Showing 15001 words to 18000 words out of 61982 words

Chapter 6 - IG AJEEMAL book1 Hausa Novel

03 Sep 2025

1538

yana washe baki, duk akunne AJEEMAL surutun dasuke, aunty shine bakizo kika karamu wasanba koh baruwana dake aheel yafada yana shagwabe fiska, daram taji kirjinta yabuga ba ita kadaiba hattasu reeda dake zaune haryanzu sun kasa tashi daga wajan dasuke,kaikace ba kowa awajan, ko mutsi basayi, se yanzu AJEEMAL ya dago yamaida kallonsa ga su fadeela daga inda suke zaune yana fadin," yau kunfi karfin zuwa kugaishenine toni bari nazo nagaisheku yafa yana kokarin mikewa, cin hanzari harsuna gwaral , cikin rawan jiki suka karisu tareda zubewa saman capet suna gaishe shi, cin sake fiska ya amsa musu yana murmushi, nan hajja mma da AJEEMAL suka buge da fira wanda yasa su fareeda tunanin komai yawuce, fadeela "

go and call me Barka AJEEMAL yafadi, okay kawai tace tanufi gun baba Barka dan kiranta, ba adadeba suka taho tare, seda suka gaisa da barka daga bisani yasheda mata cewa yau yana bukatar tahuta kartayi aikin komai gdn nan, girki ko shara kowani wanke wanke tabarwasu reeda ,zasuyi komai in akwa wajen datake da bukatan tafiya zata iya zuwa, tansan halin AJEEMAL niya fadi magana baya canzawa kuma ba atamka masa , dan haka batayi musuba tajuya tatafi, amma gsky ba karamin mugunta yashirya musuba, suma kansu da jikinsu yasaba da wahala ya suke karewa da aikin gdn, balle su yaran gdn da basusan komaiba se hutawa da kwanciyar gado,

gaba daya parlourn yadau shiru hajja mma da Nisha kallon su fareeda suke da tausayawa, sukuwa ido raurau kamar masu shirin yin kuka, wannan wani rin punishment yayansu kesunyi musu, am sekutashi kuje tabaku wani aikin kufara kafun naje nadawo,

"I think yau su Daddy zasu dawo yafada yana kallon Hajiya, eh yau sukace suna hanya, alright bunda yace kenan yamaida kallonsa gasu reeda yana fadin," so kunga yau seku farantawa ammi rai da special cook nasan zatayi happy sosai, zanfita naje nasiyo wadansu kayan abincin seku hada akai, yafada tareda mikewa yana murmushi, kallo sukabi bayansa dashi, tareda mikewa suka nufi hanyar kitchen kamar yanda ya umarcesu, Hajiya ce tabisu da kallo tana fadin,

" lallai kam za aci girki mai dadi agdn nan yo inbanda abun AJEEMAL mesu fareeda suka sani agirki banda indomie wayan nan kam se Barka tasa musu hanu dole, inba hakaba shirmensu kawai zasuyi zanga ya zakuyi inkunje gdn maza jenku ae bakowane yakecin abinci yar aikiba irin yayanku, bakaramin mamaki nisha tayiba jin basu iya girkiba, muryan Hajiya taji tana fadin," nikam bari naje bedroom nadan mike zuwa anjima tafada tareda mikewa, tafiya zakiyi aheel yafada yana kallon Hajj mama, eh zanje nadan kwanta kadan ga Auntynka katayata Hira, kozamuje can din Hajiya tafada tana kallon Nisha, aa zamu zauna anan karmuje mudameki da yawa, dariya Hajiya tayi tana fadin,


" to shikenan bari naje tana fadin haka tajuya tafita, ganin haka yasa Nisha takalli aheel tace


," jirani bari nazo tafada tareda gyara masa zama akujeran, kitchen tabisu fadeela, tundaga shigowar ta , tasan lallai kitchen yayi baki, Barka tsaye akansu tana dariya tana kallonsu, kaida kaga yanda suke aikin kasan babu alamar sabo a taredasu, daga bakin door din kitchen Nisha tatsaya tana kallon su gaba daya yanda suke wanke wanke ba tsari, gaba daya guri ya hargitse, ga fiska babu annuri, ko wacce baki kamar zai taba bango, kai yayan nan, kukawo nan natayaku gaba daya kun bata jikinku kubarshi kawai zanyi cewar Barka, amma sam basu kalataba balle sumatsa yanda ta bukata, juyawa nisha tayi takoma parlourn gaba daya sun bata dariya da tausayi, nan ta zauna kusa da aheel suka cigaba da tadibsu, yana bata labarin school dinsu papa yace ranar Monday zai cigaba da zuwa school tunda yaji sauki, se wajan azahar suka fito daga kitchen din sukayi iya abunda zasu iya suka barwa Barka sauran, suna fitowa suka nufi dakinsu gaba daya sunyi laushi,

