Showing 27001 words to 30000 words out of 155476 words

Chapter 10 - IDON NAIRA COMPLETE HAUSA NOVEL

MAMUGEE   

01 Jan 2026

412

daceba ga 'danta.

Yana fitowa bangarensa ya nufa ko zama baiyiba kiran Haj kaka yashigo wayarsa dan haka ya juya ya fice zuwa gidan haj kakan,
Yana isa haj maryamah na isowa nan take sabon rikici ya tashi qannan babansa ma su uku maza duka sun saka bakinsu a maganar amma Aqeel din ya tsaya cak akan bazai bar zainab da MARYAMAH su tagayyara.

Duk yanda ake tunanin kusanci,shaquwa da girman kaunar dayakewa Zainab wannan karon sun tabbatarda abin ya wuce tinaninsu dan haka hankali ya tashi cikin kwana daya lamarin ya zama babba dan kuwa su dangin mahaifinsa duka tsananin laifinΒ  haj maryamah suke gani Dan itace tayi watsi da 'dan ta Barwa zainab din har Aqeel din yazo gashinan idanba zainab da baya Jin kowa a ransa,

Umma tayita kiran wayar Zainab din yafi so dari da dori amma bata samu dan haka takejin kamar ta zama tsuntsuwa tazo ta samu zainab tayi mata duka,

Sun rabu da ita kowa ya kama rayuwarsa amma takasa barin yar uwarta taji dadin rayuwarta da 'danta
Yanzu gashinan itama ai ta Haifa tata yar tabarsa da tasa uwar taqi.

Hannuwansu su haj kaka suka cire sbd duk yanda sukeson tafiyarsa karatu sunfison farin cikinsa akan nasu dan haka suka hakura Akan yanda yakeso din kuma suka amince da yaci gaba da kulawa da zainab da MARYAMAH..

Jin hakan yasa zuciyar haj Maryamah bugawa qarshe dai saida aka hada da Kaita asibiti dan kuwa jininta yayi mugun hawan data kusa samun matsala.

Umma dataga zasuyi biyu babu sai gata ta iso ba shiri gashi da a ranar zai wuce Abuja Gobe su wuce UK din.

Hankalinsa sosai yatashi ganin Halinda mahaifiyarsa tashiga akan lamarin dan haka sai jikinsa yayi sanyi ya zauna tareda ita yana nuna mata kulawa da kauna qarshe umma na ganin irin tsananin son dayakewa mahaifiyar tasa itama sai sukayi magana da maryamah sukai shawara.

Shawararsu suka sanarwaΒ  Aqeel din akan haj maryamah din zata karbi zainab da 'yarta su zauna a gurinta insha Allah.

Da farko hakan bai kwanta masaba dan kuwa hankalinsa yafi kwanciya da kulawar zainab din a hannun dangin mahaifinsa amma kuma duba da yanayin unman tasa data shiga damuwar tafiya sai kawai ya amince ahakan jikinsa duk yayi sanyi.

Yanason zuwa gurin maminsa amma itama Ummansa duk takasa barinsa sbd yanayin jikin nata
Haka ya hakura.

Washe gari tunda safe ya shirya tsaf batareda lokacin wucewar yayiba ya tafi asibiti tareda umma gurin zainab.
Batayi wani mamaki ko damuwar rashin dawowarsa a jiyan ba sbd tariga tasan zuwan nasama Allah kawai yasan irin fitinar da akeyi a gidansu akan hakan.

Ganin umma ya sata jin sanyin jiki dan kuwa tasan dole sai wani abu yafaru umman ke zuwa dan haka tasan akwai wata rigimar.

Gaida umman tayi cikeda girmamawa
Umman ta amsa tareda Yimata gaisuwar mijinta da Barkan haihuwarta duk lokaci daya.

Aqeel ne da Kansa jiki a mace cikin kulawa yayi mata bayanin tafiyarsa a yau din tareda sanar da ita daga asibiti gidansu zata koma da zama komai ya wuce tsakanunta dasu ummansa sun karbeta ita da little MARYAMAH.

