Showing 30001 words to 33000 words out of 155476 words

Chapter 11 - IDON NAIRA COMPLETE HAUSA NOVEL

MAMUGEE   

01 Jan 2026

409

aikinta har biyu, daya yarinya dayar Kuma dattijuwa.

Zuwansu yasa akayo refilling duka cylinders na gidan da gas aka kawo dole itace ta Dora girkin tunda sun iso a gajiye Kuma su din Basu taba zuwa Nan ba acan Abujan aka Samar Mata su dan haka a gidan Basu San koinaba da komai.

Dayake bata taba tsallake inda takeba taje bangaren Haj Maryamah sai ya zama bangaren nata yana buqatan gyara sosai.

Masu aikin nata ne sukai aikin gyara Mata koina a sashen nata suka wanke komai tareda gogewa suka kunna AC Ac dasu fridge da sauran kayan dayake aiki da wuta.

Abincin Haj Maryamah din data Gama ta Basu suka jera Mata a dining ita sai daga baya bayan ta tabbatarda tagama cin abinci da hutawa taje ta gaidata tana rungume da MARYAMAH dataqi bacci tanata rigima sbd aikin girkin dasukai sunsha zafi.

Kallon zainab Haj Maryamah din tayi dakyau kafin ta maida kallonta kan yarinyar daketa Kika duk ta ruda palon.

Kasa magana tayi sai kawai ta amsa gaisuwarta tareda sallamarta Dan kukan gabaki daya ya rudasu su dukan.

Zainab na fitowa daki ta nufa tayiwa MARYAMAH din wanka ta canja Mata kaya cikin kayanta dasuka fara Mata kadan sbd bayan kayanda Aqeel ya siya Mata batada wasu kayan gashi tanata girma.

Baya tayi Mata wanka bacci tayi sai kawai ta kwantar da ita ta fito taje ta gyare kitchen din data Gama aiki ta tattara komai tadawo daki itama tai wanka tayi sallah ta zauna tana kallon MARYAMAH dake bacci cikin nutsuwa da kwanciyar hankalin irin na yara.


Da daddare kasa nutsuwa da gyaran da shafa Mai aikinta tayi Mata Haj Maryamah tayi sbd akwai qura sosai Sam aikin baiyiba.

Fada sosai tayiwa shafa'atu din kafin qarshe tasa aka Kira zainab itace tayi Mata gyara Mai kyau dayasa hankalinta kwanciyar tasamu ta kwanta.

Washe gari zainab bata fitoba sbd batasan me zatayiba idan ta fito
Babah ladi itace take aikin girkin gidan
Shafa'atu Kuma tanata aikin shara da gyaran koina Dan haka saita Kama kanta a daki musamman dataga suna Mata kallon wulaqanci Dan daukarsu itama Mai aikince
Gashi sunga an kushe gyaransu ansaka tayi sun dauka shiga tafisu samu agun hajiyar gidan basusan wulaqanta tafisuba.


Duk uban aikin dasuketa fama dashi kwana biyu babu Wanda Haj Maryamah ke yabawa sbd tsaurin raayinta da yai yawa,

Duk aikin dasuke Mata Dama acan Bata Jin dadinsa Kuma tana nunawa Koda yaushe Amma sbd su kadaine sai basa damuwa sunyi sabo da halinta shiyasa suka Dena damuwa,
Amma anan duk aikin dasukai bayayi saita saka zainab tayi Mata wani sai hakan yasa sukejin daci da zafin zainab din a ransu,

Musamman babah ladi data fito fili ta bayyanarda rashin kaunar zainab din dake ranta,
Ita shafa'atu tana Dan taqaitawa sbd MARYAMAH data shiga ranta Dan tana tsananin kaunar yara.

Girkin abincin gidan a hannun babah ladi yake Dan haka idan tagama kullum Dan kadan take bawa zainab
haka zataci ko Bata koshiba zata Sha ruwa ta Kama kanta gashi tana shayarwa tana buqatan abinci sosoi gashi mukullin store a hannun babah din yake koyaushe da gayya take yawo dashi a jikinta duk inda zata.