seda suka gyara dakin nasu suka share tas mai yayi need sannan suka fi suka haura sama dakin ammi dana, ganin aheel yayi bacci yasa Nisha tazameshi daga cinyarta ta gyara masa kwanciyar, daga bisani tanufi inda taga su fareeda sukayi, nan ta tayasu suka share suka goge ko ina duk dacewa dakin bawani faci yayiba, suka kuna turaren wuta mai bala'in kamshi da kama daki, nada nan gd yadau kamshi, haka suka shiga bangaran Daddy shima suka gyara shi need suna kammala wa suka nufi dakinsu sukayi wanka tareda alwala sukayi sallah, gada nan suka nemi gu suka kwanta dansu sake gajiya, Nisha kuwa tana gama shiryawa tanufi parlour ganin tabar aheel shikade yana bacci, zama tayi tasake masa matashi da cinyarta tana kallon kyakykyawar fiskar shi yayinda yake bacci, lumshe ido tayi tana sakawa da kuncewa cikin zuciyar ta, nan kuma tabude idon ta saukeshi an aheel dake kwance cinyarta, hawaye ne , yashiga wanke fiskarta, ta tuna lokacinda take kwance cinyar umman ta, itama lokacin da suke tareda umma bata rabuwa da cinyarta, kullum insuna zaune se yakasance kan Nisha a cinyar umma,

" oo rayuwa kenan allah kajikan ummana, allah ka kai haske kabarinki, yaushe zansake samun farinciki irin wanda nake acikin mahaifana, ya Allah na rokeka ka baiyanamin ma haifina, iduk inda yake kasa yana cikin koshin lapia, ubangiji ka karkatu hankalisa gareni, ahankali tasa hanu tashare hawayenta, hadeda maida kanta jikin kujera,gd yayi tsit kamar ba kowa su reeda sun dade da bacci banda Nisha datakasa rintsawa ta zauna ta tsunduma kogin tunani,

Motar AJEEMAL ne yakunno kai cikin gdn, mai gadi yabude masa geat, yashigo yayi parking, yafito tareda kiran mai gadin cikin rawar jiki maigadi yakariso yana fadin

," ah yallabo sannu da zuwa, yauwa sannu AJEEMAL yafada tareda mika masa ledojin hanusa yana fadin yakai ciki, yana fadin haka yajuya yanufi part dinsa, nan mai gadi yanufi parlourn da aikenda aka bashi, nisha yatar a parlourn yamika mata yace inji yallaboi AJEEMAL, nan ta amshi sakon tai kitchen dashi ta direwa Barka, tanufi bedroom ta tasu su fareeda daga bacci ta fada musu sakon yayansu ya ISO, seda sukayi sallahn la'asar daga bisani suka nufi kitchen suka suma aiki ba kama kafar yaro, duk abunda suka san da Daddy da ammi naso shi suka daura, Barka basa musu hanu tana nuna musu yanda zasuyi, karsu tafka shirme, duk da nisha itakam ba bayaba, wajan girki, dan lokacinda suke gda da umma ita take komai bata barin umma tayi ko hanyar kitchen sede tazama yar kallo kawai, dan haka ta zage sosai wajan nuna musu nata bajintar,

aheel ne yatashi daga bacci ya dingisu kitchen inda yake jin muryan su , Nisha naganin shi tazame hanunta daga abunda take tanufi gurinsa tana fadin,

" baby katashine, gyada masa kai yayi yana tambayar papansa bai dawoba, ya dawo muje nakaika tafada tareda jan hanunsa suka fito daga kitchen din, har part dinsu tarakashi tareda murda handle din kofar lokacin AJEEMAL yake kokarin fitowa shima cikin wani shirin mai kyau da alamar fita zai sakeyi, Nisha tsawa tayi tana kallon kyakykyawar fiskar hade da lumshi ido tana shakar daddan kamshin turarensa mai wayar mancewa dan ko zama yayi agu yatashi se ka kwana 2 kina jin kamshin wannan turaren, hankali take sakebin kamshin jikinsa tareda matsuwa ahankali, sake baki yayi yana kallonta ganin yanda ta lumshe ido tana matsushi, baya yayi da sauri yana fadin ,