Shiru tayi zuciyarta na shiga tunanin lamarin
Shiyasa umman tazo kenan dai akwai rigimar da akeyi din Wadda tasa suka aminta zasu amsheta
Amma dai kuma a yanzu datakeda 'ya batajin zamanta gidan haj maryamah din zai yiyu sbd Dalilai da dama,

Haj maryamah bazata taba son Maryamah qarama ba sbd tun asali batason masu aiki dake da qananun yara Bare ita datakeda jinjirar 'ya,

Tayaya zata iya watsi da yarta tayita aikin bautarda ko yar tasan baa kaunaci ganiba,

Bayan haka Tayaya zata koma kurkukun da Allah yasa ta fito da qyar da 'yar marainiyar 'yarta suje itama rayuwarta ta mutu kamar Tata tun kuruciya har tsufa dan kafin Aqeel yadawo ya zama Gatan maryamah din tuni ta rasa abubuwa da dama.

Ganin yanda tayi shiru yasa umma kallonta a shagube tace,

"Ko kinfi karfin zama gidan ne tunda yanzu kema kin zama uwa babu Wanda ya isa dake.

Shiru Zainab tayi batace komaiba.

Cikin dan fada umman tace,

"Da tsufana amma kullum Ina hanyar tafiya mai shegen nisa sbd ke zainab,
Duk zuwana babu na lafiya sbd rikicin halinki ne Dana yar uwarki,

Yanzu Ana fatar yaron nan ya tafi karatun nan angama komai rana tsaka sbd ke yasake cewa bazashiba
Yanzu an samu ya aminta Zaije tunda ya shiryaki da mahaifiyarsa kin tsaya tunanin ta yanda zaki sake hargitsa lissafinsa ya fasa tafiyar ko zainab?????

Mun koma ga wadda ta Haifi 'dan ga wadda muke rarrashi akansa sbd isa da ikonsa da Allah yabaki..

Jin hakan yasa zainab taqaita fitinar da cewa ta amince zata koma can din karya damu ya wuce karatunsa kawai Allah yabasa saa da nasara.

Batason fitina da tashin hankali da gorinsu umma dan haka ya yanke zancen da hakan dan a samu ya tafi
Suma su umman dan asamu ya wuce din yasa sukace sun shirya da zainab din komai ya wuce duk da kusan umma ce take kidan kuma take rawar
Ita haj maryamah dai taqi saka baki sbd jikinta da zuciyarta dasuka kasa sakewa idan ba ganin tayi Aqeel din ya tafi ba dan kuwa da gaskiarsa magana daya tak yake tsayawa akai ba tafiyar zaiyiba idan ba zainab da 'yarta yaga yabarsu a cikin kulawaba.

Yaje ganin little MARYAMAH amma basu bashi damar daukantaba saidai yaganta daga cikin kwalban Dan haka yayi mata addua sosai da fatar tsarin Allah gareta yafito.

Zainab duk inda zuciyarta take tayi rauni sosai na rabuwa dashi din amma ta boye ta danne a ranta sbd kaucewa laifi gun umma kokuma hanasa tafiyar...
Addua tayi masa sosai tareda fatan samun dibbin nasara da cigaba a rayuwarsa.

Harya baro asibitin kasa hada ido yayi da maminsa sbd yana iya hango damuwa da tashin hankalinta harma da firgicin tafiyarsa ya barsu itada little amma kuma tunda yasan gida yabarsu to tasa damuwar ta dan ragu yanada nutsuwar tafiya yanzu.
#MAMUH#
#MARYAMAH AMAL IDON NERA
#DR AQEEL ASAD
#HAJ ZAINAB IDON NERA
#life#love#hotlove#marriage#

*_ZAFAFA BIYAR_*

*RUMBUN K'AYA*πŸ”₯
Hafsat Rano

*DAUDAR GORA*πŸ”₯
Billyn Abdul

*IDON NERA*πŸ”₯
Mamuhgee

*A RUBUCE TAKE*πŸ”₯
Safiya huguma

*KI KULANI*πŸ”₯
Miss xoxo

Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200

ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN

0022419171
Maryam sani
Access bank

Shedarka ta 09033181070

MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN

09166221261

πŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺ
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*

+22799643131

Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA

*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*πŸ”₯_*Arewabooks@Mamuhgee*_
14
Yana barin asibitin ta zainab ta sauke wani kasalallen numfashi tareda sauke kanta qasa sbd idanuwanta dake kadawa jajir..

