Showing 129001 words to 132000 words out of 155476 words

Chapter 44 - IDON NAIRA COMPLETE HAUSA NOVEL

MAMUGEE   

01 Jan 2026

421

jiki da halinda ya ganta aciki yace,
"Kuka va lsa Haka,
Tell me meya faru?
Menene kikewa wannan kuka?Jikin naki ne?
Dr tayo Bata zo bane.
Girgiza Kai tayi ahankali hawayenta na sake saukowa cikin qunci Mai tsanani da damuwa.
"Mami ta gano kina kwana watara baa gidan bane??
Was hawaven masu zafine Suka Kuma gangaro
Mata ta rintse Ido tana Jin Ya zatayi da rayuwarta.
Sake sarke hannayenta Acikin nasa yay yana kallonta cikeda kulawa yace,
"Menene?
Hakan ne?
Mami ce???
Uncle ne ko su Anty Fareedah?
Waye ya gano? Meyasa Zaki damu idanma hakan ne a gurin Mijinki kike kwana waye baisan me ake nufiba da matsayin mili da aure acikinsu??
Girgiza Masa Kai tayi tana Nemo kuzari da qarfin halin dazata iya sanar dashi abinda yake faruwa din amma
bazatama iya furta kalman ciki ne ajikintaba.
Shirunta yasashi yin shirun shima sai kawai yaci gaba da rarrashinta Yana taba goshinta zuwa wuyanta yaji temperature dinta is normal sbd masifar data kunno
Mata ta warke zazzabinta take.
Qarfe 6 ta nace akan gida zata ta fito da Kansa yakaita har gate saidai ta hanasa shiga sbd mommy na gida ta hango motarta a harabar gidan.
Bayason bata ranta musamman yanzu datake cikin wannan halin Dan Haka sai kawai ya juya din ya tafi bayan ta shige.
Yana juyawa Kai tsaye Al-Amin yakira ya tambayesa
Dr tayo batazo ta duba Amal din bane?
Tazo" ya basa amsa Kai tsaye Yana sake basa
tabbacin zuwanta sbd tace saisunie asibiti da Amal
din ma amma batace komaiba Bayan hakan.
Kashe wayarsa yayi ya ajiye tareda taka motar da
speed Mai Dan garfi ya dauki hanyar asibitin sbd
bazai iva Bata lokacin nemanta a wayaba zai sameta
yaji abinda ya samu matarsa.
Itama tana shiga ba kowa a gasa suna sama
acan dinma tana hawowa ta samu duk suna Palo
kowannensu zuba Mata idanuwa sukai sbd yanayinta
daya nuna Batada lafiya da Kuma Jan da idanuwanta sukal.
Mommy kafeta da idanuwa tayi sbd takasa gane kan
Amal din gabaki daya kwanakin,
Komai nata ya sauya yanzu Kuma ciwo yaqi ci yagi
cinyewa ga jan Ido Kuma yau.Kiranta mommyn tayi tareda cewa tazo.
Dakatawa tayi daga inda take tsaye tana kasa hada
Ido da mommyn ahankali tace,
"Mommy daga asibiti nake banajin Dadi sosai please abari na Dan nutsu sai nazo Dan Allah Mommy."
Qarasa zancen tayi idanuwanta na cikowa da hawayen data kasa riqewa.
Tashi hankalin Hai Zainab da siddi yay ta taso ta nufota tana rigo hannuwanta tace,
"Meyake damunki ne Amal?
Meyasa kikaje asibitin ke kadai ai nace nice Zan kaiki sod musan Meye wanna sabuwar matsalar data bullo,
Me akace a asibitin to?Me aka gano Yana damunki???
Hawayen dake ciko idanuwanta ne suka gangaro takasa cewa komai sai kawai tace,
"Ciwon maratane ya taso shiyasa naje,
Yanzuma ciwo nakeji sosai mommy inason na kwanta.
Kallon Hai Zainab siddi tayi cikin kulawa da tausayawa tace,
"Mommy abarta ta huta da alama tanajin jikin please,
Idan ta tashi ta huta ciwon ya Dan fada anima sai kiyi maganar da ita.
Kyaleta Haj Zainab din tayi ta wuce dakinta ganin da gaske din da alamar Jin jiki atareda ita.Tana Shiga dakinta zubewa bakin gadonta tayi tareda sake sabon kuka Mara sauti tana rinse idanuwanta dake radadin kukan datasha.
A dakin sai data Jima tana kukanta kafin ta tashi tashiga toilet tasake wanka tayo alwala tayi sallar magrib tayi karatun Qur'an kadan tasamu zuciyarta ta
Dan sake tasamu qwarin gwiwar fitowa tana Dan nuna dauriyar samun sakewa Acikin familynta.
Abinci sukaci Banda ita da fruits kawai Tasha ganin
Mommy na kallonta sai ta Dan sakura abincin tana basarwa.
