Showing 39001 words to 42000 words out of 54100 words

Chapter 14 - AYNUL HAYAT COMPLETE HAUSA NOVEL

12 Dec 2024

8204

haka


_Kin kyauta abunda kikayi, ke yanzu da wanan shigar yakamata maccen aure tazauna cikin wanda ba muharamanta ba?_

_Kije ki canza kayan nan ko kuma kisako hijab dinki maza!_

Tanakai karshen message din ta tabe baki tareda gogeshi gabadaya tacigaba da aikinta

Suna gammalawa suka saka akuloli suna jerawa akan dinning

ALI jin bata ansa sakonta ba yazata taji maganarsa saidai da mamakinsa yaganta tafito ahaka suna jera abinci itada Salimat

Tuni ransa yabace wato yarinyar nan batajin maganata?

Takoyi taurin kai? Zanyi maganinki ne yafada!


Suna gama jerawa tanufi dakinta har zata shiga toilet taga wani sakon yashigo mata azatonta Hamdan ne da azamarta tadauko wayar tana dubawa taga ALI ne

_Kin nuna ban isa dake ba nakuma gode da hakan!_

_Inaso na tusarda ke biyana cikinda zakiyi bazan taba yafe miki shiba, sanadinki narasa babyna gashi haryanzu dik iyakacin kokarinda nake amma haryanzu Sajidah bata dauki wani sabon cikin ba, dan haka kishiryama daukar ciki yau ko gobe bazan taba daga miki kafa ba dan haka ki kwana cikin shirin!_


Haushi ne yakamata dajin abunda yafada tamaida masa kamar haka

_Mace nake! Haifana akayi haka nima bana gudun haihuwa bismillah ni dakai ALI! Kadameni ciki ciki shin nice nasaka hannuna nature Sajidah hartayi barin ko kai? Karka sake sakani acikin irin wanan shirmen naka kaje yanda kayi nafarko ka kara kokari da azama kamata nabiyu kona huta!_

Tana gama rubutawa ta tura ta ajiye wayar tafada toilet cikeda takaicin yanda ALI yatakurata akan dole saita biyashi cikinsa yanda kasan itace tasaka hannayenta ta ture Sajidah mtswww taja wani dogon tsaki...


Sakon yaji yashigo yana karantawa fuskarsa na nuna almar bacin rai haryakai karshe yarufe wayar batareda yamaida mata ba, aransa yake fadin zaki gane ne yarinya....!




Koda suka hadu gun cin abinci baiko kalli inda take ba itama haka har suga gama aka dawo falo...


Bayan sati daya yau Salimat tace bazata je scul ba kanta namata ciyo sosai HaYaT tanuna jimaminta akai da hartace bazata je ba itama, Daddy yace karya ne bazaiyu su zauna dikansu agida ba taje ita

Badan taso ba Haidar yakaita sai zumbure zumburen baki take ala dole ita bataso zuwa ba

Haidar yasha dariyarta amota harsaida takusa yin kuka tukuna yashiga bata hakuri

Data shiga ajinma kana kallon fuskarta kasan bata cikin walwalla kamar kullun, Malam Hamdan yalurada halinda take ciki ana fita break yakirata awaya yana tambayarta lafiya?

Aekuwa kamar kar yayi magana tafashe da kuka tana fadin Salimat ce batada lafiya kanta yana ciyo kuma gashi Daddy ya hanani zama nakula da ita

Shi kansa Hamdan yajinjina shagwaba irinta HaYaT daga tambayarta saita saka kuka inama ace da hali tana kusa dashi ya rarasheta bata waya ba...???

Murmushi yayi azahiri yace ae Daddy yamun daidai MAI SANYI rashin ganinki na kwana daya daidai yake da rashin ganinki na shekara daya, da ace yau bakizo ba to nine zan kwanta rashin lafy kinga kuwa abun zai hade miki biyu da biyu kenan ga yar biyunki Salimat ga kuma masoyinki Hamdan dan na tabbatar saina fita bukatarki akusa dani dakuwa kinga saiki tattaro yanaki yanaki kidawo gidanmu kizo kiyi jinya

Jin abunda yafada batasan lokacinda dariya ta kubce mata ba, saida tayi mai isar tukuna tace kaikam anyi ragon namiji anan wlh!

