Showing 42001 words to 45000 words out of 61982 words

Chapter 15 - IG AJEEMAL book1 Hausa Novel

03 Sep 2025

1550

yacinye idanunsu,


Abangaransu kamal da nabilah sun tattara parlourn Daddy nasiha tayi nisa ammi hajja mama goggo rabi gefe muhaiseen da mb kowa yana tofa albarkacin bakinsa, daga karshe daddy yakalli kamal yana fadin,"

gobe tafiyar taku ko an daga?

dan dagowa kamal yayi yana kallon daddy nasu fiska bayabo ba fallasa yace,"

No tomorrow inshallah, because akwai wani wasa da zamuyi cikin satin,

haba mutumin basusan kai sabon ango bane yau aka daura maka aure ba daga kafane muhaiseen yafadi yana kallon kamal cike da zolaya, ,"

ba daga kafa malam su ina ruwansu yaje yabuga wasa kawai shine magana mb yafadi yana dariya,

dariyarsu muhaiseen suka shiga masa suna tsukanarshi shikuwa kamal kallonsu yake yana hararansu yana cizon lips, "

to allah de yaba da saa yakuma baku zaman lapia yasa albarka cikin auran ku, muyiwa annabi salati,

daga nan aka shiga rufe zama da addu'a daga bisani kowa yamike yanufi turakarsa, goggo rabi da kanta tamaida nabilah dakinta inda tadauketa dazu,

Kamal kuwa suna waje yaraka abokinsa mb tareda muhaiseen dan shima ba agdnsu yasaukaba hotel yakama dan ba wani dadewa zaiyiba bikin kamalne yakawoshi yanada aiyuka da yawa agabanshi, seda yarakosu kowannensu yashiga mota mai gadi ya bude musu geat suka fice sannan kamal yajuya yanufi part dinsa,

yana shiga a parlour ya tarar da nabilah bisa kujera ta takure seda ya iso tsakiyar parlourn yakallita yana fadin,"

kitashi kije kiyi alwala kizo muyi sallah, dan dago kai tayi ta kalleshi time din har ya juya baya yanufi toilet din dake parlourn danufin alwala ganin haka yasa nabilah mikewa jiki bakwari tanufi cikin bedroom, direct tayi toilet tayiyo alwala ta dauko musu sallaya tayiyo parlour ,

atsaye tasameshi yana gyara hannun rigarshi da ya tattare wajan alwala,tana karisowa tashin fida masa sallayan daga bisani tayi baya ta shin fida nata, nan yashige gaba suka tada sallah,

bayan sun idar sun dan dade awajan suna addu'a daga bisani suka mike nabilah ta ninke sallayan tamayar bedroom ta dawo ta zauna, "

ba zama zayiba kitashi kidauko wancan ledar kamal yafadi yana kallon nabilah yana mata nuni da ido inda ledar take , ahankali tamike tanufi dining table inda ta hago ledar ta dauka daga bisani tadawo ta ajiye saman table din parlourn ta nemigu tazauna, "

kibude kici mna kamal yafadi yanadaga kishingide daga saman sofa yana latsa wayar hanunsa, "

Kai kumafa,? Nabilah ta tambaya tana kallonsa

" Akoshe nake abunda kawai yace kenan yaci gaba da abunda ke gabansa, shiru nabilah tayi tana kallonsa daga bisani ta dauke kai daga kansa tasauke kan ledar tashiga budeta, ledodine guda biyu aka sasu cikin leda daya shiyasa tun daukowa datayi taji ledar da nauyi,

chicken roasted fish se pack din irish guda biyu daya ledar kuma yoghurt kayan shaye shaye na drinks d
tareda kayan marmari bada wani bata lokaciba tasuma ci dan kuwa yunwane atare da ita,

tana tsaka daci tsulum taga ya mike yana kokarin nufa bedroom ,"

indan kin kammala kishigo ciki

to nabilah tafadi baki na fari, daga haka yajuya yashige ciki,

tana kammala wa kamar yanda ya umarceta ta tashi tanufi toilet ta wanko hand dinta tare da bakinta sannan tanufi bedroom din

akwance tasameshi time din harya sauya kayan jikinsa zuwa farar jallabiya face dinsa na kallon sama ya lullube jikinsa da blanket idonsa alumshe kamar mai bacci, tsayawa tayi kikam kamar wacce aka dasa agun tana kallonsa, "

kinemi gu kiwanta mana kintsaya, kamal yafadi yana kallon ta, ahankali tamatso jikin gadon tasuma kokarin hawa,"

