Showing 15001 words to 18000 words out of 54100 words
wlh wlh in kece sainayi ajalinki agidan nan yau!
Abunda nadauki tsawon shekara uku ina kaffa kaffa dashi shine haka kawai zaki dauke batareda yashiga hanyarki ba?
Kifito kiban kayana inba haka ba in naballa kofar nan saidai gawarki bake ba!
HaYaT tsoro ne yasake kamata cikin toilet tashige tatsaya abakin kofa idonta zuru zuru jira kawai take Faridah ta balla kofar kamar yanda tace takulle kanta cikin toilet
Faridah magana take cikin fada da takaici harda kukanta dan haushi gashi tayi tayi ta balla kofar takasa, can taji girkinda HaYaT din tadaura yafara kauri tafiya tayi takashe Gaz din tadawo
Wanan karon magiya tashiga yima HaYaT harda rarashinta tafito bazata mata komai ba itadai kawai tabata kayanta bana wasa bane
Daga can cikin toilet din HaYaT tadaga murya tana fadin nifa Aunty nakona komai bΓ’ abunda yake hannuna yanzu, kumani ban zacci kayanki bane ae
Wata irin ashariya Faridah tasaka Kan uban can...
Baki zaci nawa bane na Ubanki ne?
Dakin Ubanki ne kona Uwarki dazaki ce baki zaci nawa bane dan Ubanki?
Dan Ubanki akan hanya kayan suke balle kice sun tare miki hanya?
Kamar Faridah tana ganinta tamurguda baki tana gunguni take fadin wlh badai Uwata ba!
Ganin bazata buden bane yasata komawa falo tazauna takira Auntynta tagaya mata komai haka takira Rukky da baby nice suma tamusu bayani hankalinta tashe
Rukky ce tace bari muzo gidan muhada karfi da karfe mu balle kofar muci Ubanta mu karya banza ajefar adaji sanan arufe bakin shi ALI din ahuta!
Baby nice da takeson HaYaT tayi karaf takarbe wayar tace Faridah kina jina kuwa?
Gyada kai Faridah tayi alamar eh kamar tana ganinta
Baby Nice tace
Kibi komai ahankali kinga wanan shirinda ta wargaza shine yake zaune dake da ALI yanzu idan kika mata wani abun zai nemi dalilinda yasa kika tabata kinga idan baki gaya masa gaskiya ba ita ae bakinta ba ciyo yake ba zata iya kwashe komai tasanar dashi!
Dan haka mubi komai daki daki, yanzu kitashi dik abunda ta hargitsa ki gyara komai karki yarda kibar wata alama dazai gane wani abu yafaru, sanan kuma girkinda yakone kijuye kidaura wani
Saboda shi dinma idan yazo yatarar ba ayiba zai nemi ba'asin rashin yinsa anan dinma zata iya gaya masa abunda tagani kota nuna masa idan karya take bata kona din ba, sanan kuma kidaure karki nuna wata alamar bacin rai daga wajenki kinji?
Shawara ce idan tamiki kidauka idan kuma batyi ba zaki iya yin yanda kikeso!
Ajiyar zuciya tayi tace ya zanyi Baby? Dole nadauka inba haka ba asirina zai tonu zan iya rasa ALI dan haka zanyi dik yanda kikace shine mafita!
Takara dacewa tsakanina da yarinyar nan Allah ya isa shiyasa tun farkon zuwanta gidan nan hankalina bai kwanta da ita ba, ashe munafuka ce mai shirin tona mun asiri bansani ba
Kedai kiyi hakuri mubi komai asannu
Toh kawai tace takatse wayar
Bayan takashe wayar rigima ce takaure tsakanin Rukky da baby Nice
Ita Rukky fada take akan meyasa batabar Faridah ta aikata abunda tace da ita kodan yasaketa sudawo daidai da ita!
Baby Nice tace me kikema sauri? Ae lokacin na nan zuwa bada dadewa ba kedai kawai mujira dan nafiki jin haushin daularda Faridah take ciki bayan mun fita kyau da komai..
