Showing 57001 words to 60000 words out of 66967 words
bada Allah ya daidaitata ita Kuma Karimah babu ita a jadawali saboda kasancewarta qarama a gidannan na rasa ta Ina zan bullowa lamarin nan Allah kibani mafita"
Numfashi taja tare da yunqurawa ya taimaka Mata ta tashi zaune ta dubeshi tace “in advise ka cire jinin bayi Kuma karfa daga sashinka hakan zaisa ka rinqa samun matifa cikin rayuwarka Ja'afar don Allah kayimin wannan alfarmar inaji ajikina idan naci gaba da zama matsayin mata a gareka zamu wanzu cikin rayuwar qunci Koda kasancewar nasan duk wani Abu daya fado rayuwata to yardar sarkin sarkice Wanda baa masa dole,
Ja'afar bandamu da nakasance cikin farin ciki ba indai farin cikina zai tafa darajar wani shiyasa a rayuwata bancika damuwa da dole saina rabi wani ba tabbas abinda Hajiya Kaltume ta fada maka gsky ne Koda akasin hakan ne Toni na gasqata maka Ni yar bayice Amma ba qasqantattun bayi ba bayin Allah wadanda suke yarda da duk wani hukunci nasa a ban qasa Ina jiran ka yanke duk hukuncin da zaka yanke Allah na roqeka kada bakawa kowa ikon kawo gadon daraja idan hakan ta kasance ku koremu daga garin azare...."
Saurin rufe Mata baki yayi yana girgiza Mata Kai ta zabura ta miqe cikin bala'in da baitaba tunanin ta iyaba ta nunashi da yatsa tace masa “saime Ja'afar shine me danka kirani baiwa kuka ka kirani karfa Ina taka baiwar daka halitta sannan Ina taka karfar to duk abinda zakace ko a fada maka ka fadamin na shirya karbarsa Allah ya tsinewa Wanda ya fas...." Dauketa yayi da Marin daya sanyata kifewa a gadon daidai lkcn da Hajiya Innah ta shigo ta rafsa salati tace “meye hakan magaji bakada hankali zaka Kai hannunka jikinta yarinyar da ba lfy ta isheta ba meye ma ya farune"
Huci yakeyi kamar Wanda ya hadiyi maciji ya sake nunata da yatsa kawai sai ya juya ya fice a fusace Hajiya Innah ta matsa da sauri ta riqo Rafi'ah tace “meye ya farune kun ninkeni baibai fah" cikin kuka ta rinqa zayyanewa Hajiya Innah abinda ya faru taja fasali tace “to shine zaki tada hankalinki har kina daga muryarki sama da tasa bayan kinsan halin mijinki ko qalau yake ba hqr ya cikaba balle yanzu da kansa yake dawa Rafi'ah dole ke hqr ya Kama domin ke aka cuta"
Sosai ta rinqa kwantar Mata da hankali harda tayi shiru ta dauki jaririn ta fice dashi tunanin duniya ya damu Rafi'ah gabadaya komai ya daukar Mata zafi tanason ta samu wanda zatayi Hira dashi taji dadi babu Hajiya Innah ta saka Mata ido ko yan'uwanta ne sukazo bata barin dakin saboda kada ta fadi wata mgn da zata fallasa sirrin gidan sarautar tayi kuka kamar ranta zai fita ita daya kamata a rarrasa ita akewa tsawa harda mari saboda gskyrta wannan dare dukka bangarorin babu Wanda ya rintsa Ja'afar tunanin maganganun da Rafi'ah ta fada masa ne da Kuma mafitarsa da dansa ya hana idonsa rintsawa ita Kuma alhinin wannan jarabar rayuwa ta zaman qasqanci da boranci tun zamanin quruciya sune suka hanata rintsawa Hajiya Innah kuwa tunanin ta inda zasu bullowa wannan al'amari da yanda zaayi su samu gadon daraja ne ya hanata bacci inda Hajiya Fatsum Kuma bokanta yace daga ita har Ni'imah su tube tsirara kowacce a bangarenta su tsaya a tsaye su kwana a haka kada suyi gyangyadi domin sunayin bacci asirin da suka qullo na haukata Rafi'ah kansu zai koma itakuwa Hajiya Kaltume neman ta inda zata fara bullowa Ja'afar da iyalinsa ya hanata rintsawa Abu na farko daya kamata tayi shine tasan yanda zatayi ta qara shiga tsakaninsa da Rafi'ah sannan ta sace wannan jariri kafin wayewar gari.