Fira sukai a Palo dukkaninsu kaman yanda Suka Saba
Amma ita tana gefe kwance tareda Fahat suna firarsu kaman vanda Suka Saba Amma shine Mai surutun yau sauraronsa kawai takeyi.
Suna zaune suna firar saishi Bilkisu ta bude Masa kofar dayayi knocking Yana shigowa dukkaninsu Suka gaidasa Banda Amal datake neman rikicewa bd idanuwansa daya kafe akanta batareda damuwa da
Maminsa da sauran jamaar gidan nagurin ba.
Jin idanuwansa har lokacin akanta yasata dago nata da Basu koma daidaiba har lokacin ta Dan saci kallonsa sai gashi idanuwansu yashiga cikin na juna ta janye nata tana kallonsu Anty Fareedah da hankalinsu ke kan zancen dasukeyi na wani kayan da
zasu siya a waya.
Gurin mommy da uncle ta maida kallonta sukuma magana sukeyi dashi bilhaqqi batareda sun lura da idanuwansa na kanta ba.
Sake kallonsa tayi ganin kallon nasa kusan ya banbanta dana koyaushe..Wani tunani ne yashigeta na ko Dr tayo tayi magana dashi take gabanta yay wani irin mummunan faduwa jikinta ya dauki rawa a boye tasake kallonsa taga irin kallon dayake binta dashi idan Bata bar gurinba zai iya tasowa ya dawo gurinta agaban kowa Dan Haka ta janye Fahat daga jikinta ahankali tareda miqewa tsaye tana gin sake kallon gefensa ta daga gafafu a sanyaye cikin toro da fargaba ta nufi stairs zata
Haye..
"MARYAMAH" ya ambaci sunanta cikin wata irin nutsuwa hankali kwance Wanda fadan sunan yasa dukkaninsu kowa ya juvo Yana kallonsa sbd Babu
Wanda ya taba kiranta da sunan sun ma manta da ance sunan nata na asali MARYAMAH ne Dan har lokacin Hai Zainab Bata fadar sunan a bakinta Koda na wanine daban ta yafe fadarsa.
Ita kanta cak ta tsaya bugun zuciyarta na wata irin tsananta take idanuwanta suka ciko hawaye matugar ya bude Baki yayi maganar data danganci abinda take boyewa to zata iya yanke jiki agurin tsabar tashin hankali da mummunar kunyar duniya.Fatanta da adduarta a lokacin shine ya kasance baiyi magana da Dr tayo ba Dan kuwa tsabar tashin hankalin data Shiga yasa ta manta Bata fadawa Dr tayo din karta sanar da kowaba.
•Ha Zainab kallonsa tayi lokacinda ya dawo da fararen idanuwansa dasukai wani irin sanyi akanta Yana kallonta Kai tsaye yace,
"Amal zataje gain likitan da nay alqawarin zataje akan matsalarta,
Ta shirya gobe da safe zamu wuce Zan kaita da kaina...
Daga Hai Zainab harsu siddi da Anty Fareedah da uncle Lulu kallonsa sukai
Ita kanta Amal din juyowa tayi ta kallesa cikin yanayi biyu sod tariga ta saddakar maganar cikin jikinta zaiyi saikuma taji wanna zancen Wanda shima ta tabbatarda idan akaje duk likitan da zata gani take zai tabbatar da cewa akwai ciki ajikinta.•Hai Zainab kuwa Dadi da akasinsa ne tareda mamakin Yaya Amal zataje taga likita Babu kowa atareda ita saishi Kuma bawani sabo ko magana sukeyi da junaba babu yanda tafiyar zata yiyu a hakan
Dole saidai idan ta shirya ta bisu kokuma Fareedah ko
Siddi.
Magana zatayi uncle ya dakatar da ita da cewa,
"Amal dawo zo.
•juyowa tayi ahankali jikinta na sake mutuwa da wannan abubuwan wani bayan wani datake shiga,
Shikuma uncle ko ya taba ganinsu ne kila shiyasa shima yace tadawo.
Innalillahi wanna ilayhi rajiun" tafada cikin ranta hannuwanta na rawa ta saci kallon AQEEL dayake kallonta Kansa tsaye da alamar yariga yagama magana takuma sani tafiyar Nan sai Allah idan baayita ba Amma itama batason zuwa koina yanzu ta cikin jikinta take tukuna.
##MAMUH#
* ZAFAFA BIYAR **_Arewabooks@Mamuhgee_*
65
Kasa qarasowa sosai tayi tsakiyar palon ta tsaya daga gefenda su Anty Fareedah suke tana Dan sauke kanta qasa,abinda yasake bawa kowa mamaki kenan ganin kanta a qasa
Abinda Basu taba ganiba kenan,

