Showing 39001 words to 42000 words out of 61982 words

Chapter 14 - IG AJEEMAL book1 Hausa Novel

03 Sep 2025

1552

ido tareda girgiza kai,

Nanfa ya tsulale kasa, jiyayi kansa yayi nauyi kafafuwan sa sun gagara daukansa, jiyayi kamar ba aduniyar yake bama, Nisha na ganin haka tayi kansa da sauri tareda tsuguna wa , kusa da kansa tana tambayar sa wanda baimasan tanayiba, "

Kai lapiya kuwa mai kakeyi haka,? please katashi ga budemin kofa natafi gdnmu wajan ummana, tafadi cikin sheshshekar kuka, ganin babu alamar zai tashi yasa tasuma kokarin mikewa tsaye, carab taji yarike hand dinta,

Kallonsa tayi dashima kallonta yake da idonsa dasuka canza launi zuwa jaaa, ganin haka yasa tasuma kwace hanunta, jin yarike hanunta gam still yana kwance saman capet bayida niyan tashi,

baki takai da niyar cizonsa but kafin tayi yunkuri ya jawota saman jikinsa, ya rungume ta tsam, waro ido Nisha tayi because jitayi wani irin yarrr tsoro da firgici yasa tashiga kiciniyar kwace kanta da karfi tana bugun kirjinsa,

shima cikin zafin nama ya yunkura tareda yin kasa da Nisha shikuwa yakuma sama,"

Innalillahi wa'inailaihi raju'un hasbunallahu wani'imal wakil, abunda Nisha tafadi kenan tareda sakin wani ihu tana neman agaji,

Kb daga waje yajiyo ihunta nan da nan yasake wani ihun dadi hankali tareda rawar murna yana sakin wasu wakoki ," yaude yayi magani mara kunya buri yacika,

dan tsa gaitawa yayi da rawan jin shiru yasa yamatsa kusa da kofar yayi kusan minti 10 daga bisani ya dan murda handle din kofar yashiga lekawa ahankali, " inna lillahi wa'inailaihi raju'un kb yafadi tareda kara bude kofar da sauri, kamal ya hango kwance saman carpet kamar macecce keyarsa se fidda jini yake,

gefe kuwa kwalban da sukasha drinks dazu acikine afashe awatse agurin ," subhanallah kb yafadi atsorace tareda karisawa cikin parlourn kusa da kamal dake kwance ya tsuguna yana kallon sa, fusace kb yamike yana fadin,"

Where are you yau zakici ubanki kashemin dan uwa kikayi,? yafadi yana kama kugu, yana dan wul wul ga ido yaga daga ina zata fito, yana tsaka da surutain sa, Nisha ta fito daga bayan labulen da tabuye dama taci alwashin bazata tafiba seta illatashi shima,

yana cikin surutun nasa yaji saukan kwalba akeyarsa shima, bai fadiba seda yajiyu sukayi ido 2 da Nisha yana rike da kansa dake kokarin zubda jini, yasuma kokarin magana nisha ta hankada kirjinsa da karfi yafadi sumamme,

da sauri Nisha tayasar da rabin kwalbar dake hanunta takalli kamal dake kwance gefe takalli kb nan da nan tafashe da kuka tayi waje da kudu

Mai gadi dake zaune awaje saka makon dazu shiharta yatafi zagawa shiyasa baiga shigartaba se fita,

Mai gadin ganin yarinya tafito da gudu hakan yasa yamike atsorace yanufi cikin gdn, yana karisawa parlourn ya kamal da kb kwance cikin jini kamar mataccu, ,"inna lillahi wa'inailaihi raju'un mai gadi yafadi ya rude tareda ciru yar karamar phone daga aljuhu yashiga kiran wata number ringing daya biyu aka dauka, mai gadi nayin sallma yashiga zaiyanu abunda idonsa yagani da abunda yafaru, cikin tsoro da faduwar gaba baba mai gadi baikaiga karisa maganar ba yaji ankatse wayar,
.
ganin haka yasa yamai da wayar aljuhu yaja ya tsaya daga gefe yana kallon su kb dasuke kwance, bada wani bata lokaciba baba mai gadi yaji wani irin gawurceccen hon cikin hanzari ya karisa geat din tareda budewa,


Kyakykyawar mota black mai daukar hankali ta danno kai cikin gdn , tsakiyar compound din gdn akayi parking mai gadi yazo da sauri yabude masa murfin kofar motar yafito,