Fatan samun nasara da albarkar ubangiji tayi Masa a duk dinta yake sbd Allah ne kawai yasan ranar dawowarsa yasamesu ko wane yanayi Kuma sai yanda Allah yasa.

Zamewa tayi ahankali ta kwanta kan gadon datake tana rufe idanuwanta duk tasan ba baccin zatayiba.


Aqeel kuwa Yana Isa gida breakfast yayi batareda Bata lokaciba yagama aka fiddo da luggages dinsa suka fito hannunsa cikin na mahaifiyarsa dakejin kamar ta goyasa Dan dadi da farin ciki,
Ta matsu taga ya wuce kafin zainab ta bugo tace 'yarta ta mutu yafasa tafiyar Kuma.

Dashi da uncle dinsa alh Yusuf suka wuce
Har airport haj maryamah din ta rakasa sukabi jirgin Abuja Wanda a Daren ranar jirginsa zai tashi shima daga Abujan.

Tana dawowa wata irin lafiyayyar hamdala tayi tada tabbatarda jirginsu ya daga
At last dai tasamu 'danta yatafi
Yayi nesa da zainab
Yanzu tasamu damar da zata ringa ziyartarsa shaquwa da kaunar dayakewa zainab duk zai maido kanta ya ragewa zainab din.

Wuni sukai a gidan cikin nutsuwa da farin ciki daga ita har umma.

Saida yamma tafito a shirye Dan zuwa asibiti ganin likitanta dazai sake duba dp din nata.

Tareda umma suka tafi asibitin
Suna baya driver na jansu cikin daya daga cikin lafiyayyun motacin gidan.

Umma ma ciwon baya da qafafun datake fama dashi aka dubata akai suka fito zasu nufi mota umman tace suje haj maryamah ta dubo zainab tunda tana asibitin itama.

Da mamaki haj maryamah takalli umman sbd sanin asibitin ta kudine sosai Dan basuda ko irin dogayen dakunan ward haka
Duka dakunansu daddaya ne Amenity rooms dai Kai tsaye.

Cikin basarwa umman tace"

Atoh, ai danki ne ya kawota
Allah ne kawai yasan uban kudin daya kashe daga haihuwarta zuwa yanzu,
Ko kudin haihuwar ba qananu bane gana jinyar 'yar Kuma acan wani dakin daban..,ai wlh maryamah kinyi sake sosai,.

Ace 'danki da Kika Haifa Yana hada kainarki data wata
Duk laifinki ne Dan kece Kika barwa zainab 'dan gashinan yanzu bake kadaiba munata fama dashi
Ga shegiyar kafiyar tsiya agunsa
Shi ala dole yasan Allah baya qarya baya magana biyu.

Numfashi haj maryamah ta sauke tana kasa cewa komai sbd tarasa abin fada.

Dakin da zainab din take suka nufa tunda umma tasan dakin dasukazo tareda aqeel kafin wucewar tasa.

Koda sukaje tana kwance idanuwanta a rufe tana tunanin mijinta da 'yarta datazo ta zauna tsakiyar ranta,

Sam Bata qarar da hakan da yake zaunuwa Aran mahaifiyarsa ba sai yanzu data sake qararwa duk da har lokacin kaunar aqeel mai girma tana cikeda ran nata sai takejinsu su biyun sun cike mata zuciya tako Ina.


A tsawon shekarun datayi tana wankin wasu daga cikin kayan haj maryamah da gyaran dakinta tareda wankin toilet dinsa to tariga ta haddace qamshinta ras acikin hancinta Dan haka suna shogowa dakin tun kafin ta bude ido hancinta ya tabbatar mata da 'yar uwartace ta shigo.