Idan har tasamu taci abinci isashe yanda ya Kamata to itace tayiwa Haj Maryamah girki aranar dan bako yaushe haj maryamah din ke Jin Dadin abincin babah ba.

Shi gyaran bangarenta Kuma tuni yadawo kan zainab din da batason na shafa'atu Kuma tanada qarancin yarda shiyasa zainab kawai ke Mata gyaran daki taji hankalinta akwance da dukiyarta.

Bayan gyaran sashen Haj Maryamah harda abincinta yadawo kanta sai gashi kusan duka aikin gidan kadan ne basa kanta ga MARYAMAH da rigima sosai harma da qyuya Dan haka duk aikin dazatayi tana bayanta ko hannunta.


Ahakan suka fara Jan lokaci sosai suna wani irin mugun zama a gidan tsakaninta dasu babah..

'yarta MARYAMAH tayi wayo sosai harta iya zama da rarrafe Amma batasan kowaba bayan mahaifiyarta,

Bata sabu dasu babah ba Dan basa janta ajiki bare hajiyar gidan da iyakacinta da ita idone.

Aqeel kuwa yayi rokon,
Yayi neman ummansa ta hadasa da mamin tasa Amma kullum uzuri take basa
Har waya yace asiya abata Amma duk dai hakan bai samuba Amma tunda dai ta sanar dashi suna lafiya hakanma yasa hankalinsa ya kwanta.


Babbar matsalar da aka fara samu a gidan shine tsanar da ake nunawa 'yarta wadda ko sunanta basa Kira sbd sunan hajiyar gidan ne da hakan qarfi da yaji suke Kiran yarta da KE, kokuma 'YAR ZAINAB..wannan kalmar itace abinda yake sosa ran Zainba aduk lokacinda suka Kira MARYAMAH dinta da hakan,

Tana danne wannan lamarin ne matsala ta bullo tsakaninta da Haj Maryamah akan MARYAMAH din datake zuwa da ita gyaran bangarenta Dan yarinyar nata barna sosai.

Tun lamarin na dannuwa a ranta har abin yafara yimata yawa Dan kuwa kusan kowa a gidan kyarar Mata 'ya sukeyi.

Daga ita har yarta kamar wasu almajirai suke a gidan Dan kuwa kayansu na sakawa tuni suka mutu wasuma duk basa shigar MARYAMAH din Amma ahakn take saka Mata su tunda basuda wasu.


MARYAMAH sai datai kusan shekara biyu Ta yayeta sbd yarinyar itama yanayin rayuwar dasuke ciki yafara tabata,
Sam yanzu batada walwala ko sakewa yarinyar,
Duk da qarancinta tasan batada sakewa komai tayi na barna dukanta su babah da shafa'atu sukeyi tun zainab na kauda Kai har tayi magana sai abin ya zama fitina
Dama babah mutuniyar banza ce gidan abinci a Tasha takeda Jin gida masu kudine zaa Kai yar aikin abinci ta rufe shagonta tazo ta karbi aikin shiyasa take tsula tsiyarta son ranta tunda Haj Maryamah din Bata wani zama ba ruwanta da Yan aiki gashi yanzu itace shugaban masu aikin gidan Dan haka take zuba tsiyarta son ranta.

Zainab rayuwa a gidan tafara yimata tsanani,
Komai ya juye a rayuwar gidan ba kamar da ba,
Idan zata sashen Haj Maryamah ta dena zuwa da MARYAMAH 'dinta sbd gudun fitinar dazata biyo baya idan tayi Mata wata barnar datafi fasa Mata laptop datayi ta aikinta.

Acan dinma idan tabarta kafin Takoma sai ta tadda bacin ran wani abun
Duk tabi ta fige da masifar gidan da yanzu komai ya lalace mata,

MARYAMAH sbd tsangwama da kyarar datakesha yasa gabaki daya ta rasa walwala da kuzari tareda sakewa irinta yara,
Idan har ba ajikin uwarta takeba Bata wani dogon motsi a gidan.

Wannan yasa itama zainab din ta tasa kuzarinta gabaki daya suka koma kamar Yan gudun hijirar gidan kullum suna daki kamar masu abin kunya.