Masha Allah kyakykyawar namiji dirarre dan matashi maijin kanshi, dan gaye son kowa kin wanda yarasa , yana sanye cikin black suit face dinsa sanye da bakin glass gwanin burgewa da shaawa kamar kasaceshi kagudu,

IG AJEEMAL kenan tareda abokinsa inspector Ahmad gefe kuwa doctor fu'ad AJMAL na gaba suna binshi abaya shima baba mai gadi na biye dasu,

Seda suka shiga tsakiyar parlourn suka tsaya, IG kallo daya yayiwa parlourn daga bisani yakalli kamal yakoma yakalli kb, daga nan yakoma nisa dasu ya nemi kujera yazauna yana kuma kallon gurin su kamal inda suke kwance,"

Baba come here IG yafadi yana kallon baba tareda masa hanu alamar yazu, jikin baba mai gadi har kerma yake ya karisa kusa dashi tareda dukawa saboda yaji mai zai Fadi,

Khaleeseart Raeys ✍️

08105565439
🌴🌴 IG AJEEMAL 🌴🌴
Story and writing by Oum AmReesh ♥️
Daga ALKALAMIN khaleeseart Raeys ✍️

Free book 🥰

Page 26_27

IG seda yakarewa baba mai gadi da kallo daga bisani yashiga fadin,

What happened? meyafaru da wadannan,,? jikina kyarma mai gadi yasuma cewa,"

Yallaboi kamar yadda kace ina lura dashiga da fitan yaran nan agdn nan, yau ansamu akasi domin kuwa wata yarinya ce tasaci jiki tashigo ta aikata wannan ta asar

Kaikana ina har akashigo akayi wannan danyar aikin,? anyama macece ta aikata wannan aikan haka?, inspector Ahmad yafadi tareda tare baba mai gadi da maganar yana kuma kallon sa,

Shima AJMAL din kallon mai gadin yake yanason jin karin bayani, "

Tabbas macece yarinya karama tana sanye cikin hijabi lokacin da tashiga na dan zaga bayine dataga bakowa wajan shine tasidado tashigo, se fitanta nagani.. bai kaiga karisa maganar ba, sukaga IG yamike daga zamar dayayi yakalli doctor fu'ad yana fadin,"

Check them,

doctor fu'ad kamar jira yake dama, nan da nan yashiga checking dinsu, ya kuma tabbatar wa da IG suna da rai, "

dan matsowa yayi kusa da doctor fu'ad tareda karewa su kamal kallon da kwalbar dake watse saman capet wanda akayi amfani dashi wajan lahantasu, hankali yafurta,"

A daukeso daga nan asasu cikin mota, cikin hanzari inspector Ahmad tareda doctor fu'ad suka suma tattara su kb baba mai gadi ya taimaka musu suka kutsasu cikin motar kamar yadda IG ya bukata,

Shima AJMAL din bin bayansu yasuma kokarin yi sekuma ya tsaya yana kallon saman capet inda aka daukesu kamal, hankali ya sunkoya, yasa hanu yadauki wani hadden zuben azurfa, mai kyalkyali da ban shaawa, kallon zuben yashigayi sosae daga bisani yadan sake wata murmushi wacce nima bansan tameye bace, sannan yamike tsaye tareda sanya zuben cikin aljuhu yanufi hanyar fita,

Jikin motar ya taddasu doctor fu'ad suna jiransa tareda maigadi daga gefe, seda ya kariso indasuke yakalli baba mai gadi yana fadin,"

agyara parlourn nan yayi excels arufe shi abunda yafadi kawai yasakai cikin motar yayi mata key, mai gadi dajin haka yanufi geat yabude musu suka fice
*****Nisha***************
Aban garan Nisha kuwa tunda tabar gurinsu kamal tawatsa da gudu tafice daga gdn, bata zame ko inaba sae gd gab goshin magarib, tundaga nesa ta sallami mai adaidaita tundaga kofar gdn ta tsaya tashiga goge hawayen dake face dinta, gaba daya fiskar yayi jawur dashi, seda tagama kimtsa face din ta, daga bisani takutsa kai cikin gdn, koda shiganta ciki bakowa umma bata ciki da alama tana bedroom dibta, cikin sanda tasuma tafi domin shiga dakinta, "

Seyanzu,? Nisha taji muryan umma wacce fitowar ta kenan daga daki , hanzarce Nisha tajiyu tana kallon umma cikin sanyin murya tace," eh seyanzu munata fira da salma ban ankaraba ashe magarib tayi, Nisha tafadi tana tsili tsili da ido, "