Kiran sallar asubar farko Rafi'ah ta tashi da wani matsanancin ciwon Kai ta riqe kan da sauri tare da fara karanta izaja'a ta dan samu relief daidai lkcn da taji an bude qofar an shigo kasancewar da duhu bataga me shigowar ba ana gama shigowa Kuma sai aka haskenta ido da wata fitila me masifar haske ta yunqura zata miqe abinka da mara cikkakiyar lfy sai tashin ya gagara ta rintse idonta daidai lkcn da taji an watsa Mata wani ruwa anyi baya da sauri.
Aikuwa saita wani yi tsalle ta miqe ta qwallah qara tare da damqar jaririn ta qanqame Hajiya Innah da Ja'afar har gware sukeyi wajen shigowa, Hajiya Innah ta kunna glub ta rintse idonta da sauri saboda tashin hankalin data gani inda Ja'afar ya nufeta a guje yana fadin “ Innanillahi wa innah ilaihirraji'un Rafi'ah meye hakan lfyrki kuwa tsirara fa kikayi...." Daukeshi tayi da wani mahaukacin mari tana qara matse danta a qirjinta tana wata dariya me hade da kuka tana cewa “ina ruwanku munafukai azzalumai algungumai dukkanku saina kasheku duk Wanda yazo gurina saina harbeshi danane ni na haifi abuna babu me rabani dashi daga yau nasa masa suna mai martaba Muhammadu Mahir eh sunansa kenan sunansa kenan Allah sunansa kenan dana sunansa kenan Ja'afar ya mutu Mahir maraya ne hhhhhhh Ja'afaru ka mutu ka huta nima na mutu na huta kowa ya mutu ya huta..."
Wani baqin tashin hankali da dimuwa Ja'afar ya shiga ya matsa gurinta saikuwa ta rarumi kaskon wuta ta jefosa dashi tana qyalqyala dariya tana cewa “bazan baka danaba nawane ni kadai kufice ku fice nace ku fice ko na yankaku na shanye jininku hhhhhhh suwaye nan kowa bayasona Ni inason kowa kowa bayaqina ni inaqin kowa..….."
Tashin hankali yasa Ja'afar yin kanta a guje aikuwa suka Kama kokawa daqyar yayi nasarar karbar yaron ya miqawa Hajiya Innah da taketa sallallami da kuka ya dauki doguwar riga yasa Mata ta hankadeshi ta miqe ta nufi qofa a guje shima ya bita yasawa qofar key ya daka mata tsawa itama kuwa saita daka masa tsawa tare da fuzge ribbon din data kame gashinta dashi ta kurma ihu tana wani dukan iska tana cewa “ni kubani dana Babu inda zaa kaimin dana abani abuna ...." Hadata yayi da jikinsa ya rungumeta sosai a jikinsa kawai saiya fashe da kuka ya bude baki yace “wai... Waime kikeyi ne haka Rafi'ah meye yake damunki ne bakiga bakida lfy bane...." Hannunta ta dora a bakinta tace “shitttttt ni qalau nake nafika nafi babanka nafi babarka lfy ba sunana Rafi'ah ba sunana Deluwa yehhhhh Deluwa takan bola Deluwa takan titi Deluwa ta kowac...."
Hade bakinsa yayi da nata ta kuwa gasa masa cizo ya janye da sauri harshensa har saida ya tsage ya koma gefe yana kallonta Hajiya Innah daketa salati ta Kiran sunayen Allah tsarkaka tace “sai hqr Ja'afar sun haukata maka Mata innanillahi wa innah ilaihirraji'un....." Dagowa yayi da sauri yace “wht hauka Kuma Innah wanne irin hauka" sake kwashewa Rafi'ah tayi da dariya tace “eh da gaske ni mahaukaciya ce daga yau sunana Deluwa mahaukaciya yar macukule...........
Zubewa yayi rijib a qasa sumamme tsabar tashin hankali Hajiya Inna tayi wajen gdan a guje tana ihu tana Kiran a kawo Mata dauki nan hadimai sukayo ciki a guje daidai lkcn da Jamal ya shigo gdan shima isowarsa kenan daga Rasha ya tawo ganin dansa dan yayansa da matar yayansa da baitaba gani ba ya siyo gadon da aketa badaqala akan samuwarsa sannan ya hadowa matar yayansa kayan fitar suna akwatu guda.