Haj Zainab AQEEL ta maida idanuwanta akansa ta kalla sbd Shiga mamakin wannan halin na Amal datake tunanin da ace sunada kusancin da juna da tabbas zatace akwai saka hannunsa a sauyin da aka samu na wannan dabiar da zaa iya sakawa cikin kyawawan dabiu saukar da Kai gaban manya.

Shi kansa uncle Lulu hakan datayi sai yasashi manta ma mezai fada cikin Dan mamaki yace,

"Amal Yaya dai?
Akwai matsalane??

Dagowa tayi jikinta na sanyi da tambayarsa ta kasa kallonsa shima tace, "lafiya kalau"

Shirun da AQEEL ASAD yayi musu tareda zuba musu Ido Yana jiran abinda sukeson fada suke zagaye zagaye yasa dukkaninsu Dan rudewa da rashin sanin yanda zasu Masa bayanin yabari zuwa ko qarshen watan Nan ne sai Amal din tareda Siddi mommyn tasake kaisu.

Haj Zainab dince tayi karfin halin kallonsa Kai tsaye tana cewa,

"Qarshen watan Nan zamu koma da siddi insha Allah inaga abari lokacin yayi mutafi taren kawai.

Cikin sanyi da nutsuwa tareda girmamawa harma da kulawa yace,

"Ai Mami ba likita daya zasu ganiba,
Wanda MARYAMAH din zata gani daban ne so inaga ba amfanin jiran ta shirya goben insha Allah.

Ajiyar zuciya Haj Zainab ta sake sbd har cikin ranta batason zuwan yanzu sbd wancan likita taso Amal din tagani musamman yanzu da period din ya canja yayi latti da wuri takeson sanin menene wannan sabuwar sauyin da aka samu duk da ba dabiarta bace daddigin yaranta Dan ta yarda da abinta kawai dai ita kanta yagama juyewa yanzu Bata gane komai sosai.

Kan Amal dataqi sake kallon gefensa yayi cikin nutsuwa da kulawa yace,

"Ki Gama shirinki kafin 10....

Kallonsa ta juyo tayi tareda Dan juyawa ta kalli su Anty Fareedah harma da mommyn dake jiran ta watsar da zancensa a gurin ta wucewarta kaman yanda ta Saba har umman na fargaban yanda Amal zata karbi zancen Dan Daman ita harda sanin Amal din bazata yardaba yasata kame Kamen yabar tafiyar su saisu tafi da ita sbd abune Mai wuya Amal ta Amince tafiya dashi din tunda haryanxu taqi kallonsa a matsayin Mijinta.

Kallon mommynta tayi da Uncle Lulu ta bude Baki cikin Dan matse fuska tace bata buqatan zuwa koina yanzu abarta kawai.