Ahankali ta bude idanuwanta dasukai jajir a kumbure ta kallesu tareda sauke Kai tana sake gaida umma kafin ta gaida haj maryamah din.

Dukkaninsu kusan atare suka amsa gaisuwar sai haj maryamah data gyara tsayuwarta tana kallonta tayi mata gaisuwar rasuwar Mijinta kafin daga baya ta tambaya baby.

Amsawa zainab tayi tareda cewa ta gode Allah yabada ladan gaisuwar malam din.

Shiru sukai dukkaninsu saidai umma ce tafara maganar zainab din idan ansallameta taje gidanta tafara tattara kayanta tasan yanda zatayi dasu tukuna saita wuce can gidan haj maryamah din.

Gyada kai tayi kawai batareda ta iya bude Baki tai maganaba Dan batajin zata iya.

Basu wani jimaba suka tafi bayan haj maryamah din ta Ciro 10k daga handbag dinta ta ajiye mata a gefe
na dubiyane ko sadaka ne tabata oho.

Bayan tafiyarsu tashi tayi ta nufi toilet din dakin tasake Dan kamo ruwa ta fito Takoma ta zauna tana zubawa 10k din da itace alkhairin farko dazatace Yar uwarta tayi mata na kudi dai.

Da daddare Saida aka Kuma zuwa aka matsa nononta still har lokacin ba komai dayake Acikin siyayyar da aka rubutawa Aqeel ya siyo harda Madara Kuma kaman yasani ya siyo musu da yawa.


Washe gari da yamma tayi tunanin Kiran aqeel din sbd tasan Kila ya Isa a time din,
Tunaninta tsayawa yayi data tuno da batada waya yanzu tun rasuwar malam ta rasa wayar da rikicinta dasu umma.

Wani nannauyan numfashi ta sauke sbd shima Aqeel ya manta da batada wayar saiya nemeta yajita babu.

Sanyi jikinta Yakuma Yi sai kawai ta cire ran jinsa sai Randa Allah yabada iko.


****Cikin kwanaki hudu ita kam ta warke sumul batada ciwo ko damuwar komai a jikinta Dan haka hankalinta gabaki daya nakan 'yarta MARYAMAH da itama tana Dan samun kuzari da kulawa sosai Dan kuwa Aqeel babu abinda bai tanadarba ya biya kafin ya wuce din.

Baa kawo mata abinci daga gida Dan haka itace take siyan abincinta taci anan duk da nata jegon dakuma damuwar rashin miji duk yasa cikinta a bushe yake batason cin abincin,
Wanda ma take nace tana siya tanaci sbd tanason tasamu Nononta ya taru MARYAMAH tasamu nono.

Wasu daga cikin maqotanta sunzo har asibitin sun dubata da yarta duk da baa bada babyn
Kuma dazasuzo kusan duka sun kawo mata abici wasu kudi harda kunun haihuwa mai kyau suka kawo mata Tasha kuma taji dadinsa sbd ya taimaka mata gurin samun nonon Dan ajiyewa tai tana shansa kwana biyu kafin yaqare dayake dakin akwai fridge harma da heater ta ruwan zafi.

Samun ruwan Nononta yasa babynta tafara samun kuzari da lafiya sosai Dan haka takesan nono sosai gashi Daman ba laifi babyn tanada Dan girma kadan ba irin sosai takeda rashin girman Nan ba ko kadan.

Acan gidan haj maryamah kuwa umma sati daya tayi ta komawarta bayan tasake zuwa asibitin so daya kafin ta wuce.

Aqeel kuwa ya Isa lfy yanata kokarin fara karatunsa Amma yakasa samun Maminsa
Yayiwa ummansa magana ta sanar dashi baa sallamosuba tukuna dole ya hakura harsu dawo gidan yasamu ko ummansa zata hadasa da mamin tasa a waya.

Haj maryamah kuwa tini ta tattara ta wuce Abuja itama kafin tawuce tazo asibitin ta sake dubata so daya taqara Bata wasu 10k din ta wucewarta bataredama zainab din tasan gari zata Bari ba.


