Showing 9001 words to 12000 words out of 54100 words

Chapter 4 - AYNUL HAYAT COMPLETE HAUSA NOVEL

12 Dec 2024

8199

yake amma sam hankalinsa baya jikinsa tunani yake wacce kalar wainar zasu toya idan yatunkari Faridah da wanan maganar sarai yasan irin tashin hankalinda suke shiga idan irin wanan ta taso ko alokacin baya

Harya isa gidan yafito yashiga falon bai dena tunani ba, saidai abunda yashiga yatarar shiya kusa zautar dashi cikin mamaki yake bin falon da kallo dik falon an fasa komai ba abunda zai amfanu nan gaba

Kallonsa yakai sama yadubi hanyar dakin Faridah aransa yake fadin ya tabbatar itace da wanan danyan aiki ba wani ba!

Tuna HaYaT da yayi ne yasa yakalli kofar dakinta ahankali yaje gurin yana buga kofar yana kiran sunanta cikin rada kamar mai tsoron wani yaji kiranda yake mata

Daman idonta biyu abunda Faridah tayi agaban idanunta shiya hana bacci daukarta dan gani take kamar tahaukace ne karta kwanta tayi bacci ta iskota ta shaketaπŸ˜‚

Kamar rada taji ana kiran sunanta da buga kofar ahankali cikin tsoro tamike tsaye tana kallon kofar kamar ace ar tazuba aguje

Saida ta ajiye hankalinta dakyau tukuna tagano muryar ALI yake kiranta

Ajiyar zuciya tayi danko ba komai idan Faridah takai mata cabka akwai ALI zai shiga tsakaninsu ne, tsoronta daya ranarda Faridah zata gano wacece ita agidan nan kalamanta ne suka shiga dawo mata akunne akan wacce tayi kuskuren shigowa gidanta da sunan MATAR ALI...

Tuna hakan datayi ne yasa tasaki wani marayan kuka tareda nufar kofar tabude ahankali

Baya yaja tafito tamaida kofar tarufe

Shikuwa kallonta yashigayi yaga tana kuka azatonsa Faridah ta hada da ita wajen haukar tata

Saidai yaga bako dan kwarzane ajikinta tukuna ya kalleta yace waya dakeki?

Girgiza kai tayi alamar ba kowa!

Faridah tamiki wani abun ne?

A'a! tafada cikin muryar kuka

Fada tamiki?

Nanma girgiza kai tayi alamar a'a!

Hade rai yayi yace haka kawai jin dadin kukan ne yasa kikeyi kome?

Kara fashewa tayi dawani sabon kuka

Ganin abun nata yazama renin hankali yasa yadaka mata tsawa yace waya fasa dik abubuwan nan ne?

Aunty Faridah ce tafada da sauri cikin hawaye!

Toh meyasa baki gyara komai kin kwashe ba

Maza kije ki gyara falon nan banson iskanci da sakarci irin naki!

Jiki ba kwari batareda tayi magana ba taje falon tafara tattare guntayen kwalaben tana kuka abunta cikeda shagwaba

Tsaye yayi yana kallonta

Dan tausayinta ne yakamashi, ganin bazata iya yin aikin ita kadai ba yasa yaje yafara tayata batace dashi komai ba suka fara aikin tare

Sun kusa gamawa ne cikin rashin sa'a HaYaT tadauki wata guntuwar kwallar jus zata saka amazubin shara ae kuwa kwallabar taratsa hannunta

Kuzo kuga ihunda tasaka tana yarfe hannunta dan tsoron ganin jini take kamar me ihu take harda tsalle irina yara

Zaro ido ALI yayi ganin abunda take tsoronsa daya karta taso masa Faridah kallonsa yakai sama yaga ba lamarta dan haka da sauri yarufema HaYaT baki tareda janta yakaita kitchin

Hannunsa yadaura akan lebensa yana kallonta yace shiiiiiittt🀫

Bakida hankali ne akan dan wanan yankar zaki nemi tada mana masifa?


Itakam kokarin kwace bakinta take takasa, dawane zataji da rikon bakin ko kuma da radadin zafinda hannunta yake mata?