Daga rashin ganina na kwana daya sai rashin lafiya?

Harnafiki ragwanta keda daga tambaya kika saka mun kuka kika tashi hankalina?

Turo baki tayi kamar yana ganinta tace aeni macece!

Kwaikwayon yanda tayi magana yayi yace aenima Namiji ne!

Dariya suka saka gabadayansu suka cigabada da hirarsu har lokacin komawa aji yayi...

Yana ofis dinsa Ammiey takirasa tana fada masa karfe uku yaje scul dinsu HaYaT yadaukota dan yanzun nan zasu tafi dosso

Cikin sauri yace Ammiey lafiya? Me zakujeyi acan?

Cikin damuwa Ammiey tace mahaifin Daddynku aka kira baida lafiya shine zamuje gabadaya yanzu haka maganar nan danakema muna hanya tafiyar takamamu ba shiri shiyasa bazamu iya jiran HaYaT tazo ba

Allah yabashi lfy Ammiey amma ina Daddy?

Gashi nan Ammiey tafada!

Ina fatan dai bashi yake tuki ba ALI ya tambaya?

A'a Haidar ne karka damu!

OK Ammiey Allah yasaukeku lafiya idan kunje amasa sannu da jiki nima zanzo da zarar nasamu lokaci!

OK karka manta dauko HaYaT kartayi jira

Ba damuwa Ammiey yafada tareda mata sallama yakashe wayar.


Ana tashinsu taje inda drebansu yake jiransu kullun saidai taga baya nan, tadanyi mamaki dan akullun shiyake jiransu basu suke jiransa ba kafin su fito yana nan

Dan jim tayi tana dube dube sunanta taji ankira daga bayanta kamar muryar Hamdan tana juyawa taganshi yana nufo inda take yana sakar mata murmushi itama murmushin tamayar masa

Lafiya dai kike tsaye nan cikin rana ba'azo daukarki bane?

Dreban nake jira akwai abunda yatsaida shi da alama dan bai taba irin haka ba!

Amma ki koma ciki kafin yazo mana akwai rana sosai!

Dan murmushi tayi tace ba komai karna shiga kuma yazo bai ganni ba kaga ba dadi

Hakane yafada yana zuba murmushi wanda yazamemasa al'ada adik lokacinda yake tareda HaYaT

Jefi jefi suke hirarsu cikeda nishadi

ALI yana danno kai ya hangota sai dariya take suna hira da Hamdan wani irin kishi ne yaturnikeshi da takaici sanye yake daman da bakaken tabarau ahankali yatako motar zuwa gabansu tareda sauke glas din wanda yake kusa dasu

Mutuwar tsaye HaYaT tayi ganin wanda ke gabanta Ya ALI tafurta da dan sauti cikeda tsoro abunda zaizo yadawo ganinta dayayi tareda Hamdan

Da mamakinta sai ganin tayi yana gaisheda Hamdan

Hamdan ya ansa ba yabo ba fallasa

Kallon Hamdan tayi ta kalli ALI cikin nauyin baki tace wanan Yayana ne tafada tana nuna ALI

Sai alaokcin Hamdan yasaki fuska yasake gaisheda ALI

ALI ya ansa dakyar yana danne kishinsa

Bude gaban motar Hamdan yayi yana fadin bismillah MAI SANYI

Jitayi kamar tarusa kuka haka tashiga motar yarufe yaleko kansa ta window yace sai munyi waya ko MAI SANYI?

ahankali ta daga kanta alamar eh!

ALI dauke kansa yayi daga kallonsu

Saida Hamdan yagama yajanye kansa tukuna yaja motar da karfi yabar wajen

HaYaT jikinta harda rawa yake dan tsoro...