To seki samu kiyi sallah kizo ga abinci najiranki, to kawai Nisha tace tanu daki dasauri, umma de bin bayan Nisha tayi da kallo ganin yanda gaba daya fiskar ta tasauya bayacce tasaniba, kamar akwai wani abunda ke damunta, shiru umma tayi kamar mai nazarin wani abu daga bisani tajuya tanufi kitchen,

Nisha tana shiga daki toilet tanufa tazauna tayi kuka mai isarta tashare hawaye tayi alwala tafito, nan tashin fida sallayan tayi sallah tana idarwa tabarke da wani sabon kuka gaba daya abun ya faru yakuma dawo mata,

itakam tashiga uku ina zatakai hakin daukan rai har mutum2 wannan wace kallar kaddarace ta fada mata, lokaci daya akasi ya giftawa rayuwarta, sukuma meye dalilin su nashiga rayuwarta harsuke kokarin rushe mata gobenta, ?tana tsaka da sheshshekar kukan taji muryan umma,"

Subhanallah meyafaru meyasame ki kike kuka, ,? umma ta tambaya lokacinda ta karisu tasun kuya kusa da Nisha tana tambayar ba asin kukanta, cike da wayancewa Nisha tafada jikin umma tareda sakin wani kukan tana fadin,"

Umma ina matukar kewar abbana inason sashi cikin idona, inason sani wani hali yakeciki, Nisha tafadi nan da nan taji kukan ya hadu mata biyu, kukan kisan kai da kukan rashin abba, ba Nisha ba hatta ita kanta umma jitayi gabobinta sunyi sanyi zuciyar ta tayi wani irin rauni hawaye nasonyi zarya saman face dinta, kamar ta tayata suyi kukan tare but bazata jure ganin diyarta cikin wannan halinba, dan haka tamatse nata kwalan ta dago nisha tana fadin,"

Ya isa haka karki damu abbanki yana cikin kushin lapia kina misha fatan alkhari da addu'a a duk inda yake allah ya karkatu hankalisa gd, yanzu kitashi muje kici abinci umma tafadi tana mikar da Nisha tsaye suka fice daga dakin,

kwana2 da faruwan hakan amma sam Nisha takasa mancewa da abunda yafaru, koda yaushe jira take bincike yayi bincike taji sallaman yan sanda sunzo tafiya da ita, tana zaune tayi jugum adaki tana tunane tunane tajiyu sallama daga bakin door ana kokarin shigowa,

salma ce tafe taja ta tsaya daga bakin kofa tana kallon Nisha dake kallonta da rinannun idanuwanta, cikin hanzari salma takarisa gadon nisha ganin yanda face din ta yakoma da alamar damuwa,

salma nazama ta dafo shoulder Nisha tana kokarin magana setaga Nisha tafada cinyarta tasake wani kuka mara sauti kasa kasa,"

salma nashiga ukuna na aikata abunda ya dameni, nayi abunda bazan yafewa kainaba

dagota salma tayi tana kallon tasuma tambayar ta,"

Lafiyanki mekike? fada haka keko wani laifine kika aikata kiketa wadannan zantukan, ? dago ido Nisha tayi tana fadin,"

Kisa nayi mutum harbiyu nan Nisha tazaiyanawa salma tun farkon wakanan lamarin har karshe , yanzu tunani na sun mutu ko suna raye allah masani Nisha tafadi cikin kuka mai tsuma rai,"

suna raiye basu mutuba kamar yanda kike expecting "

how kinsan abunda yafaru ne,? Nisha tafadi hanzarce tana zazzare ido,"

Eh but naga wautanki cikin lamarin kuma banyi tsammanin akwai wani sabon lamari da zaishigo rayuwarki kibuyeminba, ko danki bukaci idea daga gareni amatsayina na kawarki kuma aminiya wacce zamu kashe mubinne tare ba wanda yaji balle yasani why,?

salma tafadi tana kallon Nisha datayi mata zuru da ido cike da mamakin magan ganuta takasa cewa wani abu, kinyi shiru inata surutu bakice komai ba salma tasake fadi still idonta bakan Nisha ,"

Please bani labarin taya kikasan wannan abun yafaru, Nisha tafadi asukwane, ,"

dan gyara zama salma tayi tana fadin," inba ki manceba mb friend din kamalne , kuma wannan abun da yafaru kanshi nazo muyi magana, shine makasudin zuwana gdnan,

Nisha share hawayen face din ta tayi hade da gyara zama tana sauraron salma da abunda zatace,"

Mb baya gari baisan mai akecikiba, yakirani yakuma sanar dani abunda yafaru, yasheda min tun bayan faruwan lamarin kamal yakirashi cikin tashin hankali da damuwa yakura masa jawabin abunda ya wakana ,