Waited! kamal yafadi yana kallon kayan jikin nabilah wani tsadeden les mai nauyi ga kuma lullube bisa kanta, "

zaki iya bacci da wannan dress din jikin kin,? cikin fiskar tausayi nabilah ta kalleshi tareda gyada masa kai alamar" eh

okay kamal yafadi tareda gyara kwanciya itama tarabe daga gefe ta kwanta ta rintsa ido daga ita harshi ba wanda ya iya rintsawa se juyi da kyar suka samu bacci ya daukesu

Guraren asuba aka suma kiran assalatu wanda ya doki kunnuwan nabilah wanda yasa tamike tazauna gaba daya baccin rabi da rabi tayishi because kayan jikinta duk sun isheta, gefe kuwa tamaida kallonta ga kamal dake kwance yana bacci hankalin kwance dan shi ko kiran sallahn dama can yayansa ajmal shike zuwa yatashisa sallah asuba ko daddy in ka rasa 1 tofa ranar amakare za ayita,

tashi tayi tanufi toilet tayi alwala nan tasamu ta sauya kayan jikinta zuwa mara nauyi yar gown mai lushi tasamu tasa daga bisani tayi gadon dumin tashin kamal,

tana zuwa kusa dashi tashiga tashinsa ,nan yabude ido tasanar dashi dayatashi yayi sallah nan ya mike ya saukko daga gadon yanufi toilet tana ganin shigarsa ta shin fida sallahya tasuma gabatar da sallahnta,

yana fitowa yasa kai yafice yana fitowa sukaci karo da daddy shima yafito da niyar fita masallaci, nan kamal ya rufa masa baya suka wuce,

nabilah na idar da sallah ta haye gado ta kwanta nan da nan bacci mai nauyi ya dauketa,

shima kamal yana dawowa daga masallaci yanufo bedroom din yasamu nabilah tayi rashe rashe tana bacci da alamar baccin yayi nisa, dan jinjina kaiyayi yana kuma kare mata kallo seda ya kalleta sosae daga bisani ya lumshe ido yabude sannan yasakai yafice daga dakin ya koma parlour kan sofa ya kwanta ya lumshe ido yanata kwancewa da sakawa cikin ransa,

karfe 10 nasafe ahali daya antattara gurin cin abinci anaci ana raha ana kuma tadi, kamar yanda suka saba dazaran sun kammala breakfast za adawo parlour acigaba da fira , yauma hantake , Nisha na kusa da hajiyanta farida da reeda suna kusa da daddy sun sanyashi tsakiya se goggo rabi da ammi suna daga gefe cikin farin ciki da annashuwa, sallaman su kamal da nabilah yasa suka dan dakata suna kallon shigowar su,

Kamal na gaba nabilah nabiye dashi tareda try din breakfast da ammi tasa baba barka ta kai musu, ammine ta kwadawa barka kira baba barka na fitowa ammi ta umarceta da ta amshi try din hanun nabilah, nan barka ta amsa tanufi kitchen dashi, hakan yabawa su kamal daman karisawa cikin parlour kamal daga gefe saman carpet yasamu guri yazauna haka itama nabilah kai sunkuye nan suka shiga gaisawa dasu daddy seda suka gama gaisawa kamal ya dan dago ya saci kallon Nisha datayi lamuda ita uwar son jiki tasanya kanta saman shoulder din hajiya kamar wata mara lapia gaba daya ya sakan kance da kallon Nisha wacce zuciyarta ke bata kamal na kallonta but sam takasa daga ido takalleshi because hawaye zai iya ziyarta idanunta,

nabilah duk tana lura da kallon da kamal ke yiwa Nisha ban sauran yan parlourn da hankalinsu ke kan hira,

Nabilah ba kallon kamal , kamal kuwa idonsa na kan Nisha duk da nabilah ta lura Nisha batasan da kallon da kamal ke mataba, gaba daya setaji zuciyarta na mata suya because nabilah tanada zafin kishi sosai musamman akan kamal
🌴🌴 IG AJEEMAL 🌴🌴

Story and writing by oum amreesh
(Khaleeseart Raeeys)

Free book πŸ€—

Page29_30

Jitayi tamkar tasa kuka ganin abunda idanuwanta ke kallah, shigowar su mb da muhaiseen yasa duk ilahirin hankulansu ya dawo garesu,