✍🏻
[8/1, 7:01 AM] Hayat: πŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’Ž
πŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’Ž

*AyNuL HaYaTπŸ‘„*
_MATAR ALI GADANGA_


πŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’Ž
πŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’Ž

*-_-_-_-_-_-_-_-_-_-*
*LaBaRi Da RuBuTaWa✍🏻*
*-_-_-_-_-_-_-_-_-_-_*

*NeEnA_CoOlπŸ‘©πŸ»β€πŸ¦±*
*-_-_-_-_-_-_-_-_-_*


*_______________________*
*πŸ‡³πŸ‡ͺNiGeR Ma FiErTΓ©πŸ€™πŸ»*


*Ψ§Ω„Ω„Ω‡Ω… Ψ₯Ω†ΩŠ Ψ£Ψ³Ψ£Ω„Ωƒ Ψ­Ψ¨Ωƒ وحب ΩƒΩ„ Ω…Ω† ΩŠΨ­Ψ¨ΩƒΨŒ وحب Ω†Ψ¨ΩŠΩƒ Ω…Ψ­Ω…Ψ― Ψ΅Ω„Ω‰ Ψ§Ω„Ω„Ω‡ ΨΉΩ„ΩŠΩ‡ ΩˆΨ³Ω„Ω….*
*وحب ΩƒΩ„ ΨΉΩ…Ω„ ΩŠΩ‚Ψ±Ψ¨Ω†ΩŠ Ψ₯Ω„Ω‰ Ψ­Ψ¨Ωƒ يارب Ψ§Ω„ΨΉΨ§Ω„Ω…ΩŠΩ†πŸ‘πŸ»*


🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
_DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN KAI✍🏻_
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷




Neenacool280@gmail.com





1⃣8⃣







Tsoronta ne yaragu ganin yadauki hanyar zuwa gidansu Ammiey aranta tace aeko ba komai bazai daketa gaban Ammiey ba!

Harda yar murnarta tafito daga motar bayan yasamu guri yatsaya da sauri tanufi ciki tun afalo take kiran sunan Salimat

Saidai taji ko ina shiru dakin Salimat tafara lekawa kafin takoma taleka dakin Ammiey bata ganta ba tana juyo aranta tana tambayar ina sukaje dik basa nan haka?

Shin kodai jikin Salimat ne yasa aka kaita asibiti?

Ganin batada ansar tambayoyinta ne yasa

Tadawo falo fuskarta daukeda da damuwa yayi daidai da shigowan ALI fuskarsa amurtuke

Ita harta manta meya faru dazu da saurinta tanufi inda yake tana fadin

Ya ALI inasu Ammiey sukaje ne? Ko jikin Salimat ne ?

Maimakon yabata ansa saiwata harara taga yawatso mata wanda sai alokacin ta tuna da dazu, jadabaya tayi tana kallon yanda gabadaya yanayin fuskarsa yacanza

Zama yayi akan kujera yadaura kafarsa daya kan daya yana girgizawa yana kallonta yace

Ina wayarki?

Nuna masa jakar makaranta tayi alamar tana ciki!

Dauko kiban ita yanzun nan
Yafada cikeda isa

Ba musu tadauko tana takawa ahankali ta isa inda yake tareda mika masa

Saida yadauki kusan sakani goma yana hararenta tukuna yamika hannu ya anshi wayar bangaren WatsaAp yafara shiga yafara dubawa

Kamar karya anshi wayar yanayin fuskarsa yakara munana harda yar zufa ta taru agoshinsa ganin irin kalamn soyayyarda HaYaT take tsakaninta da Hamdan

Kashe wayar yayi ya ajiyeta gefensa yadafe kansa

HaYaT datake tsaye tatsure guri daya ganin yadafe kansa ne yasa tamotsa bakinta ahankali tace

Ya ALI kayi hakuri



Shiru bai ansata ba tasake cewa Ya ALI dan Allah kayi hakuri takarashe maganar muryarta na rawa

Jin zatayi kuku ne yasa yadago fuskarsa ahankali yasauke idanunsa akanta yana nazarinta yanda hawaye suke zuba afuskarta wasu bisa wasu abun yake taba ransa bayaso yaganta cikin kuka ko damuwa ayanzu, saidai tamasa abunda bazai kyaleta hakan nan ba yazama dole saiya mata hukuncinda gobe ko giyar wake tasha bazata kara maimaita abunda tayi ba

Sakwaninda yagani awayarta ne na soyayya sukafi komai daga hankalinsa

Zo nan yace da ita yana kallonta

Ahankali take takawa zuwa inda yake kamar batason zuwan dan atsorace take da yanayinsa

Daf dashi tatsaya yanuna guri kusa dashi alamar tazauna

Zama tayi tana kallonsa shima din kallonta yake

Waye wanda natardaku tare dashi HaYaT?

