Showing 123001 words to 126000 words out of 155476 words

Chapter 42 - IDON NAIRA COMPLETE HAUSA NOVEL

MAMUGEE   

01 Jan 2026

411

yabar gidan.

Tana shiga palon kasa Babu kowa sai Bilkisu ta kalleta tace takawo Mata tea da cake.

Tana hawa sama har lokacin mommy da siddi na palon

Siddi na waya da Mijinta mommy Kuma tana waya da AQEEL din dayake tambayarta ko Amal din ta iso??

Eh tace Masa tana mamakin bashine yace zai dawo da itaba¿

Ahmed dinma Yana kokari wlh tafada lokacinda take ajiye wayarta ta amsa gaisuwar Amal datayi Mata a gajiye ta nufi dakinta kayan bacci kawai ta saka ta fada gadonta koda Bilkisu ta kawo Mata tea din tini tayi bacci.

Da asuba ma daqyar ta tashi tayi sallah Takoma bacci Bata farkaba sai 11 lokacin kowama na gida ranar dayake weekend ne itama badan tasoba ta tafi makaranta lecture daya tayi tadawo gida.

Tana dawowa abinci taci ta haye dakinta ta kwanta tana bacci.

Sai yamma tasamu jikinta ya sake tayi wanka tasake cin abinci da sallah tukuna tadawo daidai sunata shaaninsu cikin gidan dayake kowa ranar Yana gida.

Shima ranar Bai samu shigowaba sbd wani daurin aure Mai mahummanci da aka gayyacesa Wanda yayi haduwarsa da Amininsa da sai satin ya dawo Nigeria tareda matarsa data tattara ta bisa can suka daidaito tunda tasamu ta rabu da masifar rayuwarta wato Amal Idon Nera.

Da farko SSG yaso nuna bacin Rai da fushinsa akan AQEEL ASAD din Amma Sam AQEEL ASAD Baima bada Fuskar da zaayi maganar iyalinsa da waniba Dan bazai iya bada fuskarda Hayat din zai alaqanta Kansa da matarsaba Koda a gurin bada bayani ne Dan Haka kwata kwata yaqi nuna akwai wani Abu daban bayan asalin alaqarsu da amintarsu Wanda yasa Hayat duk yanda yaso ayi dawo da bayani Dole ya hakura yabar maganar sbd AQEEL dabai nuna akwai wani abinba bayan Abotarsu.

Da Haka ya hakura yabarwa Allah tunda ya shirya da matarsa Amma Kuma bayajin ya fasa qara auren tunda yayi niya zai samu tasa shima Mai Kamar Amal din.

Baisamu kansaba sai dare shima dan Haka ta waya yayi magana da Maminsa kawai sai Kuma mutuniyar itama dayake yasan bata Masa magana kota waya Dan Haka text yayi Mata kaman yanda ya Saba.

Washe gari yazo da safe kafin ya wuce wani taron Musulinci da aka gayyace a ranar Amma Bata tashiba tana bacci Dan Haka ko ranar Basu haduba saida aka kwana biyu duk basa haduwa saidai ta waya safe Rana dare dayake Jin lafiyanta da kewanta.

A kwana biyun ta Dan sauya sbd hutawar datakeyi sosai daga bacci sai cin abinci.

Ranar Thursday Bayan tadawo makaranta da yamma sai datayi bacci ta huta tayi wanka da sallar magrib ta fito sun zauna cin abincin dare tana zama sai gashi yashigo palon sanyeda wando da hoodie Balenciaga sweatshirt milk.

Qamshine ya yadu a palon ita tafara Ankara da zuwan nasa sbd qamshin, ta dago ahankali ta kalli hanyar palon saiga idanuwansu ya Hadu ahankali.

Idanuwansa daya zuba Mata Yana binta dasu yasa jikinta neman mutuwa tana Dan dauke idonta daga nasa tana Jin abincin na kasa shiga ci kawai takeyi Bata wani ganewa.

Bai qarasoba a Palo yayi zamansa Dan baya buqatan dinner a koshensa yake Dan azumi ma yayi ranar.