Bangaren Faridah
Haka kawai taji tanason yin kuka
Aekuwa tasha abunta son ranta bamai rarashinta saida tagaji tayi shiru dan kanta...
Haka tahakura tashiga kitchin tadafa dafa dikan macaroni kallo daya zaka mata kasan bazatayi dadin ci abaki ba.
Yau yakwaso yunwa Allah Allah yake yayi wanka yazo yaci abinci dan cikinsa kamar yaci babu yakeji, yana zuwa yabude kwanan abincin kanshin girkin ne yaji ba irin yanda yasaba jinsa ba ahaka dai yazuba yanakai lomar farko bakinsa yafurzar tsabar gishirinda yama abincin yawa
Mikewa yayi yashiga kiran sunan Faridah da tunda yazo bai ganta ba daga ita har HaYaT din
Jin kiransa ne yasa tafito tasauko tana tambayar lafiya?
Abinci yanuna yace haka kikaci?
Girgiza kai tayi tace ehhh kuma tace a'a
Wane zan dauka eh ko aa'a din?
Tsoronta karya kira HaYaT ne yasa tace
yau ni nayi abincin saida nagama ne naji gishiri yayi yawa kwacewar dabara kenan Faridah
Jefo mata tambaya yayi meya samu HaYaT din da batayi girkin ba?
Zaro ido tadanyi waje cikin inda inda tace wai batada lfy ne shiyasa nikuma nagirka
Bai jira ansarta ba yatashi yanufi kofar HaYaT binsa tayi abaya jikinta har rawa yake tana fargabar kar HaYaT ta tona mata asiri tashiga uku
Yana buga kofar yana kiran Sunanta
HaYaT datake atakure jin muryarsa ne yasata saurin mikewa tazo gaban kofa tabude tana kallonsa batareda tace masa komai ba ganinta yayi kamar atsora ce take yace
Bakida lfiya?
Ni tafada tareda dan zaro ido tanuna kanta
Hade rai yayi yace a'a ni!
Sai alokacin tayi ido hudu da Faridah girgiza mata kai take tagane me take nufi dan haka
Can tadafe kanta tana yatsina fuska kamar tayi kuka tace haka hkanee hakaneee kaina yake mun ciyo tun dazu
Da gaske ya tambaya? Yana zuba mata mayatattun idanunsa
Dan rikicewa tayi tace eh!
Ok yafada tareda juyawa
Ganin yabarta daga ita sai Faridah ne yasa taji kamar ta runtuma aguje tabi bayansa
Ae Faridah na ganin yanufi dakinsa tasha gabanta tana fadin
Karki kuskura kisanar dashi abunda kika gani inba haka ba sainakai sunanki gun boka ya haukatar mun dake kinbi daji wlh kinajina ko?
Hannunta biyu tadaura abakinta ta toshe tareda zaro idanu tana kallon Faridah kafin tace
Wlh bawanda zan gayama dan Allah Aunty Faridah karki mun komai kmar tayi kuka takarashe maganar alamar tsoro karara a idanunta
Kwafa Faridah tayi tace naji amma ki kiyayeni banda kyau wlh zan iya batar dake nasa akasheki akashe banza!
Nasani wlh HaYaT tafada zata fara kuka Faridah tace
Shitttttπ€«π€«
Kafin tace wani abu ALI yadawo daukeda maganin ciyon kai ahanunsa, kitchin yanufa yadebo ruwa yadawo
Zo nan yace da ita sum sum tabi baynsa Faridah tamara musu baya afalo yatsaya yace tazauna
Tazauna shima yazauna hannun kujerarda take zaune akai yamika mata paket din magani yace balla biyu kisha
Ansa tayi hannunta narawa ta balla ta ajiye paket akan kafafunta yamika mata ruwa tasha hankalinta gabadaya yana kan Faridah so take tayi kuka amma tana dannewa saboda tsoron Faridah
Tana hadeye wanda yabatan tasake balla wasu biyu takai bakinta tasake shan ruwa suka tafi hankalin ALI baya kanta yana duba wani abu awayarsa
Ta balla maganin na shidda zatakai bakinta ne yajuyo duba paket din yayi yaga tacire shidda daga cikin maganin da sauri yakwabe hannunta yana kallonta yace bakida hankali ne?