" ke lapiyarki meye hakan yafada cikin da ga murya ya na mai hade gira yana kallonta arazane tabude ido se yanzu nutsuwarta ya dawo gaba daya ta rude jin tsawar da ya buga mata, shikansa aheel seda yatsorata yanda yaji papan shi, ya dagawa Auntyn sa murya, bin mahaifin nashi yayi da kallo tareda matsawa kusa shi yana fadin," papa ina zakaje nima zan bika yafada yana jan hand dinsa, ✍️ .

Page 11, cikin bacin rai ya kalli nisha sekuma yamaida kallonsa ga aheel yace,

" zanje nadauko su Daddy daga airport ne yanzu zanje nadawo, sekuma ya daga kai tareda hararota Nisha da ke kokarin fita daga parlourn wanda kanshin turaransa yajawota ciki, cikin kaushin murya yace

," ke tsaya, cak tsaya tana kallonshi jin mai zaifada seta ga yamaida idonsa ga aheel yana fadin,

" kabita kukoma inda kukafito sena dawo, abunda yace kenan yasa kai yafice tareda shigewa mota yafita, cikin sanyin jiki Nisha tariko hanun aheel nanfa yaro yanuke tareda yin rau rau da ido yana shirin kuka,

" ni yaunwa nakeji nan taga ya zame hanusa daga nata ya dingisa cikin daki, bai dadeba yafito hanunsa daukeda cheeseburger yana ci nan ya mika mata haunu tajashi suka fita, zuwa yanzu gd ya dumame da kamshin abinci kota ina, nanda nan suka kammala komai suka jereshi a dining table , daga bisani suka tattara izuwa part din Hajiya nan suka baje kolinsu na hira, nan sukaita hiransu har gorin goshin magarib, motar AJEEMAL ne yakunno kai mai gadi yabude masa geat, jin ana kokarin bude geat ne ya tabbatar musu dacewa su ammi sun isu, nan suka fito tareda watsawa aguje kamar wasu babies suka nufi motar,

AJEEMAL nayin parking suka karisu suna washe baki, reeda ne tabude kofar baya ammi ta fito fiskarta daukeda murmushi, nan sukayi kanta tareda rungume cikin kewa da murna, Daddy ne yafito daga gdn gaba shima suka shiga rungumarsa suna fadin sunyi kewarsa tareda karban karamin jakar hanunsa, okay nikam ba wanda yayi Miss dinako shiyasa ba akalli inda nakebama, juyowa sukayi cikin hanzari suna fadin,

" lah ya kamal ashe kaima kadawo, aa mantani akayi acan yafada yana tura musu baki, nan suka nufushi suna dariya tareda rungumarsa, suna jan hanunsa, to nikam kukyaleni karku yadani, sewani jana kukeyi, dariya sukayi gaba dayansu tareda karisawa parlourn mai gadi na biye dasu da suran ma aikatan gdn dauke da sauran kayansu, suna zuwa parlourn suka dire kayan tareda karamusu bangaji sukafi, su reeda suka dauki jakan kayan suka karisa musu dashi bedroom dinsu, farin ciki fal zuciyoyinsu, AJEEMAL kama tunda yadiresu yanufi part dinsa yayi alwala yanufi masallaci,

haka kamal ko wanka bai tsaya yiba shima alwalan yayi yafito, yana fitowa yayi karo Daddy shima zaitafi, nan yanufa masa baya suka wuce, aban garan ammi kuwa wanka tashiga yi sosae daga bisani tayi alwala tafito, kaya mara nauyi tanema tasa tadauki hijabi ta tada sallah, bayan ta idar tayi kasa parlourn shiru bakowa nan tafito tanufi parlourn hajja mma tasan baza arasasu canba, tunkafin ta katisa shiga takejin sautin muryoyinsu, dan haka takarisa tareda tura door din tashi dauke da sallama abakinta, kallo tabisu dashi yayinda suketa hiransu, suna ganin shigowar ta su fadeela sukatashi tareda nufuta suna fadin," ammi Miss u so much wlh, da bakwa nan gd ba Dadi, gd yakoma shiru, oh dama da muke nan mukesa gd yayi hayaniya koh ,? Ammi tafadi, dariya sukayi reeda tace," ammi bafa haka muke nufiba, hakane mn, tukunna ma kunyi sallahne da kuka zauna kuna hiranan, eh munyi dazunan muka idar , okay ammi tace yayinda yamaida kallonta ga nisha da aheel yayi matashi da cinyarta yana bacci, mazawa tayi kusa da ita tayi tazauna,