Jin tayi ta koshi Amma Kuma takasa tashi sbd Babu Wanda ya Gama.

Ganin tagama Haj Zainab ta kalleta tace,

"Amal ki kawomin ruwa Wanda beyi sanyin wannan ba tunda kin gama,

Wannan yayi sanyi Bilkisu taqi Dena bamu ruwan sanyi sosai haryanxu.

Rintse Ido tayi sbd tsoron Isa palon ba kowa acan sbd Idan ba ita datake saiti da kofar palon ba babuma Wanda yasan yazo sai sun Gama sun fito zasusan ya zo.

Miqewa tayi ahankali ta fita ta shige kitchen ta dauko ruwan ta fito

Ga mamakinta Bai taso daga inda yakeba harta wuce takaiwa mommy ruwan

Idanuwansa kawai yake binta dasu tanajinsu ajikinta kamar zata harde ta Fadi.

Sallama tayi musu Dan yanzu da wuri take Shigewa ta fice ta nufi hanyar hayewa sama Amma ko Isa stairs din batayiba ya Kira asalin sunanta daya sata tsayawa cak zuciyarta na harbawa da qarfi aduk lokacinda zai kirata asalin MARYAMAH dinta Wanda bayanshi duk duniya Babu Mai kiranta hakan,

Sunanma idan bada ya bayyana rayuwarsuba batasan tanada wani asalin sunanba.

Ahankali ya Kama hannunta ya jata zuwa saman dakansa har cikin dakinta suka shige ya turo kofar Yana shinshinata yace,

"Ganina yasa Kika kasa cin abincin?

Bata fuska tayi tana cewa ah ah batareda tasan tafada dinba.

Ruwan dake gefen gadonta ya dauka ya bude ya Dora Mata abaki tafara Sha babu musu sbd ya lura da Natasha ruwaba bayan Gama cin Dan abincin datayi.

Ruwan takesha ahankali Yana Bata Yana kallon yasa take hadiye ruwan cikin sanyi da nutsuwa komai nata sanyinsa da narkewarta na sake hargitsa zuciyarsa.

Tana Gama Sha ya rufe ya ajiye yasaka hannu Yana goge Mata Wanda suka zubar Mata har cikin kirjinta.

Kallonta yakeyi yanajin kewarta sbd kusan kwana biyar kenan Basu ga junaba.

Hijabinta ya saka Mata tareda janta cikin nutsuwa Suka fito ba tsoro ba shakka ya jata har qasa suka fice batareda kowa yagansuba bare sanin ficewar tasu.

Daman shine ya kawo kansa Dan Haka yajasu Suka bar gidan.

Ita kanta yau Bata tsaya wahalarda Kansa musawa ba sbd idanma Basu bar gidanba tasan zai iyayin abinda zai sata kunyar familynta a gidan.

Suna Isa gidan Karatu a palonsa suka yada zango Saida yagama rikitasu suka gama tarwatsa pillows din west Elm sofa set dake palon kafin suka qarasa dakinsa acanma Saida suka Gama yamutsa gadon kafin komai ya lafa.

Wannan karon itace wani bacci Mai nauyin gaske ya dauketa batareda tasaniba.

Ganin tayi bacci saiya kyaleta Bai tadataba yaje yayi wanka yayi Shirin baccinsa ya rufe koina yazo yashige jikinta take bacci Mai nauyi shima ya daukesa.

Da asuba gigice ta tashi ganin inda take take tafara hawaye ya samu ya rarrasheta tayi sallah gari nafara haske kadan ta daga Masa hankali ya maidata gida Bata Bari yashigo gate da motarsaba a waje yayi parking suka shigo da qafa securities na Masa barka da asuba ya amsa Kai tsaye Yana wucewa ciki raka matarsa.

A bakin kofar palo tace yakoma

Saida ya Kuma kissing bakinta ahankali kafin ya saketa ya juya takira Bilkisu a waya ta bude Mata kofar ta wuce sama da sauri tana zuwa tashige dakinta ta kwanta sai bacci.

