΨ§ΩΩ
ΩΩππ»*
π·π·π·π·π·π·π·π·
_DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN KAIβπ»_
π·π·π·π·π·π·π·π·
1β£3β£
_WANAN PAGE DIN NAKU NEπ_
_FIDDAH_
_MOM DADDY_
_MATAR ABDALLAH_
_ZAHRA_
_Maman Baffah_
_Fiddausi Aminu_
_Leemah Subra_
_Jeee Baby_
_Ummu Ahmed_
_Oum Noor_
_Safiya Bello k_
_Amzeey_
_Bilkisu U Hamzat_
_Amzeey_
_Munzhaf_
_Jiddah_
_Teemah Galaxy_
_Ummu Irfan_
_Maman Sultan_
_Ma'eeshah_
_Ummu Irfan_
_Maman Mufeedah_
_NEENA COOL FANS GROUP_
_AISHA MUHD AUNTY FANS CLUB_
_OUR NOVELS Group_
_MARYAM SALIS MAI DALA GROUP_
_NANA FU'AD EN AISHA GROUP_
_HAKIKA INAJIN DADIN COMMENTAIRES NAKU NAGODE AKARA HIMMAπ€π»_
Washe garin ranar ALI yasaka aka kwashe gabadaya kayan Faridah aka kaisu gidansu, HaYaT da Sajidah sosai abun yabasu mamaki ba kamar HaYaT data kasa samun ansar tambayrta gwarama ita Sajidah dole ALI yagaya mata yarabu da Faridah ne
Dikda kishiya ce amma ta nuna rashin jin dadinta da faruwar lamarin ganin tazo ta tarda Faridah agidan ba dadi ace itace tfita tabar gidan, saidai shedan yafara yimata huduba akan ae yanzu saiki sakata ki wala!
Daga ke sai mijinki ba wacce zata shiga tsakaninku yanzu ALI yazama naki ke kadai...
Abakin Salimat HaYaT taji rabuwar ALI da Faridah azahiri sosai tayi farin cikin rabuwarsu dan acewarta yarabu da annoba dan Faridah bala'i ce maccenda bata zama saida bokaye aeko makwaftaka da ita masifa ne balle zama gida daya da ita...
HaYaT kai yafara wayewa samun wayarda tayi sosai take taimaka mata gun sanin wasu abubuwa da ada bata sansu ba, dikda karancin shekarunta yanzu saitaji tana tsananin kishin ALI dason zama dashi matsayinta na matarsa ba yar aikin gidan ba ayanzu HaYaT tafara sanin darajar kanta ba komai take saka hannu tayi da Sajidah ba, tadena tayata girki saidai tayi shara da goge goge haka tana gamawa take komawarta daki tajanyo wayarta Salimat ce tadauki nauyin saka mata kudi awaya kusan dik sati shiyasa sam DATA bata yanke mata
Ayanzu jin kanta take kamar wata sarauniya sai wani irin miskilanci data ara tadaurama kanta, saisu wuni guri daya da mutum bazakaji sautin muryarta natashi ba kullun cikin wanka take gabadaya tacanza fatarta ta murmure sai wani kyalli da haske mai birgewa takarayi
yanayin rayuwarta agidan ada bata fitowa waje yanzu kuma kusan kullun tana lambu dayake can bayan gida tanashan iska abunta yanzu nan ne gurin zamanta dayake daga ALI har Sajidah ba zama gida suke ba shiyasa ba wanda yadamu da lamarinta sosai.
Watarana kamar amafarki taji ALI yana kiranta falo bata ansa ba saida yakira sunanta kusan sau uku kafin tadaga baki tace na'am
Fitowa tayi sanyeda hijab dinta har kasa tazo can nesa dashi tatsaya tace gani batareda ta kalli fuskarsa ba tana wasada yan yatsunta
Shikuwa soyake tadago suhada ido da ita amma sam taki saida yagaji can yace jibi za'a koma makaranta ungo wanan yafada yana turo mata wata yar karamar akwati yacigaba da fadin
Kibude akwai komai aciki littafai da komai na bukata dan haka ki kwana da shirin komawa idan kuma bakyason cigabada da karatunki shikenan!
Tunda yafara magana takafeshi da ido wani irin dadi da mamaki ne suka rufeta bata taba tunanin zatacigaba da karatunta ba tazata tarasa wanan gatan har abada!
Ashe bansani ba ALI zai cika mun burina wayyo Allahna hawaye ne suka biyo kuncenta tadauke