Ana haka kwatsam Allah yayiwa mijin Haj Maryamah yace ta tattara tadawo Abuja gabaki daya.

Da farko shafa'atu aka fara sallama sbd idan Takoma Abuja Bata buqatar ya aiki da yawa sbd hutawa takeson Yi batason hayaniyarsu Dan can gidan baiyi girman wannan ba da bazakaji motsin masu aikinbama.

Ganin an sallami shafa'atu yasa hankalin babah tashi Dan ta fahimci zaiyi wuya a kori zainab duk da gata da 'ya da Bata barin tayi aiki dakyau.


Babban tashin hankalin farko data fara fuskanta akan tafiyar tasu Abuja shine Haj Maryamah data Kira umma akan zata Aika Mata da MARYAMAH Qarama acan Cameroon bazasu da ita Abujan ba.

Bugawar da zuciyar zainab tayi yasata dafa bango tana Dan bude idanuwanta dake Mata dishi dishi.

A gabanta umma da aka Kira Kai tsaye itama tace bazata iya riqon MARYAMAH dinba sbd tsufa yazo Mata Kuma dasuka riqe uwarta tun tana jinjira me ta saka musu dashi Banda butulci Dan haka ita ma wanna halin uwarta zatayi itakam bazata iyaba.

Haj Maryamah ma Kai tsaye ta nuna zainab bazataje da MARYAMAH dinba idan har umma bazata karbetaba to gwara zainab din ta nema dangin mahaifinta ta miqa musu ita.


Tunda zainab take Bata taba Jin daci da radadin zuciyaba akansu sai wannan karon,

'yarta ake ture turen inda zaa Kai kowa nacewa baya son saikace wani mugun abun,
Me tayi musu da tsanar dasuke Mata zata shafa 'yarta hakan wadda batasan komaiba.

Tafiyar na matsowa umma ta Dage akan bazata karbi maryamah dinba,

Kukan da zainab tayi Saida takai idanuwanta ma basa gani sosai,
Tayaya zata iya bada qanqanuwar marainiyar 'yarta har Cameroon itama taje ta taso Acikin qangi da wahala.

Kukan Rashi iyaye Dana Mijinta tayi tareda na Aqeel Wanda tuni ta cire Rai daga Kansa itada yarta.

Hada dukkanin tsumman kayanta tayi guri daya Dan tasan rigimarda zaayi idan tafada raayinta na bazata taba rabuwa da 'yartaba,
Idan har Haj Maryamah zataje Abuja da ita to zataje da yarta,

Tasan hakan zai kawo rigima tunda ansaba takuma san ran kowa zai baci Amma bazata iya barin arabata da yartaba.


Rigimar kuwa akayi sosai tareda bacin rayika alokacinda ta sanarda Haj Maryamah bazata tafi bada MARYAMAH dintaba.

Umma ranta kusan yafi na Haj Maryamah din baci sbd mamaki da takaicin zainab take tafara jero Mata gorin irin rokon da Aqeel yayi musu akan su amsheta ta zauna gurinsa shine yanzu an zabar Mata rayuwar sauki da Jin Dadi zatace bazata rabu da yartaba,
Ashe 'da yanada dadi shine ita ta raba haj Maryamah da nata Dan kullum cikin fada yake da mahaifiyarsa akanta.

Haj Maryamah kuwa tsabar takaicin da baqin ciki Kai tsaye ta Bata zabin Idan bazataba Saida yarta to tayi zamanta Amma tasan Wana gidan an saidashi gabaki daya har masu gadi tafiyarsu zasuyi.

Irin cin zarafi da tozarcinda umma tayi Mata dakuma maganganun Haj Maryamah din yasa ta sake hada kayanta guri daya.

Haj Maryamah ganin Bata bar gidanba yasa tayi tunanin ta aminta da tafiyar MARYAMAH din Cameroon Dan haka tasa babah ta shirya Dan itace zatakai MARYAMAH din har Cameroon.

Sai ranar tafiyar tun kafin asuba babah ta shirya sbd sammako zasuyi a tafiyar.