Washe gari Babu Wanda Koda Wasa ya fahimci baa gidan ta kwanaba bayan Bilkisu dake ganin ikon Allah abinda yafi karfinta.

Ranarma hakance da daddare yazo ya fice da ita bayan mommy ta shige siddi Kuma tana kicin tareda Bilkisu data saka aikin gasa Mata cake.

Kaman yanda ya dawo da ita jiyan Haka ya dawo da ita a yau Amma yauma harsunyi latti kadan ya rage Basu hadu da Uncle Lulu daya fita yau din tunda safeba.

A kwanakin komawa yayi Yana raba kwana a tsakaninta da Bilkees batareda Bilkees din Tama tsaya ta fahimci duk Bayan kwana biyu baya kwana a gidaba hakama Amal data manta gabaki daya da yanada wata Matar.

Ana cikin hakan yayi tafiyar dazata daukesa kusan sati biyu ko uku ma.

Ranar dazai tafi acan suka kwana dagacan school ya ajiyeta Koda kowa ya farka Bata gida Bilkisu tace musu ta wuce school tunda safe dayake exams Sukeyi.

Yana ajiyeta airport suka wuce shida Al-Amin Ahmed yakaisu yakoma makaranta jiranta.

Karfe uku ta fito makarantar Suka dawo gida wanka kawai tayi taci abinci ta kwanta sbd Dan zazzabin datakeji tun shekaran jiya sama sama.

Koda maraice yayi jikinta yayi zafi Sosai Haka ta Dan daure aka Bata magana tasha,

Hankalin mommy tashi yayi sbd lurada wata yaqare ciwon marartane na period zaizo wannan karonma kaman ta gota harda kusan sati daya,

Mamakin lamarin mommy tayi Amma dai ganin tafara zazzabin Mai zafi saita San ciwon ne zaizo.

A sukwane ta wuni kwance hakama washe gari ta tashi da zazzabin dayake sun Saba da ciwon nata sai akaci gaba da Bata maganin datakesha hakan saiya fara sata ciwon Mara ahankali batareda itama tayi wani tunaninba ta dauka period dinne zaizo dan harta manta da ciwon nata dataga lokaci ya wuce batai period dinmaba kwata kwata.

****Haka kawai Bilkees ta zowa su umma a wuya ta tsaya sbd gabaki daya ta tattara zancen lamarin Mijinta da aurensa ta watsar tamaida hankali gurin rayuwar Matan manya dasukeyi itada qawayenta su Nafee data dawo Suka sake dinkewa abinsu ganin kowa ya watsar da kwallon mangwaro ya huta da quda,

Ita Nafee tana sane da AQEEL ASAD Yana tareda aurensa da Amal Bai rabuba Amma taqi fadawa Bilkees din sbd kada tayi rigima auren ya mutu tasan Amal na rabuwa da aure wallahi Allah ne kawai zai Hana Mijinta aurenta Dan Haka ta zabi yin shiru tana sake Dora Bilkees din a hanyoyin da bama zatasan akwai aurenba bare tayi wani yunqurin.

Umma Babu safiyar da Bata debewa bilkees akan wawanci da haukata gashi Suma yanzu sunaji suna gani AQEEL yake qin kwana a gida wasu lokutan Wanda sune kadai sukasan inda ake gashi ba damar magana saidai Ido da guni a zuci Wanda yafi komai ciwo.

Haj Maryamah kuwa ganin da gaske suna zaune zasu iya samun mugun labarin sabuwar hadin zuria da Zainab da Haka tafara dagawa Bilkees hankali akan sake haihuwa sbd Daman can Dan ana Zaune kalau ne bata maganar asake Amma har cikin ranta 'yaya takeson AQEEL ya Haifa musu masu yawa tunda ita Shi kadaine, itama ita kadaice agun ummanta gwara shi ya hayayyafo da yawa tunda akwai arziki Mai yalwanda ko 'yayansu bazasuyi talauciba da yardar Allah hakama Shi kansa tasa yanada masifan son yara tunda sungani tun haihuwar Zainab datai ta Amal dn yabi ya rikice.