cikin hanzari Nisha sannu da Hajiya tafada tareda kokarin tazame aheel daga cinyarta, ganin haka yasa ammi tayi saurin cewa," zauna abinki, tafada yayinda take kallon Nisha, sunkuyar da kai nisha tayi tana fadin," ya hanya andawo lapia, lapia kalau alhmdllh, ya gdn I hope yana mike dadi, kuma ba matsalan komai , eh Hajiya , karna sake jin Hajiya nan call me ammi kamar yanda kikaji su fadeela suna kirana, kema yatace yar ta gaban goshima tabada tana dafa shoulder dinta, dariya su reeda suka shigayi jin abinda amminsu tafada nisha ta gaban goshine, cikin wasa ammi ta hararo su reeda dake dariya tacigaba da hira da Nisha tana fadin," kisake jikinki damu nan gdnkune, to Nisha tace tana sunkuyar dakai tana murmushi, yadae ina Hajj mama ne banji mutsintaba, ammi ta fada tana kallon reeda, dazunan tashiga bedroom sallah tode haryanzu bata fito. .,


batakaiga karisa maganar ba, Hajj mama tafito fiska dauke da fara'a tana fadin," ah mutanan US har hutun yakare , tafada yayinda take kokarin samun waje tazauna" wlh fa hutu yakare ni harna gaji da kasarma ammi tafadi, yo ae dama duk wanda yabar gd tofa gd yabarshi Hajiya tafada gami da dariya, gsky kam nan ammi tashiga gaida Hajiya, seda suka gama gaisuwan, Hajj mama tace," to kingafa new babynki, tafada tana nuna Nisha, eh naganta har mun gaisa ae, ," ayya ina mai gidana koshi bai shirya dawowa kun barshi acan dan naga yafi kaunar can abunsa, aa tare mukazu inaga yana masallaci da daddynsa , nasan yana dawowa ke zai fara nema kinsan mutumin naki ae, dariya Hajiya tayi tana fadin," eh wannan haka yake nafi kowa sanin kayana, dariya sukayi duka tareda cigaba da hirarsu, nan ammi take basu labarin irin kayanda sukayi order na bikin kamal da nabeela, su fadeela murna biki zai tashi agdnsu za ayi bikinda ba ayiba baya, dan ko bikin AJEEMAL baiyi wani gagaramin bikiba, dan haka zasu rama abunda basuyi abayaba suyishi yanzu, ana kiran isha kowa yawatse yanufi yin sallah, Hajj mama takuma bedroom sallah, haka ammi ma tanufi bangaran ta dan yin nata ibadar,

su fadeela da Nisha suka rufa mata baya hanunta dauke da aheel gudun kar abarshi shikadai suka nufi nasu dakin, kwantar dashi tayi saman bed tanufiyin alwala tayi sallah, su fareeda suna idarwa suka nufi parlour yau rawar kai se abunda yakaro ammi tadawo, zama sukayi a parlourn suna jiran sakko won ammin, Daddy ne yashigo bayansa dauke da AJEEMAL tareda kamal, shigowar su gwanin shaawa, cikin happy suka isa gareshe suna masa welcome, yayi daidai da sakkowan ammi fiskarta daukeda murmushi, tana bin yayanta damijinta da kallo gwanin burgewa tana mutukar alfahari da wannan family nata gaku wani garin da allah yabasu Nisha, karisowa tayi gunsu ahankali dauke da murmushi nan nata, tana fadin,

" gwara da kuka shigo yanzu dan yunwa nakeji gaba daya bana gane kaina, dama kekam gwanar jin yunwace Daddy yafada cike da tsokana tareda karisawa dining suma suka rufa masa baya suna dariya, waje suka samu suka zauna banda AJEEMAL da kamal dasuke tsaye ammi ne ta kallesu tana fadin,

" kufa dakuke tsaye kuzauna muci abincin mana, kamal ne yafara magana yanacewa, ni banjin cin abinci for now because ni wankama nakeson nayi, gaba daya agajiye nake, kallon reeda yayi yana fadin,