Nan su mb suka shiga gaisawa dasu daddy, daga bisani muhaiseen yakalli kamal yana fadin,"

My man muje ko,

jiki ba kwari kamal yamike ganin haka yasa nabilah mikewa itama, daga bisani Daddy da dukanin mutanen parlourn suka tashi domin yiwasu kamal rakiya,

seda suka iso filin gdn indasu muhaiseen sukayi parking, goggo rabi ta bude kofar motar gdn baya ta kutsa nabilah wacce hawaye suka suma wanke fiskar ta, ammi hajja mama reeda fadeela se allah ya kiyaye sukeyi tareda musu fatan alkairi, banda Nisha dake gefen hajja mama tayi rau da ido kamar mai shirin kuka,

Shima gdn baya inda nabilah tashiga kamal yashige ,"

Allah ya tsare yakiyaye kakula dakanka kakula da kanwarka sosai please daddy yafadi yana dafa shoulder din kamal,"

Inshallah Daddy kamal yafadi yana yar murmushi daga haka Daddy ya rufo musu kofar motar nan su mb suka shige gaba muhaiseen shine me driving ,

Nan mai gadi yabude musu geat daga nan muhaiseen yayiwa motar key suka fice, seda sukaga ficewarsu aharaban gdn gaba daya hakan yabawa su daddy daman dugumzuma su koma parlour inda suka fito,

kowannensu jiki amace abun ba dadi , haka kowa yanemigu yazauna sukayi shiru nadan wani lokaci, daga bisani Daddy yasuma kokarin mikewa, harya fara nufa upstairs se shigowar su heelah tareda mom dinta hajiya jumana, hanunta dauke da na aheel kamar wayanda aka jefo daga sama,

ganin haka yasa daddy jiyuwa ya koma yazauna inda ya tashi suna ganin isowar su, aheel cikin hanzari da dauki ya zame hanunsa daga na kakar tashi da gudu yanufi inda yaga Nisha zaune ya fada saman cinyar Nisha tareda washe baki, yana fadin,"

Aunty!

rungumeshi nisha tayi cikin farin da daukin ganin shi , "

ba shakka hajiya jumana tafadi tana tabe baki yayinda take kallon aheel da Nisha yanda suka wani rungumi juna, gefe takalli heelah wacce itama idanta ke kansu ,

seda suka karisa tsakiyar parlourn heelah da mom dinta suka nemigu suka zauna, suna bin yan parlourn da kallo wanda suma idansu akansu yake, cike da mamakin ganin su,

hajiya jumana atsatsaye ta daga musu gaisuwa suka amsa ba yabo ba ballasa, itakuwa heelah baki tatura gaba bata daniyar gaishesu jin mom dinta ta zungudeta yasa tabude baki ta daga musu gaisuwa ciki ciki suka amsa,

hakama su reeda da Nisha suka gaisheda mom ta amsa nasu reeda amma nisha ko kallo bata ishi hajiya heelah ba,

"Lapia kuwa,? Daddy yafadi yana kallon su

" Eh lapia yar kenan magana nake tafe dashi ko nace kara na kawo, hajiya jumana tafadi atakaice, ""

kara! daddy ya furta ahankali, se kuma ya kalli su fadeela ya basu umarnin su tashi sushiga ciki, nan suka mike dukansu suka nufi bedroom tareda aheel duka,

"Kara kuma karan wa kenan hajja mama ta tambaya,

rabi! dalili nakeso tabani na kama diyata taita duka kamar jaka, saboda kawai fada ya hadasu da waccen yarinyar Nisha take ko waye, rabi bata tsaya taji kan zanceba tayi kan heelah da duka ,

kunganta tanan tun jiya zazzabi mai zafi yarufeta tayiyo gd ba wanda ya damu da damuwarta balle yasa me yasameta,"

Subhanallah anan gdn kum wannan abun ya faru, ammi ta tambay

cike da yamutsa fiska hajiya jumana tace ,"

Aina kike tunanin hakan zata faru inba anan dinba, ranar da ake shirye shirye tafiya dinner hakan tafaru dalili daya hana heelah zuwa partyn kenan sbd rashin kyautawa da kunya tata cikin friend dinta, anuna mata kasawarta, angwada mata bare ta fita mutunci,

parlourn ne yadau shiru kaman ba mutane cikinsu mamaki hajiya jumana da maganganunta ya gama basu mamaki,

Daddy ne yamaida kallonsa ga rabi wacce tayi tsuri tana kallon heelah da mom dinta da irin karai rayinda suka zo dashi,"