Malaminmu ne tafada tana sauke idanunta kasa daga kallonsa

Murmushin gefen kumatu yayi yace shikuwa wanda kuke chat dashi fa?

Gabanta ne yayi mumunar faduwa tadago ido ta kalleshi bakinta na rawa take fadin

Shine wanda zan aura!

Wani irin wawan kallo ALI yamata tsananin kishi dajin haushin abunda tafada jikinsa har rawa yake

Ji yake kamar yakamata yajibgeta harsaiya wuce tukuna yabarta saidai ya hani kansa da yin haka, kokari yake yadanni kansa wani dogon lumfashi yaja tareda ajiyar zuciya yace

Kina son sa da gaske?

Da sauri da gyada kanta alamar eh!

Murmushi yayi yace shikenan, zan cika miki alkwarinki muddin kika yarda zaki biyani cikina nima daga ranar zan sauwake miki kije ki auri wanda kikeso kuyi zamanku cikin farin ciki kin amince?

Kamar tasake wani kukan tace taya zan biyaka babynka? Idan na haihu dakai ae Hamdan bazai taba aurena ba saboda baisan inada aure ba kaga kuwa idan na haihu kowa zai mun wani irin kallo ne takarashe maganar tana zubama ALI ido dan jin ansarda zai bata

Kamo hannunta yayi yana murmushin dole aransa yake fadin lallai yau nayarda Mata kwakwalwarsu karama ce..

Karki damu da wanan harki dauki ciki ki haihu bazai sani ba!

Kuma kinga koda ace yasani tunda yana sonki sosai ae wanan bazai hanasa kin aurenki ba.

Dan murmushi HaYaT tayi tana fadin

Aekuwa yana kaunata sosai nima haka! Kome yafaru dani na tabbatar Hamdan bazai gujeni ba!

Wani abu ne yadaki zuciyar ALI dakyar yake iya dannewa yabiyema shirmenta

Can tace inasu Ammiey ne?

Sunyi tafiya Kakanmu ne bayada lafiya sunje dubashi Ammiey tace naje nadaukoki saboda tafiyar takamasu ba zata shiyasa!

Rau rau tayi da ido tana fadin yanzu nikadai zan kwana agidan nan Kenan?

Murmushi yayi kafin yace a'a! Zanzo natayaki kwana idan kinaso?

Zaro ido tayi waje tana kallonsa tace Aunty Sajidah fa?

Sakin hannunta yayi tareda mikewa yace shikenan sai anjima saiki kwana ke kadai ba abunda zai sameki tunda bakyaso!

Da sauri tamike itama tace Ya ALI dan Allah karka barni ni kadai, katafi dani gun Aunty Sajidah harsu Ammiey sudawo mana?

Itama Sajidahr bata nan tare suka tafi dasu Ammiey yafada

Toh yanzu nikadai zan zauna Kenan?

Idan kinaso bagani ba? Saina tayaki kwana ae!

Dan jim tayi kafin tace shikenan!

Yauwa yace yana duba agogonsa yana fadin ki zauna zanje nadawo bayan magrib inada aiki a asibiti kinji?

Jin abunda yafada ne yasa da sauri takama hannunsa cikin shagwaba tace Allah ni saidai muje tare amma bazan iya zama nikadai agidn nan ba Ya ALI !

Yanayin yanda tayi maganar ne cikin shagwaba yatada mishi sha'arwarta dayake fama da ita kwana da kwanaki ga hannunsa data rike tun dazu tana magana tana murza hannunsa wanda ita bada gangan takeyi ba, kasa yimata musu yayi yace jeki cire kayan makaranta kizo muje!

Sakin hannunsa tayi da saurinta tanufi hanyar dakinta

Da kallo yabi mazaunanta da suke rawa idan tana tafiya kamar da gangan take kadasu ALI baisan lokacinda yalashi bakinsa ba tareda lumshe idanunsa yabude ahankali yana wani tunanin aransa yake fadin badan marrasa lafiyanda nabari suna bukatar kulawana ba da yanzu yanzun nan komai tafanjama fanjam!