Ayau zainab ta fito tayi magana Kai tsaye cewan bazata bada 'yartaba,

Tsananin fushin da haj Maryamah da umma suka dauka yasa akai hayaniya mai girman gaske da har tasa Haj Maryamah sakarwa zainab Marin daya bawa kowa tsoro.

Kasa hawaye zainab tayi sbd zuciyarta datakai qololuwar 'daci da qunci,
Ayau ta tabbatarda har abada bazasu taba kaunartaba sbd qiyayyar dasuke Mata a jininsu take...

Maganganun Haj Maryamah suka rufe ganinta saidai batajin zata iya barin ko gari ya waye tunda umma tabata umarnin barin gidan daga ita har yarta dasuke neman aibatawa sbd rufewar zuciya.

Daurin kayanta ta dauka ta fito daga gidan tana Jin zuciyarta na tiririn zafi da azaba.
##MAMUH#
#SISTERS#
#MARYAMAH AMAL IDON NERA
#DR AQEEL ASAD
#LOVE/HOTLOVE



*_ZAFAFA BIYAR_*

*RUMBUN K'AYA*🔥
Hafsat Rano

*DAUDAR GORA*🔥
Billyn Abdul

*IDON NERA*🔥
Mamuhgee

*A RUBUCE TAKE*🔥
Safiya huguma

*KI KULANI*🔥
Miss xoxo

Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200

ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN

0022419171
Maryam sani
Access bank

Shedarka ta 09033181070

MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN

09166221261

🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*

+22799643131

Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA

*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*Thanks for choosing us*🔥*_Arewabooks@Mamuhgee_*
16

*_MG'S SKINCARE_*🔥🔥
Kunji takennan kunsake jinshi shin yar'uwa nace wai haryanzu baki jaraba products dinsu ba😵‍💫yar'uwa mace fa yar ado da kwalliyace koda kina dakyau akace kikara da wanka😍sufa kayan mg's basa bleaching duka kayansu 💯 natural ne sannan organic zasu gyara sukuma goge Miki jikine kawai yakara bayya ar da ainihin zallar Madarar kyawun halittar da Allah yayimiki🥰
Wai kinafama da pimples da spot afuska amma haryau baki nemi mg's ba🤔duk Mai tantama akan kayan gyaranjiki yacire mg's domin babu shakka sudin na dabanne indai problem dinki matsalan fatane yar'uwa kijaraba koda soap dinsu bi'iznillah zaki godemin👯‍♀️kayansu ga kamshi inkinjaraba kinga yanda suke na tabbatar bazakiso su Yanke Miki ba🤩08062991549 anatayi Baku sisters kusamu kugwada koda b duka kit din na gyaranjiki ba zakuga sauyin da fatarku zata samu cikin lokaci kalilan🥳jikin yazama so fresh ko Ina kikashiga kita glowing fatarki na walwali kamar madubi😘keda kanki zakina burge kanki balle wasu🤗08062991549
Adade anayi sai gaskiya sannan siyan nagari Maida kudi gida ❤️
Duk Mai bukatar products din mg's kutuntubi wadannan numbers din domin tasune kawai zaku samesu🙏
Chat 08062991549
07046881166,07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare

Team glow🧖‍♀️


Yauwa nace ba masu bukatar zuma original munadashi mekyau ba hadi Mai bukata yayimin mgn 08062991549



***********
Haj Maryamah na tsaye na kallonta cikeda zafi da dacin zuciya da wani mummunan nauyi a zuciyarta zainab din ta fice daga gidan rungume da yarta,

Babah dake gefen Haj Maryamah tsaye cikin shirinta tsaf na tafiya Cameroon duk jikinta neman mutuwa yakeyi da ganin samu da Rashi Dan kuwa da anbata 'yar saita Gama biye biyenta inda takeson zuwa kafin ta Isa Cameroon din.

Masu gadin gidan dasuka San zainab tun kuruciya da girma suna kallon wannan tashin hankalin zuciyoyinsu na kunci ta tafiyarta da 'yarta,

Babban tashin hankali da tsoronsu har ita Haj Maryamah din dawowar Aqeel ba zainab babu 'yarta Amma Kuma zuciyarta ta rinjayeta komai ya lalace tsakaninta da qanwarta.