Maganin gabadaya kikeso kishanye kome?
Hawayenda take makallewa dole ne suka biyu kuncenta muryarta tafara rawa tace banida lafiya fa Ya ALI tana magana tana taba wuyanta ala dole yayi zafi
Yanayin yanda tayi maganar ne yaso yabashi dariya cikin ransa yke fadin yarinyar nan tacika shagwaba da yarinta azahiri kuma yace da ita
Dan bakida lafiya sai akace ki shanye maganin gabadaya? Dana barki zaki shanyesu kenan?
A'a tace dashi tana share hawayenta hade rai yayi yace kinmaci abinci kuwa?
A'a tafada !
Kallon Faridah data tsure su da ido tana kallon ikon Allah yanda ALI yakema yarinyar nan wani irin kallo akwayar idonsa tanaso tagane wani abu dayake boye aciki, kishinsa ne yataso mata da haushin HaYaT daya taru yatokare mata zuciya
Ka kalleni?
Wata jinjira ce dazan tasota gaba nace tazo taci abinci kome?
Girgirza kai kawai yayi yamaida kallonsa ga HaYaT datake kokarin yin amai sakamakon maganinda tasha yawuce kima
Kafin yayi wani yunkuri harta kwarara masa aman ajikinsa gabadaya
Ga mamakin Faridah jira kawai take yadau mataki akanta ta hanyar marinta ko fada amma saitaga sabanin haka!
Tallafota ALI yayi tarangada jikinsa yashiga shafa bayanta yana mata sannu har izuwa lokacin kokarin yin wani aman take amma ba komai acikinta yasa takasayi idanunta sunyi zuru zuru
Yoo daman fa mutum lafiyarsa kalau ace yasha magani ba gaira ba dalili ba dole tayi amansa ba!
Mutuwar zaune Faridah tayi ganin ALI yanda yakema HaYaT shida ada ko kallon mace bayayi agabanta amma yanzu ace harda janyo mace ajikinsa yana shafa bayanta?
Cabdijam! Lallai da aiki mai yawa agabana tafada aranta inyyheee....????!!!!
Shafa bayanta yake harta dena yukurin amanda take tukuna yataimaka mata tamike tsaye dakanshi yakaita dakinta yahada mata ruwan wanka yakaita toilet yafito
Dakinsa yanufa yana kokarin cire kayansa ne Faridah tashigo cikeda masifa tana fadin
ALI agabana kake kama mace harda hadata da jikinka ko shakkata bakayi?
Kuma yarinyarda kace matar aure ce kasandai ko taba hannunta ya haramta agareka ko?
Kallonta yayi asheke kafin yace
Indai baki manta nace miki matar aure ce ba ina tunanin bazaki taba mantawa nace miki kanwar abokina ce, dan haka kinga kuwa nima kanwata ce tabatanda nayi bazai zama laifi ba!
Yana gama fadin haka yayi shigewarsa cikin toilet yabarta nan tsaye
Zubewa tayi kan gado tana rike kanta daya fara Sara mata kamar yarabe gida biyu hawaye ne masu zafi suka shiga bin fuskarta tasa hannu tashafe tamike tanufi dakinta tadauki wayarta takira Aunty Balki
Ba abunda taboye mata daga abunda yafaru yau agidansu daga zuwan ALI, nan Aunty Balki tashiga bata hakuri damata alkwarin zuwa inda bokanta gobe tunda safe...
Dakyer tasamu tayi wanka tafito jiri nadibarta gefen katifarta tasamu takwanta tadafe cikinta wanda takeji kamar anmata satar yayan ciki ba komai acikinsa idanunta arufe take tunano abunda yafaru da ita da ALI yanzun nan...
Yana fitowa yashirya yafita kusan minti talatin yadawo da abinci gasassun kaji ne da madara lafiyaya yasiyo musu
Dakin HaYaT yaje yakai mata nata ganin halinda take ciki ne yasashi zama yasa taci dole
Ita kunyarsa takeji gashi yatsareta da idanunsa kamar maye ko motsin kirki tayi akan idonsa, tadanci kusan rabin abincin tace takoshi!