Tun daga bakin qofa yasan gidan babu lfy yana shigowa yaga wata mace ta fice qunshe da Abu a hijjabinta da mugun gudu ganin yanda gidan yake a hargitse ga Kuma gajiya yasa baibi takanta ba ya nufi cikin gidan inda ya hangi mutane dodo guda a qofar bangaren Hajiya Innah haka ya rinqa kukkutsawa har ya Isa cikin part din wata muguwar faduwar gaba yaji lkcn daya riski yayan nasa warwas a qasa kamar matacce aikuwa wata alkafura yayi ya dira kansa ya fara danna Masa qirjinsa tare da neman ruwa ya fara quga Masa tsayin lkc sannan ya fara sauke ajiyar zuciya ya bude bakinsa da sunan matarsa.
Sai lkcn aka ankara da bata cikin dakin aikuwa nan aka bazama nemanta lungu da saqo Amma Babu ita babu lbrnta Jamal ne yace lkcn da Yana shigowa yayi karo da wata mace ta fice daga gdan a guje Amma baibi takanta ba ya zaci mahaukaciya indo ce, salati Innah da Mai martaba dama sauran mutanen dake gurin suka dauka Ja'afar kam hade Kai yayi da gwiwa duk wani tunani ya qwace masa baimasan meye zai tuna ba a hankali yace “suwaye suka haukatata me tayi musu suka azabtar da ita da ciwo me cin zuciya da lalata ruhi Ina zata Ina take me suke nema me tayi musu sun illatata......."
_Hqr My Fan's am sick wlh_
_More comments_
_More Typing_
*_47-48_*
_____________________________
_____________________________
Shiru ce ta ratsa gurin na dan wani dogon lkc kowa zuciyarsa na searching abubuwa da dama mabambamta, zumbur Ja'afar ya miqe ya nufi qofa zai fita Mai martaba ya rufa masa baya shima Jamal miqewa yayi suka fita daga gdan duk wani guri da suke tunanin rafi'ah sun kasa samunta wasa wasa sai ga lkc yanata tafiya har goma na safiya shikam Ja'afar ya zamana kamar wani robbot ko bakinsa bai iya budewa sai tafasa da zuciyarsa takeyi.
Mai martaba ne yace da Jamal su juya suje gdansu Rafi'ah sugani ko taje can hakan ce ta faru suka nufi gidansu Rafi'ah Mai martaba yasa akayi masa sallama da Abba dake asabar ce Abba ya fito ganin Mai martaba da kansa yasashi qarasowa da saurinsa yanayi musu sannu da zuwa yanda yaga dum jikinsu a sanyaye ya fadar masa da gaba yace “meye yake faruwa ne naga kamar Kuna cikin damuwa?"
Ja'afar ne ya magantu a karon farko yace “Rafi'ah batazo ba ko Abba shikenan na shiga ukuna ta shiga duniya Ina zataje hannun wa zata fada....." Jiri Abba yaji yana dibansa yayi saurin matsawa jikin motar yace “ban fahimta ba Ina Rafi'an ta tafi da danyan jego?"
Mai martaba ne ya zame rawaninsa ya goge gumi yace “wato yau mun tashi da wani iftila'i ne Alh Nuhu lfy Lau muka kwana da Yarinyar nan Amma da asuba sai ta tashi da wani yanayi me kama da samuwar tabuwar kwakwalwa hakan tasa mijinta yanke jiki ya fadi wai kafin a samu a shawo kan tashi matsalar baa ankara ba ta sulale ta dauke danta ta fice munyi yawo sosai a garin nan tun asuba muke zagawa ko zamuyi katarin ganinta Amma Babu ita babu alamarta duk inda muka tambaya sai ace baa ganta ba to shine mukayi tunanin ko nan ta taho Kuma gashi alamu sun nuna batanan"
Durqushewa Abba yayi yana furta Hasbunallahu wani'imal wakil cikin mummunan tashin hankali miqewa yayi ya bazama gidan da sauri ya zaro wayarsa ya fito suka sake fita sune police station sune transport agent Amma Babu wani lbr me dadi saina godiyar Allah kawai ranar yini sukayi ko ruwa basusa a bakinsu ba Basu suka hqr ba sai taran dare suka koma gda kowa zuciyarsa cike da matsananciyar damuwa suna komawa gida Ja'afar ya shige bangarensa abin mamaki saiya tarar da Ni'imah a parlourn taci uwar kwalliya tana jiran dawowarsa.