Kusan minti biyar saigata tafito sanyeda doguwar rigar atamfa ta yafa wani dan karamin gyale bawani kwalliya tayi ba amma ALI saiyaga tamasa wani uban kyau sosai

Harta karaso daf dashi tana fadin Ya ALI muje

Kallonta yayi yaga dan guntun gyalenda tasaka kamar yace mata taje ta canza kome yatuna oho sai juyawa yayi yafara tafiya ba tareda yace mata komai ba

Tunda suka shiga motar yake satan kallonta yake yanaji kamar ya janyota ajikinsa... har suka isa asibitin yafaka motarsa suka fito ofis dinsa suka nufa


Kan kujerar zamansa yamata nuna data zauna ba musu tazauna tana karema ofis dinsa kallo kamar yau tafara shigowa ciki

Ki zauna karki sake kifita ko ina zanje akwai marar lafiyanda zan dubasu zan jima ban dawo ba, idan lokacin sallah yayi kishiga toilet kiyi alwarlla yanuna mata abun sallaya yace gashi nan basaikin fita nema ba kinji?

Gyada masa kai kawai tayi alamar eh

Ajiyar zuciya yasauke tareda juyawa zai fita yaji takira sunansa juyowa yayi ahankali yana kallonta yana jiran ji me zatace dashi ?

Ya ALI wayana fa? Kaban kozata rage mun zaman kadaicin nan mana

Kallonta yake nawasu yan sakani tukuna yazaro wayar daga aljuhunsa ya ajiye akan table din da ke gabanta yajuya yafita...

D'aukar wayar tayi tana murmushi tafara leka number din Hamdan nan ta tarar yaturo mata sakwani kusan uku ajere fuskarta daukeda murmushi tashiga karantasu daya bayan daya saida tagama tashiga maida mashi ansa...

Bata gushe ba suna hira da Hamdan har lokacin sallahr la'asar yayi dakanshi yace taje tayi sallah ajiye wayar tayi bayan sunyi sallama taje tadauro alwarlla tadawo tayi sallah

Tana gamawa tashiga jero adu'oi anan kan sallayar taji bacci yafara d'ibarta ahankali takwanta ba jimawa bacci mai nauyi yad'auketa....

Sajidah na zaune wajajen karfe shidda na yama taji sako yashigo wayarta tana dubawa taga number Baby dinta ne, murmushi ne ya bayana akan fuskarta

Saidai tana fara karanta message din annurin fuskarta yafara d'aukewa ahankali harta suke fuskar tamau tana gama karantawa taja wani dan karamin tsaki tareda ajiye wayar

Kiran sabuwar mai aikinta Larai tayi

Larai tana zuwa tace Aunty gani

Sakin fuskarta tayi kadan tana fadin, jeki d'aura mana girki yau mai gidan bazai kwana agida ba dan haka kiyi girki hardani!

Angama Larai tace tareda mikewa tabar falon...


Ana kiran sallahr magrib ALI bayan yayi sallah yashigo yaganta sai baccinta take kare mata kallo yayi yanda hartaji dadin bacci akasa hakan nan ba tareda wata damuwa ba

Ganin dole ta tashi tayi sallah kuma suje gida yasa yashiga tashinta

Ahankali tabude idanunta tareda tashi tazauna tana kallon ALI

Kitashi kiyi sallah muje gida anyi sallah tun tuni!

Mikewa kawai tayi tafada bayi jim kadan tafito tahau kan sallaya tafara gabatarda sallahrta

Zuba mata ido yayi yana nazarin yanda take ibadarta cikin nutsuwa da sanin abunda take nan yaji takara shiga ranshi ba kadan ba...

Tana gamawa bayan tayi adu'ointa tashafa saidai bata tashi daga zamanda take ba

Muryarsa ce tadaki dodon kunenta yana fadin

Tashi muje idan kin idar ko?

Mikewa tayi ba tareda tayi magana tafito kai tsaye ta fita bata jirasa ba gun mota taje tatsaya tana jiransa jim kadan saigashi yazo ya kalleta yace shine baki jirani munzo tare ba?

