Showing 33001 words to 36000 words out of 54100 words
take na takaici da bakin cikin rasa cikinta da tayi ta sanadiyarsu shida HaYaT
Magana ALI yake mata amma tayi banza dashi ba irin magiyarda bai mata ba ta saurareshi taki
Saida tagaji dan kanta cikin muryar kuka tace kun cutar dani kaida HaYaT bazan taba yafe muku rasa cikin jikina da kukayi sanadiyar rasashinda nayi ba ALI!
Ni na tabbatar akwai wani boyayyen sirri tsakaninku da ita amma inaso kasani koma menene bazan sake zama gida daya da ita ba wallahi saidai kazaba zamana agidan ko kuma zamanta agidan acikin mu biyun!
Tunda tafara magana yake kallonta cikin mamaki azuciyarsa yake fadin daman Sajidah ta iya masifa haka?
Saidai baiji haushinta ba saboda sune silar rasa d'an cikinta
Amma Sajidah meyasa baki taba sanar dani kina daukeda ciki ba? Banda abun nan daya faru saidai cikin yafito naganshi da idona kuru kuru kome kike nufi?
Dagani har cikinda kukayi sanadiyar fitarsa bama bukatar kulawarka ALI! Kaje kabawa HaYaT dakake mayen kallo dik safiya kamar ka hadiyeta, gani nayi kuma baka damu dani ba dik kwanan nan inhar ba bukatarka ganina ashimfidarka yatashi ba ae banida wani sauran daraja a idonka!
Ya isheki Sajidah yafada cikin tsawa
Ganin tafashe da kuka ne yasashi sassauta muryarsa yashiga bata hakuri
Saidai Sajidah kisani naji zafin rashin sanar dani cikin nan da bakiyi ba, karki sake irin wanan takara faruwa wallahi kowane irin hali muke ciki dake kuwa!
Shiru tayi takyaleshi yana magana saida yagaji yatashi yafita
Hango HaYaT da Salimat yayi guri daya, wata irin harara ya watsa musu kafin yayi gaba
Dikansu sunja jinin jikinsu da irin kallonda yamusu
Da dare daman ka'ida ne asibitin ba'a bukatar dan jinya hakan yasa yacema Ammiey data dawo bayan magrib sutafi da HaYaT gida sai Sajidah taji sauki tukuna
Aekuwa murna gun Salimat dama HaYaT din ba'a magana...
Yau kwana biyu kenan Sajidah na jinya ALI ne zaune kusa da ita yabare mata ayaba yana bata abaki tanaci ko kunyar idon Salimat da HaYaT bayayi dasuke zaune gefe
HaYaT sai satan kallonsu take tanajin wani abu aranta wanda ita kanta batasan meye ba
Ayaba rabi taci tace takoshi!
Cinye rabin ALI yayi kafin yakallisu HaYaT da sukayi shiga iri daya kamar tagwaye da salimat yace kutashi kufita kuban waje munafukai kawai
Sum sum suka mike suka fita sai gunguni Salimat take
Suna fita yajuyo kan Sajidah cikin taushin murya yafara magana
Baby na yanke shawara HaYaT zatacigaba da zama gidan Ammiey har zuwa lokacinda mijinta zai nemeta dan haka ki kwantarda hankalinki anjima zan mayar dake gida
Hawaye ne sukabiyo kuncen Sajidah da sauri ALI yasa hannu yagoge yana fadin dan Allah kidena kukan nan hakan nan mana!
Kin gaya mun sharadinki nabi meye kuma abun kuka anan?
Girgiza kanta tayi tace
Haryanzu inajin zafin abunda kuka mun ALI kaine silar komai kuma...
Da sauri yasaka bakinsa cikin nata yashiga kiss dinta suna cikin wanan halin ne Ammiey tashigo da sauri yasauka daga kan gadon cikin kunya yana gaida Ammiey
Ita kanta Sajidah kunya kamar tanutse kasa takeji
Bayan sun gaisa ne Ammiey cikin murmushi tace ALI yakamata ku tattara ku koma gida hakan nan ae inaga Sajidahr taji sauki ba?
Dan sosa kansa yayi cikin kunya yana fadin
Eh Ammiey daman yanzun nan nake fada mata zata koma gida tunda taji sauki
Gwara haka Ammiey tafada!