Bilkees ganin masifar dasuka bullo Mata da ita ta maganar haihuwa ba arziki Ido a rufe gabaki daya sun sauya Mata Dan ita umma harda maganar Daren farkon Nan tana ranta takasa cirewa ace matar dasuka kawo Masa Babu Wani motsi salin alin Amma 'yar karuwa anzo Anata neman madinka da likitoci hardasu gashe gashe Dan Haka akwai zance a qasa tsakaninta da uwar Bilkees idan Takoma Cameroon bata yarda dasuba rufa rufa sukai Mata aka bata ta aurawa jikanta.

Bilkees da mufeeda dataji abinda sukewa mahaifiyarta binsu suka ringa Yi da magana

Bilkees Babu ranarda Bata debewa tsufan umman Cameroon albarka tana fatan ta tattara Takoma Cameroon sbd itace mahadin komai.

##MAMUH#

*_ZAFAFA BIYAR_*

*RUMBUN K'AYA*🔥

Hafsat Rano

*DAUDAR GORA*🔥

Billyn Abdul

*IDON NERA*🔥

Mamuhgee

*A RUBUCE TAKE*🔥

Safiya huguma

*KI KULANI*🔥

Miss xoxo

Littafi daya---400

Biyu---600

Uku----800

Hudu-----1k

Biyar din duka----1200

ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN

0022419171

Maryam sani

Access bank

Shedarka ta 09033181070

MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN

09166221261

🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪

*Ina yan uwa 'yan nijer?*

*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*

+22799643131

Littafi daya---450CFA

biyu---650CFA

uku----850CFA

hudu----1050 CFA

Biyar----1250CFA

*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*

*Thanks for choosing us*🔥Mamugee
63


•Abu na farko daya sake biyowa bayan zazzabinta shine yawan baccinta,
Ga zazzabi koyaushe Mai karfi ga yawan baccin saikuma Dan ciwon marar gashi period din yaqi zuwa,
Hankalin Haj Zainab fara tashi yayi akan ciwon duk da hankali ko tinaninta Bai taba zuwa kan wani tunanin wani Abu Mai Kama da wani abinba Amal zata iya alkatawa.
Ita kanta Amal din gain lamarin na neman ja Mata attention din mommyn sosai sbd abinda tafara magana shine meyasa wanna Karon Babu wannan ciwon marar kwata kwata sbd Dan wannan datakeyi bama ciwo bane akan Wanda ta Saba.
Tashin hankali tashiga sbd sanin meyasa batai ciwon marar ba kaman vanda vafada Mata ai bazata garaba ayanzu sbd….....kasa qarasa tunanin tayi sai ta aro qarfin halin gaske ta dorawa kanta qarfin danne ciwon.Asibiti mommy tace zasuje a washe gari Dan Haka cikin mummunan yanayin tsoro da tashin hankali da kunar suie asibitin ace any wani abin da itane shiyasa ta Dena ciwon Mara.
Da wane Ido zata kalli mommynta da familynta musamman idan sukaji Wanda yayi wani abun da ita.
Kasa daukanta bacci yayi duk yanda kuwa take da tsananin bacci a kwanakin.
Da kanta ya cake cikin tashin hankali da fargabar wayewar gari kuka ta fashe dashi tana rufe idanuwanta Dan Bata taba tunanin akwai dalili akusaba Wanda zaisa a iya ganewa.,
•Fatanta Allah yakawo dalilin dazai hanasu zuwa asibiti har aje aji wani abin tayi idanma ance tabbas zatayi denying Kai tsaye sbd bazata yarda da wanna zancenba.
Sai guraren asuba bacci ya dauketa da ciwon kai Mai
Dan tsanani.
Batafi awa biyu tana baccinba ta farka tana duba agogo taga 8 saura Dan Haka ta tashi ta sauko gadon kanta na sake tsananta Mata ciwo ta nufi toilet.