Zainab kuwa tafiya kadan tayi aka fara Kiran sallar asuba Duk da hakan bata tsayaba tafiya takeyi batareda tasan inda take jefa qafafuntaba sbd rufewar ido Dana zuciya.

MARYAMAH dake goye bayanta tanajinta ba bacci takeyiba sbd tashin hankalin tuni ya tadata bacci gashi babah tsabar son tafiyar yasa Ana fara  rikicin ta dauketa ta tsala Mata wanka da ruwan sanyi.

Har akai sallar asuba aka fito gari yafara haske tafiya takeyi batareda tasan inane gurin zuwantaba
Idanuwanta kuwa sun kada sunyi jajir sun bushe Dan kuwa kukanta tuni ya tsaya harna zuci.

Tafiya taci gaba da Yi har asalin anguwarsu na gidan ubansu Wanda daqyar takawo kanta harta gane saidai tana shogowa layinsu Bata hango alamar gidansuba Dan kuwa wani mahaukacin gida take hangowa Mai girman gaske dayake nuni da gidan manya ne,

Anguwar gabaki daya ta canza tazama kamar anguwar Yan shiyasa sbd kalar samari da mutanen datake gani marasa kamun Kai sai Yan siye da siyarwa dasukai yawa.

Kofar qaton gida data tabbatarda Nan ne gidan ubanta harma da kusan gidajen hudu da aka hade akai gida daya dasu take kallo da idanuwanta dasuke qara rinewa da tsananin qunci da radadin zuciya.

Batada komai batada kowa sai wannan gidan na ubanta Wanda takeda gado acikinsa,
Saidai Kuma wannan tsarin data tadda yasa tarasa Duk wani Dan kuzarin datake ganin ta hangowa kanta.

Guri tasamu daga gefen gidan ta zame ta zauna tareda rintse idanuwanta wani zazzabin sabon tashin hankaline  yarufeta.

Agurin ta zauna tana Jin jikinta na rawar tashin hankali,

Wa zata tinkara da zancen Ina aka Kai gidan ubansu?
Wayema ya santa?
Maryamah da umma Kawai aka sani barema duka gidajen data sani na maqotansu babu gabaki daya anguwar ta zama kamar kasuwa kamar dandalin siyasa, ta Ina zata Samu mutumin arzkin da zata tambaya???

Shiru tayi tareda sunkuyar da Kai tana rasa tunanin kamawa,

MARYAMAH dake bayanta lafewa tayi a bayan nata sbd zazzabin wanka ruwan sanyin da babah tayi Mata tun kafin asuba hakama tagansu a inda Bata taba ganin sunzo ba Dan kusan MARYAMAH din Bata taba fitaba kullum suna gida Kamar mayu.

Ta Jima agurin zaune har Saida ta Dan dawo hayyacinta kadan kafin tafara kokarin miqewa sai kawai taji ihu da hayaniya ya gauraye koina
anguwar take ta dauki ihu anata gudu....

A tsorace take kallon mutane dake gudu ta miqe tana neman hanyar tsira saidai tuni anguwar ta dauki wani irin yamutsin fada na Yan ta'addar siyasa harda makamai dasu tiya gas.

Jefarda kayanta tayi tana neman hanyar gudu Amma babu Dan kuwa sare sare akeyi sosai
A rikice tasamu ta fada gidan dake kusada babban gidan masu gidan na neman tufewa ta fado suka rufe sunata masifa da zage zagen wannan masifa dataqi qarewa kullum haka suke a anguwar.

Itadai shirun tayi bayan babbar kofar jikinta babu inda Baya rawa sbd tashin hankali da quncin wannan rayuwar data samu kanta aciki Kuma.

Tana tsaye agurin itada wasu da yawa wainda da alama baqi ne a anguwar suma Dan hankalinsu duka a tashe yake saidai su dukkaninsu daga cikin gidan suka fito sabanin ita da shogowa tayi.