Shikam yashagala sosai gun kallonta ayanzu ji yake komai tayi birgesa take yanajin wani abu game da ita ayanzu baiki ace yajita ajikinsa ba kamar dazu inda halima yaga surar jikinta kamar ranar yakare mata kallo shikadai ya ishesa!
Haka kawai yaji yana sha'arwata baimasan tayi magana ba saida ta maimaita nakoshi tukuna yadawo hayyacinsa
Mikewa yayi tsaye yanufi hanyar fita batareda yace da ita komai saida yakai daf da kofa yaji muryarta cikin bazata tana jefo masa tambayarda shikansa yayi mamakin jinta abakinta
Ita kanta batasan lokacinda tajefa mashi wanan tambayar ba da gaske aure zakayi?
Tambayar tajima tana masa amo akunne kafin yajuyo da kallonsa zuwa gareta
Dauke idanunta tayi kamar ba ita tayi maganar ba, dan guntun murmushi yayi yace eh aure zanyi nanda sati daya!
Kinada matsala dayin hakan ne? Ya tambaya yanamai tsure da idanunsa yanaso yagano wani abu akanta
Idanunta ne suka ciciko da hawaye da sauri ta girgiza kanta tace a'a so kawai nake na tabbar!
Hawaye ne suka gangaro kan fuskarta tayi saurin saka hannu tagoge dan bataso yagane halinda take ciki wanda ita kanta batasan me yake nufi ba na damuwa da lamarin aurensa!
Yaga lokacinda tasa hannu tagoge hawayenta, baice da ita komai ba yajuya yafita...
Saida yazo kwanciya abubuwa suka shiga dawo masa tunani yake akan HaYaT da halinda tashiga dazu da tambayar da tamasa akan aurensa harda hawayenda tayi da damuwarda yagani karara akan fuskarta tambayar kansa yake meye dalilin damuwarta?
Wata zuciyar ce tabashi ansa da cewa kaunarka take! Kai kanka kasan baka mata adalci ba ALI..
Wata zuciyar kuma cewa tayi dashi karkayi abun kunya me zakayi da wanan kwailar yarinyar? Damadarda kake bata kwana biyun ne yasa takeson renaka tana gani kamar zaka kaunaceta alhali kuma kafi karfinta kawuce ajinta!!!
Tsaki yaja dan ya aminta da HaYaT ganin damarsa tayi har take kokarin renasa, amma zai iya takonsa akanta tun kafin tagama renani yafada aransa...
Bayan kwana biyu tsakanin HaYaT da Faridah ko gaisuwarta bata ansa gabadaya tadena sakata aiki kota hanata, tama dena cin abincinta kullun cikin dafa indomie take tanaci tasha ruwa abincinta kenan
Tsakaninta da ALI kuwa komai yacanza yanzu abu kadan zatayi saiya hauta da matsifa, gabadaya yadena nemanta sai in ita din ce takai kanta garesa ahakanma saiyaja mata aji tukuna yake kulata ada saiya kwanta da ita sau uku ko sau biyu adare dik lokacinda ta yarda
Amma yanzu takai kanta amma bai wuce yayi sau daya yatashi yabarta kwance cikin takaici
Abunda Faridah bata saniba shine tun ranarda HaYaT takona sihirinda tayima ALI yadena ganinta da kima kamar da zaune kawai yake da ita badan yanaso ba, shi din mai adalci ne shiyasa yaki nuna mata tsanarda yake mata yanzu shiyasa baya nemanta saidai idan taka kanta yana iyakacin kokarinsa wajen biya mata bukatarta dikda bayajin komai game da ita jinta yake wayam bawani dondano tattare da ita!
Daman can ae sihiri ne yayi tasiri akanka ALI
Lokacin biki na karasowa yamaida gabaya hankalinsa akai saboda soyake yafaranta ran iyayensa wanan karon...