Am ALI daman inason magana daku biyun nan
Gaban ALI ne yayi mugun faduwa dan baisan dame Ammeiy tazo ba
Ita kanta Sajidah tadan tsorata
Ganin sunyi shiru ne Ammiey tace
HaYaT nakeso kubani tadawo gurina dazama har zuwa lokacinda mijin nata zai dawo takoma dakinta!
Cikin sauri ALI yayi karaf yace Ammiey aeba damuwa! Ko yanzun nan saiku koma tare da ita inyaso saina kamata kayanta har gida ko?
Yafada yana kallon Sajidah tareda kifta mata ido dan tace wani abu
Cikin murmushin yake Sajidah tace ae Ammiey ba komai dakai da kaya dik mallakar wuyane kunada iko damu balle HaYaT
Allah yamuku albarka Ammiey tafada....
Alhmdllh ALI yafada aransa faduwa tazo masa daidai da zama!
Kamar kullun suka koma gida da Ammiey da Salimat saidai da mamakinta koda ta tashi daga bacci da safe taga kayanta gabadaya adakin Salimat, saidai Salimat bata ciki balle ta tambaya waya kasu kuma meyasa?
Tashi tayi tayo wanka tadauko daya daga cikin kayanta atamfa tasaka tafito
Salimat nakan dinnin itama can tanufa sukayi break saida suka gama ne suka dawo falo Salimat tace Sis HaYaT kinga kayan sakawarki ko?
Dazun nan nima ina tashi nagansu na tambaya Ammiey take fada mun cewa Ya ALI ne yakasu ita taroka abarki kizauna anan gabadaya
Salimat takarashe maganar tana murmushi idonta akan HaYaT dan ganin irin murnarda zatayi
Saidai da mamakinta saitaga HaYaT murmushinda baikai ciki ba tayi
Cikin damuwa Salimat tace bakiyi farin ciki bane?
Dariya HaYaT tayi danta fidda shakku azuciyar Salimat tace ke banza ce Sis
Farin cikine nama rasa me zance kona komai ae yanzu bamai rabamu kullun zai kasance muna tare abunmu...
Sunzo cin abinci akace sabo turken wawa
Kallo ALI yakai kan kujerarda ta kasance inda HaYaT take zama kullun in zasuci abinci yaji wani iri aransa saidai yayi saurin dauke idanunsa akai dankar Sajidah taganosa
Aekuwa yamakaro batareda ta kalleshi ba tace
Baby nacika son zuciya ko?
Nice silar raba HaYaT da gidan nan bayan na tarda ita aciki, nice silar rashin cika alkwarinka daka daukarma abokinka
Meyasa nazama muguwa maison kaina ne ayan kwanakin nan? Tafada hawaye suka fara bin fuskarta
Tashi ALI yayi yazo inda take yarungumota daga zaunenda take yadaura kansa akan wuyanta saida yashaki kanshin jikinta tareda lumshe idanu yabudesu lokaci daya yace
Keba muguwa bace Baby sam wanan kalmar bata kamaceki ba!
Idan ana neman mace tagari yar aljana toh kece, kiduba abunda namiki nine natureki da gangan har kikayi bari amma baki sanarwa iyayenmu gaskiyar lamarinba sai kika rufama mijinki asiri ta hanyar fadin sulbewa kikayi kika fadi
Sajida yanda kika rufa mun asiri anan duniya ina rokon Allah daya rufa miki asiri duniya da lahira ina alfahari dake...
Faridah zaune kan tabarma abunda tashuka shi take girba ahalin yanzu dan lokacinda tafadi kasa sumamiya din nan alokacin tsohon ciyonta yasake ballewa sunyi magani harsun gaji abu yakici yaki cinyewa
Karshe akace saitaje ancire kafar danta lalace ita kuwa tace sam batasanda wanan ba!
Tana nan zaune sai famada ciyo take tana korar kuda koda yaushe, mahaifinta kuwa kudinda ALI yabasu rabin dik sun tafi anemar mata lafya
Dayaga nema take tacinye kudin gabadaya yasa yaje yasari kaya da sauran kudin yafara kasuwancinsa...