Hawaye saibin fuskarta suke can dabara tafado mata

Ba zato ba tsammani ALI yaji ta gantsara masa wani irin cizo mai zafi

Sosai ta ciji hannun nasa cikin takaici saida tadauki sakani kafin tasaki hannun tacigabada kukanta tana yarfe hannunta saidai wanan karon tabar tsallenda take afalo

Shikuwa ALI daya saketa yakoma ta hannunsa duba hannunsa yake dan sosai yaji zafin cizon har cikin ransa kuwa

Daga hannu yayi daniyar zuba mata wani wawan mari

Ita kuwa ganin zai mareta ne tsoro yasata sakin wata kara mai karfi wanda saida ALI din yarufe kunnensa ba shiri

Kallonta yake da mamaki yanda take wanan karar cikeda haushi ba abin yagwada sake marinta ba tasake saka wata karar

Itama kallonsa take ido cikin ido zufa da majina da hawaye dik sun wanke fuskarta shabe shabe

Ahankali take sulalewa rikeda hannun idanunta akan ALI tazauna kasa kafin tadena kallonsa takai hannunta daya tacire Hijab dinta tajefar dashi gefe danji tayi gabadaya yatakurama lumfashinta

Wata doguwar rigar atamfa take sanye da ita kanta ba dan kwali gashintama bata saka chouchou ba dan haka hijab dinda tacire ne yabawa gashin kanta damar barbazuwa ako ina kan kafadarta wani kuma yarufe mata fuska

HaYaT komai take cikin yarinta wanda ita batamasan tanayi ba ta hannunta kawai take

Kallonta ALI yake cikeda mamakinta

Ahankali yadurkusa wajenta tareda kamo hannunta

Kama hannunta dayayi ne
yayi daidai da lokacinda tabude baki iya karfinta zata saka kara wacce tafi ta dazu amo

A 360 ALI ba shiri yasaka hannunsa da sauri yarufe mata baki...







✍🏻
[8/1, 6:58 AM] Hayat: πŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’Ž
πŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’Ž

*AyNuL HaYaTπŸ‘„*
_MATAR ALI GADANGA_


πŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’Ž
πŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’Ž

*-_-_-_-_-_-_-_-_-_-*
*LaBaRi Da RuBuTaWa✍🏻*
*-_-_-_-_-_-_-_-_-_-_*

*NeEnA_CoOlπŸ‘©πŸ»β€πŸ¦±*
*-_-_-_-_-_-_-_-_-_*


*_______________________*
*πŸ‡³πŸ‡ͺNiGeR Ma FiErTΓ©πŸ€™πŸ»*


*Ψ§Ω„Ω„Ω‡Ω… Ψ₯Ω†ΩŠ Ψ£Ψ³Ψ£Ω„Ωƒ Ψ­Ψ¨Ωƒ وحب ΩƒΩ„ Ω…Ω† ΩŠΨ­Ψ¨ΩƒΨŒ وحب Ω†Ψ¨ΩŠΩƒ Ω…Ψ­Ω…Ψ― Ψ΅Ω„Ω‰ Ψ§Ω„Ω„Ω‡ ΨΉΩ„ΩŠΩ‡ ΩˆΨ³Ω„Ω….*
*وحب ΩƒΩ„ ΨΉΩ…Ω„ ΩŠΩ‚Ψ±Ψ¨Ω†ΩŠ Ψ₯Ω„Ω‰ Ψ­Ψ¨Ωƒ يارب Ψ§Ω„ΨΉΨ§Ω„Ω…ΩŠΩ†πŸ‘πŸ»*


🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
_DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN KAI✍🏻_
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷







7⃣







...kinsan Allah wanan karon kika mun ihu akunne saina miki dan banzan duka agidan nan kuma ba Ubanda zai kwaceki ahanuna yafada yana zare mata ido ala dole saitaji tsoronsa

Shiru tayi kuwa, ahankali yasauke hannunsa daga bakinta yana fadi duba hannun zanyi nagyara miki, nutsuwa tayi tabari yaduba hannun dikda zafinda takeji

Gashinda yarufe mata fuskarta yagyara yana mamakin arzikin gashi irin nata, ganinta bakar fata bai taba zaton tanada gashi mai tsayi da laushi irin wanan ba, ahankali yaduba lallai taji ciyo sosai yafada aransa dikda HaYaT tacika raki sosai.

Tashi yayi yace mata tajirasa yana zuwa yanzun nan

Saida yaje sama yashiga dakinsa yadauko kayan aiki na taimakon gaggawa yazo dakyer tabari ya wanke mata ciyon yasaka mata magani tareda rufe ciyon da bandeji

Falo suka dawo zamanta tayi akan kujerar falon tana kallonsa shi yayi shara ya tattare komai falon yadawo hankalinsa tukuna yace ta tashi takoma dakinta ta kwanta

Kin tashi tayi bakinta sai motsi yake alamar tanaso tayi magana

Kallonta yasake yi yace dake fa nake!