βπ»
[8/1, 7:01 AM] Hayat: πππππππππ
πππππππππ
*AyNuL HaYaTπ*
_MATAR ALI GADANGA_
πππππππππ
πππππππππ
*-_-_-_-_-_-_-_-_-_-*
*LaBaRi Da RuBuTaWaβπ»*
*-_-_-_-_-_-_-_-_-_-_*
*NeEnA_CoOlπ©π»βπ¦±*
*-_-_-_-_-_-_-_-_-_*
*_______________________*
*π³πͺNiGeR Ma FiErTΓ©π€π»*
*Ψ§ΩΩΩΩ
Ψ₯ΩΩ Ψ£Ψ³Ψ£ΩΩ ΨΨ¨Ω ΩΨΨ¨ ΩΩ Ω
Ω ΩΨΨ¨ΩΨ ΩΨΨ¨ ΩΨ¨ΩΩ Ω
ΨΩ
Ψ― Ψ΅ΩΩ Ψ§ΩΩΩ ΨΉΩΩΩ ΩΨ³ΩΩ
.*
*ΩΨΨ¨ ΩΩ ΨΉΩ
Ω ΩΩΨ±Ψ¨ΩΩ Ψ₯ΩΩ ΨΨ¨Ω ΩΨ§Ψ±Ψ¨ Ψ§ΩΨΉΨ§ΩΩ
ΩΩππ»*
π·π·π·π·π·π·π·π·
_DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN KAIβπ»_
π·π·π·π·π·π·π·π·
1β£0β£
Tun ranarda yasata cin abinci agabansa rabonta daya tsaya yamata magana daman yanzu ba fitar take ba takoma kamar da idan kaganta falo ko kitchin toh aiki take tana gamawa take komawa dakinta tazuana cikin kadaici da damuwa da kewar mahaifiyarta dikda bata santa azahiri ba
Faridah kuwa su Rukky sunka mata magunguna wanda acikinsu badai na gaskia dakansu suka hada abunsu
Ita kuwa ta ansa ta aikata dik yanda sukace bokan yace, saidai lokacin aure na karasowa haryanzu bataga canji ba saidai tadaura dik laifin akan iyayensa dan cemata sukayi ae boka yace su suke karya dik wani sihiri idan yayi dan suma sunada nasu babban bokan mai karfin sihiri
Aunty Balki kuwa dataje gun boka yace saitazo dakanta, gashi ALI ya hanata fita yanzu ba kamar da bΓ’, dan tsoronsa take yanda gabadaya yacanza mata tanaso tayi satar fita tana tsoro yamata zuwan bazata yatarar bata nan kashinta yabushe, shiyasa take jiran ranarda ta tabbar yanada aiki har dare tukuna tafita
Ana sauran kwana daya auren tasamu tafita aekuwa bokan ya hadosu da magunguna kala kala yace musu inhar tayi aikin yanda yace zataga yanda zaiyi aiki kamar yankan wuka!
Harsunyi sallama da bokan zasu tafi tadawo tazauna tace boka akwai wata yarinya agidana tayi mun abunda bazan iya yafe mata ba itace sanadin jefani halinda nake ciki inaso kahadata da bakin aljani ya wahalarda rayuwarta daga karshe yashanye jinin jikinta gabadaya tamutu !
Dariya bokan yayi yace wanan babban aiki ne mai zaman kansa kuma yinsa yanada wahala fiyeda sauran, shi bakin aljani dayan biyu ne idan aka aikashi gawani yakasa aikata aikin akan wanda aka turasa gurinshi toh fa akan wanda yatura zai dawo kin amince ayi bawata matsala?
Eh boka ba matsala nayarda sonake kawai naga karshenta shegiya
Ba damuwa zaki kara kudi fiyeda wanda kika bayar!
Batareda shakkar komai ba tadauki bakudan kudade tabawa bokan cikeda murnarta tanufi gida, taci sa'a kuwa ALI baizo ba dan haka tayi aikinta normal harta gama taci sa'a HaYaT bata ganta ba balle tahana ruwa gudu.