Amal ce nahango tsakanin kafafun wani saurayinta dan scul dinsu zaune cikin falon gidansu, dayake sun saba da holewarsu a scul yasa cikin hutun nanma suka kasa hakura dajunansu tagayyaci saurayin har gidansu sudebema juna kewa dan Abbunsu yayi tafiya
Ita kuma Anna tafita unguwa taredasu Jamila da Jamal dan haka Amal ce kawai agidan sai saurayinta data gayyata suna sheke ayarsu son ransu...
Kwana biyu Hamdan yashiga matsanan ciyar damuwa jin HaYaT shiru kwana biyu gabadaya ya hana kansa sukuni wasa wasa har zazzabi yakamasa ya kwanta jinya saidai karfin hali yake yana tashi saboda baison saka mahaifiyarsa tilo cikin damuwa dan idan yakwanta rashin lafiya itace maishan wahala fiyedashi kanshi
Hamdan shikadai mahaifiyarsa tahaifa kafin rasuwar mahaifinsa , tallakawa ne tun yana yaro yake daukar nauyin kansa dana karatunsa harda iyayensa kafin Allah yakarbi ran Mahaifinsa, hakan yasa mahifiyarsa tadauki son duniyar nan tadaura akanshi bataso taga komai yataba mata tilon d'anta kwaya d'aya aduniya, shiyasa dikda zazzabinda yakeji yana iyakar kokarinsa dan kar Mahaifiyarsa dayake kirada Maa ta damu
Kuskurensa daya ya manta sam yatambaya HaYaT adresse din gidansu gashi yanzu yana tsananin bukatar sanin halinda take ciki yasa yajita shiru amma baisan inda zai nufa baisan ta inda zai fara nemanta ba.
Yau batasan dalili ba wuni tayi tunanin Hamdan dinta haka tawuni shiru shiru da Ammiey talura da hakan take tambayarta lafyanta kuwa? cema Ammiey tayi kanta ne yake ciyo shiyasa!
Magani Ammiey tabata tace taje ta kwanta tahuta kafin ta tashi zai dena insha Allah!
Dakinda yazama mallakinta ayanzu shita nufa taje takwanta akan makeken gadonta tareda janyo lallausan bargonta tarufa dan lokacin sanyi ne garin da sanyi sosai gashi kuma wajen karfe tara na safe ne akwai sanyi
Dayake tun asuba data farka bata koma bacci ba yasa tana kwantawa bacci yayi awon gaba da ita...
Cikin baccinta ne take mafarkin Hamdan yana cikin mawuyacin hali sai kiran sunanta yake yana kuka yana fadi ta taimakesa tazo kareshi
Ita kuwa tsaye take tana kallonsa itama kukan take tana fadin ba abunda zan iya maka Hamdan dole zamu hakura dajunanmu saboda wani babban dalili dan haka...
Katseta yayi yana fadin shikenan ni banida wani sauran amfani aduniyar nan! Daman nasani bazaki taba son talaka Irina ba, amma kisani kudi mulki da arziki dikna Allah ne!
Dan haka sai watarana gwara kawai namutu nahuta
Kafin HaYaT tayi magana sai wuka taga yaciro daga aljuhunsa yacakama kansa ita take kuwa yafadi kasa amace wata irin kara tasaka tana kiran Hamdannnnn
Ammiey da Salimat ne suke rige rigan shiga dakin Ammiey tayi saurin dago HaYaT dataketa faman ihu gashi kuma idanunta arufe jijigata tashigayi tana kiran sunanta
Ganin taki dena ihun ne yasa Salimat yanka mata mari tana fadin ke HaYaTπ
Ba shiri HaYaT tayi shiru dan marin Salimat yashigeta sosaiπ tadawo hayyacinta
Kallon Salimat tayi ta kalli Ammiey tafada jikin Ammiey tasaka kuka
Shafa bayanta Ammiey tashigayi saida tanutsu tadena kukan tukuna Ammiey tace mafarki kikayi?
Gyada kanta tayi hawaye nabin fuskarta alamar eh!
Na tabbata bakiyi adu'a kafin ki kwanta ba HaYaT, sunkuyarda kanta kasa tayi, Ammiey tashiga yimata fada akan karta sake kwantawa batareda tayi adu'a ba kafin ta tashi tafita tabarsu da Salimat
Sis mafarkin me kikayi haka?