Dan Allah dan Annabi dan Allah takarasa da kuka

Shikam kallonta kawai yake cikin mamaki da takaicinta

Ganin tayi shiru sai kukanta take yasa yajuya zaibar wajen da saurinta tamike tasha gabansa

Turus yayi yana kallonta kafin tace

ALI dan Allah nayarda na amince zan zauna agidan nan har iya karshen rayuwata! amma dan Allah kasauwake mun karabani da igiyoyin aurenka dasuke kaina


Aunty Faridah kasheni zatayi inhar tagano ni din matarka ce!

Ni ni nii nitsoronta nake tafada tareda ajiye kanta kasa hawaye nabin fuskarta

Ahankali yatako har zuwa daf da ita hannu daya yasa yadago fuskarta daya hannun kuma yashiga shafa gashin kanta yana tattara wanda yazubo gaba yana maidasa baya ido kur yake kallonta kafin yadaga lebe yace

Karki damu da Faridah da matsalar Faridah wanan dik bai shafeki ba kuma bazai taba shafarki ko nan gaba ba!

Dan haka maganar sakima kibarta!

Ke haryanzu yarinya ce kinyi kankanta da akiraki da BAZAWARA ko SAKIN WAWA!

Yana gama fadin haka yajuya yabarta nan tsaye kamar mutum mutume tana jujuya maganganunsa aranta, takai minti biyar awajen kafin ta iya motsa kafafunta takoma cikin dakinta ta kwanta...


Kai tsaye dakinsa yanufa saida yayi wanka yafito da gajeren wando yanufi dakin Faridah da mamakinsa ganinta yayi kwance akasa ga magninda tasha nan gefenta dauka yayai yaduba yakarence tsaf kafin yagirgiza kansa yafita yakoma nasa dakin ya kwanta saidai bacci sam yaki zuwa idanunsa tunaninsa daya irin tashin hankalinda yake fuskantarsa nan gaba da Faridah

Wasa wasa har karfe daya tabuga bacci yakasa dibarsa dan haka tashi yayi yadauro alwarla yashiga jera nafiloli sai wajen karfe biyu yaji yakasa tukuna yazauna yayi adu'a yashafa kafin yamike tsaye yanufi frige dan kishirwa ta takurasa bai zaton rasa ruwa aciki ba wani dan tsaki yaja kafin yafita yanufi dakin Faridah itama dakin nata ba ruwa aciki hasalima ita takashe nata frige din gabadaya!

Dole saida yasauko kasa yanema,
saidai me HaYaT ya hango atsakiyar falon tana kai kawo hannunta wanda taji ciyon dashi akanta hawaye kuwa kamar an bude famfo haka suke zuba afuskarta

HaYaT ciyonda hannunta yake ne yahanata bacci kamar karta kwanta wajen karfe daya ciyon yatasheta jitayi gabadaya dakin bazai dauketa ba dan haka tafito falo

Ahankali yakarasa saukowa yanufi inda take ke yadaka mata tsawa meye haka?

Cak tatsaya tana kallonsa cikeda shagwaba tace hannuna zafi tun dazu nakasa bacci

Shi sai yanzuma yatuna bai bata maganin kashe ciyo ba, aransa yace dole ki kasa bacci HaYaT!

Ina zuwa yace da ita komawa yayi sama yaduba dik inda yake ajiye magunguna babu wanda yake nema aciki, cikeda takaici yasauko hannunsa daukeda makullin motarsa tana ganinsa yana saukowa tanufi inda yake har alokacin bata sauke hannunta dake kanta ba

Ba maganin yace da ita, amma jirani yanzu zanje nadauko nadawo saikisha!

Yana fadin haka yafara tafiya bin bayansa tayi kamar wata karamar yarinya saida yabude kofar zai fita yarufe yaga tayi wuf tafito itama da mamaki ya kalleta

Ke meye haka?

Zan bika tafada atakaice!

Banson iskanci yafada ransa abace ni sa'an wasanki ne wai?

Dan kinga ina tausaya miki shiyasa kike neman raina mun hankali ko?