Bakin aljaninda aka aiko yashiga jikin HaYaT yafira gidan tareda shiga dakin HaYaT saidai yakasa isa gareta saboda zaune take tana karatun alkur'ani dan yaye damuwarda ke damunta shiyasa tadauko tana karatu
Komawa aljanin yayi gun boka yasanar dashi halinda ya riski HaYaT ciki
Umarni bokan yabashi yaje yacigaba da dakonta har zuwa lokacinda zakasamu nasara akanta....!
-------------------
Rana bata karya saidai uwar diya taji kunya yau aka daura auren ALI GADANGA da amaryarsa SAJIDAH
bangare biyu gidan ango dana amarya anashan shagali an kashe naira kamar ba'asan zafin nemanta ba
Dare nayi aka kai amarya dakinta gida daya da Faridah dayake gidan yanada girma sosai dan dakuna ne asama sunfi biyar dalilinda yasama iyayensa sukace kawai ya hada kan iyalansa!
Faridah da Auntynta sai kawayenta Rukky da Baby nice suka zauna mata dan batayi taro ba sam bayanda ALI baiyi da itaba tayi tace bata son damuwa
Lokacinda akazo aka danka amanarta ahanun Faridah tanuna ta ansa hannu biyu biyu batareda tanuna wani damuwa ba.
Saida yan kai amarya suka tafi Aunty Balki itama ta tafi akabar Faridah dasu Rukky wai zasu tayata kwanan dannar kirjin uwar gida, aekuwa daki suka nufa suka bude babin gulmar dangin amarya dama amaryar ita kanta, itakam Faridah yayar ALI tafi kowa bata takaici ganin yanda sai wani rawar kai take ita gata dan uwanta ya auri wacce sukeso! Aranta tace muzuba mugani ni daku shege ka fasa...
HaYaT tun safe take famada ciyon ciki dan yau ko lekowa batayi falon ba sam, da alama pΓ©riode dinta ne zaizo karo na biyu gabadaya tafita hayyacinta tanaji lokacinda aka shigo da amarya gabadaya taji jikinta yakara rikicewa tajima tana murkususu akasa kusan minti talatin kafin ciyon yadan lafa mata tasamu bacci yadan dauketa ta manta batayi adu'ar bacci ba gashi kuma jinin haila yazo mata abunda yabawa aljaninda aka turo damar shiga jikinta kenan...
Ango yashigo da abokanansa sun saye baki daga nan abokan ango suka maida abokanan amarya kowacce gidansu akabar amarya da ango kawai adaki,,, idan kukaga bakin ALI yau baya rufuwa yau farin ciki yake zallah
Zuwa yayi dakin Faridah dan yamata saida safe yatarda su Rukky sun baje adakin dawowa yayi baya cikeda mamaki
Fitowa Faridah tayi ranta adagule kallo daya yamata yadauke kansa yana fadin su Rukky anan zasu kwana kome?
Eh tace dashi saboda sutayani kwanan bakin ciki yau da takaici ranta abace tayi maganar dan takasa sarrafa kanta wanan karon yaga bacin ranta Karo na farkon akan auren
Aransa yace bazan kulaki ba muyi abun kunya wanan daren daga zuwan amarya tafara fuskantar matsala dake tun yanzu!
Hannunta yaja yakaita dakinsa abakin gado yazaunar da ita shima yazauna yana kallonta kafin yace
Haba Matar karki badani mana hakurinda kikayi na kwanakin nan yatashi abanza, nasan da ciyo kishiya kuma kishi dole ne, halal, nasani sonda kike mun yasa dole kiyi kishina nakumaji dadin hakan!
Amma abunda nakeso kigane shine karin aure ba laifi bane musaman in akace iyaye sun saka mutum dole yayi kinga kuwa ba makawa inhar inaso naga daidai arayuwata dole nayi, kuma shi karin aure halal ne kodan rashin haihuwar nan dayake damun mu kinga yanzu saimu samu yara masu tayamu fira acikin gida kafin ke kisamu naki, saidai ina fata ace yanda kika fara uwar gidata haka ace kece kika fara zama uwar yayana!
Kuma
kisani dik matarda na aura dole tabiki sau da kafa dan kina gaba da ita kuma ba rashin sonki bane yasa na aurota ba a'a! Nan yacigabada