Maimakon tabawa Salimat ansa sai cewa take dan Allah Salimat kiban aron wayarki mana?
Me zakiyi dawaya kuma keda yanzun kika gama ihu abacci?
Dabara ce tafadoma HaYaT da sauri tace Yayana nayi mafarki cikin mumunan yanayi shiyasa natsorata da yanayin
Dan Allah kiban aron wayarki nakirasa naji lafiyanrsa ko hankalina zai kwanta
Ba musu Salimat tafita jim kadan tadawo rikeda wayar tabawa tabata
Hannunta har rawa yake ta ansa tasaka number Hamdan
Yana kwance kusada Maa dinsa yaji wayarsa tafara kara yana dubawa yaga bakuwar number kin dagawa yayi yamaida wayar ya ajiye
Maa ce tace bazaka daga ba?
Maa bansan number ba karshenta ma wani ne kawai yayi baton number yakirani!
Toh basaika daga kaji ba inma hakane saikace baton number ne shikenan
Saida tatsinke ba'a daga ba hakan yasake jefa HaYaT cikin fargaba sake kira tayi kamar tafashe da kuka idanunta akan Salimat da itama ta kagu taji an daga dan taji lafyar yayansu
Maa ce tasaka dole wanan karon yadaga da sallama
Muryarsa mai sanyi ce tadaki dodon kunenta lumshe idanunta tayi zuciyarta taji tayi wasai dajin muryarsa tun kafin takaiga ta tambaya koya yake yana lafiya ko akasin haka
Ganin tayi shiru taki magana ne yasa yashiga fadin waye akan wayar?
Yayi magana harya gaji yakashe wayar batace komai ba
Salimat ce tace meyasa kika ki magana?
Mikama Salimat wayar tayi tana zuba murmushi tana fadin ungo wayarki jin muryarsama ya wadatar dani!
Takoma takwanta tana zuba murmushi
Umm nagane, watau ni zaki maida hamago ba? Toh nagane mijinki ne shine zaki fake da cewa yayanki? Tona harbo jirginki ae wallahi saina fadama Ammiey wanan labarin azo akaiki inda yake kawai karki haukace mana tunda gashi kin fara ihu cikin bacci nan GABA bamusan me zakiyi ba kuma
HaYaT jin hakan batasan lokacinda ta diro daga kan gadon ba tana fadin dan Allah Salimat kirufa mun asiri nifa ba haka nake nufi ba
Aekuwa Salimat takwasa aguje tayi waje itama HaYaT binta tayi dayake Ammiey tana lambu Salimat tana fita ta hango ALI yana shirin shigowa cikin falon
Da gudunta takarasa fita waje saura kiris ta bangajeshi
Cikin takaici yajuya yana kallonta yana fadi afili yarinyar nan mahaukaciya ce haryanzu bata ganin tagirma toh wallahi kigama iskancinki aure zan saka Daddy yamiki ko kin girma banza kawai
Kafin yagama rufe bakinsa daidai yashigo falon yayi taki uku saiji yayi garam HaYaT tazo da gudu ta bangajeshi
Saida yayi da gaske yasamu yatsaya da kafafunsa yariketa baimasan wacece ba dan atunaninsa Salimat ce, dan yanzu kullun kaya iri daya suke sakawa
Ba tsammani HaYaT taji yatsu biyar akan kumatunta
ALI yazabga mata mari yana fadin kedan iskanci dazu na kauce miki shine zaki dawo ki bangajeni haka?
Nadan...
Shiru yayi bai karasa maganar ba jin sautin kuka irin murayar HaYaT
Sai alokacin yagane da ita ce ba Salimat ba....