Harbe harben bindigar da akeyine yasa zuciyarta qarasa daskarewa sukuwa sauran sake shiga tsoron suka sbd tsoron kada ayi Kamen harna cikin gida tunda hukuma ce tazo ake harba bindigar.

"Allah dai ya tsinewa wainnan yayan banzan da Allah bai saka musu hakuri ba,
Ana abu daya duk zasubi su ishemu da kayan hayaniya,
Ina ramuwar baccin da banyiba sbd kasuwar Daren jiya shine zasu ishemu harda harbe harbe.""""

Daga bayansu zancen ke fitowa Dan haka dukkanin Maza da matan gurin tsoro da fargabansu yafara raguwa Dan kuwa LULU ce da kanta tafito take magana wato shahararren 'dan daudun daya Gama riquwa a bariki tareda gogewa a harkar duniyanci.

Fari ne tas dashi kyakkyawa Amma babu wani Abu daya nuna tsoro ko fargaban halinda suke ciki.

Kofar ya nufo Kai tsaye ya bude Yana cewa"

Kuzo ku fice qartin banza da wofi wlh sai antafi daku ai Dama na Hana kowace shegiya kawomun Maza a gida ku wuce.

Bude kofar yai gabaki daya ya fito batareda tsoro ba ko shakkar abinda yake faruwa a wajen.

Take kuwa yayiwa mazan cune aka shigo aka kamesu duka cikin tsautsayi aka hada harda zainab wadda kwata kwata takasa gane meke faruwa Dan hankalinta ya Jima da barin jikinta.

Har ansakata a mota ganinta da goyo Kuma kamar Bata hayyacinta yasa LULU cewa Banda ita.

Ba musu aka sauko da zainab Yan sandan suka wuce bayan sun cika mota uku da Yan ta'addar dasuka tada fadan Dama kwartayen dasuka kwana gidan karuwan LULU.

Bayan Kamen Yan sandan sun wuce anguwar ta lafa aka fara firfitowa kowa naci gaba da harkar gabansa..

Zainab kafafuwanta dake rawa takasa dagawa sbd tashiga babbar firgici na abinda yafaru din kamar kyaftawar ido.

Rasa nutsuwarta take neman Yi
Tafara rarraba ido tana neman daurin kayanta tabar anguwar..

A dage Lulu ya kalli zainab din cikin gatse yace"

Ke Kuma daga Ina haka?
Da Alama baquwar zuwa anguwar ce
To maza kija qafafunki kibar anguwar Dan ba gurin zuwan irinki bane..

Da sauri zainab tayi gaba har tana tuntube zata Fadi...

"Ke dawo, zo
Shege kikai Kika baro gidane??

Kasa magana zainab tayi sai tayi gaba tana fasa neman kayanta duk da taso Kayan Dan basuda wasu saina jikinsu daga ita har MARYAMAH.

Ganin yanda take a kamar Mata hankali tana kallon babban gidan da gadonta yake ciki yasa LULU biyota ya kirata zaiyi magana yaransa suka iso mota kusan biyu suna masa kirarin,

"sai hajiya LULU"

Washe Baki yahau Yi Yana kallonsu sbd sune abin Alfaharinsa
Dan kuwa sune masu cire Masa baqin cikin aike kowane irine.

Kallon wadda ta iso gefensa yayi yace"

Siddi ki kaimun baquwar Nan ciki Ina tafe.

Kallon zainab yayi yace,

"Kibita Ina zuwa zamuyi magana.

Qin binta zainab tayi saidai Kuma ganin shine maqocin babban gidan yasata tunanin jiran ko zata Samu bayanin dazai isar da ita inda gidan mahaifinsu yayi.

Shikuwa Lulu ganin yanda take kallon babban gidan makocinsa Kuma maqiyinsa yasashi son tsayar da ita yaji
Babbar fatarsa ace MANDE DS ne yayiwa matar wani abun yayi amfani da hakan ya lalata Masa suna da komai ya nuna Masa iyakarsa.

LUKMAN AHMED Wanda ake duniya ta sani da Lulu Asalin Dan anguwar ne Wanda mahaifinsa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login