Ba damuwarsa illan dakika masaba, damuwar shi baisan mai ya aikata agarekiba fatan shi Allah yasa ba abunda yashiga tsakaninku ,

duk wannan abubuwan da suka faru babu laifin kamal, wannan duk shirin kb ne, yayi duk yanda zaiyi dan yacutar dake ta dalilin magan ganu mara dadi da kuma marinshi da kikayi

🌴🌴 IG AJEEMAL 🌴🌴
Story and writing by oum amreesh
( Khaleeseart Raeeys)

Free book 🤗

Godiya mai tarin yawa gamasoya abun alfahari ina alfa hari daku koda yaushe 🤝

Page28

Kamal yayi iyaka kokarinsa wajan ganin ya tare duk wata hanya da hakan zai kasance

ganin haka yasa kb yayi amfani da kamal wajan cutar dake ta hanyar zuba masa abu cikin abunsha batare da saninsaba duk abunda kikaga yafaru time din kamal baisan da kasan cewarsaba,

dan nunfasawa salma tayi kafin tacigaba da fadin," allah sarki yanzu suna can suna amsar magani kamal duk ya gama daburcewa cikin wannan lamari da ya afku, kwata kwata baida masaniyar abunda dan uwansa ke shiryawa,

gaskiya kb takadarine hmm Allah ya kyauta yacigaba da karemu daga sharrin masu sharri,"

amin Nisha tafurta asanyaye, salma duban Nisha takumayi wacce tayi kalar tausayi se kuma tamai da idonta ga phone dinta dake gefen cinyarta tadauka tareda kai hand tadauki dan ma daidaicin phone din nisha,

wani number salma tashiga jerawa Nisha cikin phone dinta sannan tamikawa Nisha wayar tana fadin,"

gashi wannan numbern dakike gani nasanya miki cikin phone numbern kamal ne shiya bukaci da abaki because yace inda akwai wani issue daga gareki you can call him dan haka ki barshi cikin wayarki tana gama fadin haka tamike tana fadin,"

To nikam bari nawuce sena jiki tafadi tareda shigewa gaba itama Nisha mikewa tayi tarufa mata baya suka fice, kishingide umma take saman kujera wacce tun shigowar salma gurin ta sameta, ganin fitowarsu yasa umma ta mike tana fadin," har anfito

"Eh umma salma tafadi tana washe baki yayinda Nisha ke biye da ita,

" To kigaida gd kice ina gaida ummyn taki,

"Zataji inshallah daga haka sukayi sallama nisha itama daga bakin parlourn sukayi sallama tajiyu ta dawo kusa da umma tareda yin matashi da cinyarta tana sauke ajiyar zuciya ahankali jitake zuciyarta fes,.

dan shafo suman kan Nisha umma tayi tana fadin,"

Ina zuben da abbanki yasemikine kwana 2 ban ganshi ayazunkiba kin gaji dashine ko yardashi kikayi awani guri dan nasanki da shiririta wani lokacin,

rass nisha taji kirjinta yabuga nan ta sulale tamike daga kwanciyar tashiga kallon yatsun hand dinta sam ko batayi da zuben baya hanuntaba se yanzu da umma ta ankaradda ita "

to ina zuben yashiga kuma ina nayaddashi? Nisha tashiga tambayar kanta cikin zuci, ganin umma ta tsareta da ido yasa Nisha kirkiro murmushi tashiga sosa keya tana fadin,"

Nima bansan wani lungun yashigaba tunda natashi abacci ban kalleahiba maybe ya yashiga wani gurin kinsan dama bai kama yatsun hand dina sosaiba, amma dai zan dubashi bata jira taji mai umma zatace ba tawuce fuuu tayi daki tabar umma awajan,

tundaga wannan lokacin nisha ke neman zuben ta dan zubene mai matukar mahimmanci agareta zuben da abba ya bata lokacin da yasa kafa yabar gdn bai sake waiwayan suba,

batan zuben ba karamin taba zuciyarta yayiba duk lokacin da take tare da zuben jitake tamkar da abba take tare, gashi yau tawayi gari babu shi atare da ita bata kumasan inda taya dashiba,

aban garan kamal kuwa kullum tsumayin kiran Nisha yake dan atuna ninshi kiranta agareshi tamkar tayafeshini komai ya wuce,

ita kuwa Nisha tun time din da salma tasanya number kamal cikin phone dinta batayi tunanin kiraba bata kuma ji alamar zata kiraba har se lokacin da umma ta kwanta rashin lapia sannan tasamu daman kiranshi nanma ba yanda ta iya batada kuma wani zabi because tasan yana da arzikin da zai iya taimaka musu , awannan yanayi Nisha ta dangana ga kamal wanda lokacin sukayi ido biyu da nabilah wacce ta daura mata karan tsana duk da batasan dalilin zuwan Nisha wajan kamal,