Hawaye ne suka zuba fuskarta batareda tace masa komai ba tasauke idanunta akasa

Tausayi tabashi dan haka kulle kofar kawai yayi yacigaba da tafiya zuwa wajen mota tana biye dashi

Dakanshi yabude mata gaban motar tashiga yarufe saida yaje yatado mai gadi yazo yabude yafita

Ahankali yake tuki yana satar kallon yanda taketa kokarin danne kukanda yakeso yakubuce mata dan azabarda zafin hannun ne mata

Saida suka isa asibitin zata fito anan yalurada ko dan kwali bata dashi balle hijab dakatarda ita yayi daga kokarin fitarda take yace kitsaya anan naje nadawo.

Bata fuska tayi tabi harabar asibitin da kallo bawanda yake yawo dagasu sai wani namiji dayake kwance tsakar asibitin da alama dan uwan mai jinya ne yazo nan yanashan iska

Saida tagama kallo tsaf tamaida kallonta gareshi gyara zamanta tayi tadena kokarin fitarda take

Kizauna ba abunda zai sameki yanzun nan zan dawo kinji ko?

Da ido kawai tabishi yafita yakulle motar yabarta nan.

Kusan minti biyar saigashi yadawo hannunsa daukeda ledar magani da robar ruwa

Saida yabata maganin kafin yaja motar suka nufi hanyar gida, aekuwa maganin yamata aiki dan zafin yadena damunta jim kadan dashansa,,,,,, ba jimawa tafara gyangyadi kan kace me har bacci barawo yayi awon gaba da ita.

Lokacinda suka iso har lokacin bacci take batasan sun iso ba, ke yafara cewa da ita

Batako motsa ba, kiran sunanta yashiga yi nanma shiru

Wani dogon tsaki yaja tareda fitowa yarufe kofa yazagayo inda take tabata yafarayi yana kiran sunanta

Ahankali tamotsa tabude idanunta tasaukesu akansa ganin shine yasa tayi saurin bude idanunta da sauri dikda nanauyan baccinda yake damunta

Cikin sanyin murya tace yi hakuri bansan mun iso bane tafada tareda fitowa bata jirasa ba tanufi hanyar cikin gida saida takai bakin kofa dole tatsaya yazo yabude kofar

Daya iso kallonta yayi yace dana zata akwai ta inda zaki wuce ae bazaki jira nazo nabude ba yanda kikayi kuza kuza kikayo gaba dan renin sense ko murfin motar baki tsaya rufewa ba dan kin renani ba?

Itadai batace dashi komai ba, danko jinsa batayi dakyerma take bude idanunta burinta yabude kawai tashiga ta kwanta!

Yana budewa tayi wuf tashige kai tsaye dakinta tashige tana zuwa ta kwanta da bismillah ba jimawa bacci yayi awon gaba da ita...


Yau bashine yatashi ba saboda makararda yayi wajen kwanciya sai ana tada Sallahr asuba dan haka anan yayi Sallahrsa agida yakoma bacci bayan yayi yan adu'oi dan bacci ne sosai a idonsa.

HaYaT kuwa daman idan ta tashi Sallah bata komawa bacci saitagama aikinta gabadaya tukuna


Yaukam takasa koda d'aura ruwan zafi ne ga bacci bai isheta ba ga hannunta kuma bazai moru ba, dan haka kawai baccinta takoma abunta yau harda mafarkai masu dadi kala kala...

Wajen karfe tara da rabi Faridah tafito bayan tayi wanka tasaka atamfarta wanan karon bata saka karin gashin dokinda kullum yana kanta ba, saima tafi kyau ahaka!

Ganinda tayi ba komai akan table yasa taleka kitchin tananma taga wayam aekuwa batasan lokacinda tafurta kan uban can inyeee yaushe tazo gidan har zata fara mana iskancin nasu na yan aiki?

Juyowa tayi tanufi hanyar dakin HaYaT buga kofar tafarayi tana kiran sunanta

HaYaT datake toilet tana wanka taji kiran gabanta ne yayi mumunar faduwa dan ita yanzu harga Allah tsoron Faridah take har ranta


Kafin wata dabara tafado mata har Faridahr tabude kofar dakin tadira ciki cikeda bala'i take fadin au toilet kika shige?

Zaki fito ne kosaina Balla kofar nan na iskoki naci Ubanki idan baki gaya mun dalilinda ya hanaki yimana break ba

HaYaT daga ita sai karamin zaninta wanda take shiga dashi idan zatayi wanka tatsane jikinta a aciki toilet din, so take tafito kuma tana kunyar yanda zata tsaya haka agaban Faridah gashi kuma batasan wane irin hukunci zata mata ba!