Rabi kinji abunda hajiya tazo dashi daddy yafadi,"

Naji sede amma sun fadi sun zuciyarsu ne indan zasu fadi yanda zancen yake heelah ce batada gsky nikuma amatsayina na babba nayi hukunci yanda ya dace, "

Oh hakama zakice mun fadi sun zuciyarmu to shikenan nida kaina zanyiwa tufkar hanci dama nazo nafadane dan kusani but tunda kun sani shikenan, hajiya jumana tana gama fadin haka tasuma kokarin jan hanun heelah, ,"

Dakata mana yakuna abu sekace wasu kananan yara kutsaya abin abun abun asunnu mana, daddy yafadi yana kokarin dakatar da hajiya jumana daga kokarin tashin da take, "

kin kawo karanki munji mun gamsu muna baki hakuri bisa kuskuren da ya faru, hakan bazata sake kasance waba,

kuma batun rahilah ta koma dakinta tazauna duk abunda yake damunta za amata magani anan, batun bata da lafiya ta koma gd duk bai tasuba, "

Mijintafa baya nan kuma ko sanar da ita baiyiba balle tasan time din da zai dawo , ya barta ita kadai ba waya ba komai se bautar dansa datake ko time din zuwa aiki yanzu batadashi , baisan wani hali suke ciki ba wayarsa akashe,

dan haka kubarni zan kula da abuna agdna har ta warke ta kuma haiyacinta idan da yiyuwar da wowa seta dawo ai ga danku shikam nasan yafi kaunar zama anan, dama nan din yafi dacewa dashi, nabarku lapia,

daga haka suka mike suka fice, baki bude daddy yabi bayan matar dan uwan nasa da kallo daga bisani ya jin jina kai tareda sunnar da kai kasa

Nanfa daki yasake daukan shiru, jiki asanyaye daddy yatashi ya haura sama, yabarsu ammi saune suna jimami, ba wanda yacewa da dan uwansa kala,

jim kadan hajiya tamike tanufi hanyar fita goggo rabi ma sidi sidi ta tamike tabi bayan hajiya, ganin haka yasa ammi tashi itama jiki ba kwari tabi bayan mijinta,

Yaufa zama sam bata kare da dadiba kamar yanda aka saba, aheel yanacan bedroom dinsu Nisha yanata zuba musu surutunsa da yasaba baisan su mummynsa sun tafi sun barshiba, su kuma sun biyeshe da shirmensa basu san wainar da aka gama tuyawaba ,

rayuwa tacigaba musu kamar yanda suka saba cikin farin ciki da annashuwa Nisha da kanta tashiga da wai niya da aheel cinsa shansa duk ita ke kula dashi, domin ammi tasanar dasu heelah batada lapia tana gun mom dinta ke kula da ita shiyasa tabar aheel anan, jin hakan ba karamin dadi yayiwa Nisha ba dan tanaso yaron sosai kuma tana son kasan cewa dashi

shiyasa ta dau ragamar kula dashi tare suke kwana su tashi ta shiryashi cikin uniform tarakashi har mota drive yakaishi

aban garan hajiya kuwa takasa mancewa da abunda uwar heelah tazo tayi , na maganganu na rashin da'a dacewa da samarwa karya wajan zama. ,

gaba daya abunda tazo tayi yabata mamaki batasan tsaurin idon jumana ya kai hakaba , ba inda diyarta ta barota, ashe gurin uwarta take koyan wasu halayi da da'biu gaba daya tagama shagwabasu da lalata tarbiyarso da sunan wani so,

Itade hajiya tun daren ranar tagaba yanke hukunci kuma very soon zata zartar dashi kuma dole akarba huncin da tayanke ko anaso ko ba aso tunda kowa kasa yake da ita🌴🌴 IG AJEEMAL 🌴🌴

Story and writing by oum amreesh

(Khaleeseart Raeeys)

Page 31

Bayan yanke hukunci na hajiya take ta dau waya ta dannawa abban heelah kira tasanar dashi tana bukatar ganinsa nan yasheda mata baya gari but inshallah allah in ya dawo zaizo dajin haka hajja mama ta katse wayar tasa ido rana da lokacin zuwansa,