Ahankali ahankali Saida zainab ta share kusan sati uku a asibitin kafin aka sallameta ta nufi gidanta da 'yarta.

Gidan yayi datti sosai dayake lokacin iska ne Dan haka dole ta goya Maryamah tafara aikin gyaran gidan.

Saidata gyare koina ta share ta wanke kafin ta fito ta samu yaro ya siyo gawayi ta Dora ruwan zafi tayi wanka tayiwa maryamah da aka koyo mata yanda zatayi mata daga asibitin.

Ruwan zafin Tasha da Lipton ta kwanta suka Dan samu bacci tana tashi maqotanta Wanda Basu samu zuwa asibitinba suka shigo sunatayi mata barka da qarin gaisuwar malam.

Da daddare Dole ta dafa shinkafa dayake akwai sauran abinci dasuke dashi.

Da manja taci shinkafar tasake Shan ruwan Lipton tagama sauran ayyukanta ta kwanta.

Washe gari ma haka ta wuni ita kadai a gidanta daga ita sai 'yarta dare yayi suka kwanta abinsu.

Haka ta runguma rayuwarta data 'yarta data zama sanyin idaniyarta Kuma sanyin zuciyarta,
A yanzu duniyarta 'yarta itace babban abinda yake gabanta,
Batada buri ko buqatan daya wuce inganta rayuwar yarta data warware abinta tayi mulmul sbd nono mai kyau da sauran madarar datake Bata wadda har lokacin sunada sauran kusan gwanwani biyu da Basu fasaba.

Aduk lokacinda tayi sallah iyayenta da Malam da Aqeel sune farko a adduarta da 'yarta kafin kanta,

Ayanxu wata rayuwa take gudanarwa ta kadaici da rashin kowa,

Batada wani farin ciki ko jin dadi
'yarta kawai take kalla taji qwarin gwiwa da farin cikin rayuwa,

Ba laifi tana hulfar arziki da maqotanta duk da babu Wanda ya taba zuwa yabata taimako ko tallafi daga cikin mutanen malam harna Aqeel Dan haka taci gaba da lallaba abubuwan datake dasu Shi abincinta tuni ya qare dole kayayyakin gidan ta tattara ta Saida tabar katifar kwanciyarsu kawai da kayan kitchen.

'yar sanaar Saida gawayi da kayan Miya tafara Amma mutane sun maida komai bashi take suke kwashe komai data kawo Amma bashi
Qarshe Kuma wasu da yawa basa biya haka zataita yawon bin bashin kudin Amma basa bayarwa koyaushe da qaryar da zasu fada.


Babu inda sanaar taje komai ya karye aka rasa kudin gabaki daya Takoma tana kame kame.

Watanta uku da dawowa hayarsu ta qare masu gidan suka Bata notice dole tafara tunanin barin gidan.

Batada gurin zuwa,
Batasan Ina zata da jinjirar 'ya ba gashi bazaso 'yarta tayi tashin garari ba.

Har notice yacika batada gurin zuwa,

Ana hakan ne Daren wata asabar wani mummunan tsautsayi ya sameta na shogowar qato gidanta
Allah bai basa ikon yimata komaiba saidai fuskarta ta kumbura da irin Marin daya ringa zabga mata sbd taqi yarda yayi Mata komai
Qarshe haka ya gudu bai samu damar lalata mutuncintaba haka itama Bata samu taga fuskarsaba.

Tunda take hankalinta bai taba tashi da tsoroba irin hakan Dan haka gari na wayewa takai maganar gurin Mai anguwa Amma qarshe dai haka mutuncinta ya zube babu wani takamaimai sheda ko tabbacin abinda ta fada din sbd kusan duka anguwar ansan juna
Basuda samari duka dattijai ne da tsofi
To tayaya take tunanin zasu yarda kowa da mutuncinsa zai shiga yayi irin hakan.

Qarshe hakuri aka Bata akan saidai daga wata anguwar aka shigo aka Mata hakan.