Brush da wanka tayo tana fitowa ta shirya cikin doguwar Abaya blue da simple gyaran data saba ta fito wayarta da hanbag dinta a hannunta ta fice gidan kowama Bai tashiba Daman takira Ahmed tana fitowa
Suka wuce makaranta sbd tunda Suka kammala exam har aka guntun hutun aka dawo batajeba tana fama da kanta.
Yanzune aka dawo Dan Haka ba waima angama dawowa hutun bane gabaki daya Dan Haka Babu Wani karutu sosai ko mutane sosai Sosai dasuka dawo ita kanta Bata fara zuwa da wuri Idan aka dawo
Amma yanzu ba yanda ta ivane tana cikin tsananin
Hali na damuwa da tashin hankalin mommy da zasu asibiti a yau din shiyasa ta gudo.
A mota tayi zamanta tunda Suka iso makarantar ahakan bacci ya dauketa
Ahmed saiya fita motar yabar Mata ita a kunne sbd
AC Tasha baccinta tsawon lokaci kafin Kiran mommy ya farkar da ita dakuma yunwa da zazzabi Mai garfi daya sake sauko Mata,
Cikin fada sosai mommy ke tambayarta tana inane?
Dan daidaita muryarta tayi ta sanar Mata tana school kiranta akai akan akwai lecture din da zasuyi Mai mahummanci da safen.
Rasa abin fada Mommyn tayi sbd takaici sai kawai ta kashe wayar tana cewa,"Neman lafiyar takima sai an ringa binki Ana rarrashi.
Ajiyar zuciya Amal ta sake jikinta na sanyi sbd duk abinda mommynta tace tayi shi takeyi Basa tsallake maganarta duk freedom da rayuwar yancin dasukeyi ba takura ba saka Ido to sunada tarbiyar data Basu shine basada rashin kunya ko gadara tareda reni ga wainda sukasan manyansu ne musamman ita datake mahaifiyarsi,
Amma ita yau gata a tsaka me wuya na wanna yanayi daya sameta,
WIh batasan tayaya zata iya kallo ko Shiga gidansuba idan akasan me tai ta Dena ciwon Mara din.,
Me ma zatace Akan AQEEL ASAD din Wanda ko gaisawa baa San sunayiba bare kalion juna har irin wannan abin yashiga,WIh musawa zatayi duk likata ta bada tabbacin cewa
tagano kila tayi sex ne ta dena.
Fitowa makaranta sukai tace suje talindo steak house.
Suna zuwa shine ya Shiga yayo Mata order na
abincinsu da AQEEL ASAD ya koya Mataci sbd acan
kawai ake siyo musu abinci.
Brown spaghetti sauce dinsu takeso sosai kaman maita kusan duk suna tare sai ansiyo Mata duk da
Bata taba fadaba Amma yanda take cinta yanayinta
Yana nuna yanda takejin dadin cin nata yasa ya
fahimci tana tsananin sonta Dan Haka duk zaa kawo
musu abinci sai anhado da ita Kuma Idan so nawa
zataji saita lumshe Ido cikin Jin dadinta.
Suna barowa Kai tsaye school Suka koma acan taci
abincin ko gamawa batayiba vau din sai amai ya biyo
baya sbd ba ahaka ta Saba cintaba,Yawanci a zaune kan gafafunsa yake zaunar da ita a dining ya ringa Bata abaki tanaci atmosphere din bama daya Dana makaranta ba aikuwa take cikinta yakasa amsa ta ringa amai Mai qarfi da galabaitarwa.
Hankalin Ahmed tashi yay ya rasa ya zaiyi Kuma waye zai Kira gashi ba Daman tabata,
Bottle water guda uku ya siyo Mata masu Dan sanyi yakawo ta karba da gyar ta iya wanke fuskarta da bakinta wani mummunan jiri na dibanta ta dawo mota tana shiga jikinta ya ringa kakkarwa.