Ranar alhamis da dare bayan sun kammala dinner yau ba dan wani dugun hira sosai kowa yanufi ma kwancinsa ,

goggo rabi da hajiya suna zaune parlour suna jiran dawowan su Daddy da abban heelah domin sun sanar da hajiya suna tafe tare,

ba dadewa motarsu ta kunno kai cikin gdn mai gadi yabude musu geat suka shigo, sunayin parking direct part din hajja mama suka nufa,

haka su daddy suka shigo cikin parlourn daya nabin daya suka nemigu daga gefe suka zauna,

nan suka shiga gaisawa da hajiya daga bisani sukayi shiru dan jin meys makasudin ganinsu da hajiya takesonyi , "

Modi wai meya yake faruwa agdn kane, hajiya ta fadi tana tambayar abban heelah, baki na bari yasuma maganaa,"

Haj.. hajiya mai kuma yafaru,?

Magana nake akan matarka da heelah naga kamar yanzu sundauko wata da bi' a narashin ta ido,"

Hajiya gwara kiyiwa yaya modi bayani yanda zai gane ba se anbita wani dugun turanciba, bari nina kura masa jawabin abunda ya wakana bayanshi, goggo rabi ta karbi maganar,

Heelah da mahaifiyarta bakaga iban albarka da rashin kunya da sukazo suakayi agdn nan ba agaban hajiya,

Nan goggo rabi ta labarta masa abunda yafaru wanda jin hakan ba karamin mamaki yayiba, duk da yasan halin jumana sarai za ta aikata ,

Shiru yayi kansa kasa yakasa cewa komai, se tsinkayar muryar hajiya yayi dacewa,"

Ni baruwana da rashin kunyar da sukazo suakayi duk wanda yayi na gari dan kansa, tunda tace yarta baza tazauna tayi zaman aure kamar yanda kowa yakeyiba ba matsala gari da yawa maye bazaici kansaba,

duk lokacin da taji zata iya dawowa dakinta yana nan yana jiranta , amma kafin nan akwai hukunci dana zartar hajja mama tafadi tana kallonsu,"

hukunci kuma hajiya? wani irin hukunci?"

Gobe in allah ya kaimu bayan sallah jumma'a ina bukatan adaura auran MODIBBO da yarinyar nan Nisha"

Hajiya aure kuma? please kar ayi gaggawar yanke wannan hukunci mana, idan baki manceba ko auran MODIBBO na fari bawai da amincewar sa bane kekika bukataci ahadasu muka hadasu yanzu kuma ake shirin kakaba masa wani,.. daddy yafadi cike da damuwa ,"

Nasani idan yanzu kowa bayida bukatar hakan ni inaso, kamar yanda nabukaci nabaya akayi to wannan ma haka nake bukatar akullashi ,

dan haka bana bukatar shawarin kowa umarni nake baku ba shawaraba, koshi MODIBBO danake shirin kara masa auran bai isa ya kaucewa magana taba ,

naso agabana za adaura auran ina gani amma kasancewa ana bukatan shaidu shiyasa nabarshi zuwa gobe, dan haka indan allah ya bamu tsawon rai zuwa gobe ashafa fatiha,

Daga Daddy har abban heelah shiru sukayi suna jinjina maganar hajiya ammade wannan hukunci data yanke da tsauri yake, to amma uwarsuce ba yanda suka iya basu isa sukaucewa maganar taba,

Goggo rabi kuwa se washe baki take ranta kal zuciyarta fes ba karamin jin dadi hakan tayiba"

To kutashi kutafi dare yayi se allah yakaimu goben, hajiya tafadi, jiki asanyaye suka mike suka fice ,

Daga waje suka tsaya sukayi sallama abban heelah yashiga motarshi mai gadi yabude masa yafice, daddy nagani tafiyar dan uwan nasa shima ya kutsa kai cikin parlourn haurawa yayi sama cikin bedroom dinsu,

a zaune ya tadda ammi gaban mirror tana shafa mai, ganin shigowar sa yasa ammi mikewa tashiga masa sannu da dawowa, "

Yauwa ya amsa tareda neman bakin gado yazauna yana dan dafo goshinsa,"

Bari naje nashirya maka dinner,"

Ah no da kinbarshima, akushe nake, daga fadin haka ya mike saman bed din face dinsa na kallon sama,

cike da nitsuwa ammi ta matso kusa da bed din gefe tanzauna, tana tambayar shi,"

Allah yasade lapia naganka kamar cikin damuwa, bayida niyar fada mata halinda ake ciki, but amma ba amfanin boyewar tunda dole zata sani koshi bai sanar da itaba, "

Hajiya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login