Tanajin idanuwansa akanta lokacinda tayi maganar.

Jin wannan maganar yasashi miqewa batareda yasake cewa komaiba akan maganar yayiwa Maminsa da itama takeson ya tsaya ayi maganar dalla dalla asan abinda zai yiyu acikinta Dan tafi kowa sanin rigimar Amal din, Saida safe yamasu tareda uncle ya fice daga palon Yana Hana Kansa janyo matarsa a gurin ya rungumeta ko zai dawo cikakkiya nutsuwarsa daya rasa na Abinda Dr tayo ta sanar Masa.

Yana ficewa Haj Zainab ta kalli Amal data Gama kasheta da mamaki tace,

"Kinji abinda ya fada ai,
Ki bude Baki kiyi magana ki roka yabari sai lokacinda zamu din kiga wancan likitan Amma kin tsaya wani Sumi Sumi,Wai Ni mema ya sameki ne da wannan dabiar??
Meya samu duka Baki da kuzarin naki be Wai?

Siddi data kasa rike nata mamakinta Kai tsaye tace,

"Mommy shakkarsa takeyi fa,
Kina ganin AQEEL ASAD dinnan bafa Wasa ko fuskar Wasa a lamuransa,
Gashinan karfi da yaji yaso hanata karutu Allah yasa ya sassauto yanzu gashi tsakanin gaskia da gaskia ya hanata driving da kanta saidai driver duk inda zata kaman tsohuwar mace,

Mami kema fa kina Dan shakkar wannan fuskewar ta 'dan ki bare mu,
Nidai gaskia karma asani tafiya binsu bazan iya binsa ba Kinga ko kallon Mata bayayi itama datake matarsa Baga Yana kallonta bare,

Saidai ko Anty Fareedah zataje Ni Abuja ma zankoma satin Nan.


Amal datayi nisa a tinani batama San gardamar dasukeyi ba Dan kuwa Anty Fareedah ma duk da tanason zuwa ko Dan taga likitan itama haihuwar takeso tasake ko dayace kamar me Amma itama hakanan take shakkar tafiyar Dan zaiyi wuyama yaje da kowa tunda iya Amal din yace.

Itama dai zuqewa din tayi ta nuna gaskia bazata iya zuwaba Suje Ana fada bazata iya komai akai ba sbd tasani Sarai Amal zafin Kai zata nuna Masa shima nasa zafin kan ya shanye na kowa da alama, gwara ta Kama kanta bazataba gaskia.

Shiru mommy tayi sbd itama ba iya zuwan zatayiba a gabanta Amal ta ringa Masa abinda taga dama takasa hanata yaga rashin mutunci da kaman rashin tarbiya a tareda ita.

Uncle Lulu kuwa Kai tsaye yabada shawarar abari suje din idan Amal taga ba kowa zata iya Dan sassauta fushi da zafin auren idan har zata samu lafiya ai komai Mai sauki ne bare a tinaninsa AQEEL din dawowa zaiyi idan ya kaita Dan bazai iya zama acan ba tsawon lokaci tunda akwai ayyuka na office Dana mutanensa daya Bari.

Amal Suka kalla ganin tayi nisa a tinani sbd tana cikin wani matsanancin Hali na rashin qaqanikayi akan abinda yake tareda ita,babban tunani da wasi wasinta shine idan AQEEL ASAD din yasan da cikin?
Tana tsoron ace yasan da maganar Dan bataga dalilin wata tafiya zuwa ganin likita ba yanzu bayan shi da ita sunsan ba lallai ta sake ciwon marar ba Idan harda gaskene bazaka sake ciwon mara ba sosai after first sex zuwa uku haka,ita da bama zata iya cewa so nawa hakan ya faru da itaba.

Ganin damuwa sosai atareda ita sai Haj Zainab din ta sauke ajiyar zuciya tana tunanin damuwa da quncin tafiyar ne Dan Haka ta Dan rarrasheta tabata qwarin gwiwar tafiyar tareda yimata fadan kada Tai Masa abubuwan da Basu Kamataba ta lallaba ta danne zuciyarta da duk fushi da zafin datakeji akan auren a Nemo Mata lafiyarta datafi komai.