+22792838015
βπ»
[8/1, 7:01 AM] Hayat: πππππππππ
πππππππππ
*AyNuL HaYaTπ*
_MATAR ALI GADANGA_
πππππππππ
πππππππππ
*-_-_-_-_-_-_-_-_-_-*
*LaBaRi Da RuBuTaWaβπ»*
*-_-_-_-_-_-_-_-_-_-_*
*NeEnA_CoOlπ©π»βπ¦±*
*-_-_-_-_-_-_-_-_-_*
*_______________________*
*π³πͺNiGeR Ma FiErTΓ©π€π»*
*Ψ§ΩΩΩΩ
Ψ₯ΩΩ Ψ£Ψ³Ψ£ΩΩ ΨΨ¨Ω ΩΨΨ¨ ΩΩ Ω
Ω ΩΨΨ¨ΩΨ ΩΨΨ¨ ΩΨ¨ΩΩ Ω
ΨΩ
Ψ― Ψ΅ΩΩ Ψ§ΩΩΩ ΨΉΩΩΩ ΩΨ³ΩΩ
.*
*ΩΨΨ¨ ΩΩ ΨΉΩ
Ω ΩΩΨ±Ψ¨ΩΩ Ψ₯ΩΩ ΨΨ¨Ω ΩΨ§Ψ±Ψ¨ Ψ§ΩΨΉΨ§ΩΩ
ΩΩππ»*
π·π·π·π·π·π·π·π·
_DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN KAIβπ»_
π·π·π·π·π·π·π·π·
Neenacool280@gmail.com
WatsaAp +22792838015
1β£6β£
_Sam banyi niyar yin post yauba saboda nagaji sosai banyi edityng ba kuma yafi komai bani hawala, amma yanda dik groupe dinda naleka neman *AyNuL HaYaT* ake yasa nadaure nayi yanzu._
*TEEMA GALEXY SANNUNKI MAI MAFARKIπ* Allah kin ban dariya
_JIYA NASAKA *JIDDAH*, AMMA BA WANAN SUNAN NASO RUBUTAWA BA *FIDDAH* NAKESO NASAKA_
_SIS *FIDDAH*π·_
Bale baki tayi tana kuka kamar wata karamar yarinya kasake yayi yana kallonta danshi mamaki tabashi
Ganin taki yin shiru ne yasa yadaka mata tsawa
Keee wanan wane irin iskanci ne haka kinama mutane kuka saikace dukan gaskiya namiki?
Dafe kumatunta tayi tareda rage sautin kukan tana kallonsa batayi magana ba
Yar tazarda tabashi yatako yakarasa inda take yamatse mata baki sosai tanaso tayi ihu takasa, saida yaga tasha wuya tukuna yasaketa yana murmushin mugunta yace
Ina babyna da kikayi sanadiyar bararwa?
Turo lebenta take tana dubawa takara shagwabe fuska hawaye nabin kuncenta jin abunda yafada ne yasa tadago da sauri ta kalleshi kafin tace
Ya ALI ni bazan iya biyanka babynka ba, dan Allah kayi hakuri tun ranar nabaka hakuri ba?
Takarashe maganar cikin shagwaba wacce tazame mata jiki idan tanayi batasan tayi ba
Kallon yanda take magana yake cikeda sha'awa da birgewa baiki ace su wuni ahaka tayita masa shagwaba yana kallonta agefensa ba...
Au kina tunanin hakurinda kike bani zai iya dawo mun da Babyna?
Da sauri ta girgiza kanta alamar a'a!
Toh kuma kike cewa nayi hakurin kin renani ko?
Ya ALI idan bance kayi hakuri ba mezan ce? Kaddara ce tariga tafaru dan Allah kayafe mun wlh bazan sake ba!
Tarufe baki wasu sabbin hawaye nabin kumatunta
Wuyanta ya danko ta baya yahada goshinsa da nata yana kallonta cikin ido itama kallonsa take cikin tsoro
Kin manta me nace miki ranar wai?
Cikin rawar murya tace na manta wallahi Ya ALI na manta kayi hakuri
Ok barina tunatarda ke idan kin manta!
A asibiti acikin ofis ranarda abun yafaru nace miki bazan yarda nayafe miki ba har abada , dan haka biyana kawai zakiyi!
Ya za'ayi nabiyaka bayan nagaya maka banida kudi?
Dan yatsansa yanuna acikinta yace d'aukar ciki zakiyi wata tara ki haifa mun baby mace ko namiji dik wanda kika samu inaso, inyaso daga nan saina sauwake miki kije kiyi aurenki da wanda kikeso kinga shikenan kin huta dani!
Fisge wuyanta tayi daga rikonda yamata tayi baya tana kallonsa tace
Dikda kananun shekaruna ALI niba sakarya bace nasan me nake karka d'aukeni wacce batasan kanta ba mana!