Atakaicede wannan shine labarin abubuwan da suka faru abaya***********

Parlourn ne yadau shiru tamkar bakowa, kama daga su fadeela muhaiseen da sukejin abun da yafaru abaya da kuma abunda kb ya aikata, kowa da abunda yake sakawa cikin zuci,

Nabilah kanta kasa tagagara daga kai gaba daya kunyan Nisha da tausayinta sungama mamaye kwanyarta, ta kaicin abunda dan uwanta kb yayi yagama bata mamaki duk da tasan ba bakon al amari bane agareshi komai akace yayi babu makawa zai aikata, suna tsaka da wannan alhinin sukajiyo sallama ana kokarin shigowa,

dagowa sukayi sukayi dukansu suka tsurawa kofar door din ido dan ganin mai shigowa, goggo rabi ne tafe tana sanyi cikin lullube fiskarta cike da fara' a ta kariso tsakiyar parlourn tanabin kowannensu da kallo daga bisani ta tsaida idonta kan nabilah dake ta matsar kwalla, "

oh haryanzu kukan bai kare bane goggo rabi tafadi tareda matsawa kusa da ita ta dagota tamikar da ita tsaye tana fadin,"

Kukan nan ya isa haka, kukuwa duk taronku nan arasa mai lallashita, barinma kai kamal kana kusa da ita kanaji tanata asarar hawayenta, to kutasu muje Daddy ya dawo yana nemanku a parlourn sa, tana gama fadin haka ta tusa nabilah agaba kamal da mb tareda muhaiseen suka rufa musu baya jiki amace kamar wayanda aka zarewa laka,

reeda fadeela Nisha anrasa mai kwakwaran mutsi acikinsu, Nisha hawayen idonta tanema tarasa sotake tayi kuka ko abunda takeji cikin zuciyarta zai ragu but hawayen yaki zuwa balle kukan yabiyo baya, "

kutashi mutafi muje mukwanta , reeda tayi magana cikin karfin hali yayinda tamike taja hanun fadeela da Nisha suka fice ,

parlourn bakowa duk sun hauwa sama parlourn Daddy hakan yabasu daman shige bed room dinsu domin shirin bacci, seda kowannensu ya kimatsa yayi night dressed daga bisani sukanemi guri suka kwanta, amma sam bacci yaki zuwa se kwafa suke suna tsake in fadeela tayi se reeda takarba itama se juyi suke sun kasa bacci gaba daya haushin kb yagama cikasu jisuke inama ace zasu ganshi yanzu se sun hadu sunmasa dukan da se yagagara tashi, duk da sunsan sangarcewa irin tashi mom dinsa tagama san gartashi but basusan abun yakai hakaba yana kokarin lalata yayan wadan su da kuma son daura yayansu kan turban da bai daceba,

Nisha shiru tayi ta lumshe ido kamar mai bacci duk tanajin yanda su reeda suke juyi sun kasa bacci saboda damuwar dan uwansu,

itama bacci yaki daukarta gaba daya tausayin kamal da kaunarsa suna taba zuciyarta , kwata kwata batasan da kaunar da kamal yake mataba se yau da labari yasa tasani , to amma yanzu haryanzu yanajin sonta cikin zuciyarsa kamar yadda yafadi abaya ko kuwa yashafeta cikin heart dinsa yanzu Nisha tashiga tambayar kanta

🌴🌴 IG AJEEMAL 🌴🌴
Story and writing by oum amreesh ❤️

(Khaleeseart Raeeys)

Free book 🤗 to all my lovely fans

Page29_30

Duk da tasan abaya tasawa zuciyarta babu wani tunanin akan so ko soyayya cikin rayuwarta amma ko yanzu kamal ya gabatar da kaunarsa agareta zata amince dashi batare da wani jayayyaba,

saide yanzu tasan hakan ba mai kasan cewa bane because yanzu yana da mata kuma tasan sonda nabilah keyiwa kamal akwana atashi zai manta da wani sonta da yatabayi gashi yanzu zuwa gobema wata kila basa kasar se yanda tayi dashi,

da wadannan tunane tunanen bacci barawo yayi awun gaba da ita suma su fadeela tuni bacci

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login