Amal har lokacin bata wani gane maganganunsu sbd abinda yake cikin kanta ta rasa nutsuwa harma da hankalinta takeji,

Qafafunta ba kuzarin komai ta ja kanta ta Isa dakinta tana Shiga ta zauna bakin gado tareda tallafe kanta dake sarawa Mai tsanani tana rintse idanuwanta.

Ta Jima ahakan saiga siddi da Anty Fareedah sun shigo suna Dan kokarin tsokanarta da Wasa da cewan sune zasu hada Mata kayan tafiyar farko da miji.

Siddi datafi kowa yanko zance cewa tayi da itace bazata dawoba saita sakashi ya San ita din mace ce ba kaman matarsaba Dan kuwa ita tun Randa taga matarsa ta Renata batajin matar tasan abinda takeyi sbd alfahrinta yasa take tunanin Yar matsiyata ce yake aure.

Anty Fareedah ma zancen ta karba sunayi da Siddi
Amal din dai takasa ko motsawa Bare tankawa qarshe zamewa tayi ta kwanta a kife tareda rintse idanuwanta tanajin ciwon kanta na qaruwa.

Bata San lokacinda Suka Gama yamutsa Mata daki da sunan hada Mata kayanta ba suka fice.

Da asuba daqyar ta iya bude idanuwanta ta tashi jiki ba qwari ta nufi toilet tayi brush da alwala ta fito tayi sallah Takoma ta kwanta har lokacin da ciwon kai atareda da ita.

Bata samu Takoma bacci ba sbd tinani da damuwa Mai tsananin gaske,
Ta rasa tinanin yi ko Wanda zata fadawa ta rage nauyin zuciyarta akan cikin dake jikinta,

Idan da gaske AQEEL ASAD yasan da cikin me zatayi Dan batajin zata iya kallon mommynta dasu Uncle da cikin nanba idan suka sani,

Mezatace musu?
Yaushe?Ina? Tayaya? Duk a wane lokacin hakan ta faru zasu tambaya
Amsar da itama batasan me zataceba.

Hawaye ne suka gangaro Mata daga idanuwanta dasuka kasa komawa daidai daga lokacinda tasan tanada cikin har yanzu.

Hawaye taci gaba da tsiyayar daga kwance tana Jin zuciyarta na nauyi Dan batada makamar wannan lamarin,

Ita ko tunanin Ana zubarwa Bai zo kanta da tinanintaba Dan batasanma ta inda ake zuwa a zubda dinba.

Wayarta ce tafara ringing a hankali ta da bude idanuwanta ta kalli inda wayar ke ajiye gefen pillow dinta.

Tana ganin shine Mai Kiran sbd zuwa yanzu ta haddace numbernsa Amma batai saving ba,

Jin tayi jikinta ya dauki sanyi da zafi lokaci daya Kuma taba buqatan Wanda zatayi maganan dashi kafin kanta da zuciyarta su buga.

Daukan wayar tayi tareda dorawa kan kunnenta tayi shiru hawayenta na gudu.

Shima shiru yayi ahankali Yana sauraran yanda sautin numfashinta dayake bayyanarda kuka takeyi ahankali Mara sauti.

Wani nannauyan numfashin Mai sanyi da nutsuwa ya saki tareda Dan rufe idonsa ya bude cikin sanyi ahankali yace,

"Wannan kukan zai sakaki ciwon kai fa,
Ki shirya yanzu basai 10 dinba ganinan zuwa na daukeki bazan iya wannan jiranba,kukan Nan naki is driving me nuts..

Kawai sake Masa sabon kuka Mai qaramin sauti tayi batareda ta saniba tana cewa,

"Banason zuwa koina,
Ni kaina ma fashewa zaiyi, zuciyana ma ciwo takeyi komaima banaso Ni.......fashewa tayi da sabon kuka tana rasa yanda zatayi da kanta.

Dif taji ya kashe wayar batareda yace komaiba itama wurgi tayi da wayar tana sake tsiyayo hawaye fuskarta.