Daman inaso nasanar dakai cewa nasamu wanda nakeso zan aura yau ko gobe ashirye yake daya aureni nima haka, dan haka kaban takarda ta ko kuma ka furta kasakeni yanzun nan kaima kahuta da matsalolina!
Wata irin harara ya watsa mata tuni idanunsa suka kada sukayi jajur cikin shakewar murya yace dawane dan iskan kika fara soyayya?
Bakida hankali ne kuma da igiyoyin aure akanki kike kula wani namiji HaYaT?
Dikda tsoronda yanayinsa yabata bai hana cemasa kaifa kabani damar yin hakan koka manta?
Hannunsa yadunkule yadaki bango sosai yadaku tuni hannunsa jini yafara zuba bai damu ba yace
Naji ni nabaki wanan damar! Amma na janye dik randa kika sake naganki ko naji labarin kina kula wani dan iska wallahi saina wulakantaki saina baki mamaki
Cikin muryar kuka tace saboda me toh? Nidai nasan basona kake ba kasha fadan hakan, amma meyasa kakeson ganina cikin kunci da bacin rai ne?
ALI meyasa kakeson takura rayuwata?
Shin nice natura Aunty Sajidah hartayi barin ciki?
Narasa gane takamamen nufinka akaina!
Toh wallahi nagaji aeniba baiwa bace nima inada yancin nayi rayuwata yanda nakeso, dan haka soyayya sainayi kuma banga ubanda ya isa y'a hanani ba wl...
Wani wawan mari yasakar mata yana huci kamar zaki yana kallonta
Soyake yayi magana amma yakasa, gani yayi muddin yacigabada tsayi gurin zai iya illatata yasa yajuya yafita yabarta rikeda kumatu hawaye nabin fuskarta...
Dakinta takoma ta kwanta tana kuka maicin rai kuka take tana kiran sunan Abbu
Abbu kacuceni kacutarda rayuwata bazan taba manta zaluncika agareni ba...
Tsawon sati daya basu sake haduwa dashi ba, Haidar yaga zaman banzansu yay yawa HaYaT da Salimat yamaidasu makarantar islamiya kafin hutunsu yakare
Daman Salimat tana zuwa saidai bata maida hankali akai ne, yanzu kam ganin HaYaT tadage tanakai hardarta kullun yasa itama tadage tana d'aukar hardarta yanda yakamata Ammiey taji dadin canjin halin Salimat nakin zuwa makarantar islamiya
Tare suke zuwa da Shuraime Auta dayake islamiyar hardata maza aciki saidai kowane da bangarensu.
Daddy daman ba mazauni bane bai cika zama akasar ba yau yana nan gobe yana can harkar kasuwancinsa.
Ammiey rashin ganin HaYaT na waya da mijinta ko Yayanta ne abun yake dan damunta tana zaune dakinta bayan tagama waya da Daddy Shuraim na gefenta tace masa jeka kira mun Auntynka HaYaT
Da gudu yafita ba jimawa yadawo yace Ammiey Nagaya mata, murmushi tayi tashafa kansa tace toh sannu da kokari
Tana rufe bakinta saiga HaYaT tashigo da sallamarta Ammiey ta ansa
Neman guri tayi kusada kafafun Ammiey tazauna tareda gaisheda ita Ammiey ta ansa cikin sakin fuska tana fadin ae lokacin zuwa islamiya yayi ba?
Lah Ammiey yaufa laraba kun manta?
Yar dariya Ammiey tace kinsan abunka da tsufa caf na manta wlh
Murmushi HaYaT tayi tace Ammiey haryanzu fa da yarintarku kamar baku kuka haifisu Khadija ba!
Kinganki HaYaT ganin idona ba
Allah Ammiey da gaske ba wasa ba koba hakaba Auta?
Ta tafada tana kallon Shuraime
Hakane Aunty yafada yana dariya kasa kasa
Ammiey ta kalleshi tace tafi gun Salimat kuyi wasa zanyi magana da HaYaT
Toh Ammiey yace yasauko daga kan gado yafita da gudu..
Kallonta Ammiey tayi tace nikam HaYaT tambayarki zanyi?
Ras ras ras HaYaT taji gabanta nabugawa tayi wuru wuru da ido tana kallon Ammiey takasa magana
Ammiey tacigabada fadin
Yau kusan kwananki goma agidan nan amma haryanzu banji