Ganin batada mafita dan Faridah sai masifa take batada alamar barin dakin

Hakan yasa tafito ahaka tuni harta fara kuka

Yauwa fito munafuka gaya mun wane dalilin ne yahanaki aikinda yazama dole akanki yar baka mai bakar fuska?

Hannunta take kokarin nunama Faridah tanaso tamata bayani

Saidai me kafin tace wani abu wani mahaukacin mari ne yaziyarci fuskarta batareda shiri ba tasaki wata uwar kara mai karfi cikin firgici tareda zubewa kasa dan sosai marin yashigeta bada wasa ba

Jin kararta ne yasa ALI saukowa dasauri da daman yayi shirin fita sai yaji ihun HaYaT

Wajen sauri har yana hada matattakalan benen uku uku biyu biyu

Kamar walkiya suka ganshi agabansu

Faridah datake shirin cigaba da jibgar HaYaT tsayawa tayi tana watsa masa wani irin kallo na karka kuskura kasaka bakinka aciki

Meye haka Faridah?

Ban saniba ka tambayeta! Tafada tana harararsa

HaYaT datake durkushe tana kuka jin muryarsa ne yasata saurin tashi takoma bayansa tabuya kamar wata baby tarike gefen rigarsa gam gam

Kinsaba daman dukan yan aiki akan kankanin abu, amma nagaya miki wanan amatsayin kanwata take gidan nan ba yar aiki ba, taimakonki take dan haka wlh wlh wlh Faridah karki kuskura kisake taba yarinyar nan inhar kinason kwanciyar hankali agidan nan!

Zaro ido tayi ganin wai yau ALI dakanshi yake mata barazana kuma akan wata can banza yar aiki kanwar abokinsa!

Cab lallai da sabon lalee tafada!

ALI akan wanan banzar kake gaya mun magana ni matarka ta Sunnah?

Tafada tana nuna HaYaT dake bayansa

Ke kike daukarta haka Faridah, darajar dan Adam tawuce yanda kike tunanina dan haka ki kiyaye nan gaba yazamana wanan shine nafarko kuma na karshe!


Inyeeee....


Toh wallahi yau basai gobe ba yarinyar saita bar gidan nan sainaga Ubanda yatsare mata tunda akanta kake gaya mun magana harda baraza!

Nine nan Ubanda zan tsaya mata, kuma barin gidan nan sai inke zaki barsa amma ba ita ba!

Saboda ni nasan darajar amana kema kinsan amanarta nadauko kuma akanki da banzan ra'ayinki nakin jinin talaka bazai saka nakoreta ba!

Haka kace?

Eh haka nace!

Haka kace?

Eh haka nace Faridah!!!

Yafada cikin tsawa ba alamar wasa afuskarsa.

Ba HaYaT ba hatta da Faridah saida ta tsorota dashi wanan karon!

Tuna maganar bokonta tayi akan karta kuskura tabiye mishi adik lokacinda taga irin yafaru, idan kuwa ta dage komai zai iya faruwa da aurensu dan daman can ba soyayya atsakaninsu sihiri ne yake tasiri akanshi

Kwafa tayi cikeda takaici tace dagani sai ita za abari agidan nan ae

Tana fadin haka tabar dakin cikin sauri har tana tuntube


Sakin rigarsa tayi tareda saka wani sabon kuka tanufi inda kayanta suke

Tana budewa tadauko wanan ta ajiye tadauki wancan dik tana kukanta maidan sauti saida tadauko wanda takeso tasaka tukuna tamike tsaye

Tama manta dawani ALI acikin dakin gabadaya

sakin zanenda ke daure akirjinta tayi tasaka fant dan haryanzu bata fara saka bra ba tasaka wata doguwar rigar lesh rigar tamata kyau sosai
Batabi takan gashin kanta ba wanda dik yabi yacakule kamar mahaukaciya hijab dinta tasaka tanufi hanyar fita har alokacin kuka take kamar wata karamar yarinya

ALI da tun lokacinda tasaki daurin kirjinta yazuba mata ido yana kare mata kallo gabadaya hankalinsa da imaninsa yana kanta kallon irin kyan hallitar hips dinta da Allah yabata, da yake ganin batada wasu na fulani dan yanzu nema tafara kirgon dangi tafara kan *Mom Daddy*😜 kafin takaiga sauran

Dan haka bai taba zaton tanada baya maikyau haka ba! Danshi haryanzu kallon karamar yarinya yake mata sosai.