Kaman a mafarki batafi mintina arbain da jefar da wayarba mommynta ta shigo dakin tana kallonta ko saukowa gadonta batayiba idanuwanta sunyi jajir alaman kukan datasha.

Cikin sanyi mommyn ta qaraso gadon ta zauna tana cewa,

"AQEEL yazo Yana jiranki inaga tun 10 din Bata qarasa ba zaku wuce.

Rintse idanuwanta tayi sbd harga Allah Bata buqatan zuwa koina ta kanta din takeyi,
Hakama batasan menene wannan tafiyan take nufiba.

Haj Zainab data dauka tsananin rashin son tafiyar ne yasa Amal din wannan halin duk sai jikinta yayi sanyi Amma Kuma tunda bama qasar zasu bariba yace cross River ne zasu ita wannan lamarin batasan wane irin likatane zaa iya ganiba acan,

Dan Haka tabar zancen Akan idanma sunje yanzu itama idan zata gaskia zata tafi gurin nata liktan da Amal din zata sake zuwa.

Shafa Fuskarta tayi tareda Kiran sunanta ahankali tana rarrashinta akan tayi hakuri taje din ba komai bane idan taje taga wannan likitan insha Allah Suma idan zasu nasu bazai hanaba zai barta suje gaba dayansu.

Kasa magana tayi bare motsawa tayi shiru kanta na sake sarawa,

Jin takeyi inama Bata tareda abinda take ganinsa kaman abin kunya data kwanta jikin mommynta taji sanyi Amma yanzu ita kanta kunya da takaicin kanta takeyi da bazata iya dogayen motsiba ganin takeyi kaman zaa gane metake dauke dashi.

Mommy da kanta ta tayar da ita tasata tayi wanka jikinta a sanyaye ta shirya Suka fito siddi ce ta fidda Mata kayanta suna fitowa Bata gansaba yariga ya fice sbd bayason Yana ganinta a yanayin datake agaban mutane coz a yanda yake jinta dinnan zai iya rungumeta gabansu Kuma yasan bazataso hakan ba.

Tea kawai tasha sama sama har lokacin batada walwala ko kadan
Ita kanta mommyn zuwa yanzu tanason Amal din taje taga likitan tunda ya buqata hakan
Daga nasa likitan har nasu basusan Ina Saar samun lafiyar takeba.

Mommyn daga na palon tayi bankwana da ita Takoma sama sbd batasan rakiyar me zatayi Mata har waje ba.

Siddi ma daga kofa ta tsaya ta Dan rungumeta tareda Mata sallama ta juya tana cewa,

"Amal Dan Allah ki Dan sake Masa fuska kafin kudawo.

Batada energy na iya amsawa zancen siddin Dan Haka ta shareta kawai kafin tayi wani motsin tajisa a bayanta ya qaraso cikin nutsuwa.

Juyowa tayi ta kallesa da idanuwanta dasukai jajir take taji jikinta yasake mutuwa da wani irin damuwar halinda ya sakata a yanzu.

Hannunta ya Kama ahankali batareda yace komaiba ya nufi mota da ita tana tafiya kaman Mara lafiya ba kuzari ko kadan,
Tun kafin su qaraso Ahmed yabude masu mota
Shine yafara shigar da ita ya rufe Mata kafin ya zagaya ya shiga nasa bangaren Ahmed ya rufe Masa.

Suna barin harabar gidan Kai tsaye airport suka nufa duk da akwai sauran 1 hour kafin tashin kirjinsu.
#MAMUH#



*_ZAFAFA BIYAR_*

*RUMBUN K'AYA*🔥
Hafsat Rano

*DAUDAR GORA*🔥
Billyn Abdul

*IDON NERA*🔥
Mamuhgee

*A RUBUCE TAKE*🔥
Safiya huguma

*KI KULANI*🔥
Miss xoxo

Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200

ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN

0022419171
Maryam sani
Access bank

Shedarka ta 09033181070

MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN

09166221261

🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*

+22799643131

Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA

*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*🔥*_Arewabook@Mamuhgee_*
66
Koda suka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login