" please in kin kammala ki kawomin nawa bedroom dina, to tace masa daga bisani yajuya yafita, kaikumafa Daddy yafada yana kallon AJEEMAL dake tsaye yakama kugu kazu muci abincin mana, a no akoshe nake, yafada can kasa, wul wul ga ido yayi yana su yatambayi aheel amma yasan bazai wuce suna tareda waccan yarinyar ba tunda bai ganshi a parlourn ba , guntun tsaki yaja ahankali tareda sakai yafice daga parlourn, bayanshi sukabi dakallo kawa tareda cigaba da cin abincin su, ammine tadan bugi reeda abayanta,ashhh ammi meyafaru mekuma nayi, saboda mun dawo har kun mata da kanwar taku koh,? to maza kutsaida cin abincin nan kuje kukirata tazo taci abinci, cikin hanzari fadeela ta tashi reeda tabi bayanta,

zaune suka sameta cinyarta dauke da kan aheel tana shafa kansa, reedane ta karisu tareda dauke kan aheel daga cinyarta takwantar dashi gefe tareda jan hanunta Nisha batareda tace mata komaiba suka fito parlour, seda takaita har dining ta zaunar da ita tana fadin," to ammi ga shalelen babyn taki, ganin Daddy da Nisha tayine yasa tazame wa ta gaisheshi, cikin fara'a ya amsawar tata , yana fadin," ina kika shiga kowa ya halarci wajan cin abinci amma banda ke, kefa ba bakowa bace, as from now dazaran time din cin abincin yayi to naganki awajan, kuma duk abunda kikaga wani yayi agdn matukar mai kyaune kema kiyishi, duk abunda kikeso ko kike bukata gani ga madam kitambaya batareda shakka ko tsoroba, muma iyayenkine kinjiko, cikin sanyi murya nisha tace,"to inshallah, to baza kici abincin fadin ammi yayinda ta dire mata plate din abinci gabanta, nan sukaci gaba da cin abinci suna hira cikin raha da nishadi, Nisha taci abinci sosae kuma ta sake dasu sosae ,

seda suka kammala suka dawo parlourn suka cigaba da hirarsu, yayinda Barka tazu ta kwashe abubuwan da akayi amfani dasu tayi kitchen, nikam kaje gurin Hajiya kuwa,? Ammi ke tambayan Daddy," eh na leka mun gaisa dawowana daga masallaci muka biya, okay to ae shikenan, wayan fadeela ne yayi kara taduba screen din wayan taga kamal ne ke Kira, cikin sauri tamike tana fadin," oh my God, na manta daya kammala yace nakawo mishi abinci, cikin hanzari ta tashi tanufi kitchen domin hada masa abinci," hira yayi dadi kin manta da batunsa zaku hadu ae ammi tafadi tana dariya , Nisha kam tunda fadeela ta furta sunan kamal gabanta yafadi, kwata kwata tamanta dame irin sunansama, ya ilahi wannan wani irin rayuwace, mutumin da yabata makudan kudi dan ta cece rayuwar mahaifiyar ta, shine tayi saurin matawa dashi haka, se yanzu yafado mata ko daran da umma zata rasu taga miss call dinsa, still tasake ganin kiransa bayan zuwanta gdn nan , kin karbi kudinsa kin kuma manta dashi balle kisan duniyar dayake, nashiga uku tafadi afili wanda ita kanta batasan maganar yafitoba,

cikin hanzari tasa hanu tarufe bakinta tanabin yan parlourn da kallo, jin yarda ta tashi azaburene yasa duk suka nufota suna tambayar lapiya, yanda taga sundamu suna tambayar ta yasa tace," bakomai jinayi gabana yafadi, ammine tajawota jikinta tana fadin," ba nashiga uku zakiceba, idan kinji irin haka nan gaba cewa zakiyi ina'lilla hi wa inna ilahi raju'un, bana shiga ukuna kinjiko, gyada mata kai tayi, to maza kije ki kwanta kuma kiyi addu'a kafin kwantan kinjiko, cikin sanyin jiki Nisha tace,"to, tareda juyawa tayi daki , gaba daya suka bita da kallon tausayawa, daga ammi har Daddy ba wanda Nisha bata kwanta masa araiba, duk da dama Nisha yarinyace mai shiga zuci, ga hankali da nitsuwa, tana shiga daki tafada saman bed kusa da aheel, hanu tasa ta lalubo yar karamar phone dinta, tabinciko numbern kamal tayi dealing koda takira

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login