Saida tagama komai idanunsa akanta tajefashi cikin wani hali mai wuyar fassarawa,,,, ganin zatabar dakin ne yasa yabi bayanta.

Atunaninsa kitchin zata nufa saiyaga tanufi hanyar fita waje gabadaya, saida takusa bakin kofa tukuna yayi saurin shan gabanta tareda jefa mata tambaya ina zata je?

Cikin kuka tace

Wlh ni bazan zauna agidan nan ba Aunty Faridah ta kasheni, kanaji fa me tace dagani sai ita zaka bari agidan nan dan haka ni tafiya zanyi!

Ook yafada tareda gyara tsayuwarsa yasaka hannayensa cikin aljuhu yace

Yanzu idan kikaje ina zaki nufa?
Kinada inda zakije ne?

Cak kukanta yatsaya tadaga idanunta alamar tunani kafin tace gidanmu zanje!

Daga kafadarsa yayi alamar ko ajikinsa tareda bata hanya ta fita.

Fitan kuwa tayi...

Da taje bakin kofar mai gadi hanata fita yayi harsaida ALI yamasa alamar yabarta ta fita tukuna yabude mata ta fita ko waiwaiye batayi ba tasa kai

Daman umarnin ALI ne, tun ranarda yakata yacema masu gadin kar wanda yabarta ta tafita harsai inshi dakanshi ne yabukaci hakan.....






_Tayaya zan gane labarin yana muku yanda kukeso bayan ban ganin comments dinku saidai akaranta ace muna jiran cigaba Neena dan Allah kimana typing mai yawa? Haba dai fans...!!!!????_













✍🏻
[8/1, 7:01 AM] Hayat: πŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’Ž
πŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’Ž

*AyNuL HaYaTπŸ‘„*
_MATAR ALI GADANGA_


πŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’Ž
πŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’Ž

*-_-_-_-_-_-_-_-_-_-*
*LaBaRi Da RuBuTaWa✍🏻*
*-_-_-_-_-_-_-_-_-_-_*

*NeEnA_CoOlπŸ‘©πŸ»β€πŸ¦±*
*-_-_-_-_-_-_-_-_-_*


*_______________________*
*πŸ‡³πŸ‡ͺNiGeR Ma FiErTΓ©πŸ€™πŸ»*


*Ψ§Ω„Ω„Ω‡Ω… Ψ₯Ω†ΩŠ Ψ£Ψ³Ψ£Ω„Ωƒ Ψ­Ψ¨Ωƒ وحب ΩƒΩ„ Ω…Ω† ΩŠΨ­Ψ¨ΩƒΨŒ وحب Ω†Ψ¨ΩŠΩƒ Ω…Ψ­Ω…Ψ― Ψ΅Ω„Ω‰ Ψ§Ω„Ω„Ω‡ ΨΉΩ„ΩŠΩ‡ ΩˆΨ³Ω„Ω….*
*وحب ΩƒΩ„ ΨΉΩ…Ω„ ΩŠΩ‚Ψ±Ψ¨Ω†ΩŠ Ψ₯Ω„Ω‰ Ψ­Ψ¨Ωƒ يارب Ψ§Ω„ΨΉΨ§Ω„Ω…ΩŠΩ†πŸ‘πŸ»*


🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷
_DA SUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJIN KAI✍🏻_
🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷







8⃣







Tafiya take batareda tasan inda take nufa ba itadai bin hanya kawai take abunda yakara rufar da ita shine gabadaya unguwar gidajen irin daya ne wanda bata lura da hakan randa sukazo da randa sukaje asibiti ba saiyau, gashi ba motsin kowa balle ta tambaya ta ina zataga titi

Ganin abun yakici yaki cinyewa ne yasa tasare da lamarin ahankali tarage saurinda take cak kuma tatsaya abunda yafaru tsakanknta da mahaifinta ne yashiga dawo mata akai kamar alokacin yake faruwa

Kuka taso tasaki mai karfi saikuma yasaka hannayenta dika biyu tadafe bakinta tana girgiza kai

Dakyer tasamu ta hadiye kukan taja wani dogon lumfashi tadaura hannunta daya akan kirjinta tace bai kamata nazubarda hawayena akanka ba Abbu kacutar dani kacutarda rayuwata katsaneni tun bansan kaina ba har izuwa girmana batareda namaka wani abun ba, shin laifina

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login