Sake shiga damuwa Ahmed yay Yana Tunanin kaita gida Amma Kuma ya lura kaman yau tsoron zuwa gidan takeyi baisan meyake faruwaba kada yakaita ya lalata Mata shiri ko wani abinda takeda niyar Yi Dan
Haka saiya sake shiga damuwa.
Wayar AQEEL ASAD yafara Kira Amma sam baya dauka bd tana silent Yana meeting da mutane Kuma tana kife ne a gefensa so bazaiga ko hasken kiranba.
Kira kusan biyar yay masa Bai dagaba Dan Haka ya lalubo numbern Al-Amin ya saka kiransa.
Na farko Bai dagaba shima bd meeting din Amma ganin Ahmed ya sake Kiran yasan maganace data shafi Amal da ogansa tunda Shi duk kiransa Akan abinda ya shafa Amal ne bd Dan ita kawai aka daukesa aikin.
Ahankali Al-Amin din ya miqe ya fito daga office na meeting din ya Dan Yi gaba kadan kafin ya daga Yana cewa,
"Yes, Ahmed lafiya dai ko??
Ajiyar zuciya Ahmed ya sauke cikin damuwa Mai tsananin gaske ya sanar dashi Ms Amal ce batada lafiya sosai.
Dan juyawa Al-Amin yayi ya kalli kofar daya fito kafin mamaki da kulawa yace,
"Baa kaita asibiti bane?
Tana inane?
Bayani yayi Masa a tagaice cewan kaman batasan zuwa gida Kuma ga ciwon sosai Yana damunta shi baisan ya zeyi bane shiyasa yakira Sir AQEEL yafada
Masa sai ya sanarda yanda zaayi idan ya kaita gidane kokuma asibiti.
Sake Shiga mamaki da Dan abinda zaayi din Dan shima anan din Kam baisan mezaice ba sbd maganar ivalin AQEEL ASAD din ake magana Kuma ko Dan tsakanin Nan yanzu yafi kowa sanin Amal ba garamin matsayi take dashiba a zuciyar Sir AQEEL din Dan
Haka shima bazai zage ya Fadi komai Dan Haka sai Sake Shiga mamaki da Dan abinda zaayi din Dan shima anan din Kam baisan mezaice ba sbd maganar ivalin AQEEL ASAD din ake magana Kuma ko Dan tsakanin Nan yanzu yafi kowa sanin Amal ba garamin matsayi take dashiba a zuciar Sir AQEEL din Dan
Haka shima bazai zage ya Fadi komai Dan Haka sai kawai yace Ahmed din yakaita gidan karatun zaa turo likita yanzu idan ya fadawa AQEEL ASAD din.
Ciki ya dawo ya qaraso gurin AQEEL ahankali tareda
Dan ranqwafowa cikin tausasa murya qasa gasa yace,
"Sir Ms Amal ce ba lafiya sosai inji Ahmed,
Nace yakaita gidan Karatu Dr tayo na zuwa insha
Allah.
Shiru yayi ya dauke wuta gaba daya kaman Wanda Bai fahimta hausar ba kafin ya juyo ahankali ya kalli
Al-Amin din Yana zuba Masa idanuwansa ya bude
Baki yace, "MARYAMAH??
gyada Kai Al-Amin yayi ahankali Yana saka Kiran Dr tayo ya juya ya fice cikin gaggawa yace taje ta duba
Amal din.
Yana dawowa Kai tsaye AQEEL yace ya siya musu tickets zasubi jirgin yamma idan akwai.
Amal kuwa gidan Karatu suka Isa suna Isa ta fito ta lallaba tashiga ciki sbd itama bazaso zuwa gidaba a wanna yanayin zai sake dagawa mommy hankali da zuwansu asibiti.
Kai tsaye bedroom dinsa ta nufa ta shiga ta zube gasa ta kwanta tana maida wani irin numfashi Mai
Dan wahala
Tun tana juye juye hartasamu bacci Mai garfi ya dauketa cikeda azabar zafin ciwon zazzabi.
Tana grin tana bacci saiga Dr tayo wadda da Bata gantaba a koina ta iso dakin tayi knocking daqyar
Amal din ta farka ta jita

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login