Wannan lamarin ya sake firgita tsayuwarta ta rasa inda zata saka kanta da 'yarta,
Tsoron gidan da anguwar ma takeji kwata kwata Dan kuwa duka rayuwarta ko yanda ake fyade Bata saniba sai yanzu da hakan yaso faruwa da ita,

Ba kanta takejiba
MARYAMAH dinta takeji tunda fyaden yanzu har yara qanana Ana yiwa,

Wannan tunanin ya toshe dukkanin wata basirarta da tunanin,...

Tunaninta kan rayuwarta na baya yakoma,
Da wani abun yasamu 'yarta gwara taje tayita bauta har tsufa acan din.

Batada zabi, batada dabara, batada mafita tunda ko abin kanta batada dolenta ta juya ta fuskantar bayanta.

Littafan addini da Alqur'anan malam masallacin anguwarsu ta bada aka aje Dan masu karatu hakama siturunsa badawa tayi akaiwa dattijan anguwar kyauta
Sauran kayan tarkacenta na kitchen saidawa tayi wasu Kuma ta bada sbd duk ba wasu kayan kirki bane.


Koda ta iso babban tsohuwar kurkukunta wato gidan haj maryamah Adam Asad babu kowa gidan sai masu gadin gidan biyu.

Dukkaninsu sun santa Dan haka babu Wanda ya hanata shiga saidai Basu bari ta qarasa cikiba dan koina a rufe yake Saida aka Kira Haj maryamah din tace abarta tashiga tukuna suka bata mukullan gidan.

Kai tsaye bayan ta bude koina inda tasan kanta a dah can takuma Kai kanta goye da 'yarta.

Babu inda baiyi wata irin quraba da datti a gidan,

Kallon kanta tayi taji hawayen baqin ciki na gangaro mata Dan kuwa tasan rayuwar data Bari ce tadawo
Amma Kuma zata iya kowace irin wahalace akan MARYAMAH dinta tasamu rayuwa a natsatsen guri da rayuwa Mai kyau.

Babban aikinta na farko data fara komawa shine aikin shara..

Goya MARYAMAH tayi ta rufeta sbd qura tafara aikin shara da gyaran koina.

Har harabar gidan sai data share ta gyare koina tas tadawo ta gyara Mata dakin ta wanke toilet tukuna ta sauke Maryamah sukayi wanka tazo tayi sallah ta kwanta daqyar tana rintse idanuwanta sbd ciwon baya Dana kwankwaso mai qarfi daya taso Mata.
##MAMUH#
#MARYAMAH AMAL IDON NERA
#MARRIAGE/HOTLOVE
#ZAINAB IDON NERA



*_ZAFAFA BIYAR_*

*RUMBUN K'AYA*πŸ”₯
Hafsat Rano

*DAUDAR GORA*πŸ”₯
Billyn Abdul

*IDON NERA*πŸ”₯
Mamuhgee

*A RUBUCE TAKE*πŸ”₯
Safiya huguma

*KI KULANI*πŸ”₯
Miss xoxo

Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200

ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN

0022419171
Maryam sani
Access bank

Shedarka ta 09033181070

MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN

09166221261

πŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺπŸ‡³πŸ‡ͺ
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*

+22799643131

Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA

*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*πŸ”₯*_Arewabooks@Mamuhgee_*
15
Babu komai na abinci a gidan tunda ba kowa Dan haka sai data fita ta siyo bread da lemu tasha takwanta ita kadai a qaton gidan Kamar mayya.

Kusan ko anan dinma a tsorace take,
Tunda wancan lamarin ya faru da ita kowane dare a firgice take kwana rungume da MARYAMAH dinta.

Washe gari haka ta wuni zaune shiru Kamar hoto
Sai yamma sosai saiga drivern gidan shafi'u yazo da kayan abinci masu yawa an zuba a store.

Koda aka kawo abincin harya kwana biyu Bata tababa sbd babu gas Kuma batason tabawa tunda ba cewa akaiba nata ne.

Kullum bread da lemu ko garinta take siyowa Tasha tayi renon yarta dare yayi su kwanta.

Sai datai sati biyu ahakan saiga haj maryamah din tadawo da masu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login