Miskilancin HaYaT ne yatashi dan ko wanan karon bata ansashi ba

Dan guntun murmushi kawai tayi tareda sauke kanta kasa tana wasada yan yatsunta

Hmm yace afili yabude motar suka shiga

Akan hanyarsu ne yatsaya wani restaurant yafito ba tareda yace da ita komai ba

Da kallo tabishi harya shiga ciki jim kadan yadawo hannunsa d'aukeda wasu ledodi har uku

Bayan motar yabude yasaka kafin yashiga yatada motar suka d'au hanya

Koda suka iso gida nan falo tabarshi tashige dakinta

Wanka taje tayi saboda jikinta gabadaya yake mata ciyo dan baccinda tayi akasa

Tana fitowa tasaka wata doguwar rigarta yar kanti marar nauyi gashin kanta kuwa haka kawai taji tanason barinsa hakan nan ba tareda ta d'aureshi da ribon ba haka yabazu kan kafadunta har gadon bayanta

Ae kuwa tayi kyau ba kadan ba tana fesa turarenta da kullun yazame mata jiki saita saka koda zatayi bacci ne

Jin cikinta na neman agaji dan tun break din safe haryanzu bata saka komai acikinta ba

Fita tayi falo da nufin tad'aura indomie taci

ALI daya yajima yana tsumayen fitowarta saiyaga tafito tana nufar hanyar kitchin

Ina zaki? yace da ita yana kallonta

Turo dan karamin bakinta tayi cikeda shagwaba tace abinci zan dora naci mana!

Kallonta yayi dakyau yakalli abincinda yasiyo harya zuba a plat yace wanan din fa? Wazaici Kenan?

Ita sai alokacin ta tuna daya siyo abinci dazu akan hanyarsu ta dawowa

Murmushi ne yabayana afuskarta da sassarfa ta iso inda yake tazauna

Gasashiyar kaza ce da hadadden couscous wanda yaji hadin kayan lambu sai kanshi yake tashi kallo daya zakama abincin nan yawunka su sinke

Gefe daya kuma madarar roba ce mai sanyi da jus sai cup guda biyu da ALI yad'auko

Kallonta ALI yayi ganin tafara ci yace shine bazaki jira mufara ci ba?

Tun dazu fa nake jiranki amma ke gashi daga zuwanki harkin saka hannu kin fara ci

Rau rau tayi da ido tana fadin

Kaine fa ka kaini asibitinku banci abincin rana ba yunwa nakeji sosai shiyasa kayi hakuri

Tausayinta yakamashi cikin muryarar rarashi yace toh ci ahankali karki kware

Dan murmushi tayi kafin tacigaba dacin abincinta ba tareda wata damuwa ba.

Shikuwa aiki biyu yake alokaci daya, yana cin abinci ahankali kuma idanunsa nakanta ko kiftawa sai can yake yinta badan yaso ba saidan tazamar masa dole ne kawai...

Suna gamawa dakanshi yakwashe kayan yakaisu kitchin yadawo

Zama akan babbar kujerar falon bayan yakunna TV ita kuwa HaYaT tana zaune akan kujerar zaman mutum d'aya

Yana kallon TV yana satar kallonta ganin yanda tayi bala'in kyau musaman gashin kanta yakara mata kyau sosai so yake yakirata tazauna kusa dashi

Saidai yafasa dan ankusa kiran sallahr isha so yake saiya dawo tukuna...

Haka kuwa akayi ana kiran sallah yace ta tashi taje tayi sallah shima yanzun nan zaije yadawo...!

Koda yadawo bata falon zama yayi yana jiran fitowarta amma yaji shiru

Kiran sunanta yafarayi

HaYaT daharta kwanta rikeda waya tana chat da Hamdan taji muryar ALI yana kwala mata kira

Wani dan guntun tsaki taja tana turo baki tafito ba tareda ta ansa ba saida yaganta kawai

Kallo daya yamata yaga yanayin fuskarta bataso kiranda yamata ba


Zaki gane kurenki yafada aransa, azahiri kuma yace harkin kwanta ne?

A'a tace dashi atakaice!

Toh zo muyi magana dake yafada yana nuna mata kusa dashi

Badan taso ba taje tazauna hankalinta gabadaya yanakan wayarta

Hannu ALI yasa ya kwace wayar tareda ajiyeta gefensa yana kallonta yace

Kin gayyatoni na tayaki kwana kuma shine zaki shige daki kibarni anan saikace wani marar galihu kodai nayi tafiyata ne daman

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login