Baikobi ta kanta ba ya shige ciki ya bude dakinsa tare da dauko key din daya dakin na Rafi'ah ya datse ya koma dakinsa ya haura kan gado ya hada tagumi yanajin wani zugi da radadin zuciya da bashi da misali baiji shigowarta ba saiji yayi tana wani shafa sumarsa ya dago idanunsa da suka kada sukayi jawur ya saukesu akanta take taji tsoro ya lullubeta Amma saita dake tace “we meye na tada hankalin hakane bafa wani hauka da takeyi tsabar iskanci ne dama ba sonka takeyi ba shine take neman hanyar rabuwa dakai cikin sauqi...."
Dagowa yayi ya sake saita injin idonsa akanta sosai take a tsorace Amma batason tabar zuciyarsa ta zauna kurum kamar yanda mahaifiyarta ta qyara Mata idan ya dawo tasan duk yanda tayi tasashi jin haushin Rafi'ah ta hanyar nuna masa tana sane ta Kama hauka don ta samu damar guduwar masa da dansa, hawaye ta dauke tace “na dade Ina jiye maka zuwan wannan ranar saidai Kai ka kasa fahimta Koda yake nasan bayin kanka bane asiri ne ke dawainiya dakai badon haka ba mema zakacj da Rafi'ah Ja'afar nidai Ina baka shawara ka cireta a ranka muci gaba da rayu....."
Tsawa ya daka Mata tare da daga hannu zai dauketa da Mari sai Kuma ya fasa ya miqe tare da shigewa bathroom ya sakarwa kansa ruwa yana furzar da iska ya fito tana zaune inda ya barta yaja dogon tsaki ya dauki doguwar rigarsa yasa ya fice daga dakin ya bude Wanda ya rufe dazun ya shiga ya tada sallar nafila ya nata jerawa ba qaqqautawa bayan ya idar ya jima yanayiwa Rafi'ah da Mahir fatan fadawa hannu na qwarai.
Alqur'ani ya dauka fara karantawa zuciyarsa na karyewa sosai yanajin yanda ruhinsa ke ciwo tabbas yasan a zaman da sukayi da Rafi'ah wata ukune kawai sukaji dadinsu watanni biyar duk sun tafi a banza ne to ko watsin da yayi da ita da rayuwarta a lkcn da tana da cikin ne yasats yanke Masa wannan hukuncin na rabashi da kanta da gudar tsokarsa Mahir?
Tambayoyine da bashi da amsarsu hakadai ya rinqa zauniya Koda yayi abinda ya sawwaqa cikin karatun qur'anin saiya rufe ya rafsa tagumi yanajin yanda jikinsa ke daukar zafi alamun damuwa ta fara ratsa bargonsa ta zuba Masa ciwon gabobi da zazzabi me zafin narkar da nutsuwar ruhi.Zamewa yayi ya haye gadon ya kwanta yanajin yanda jijiyoyin kansa suke wani tartsatsin wutar azaba qwanyarsa tana neman tarwatsewa gashi Babu mataimaki sai Allah yaji sanda Ni'imah ke buga qofar yayi Mata banza saboda baisan meye yasa ba tunda ya dawo Azare ya barota a Abuja ganinta ma bayason yi idanma ya kalleta gabansa faduwa yakeyi.
**********
Baiwar Allah Rafi'ah kuwa lkcn data fita daga gidan sarautar da asuba ta yanki shara a guje gudu takeyi na wucce saa da danta qunshe cikin towel ta sake qudunduneshi da hijjab dinta haka taketa keta dajin batare dako takalmi a qafarta ba haka take gudu a jeji gar ta fita daga Azare gabadaya ta shiga wani jeji me surquqi ta rinqa gudu ba qaqqautawa tana cilla qafarta ko Ina qaya zafin Rana baisa ta sunkuya, babban tashin hankalin idan ta waiwaya baya sai taga wuta naci a bayanta ganga ganga tana lasota haka zata qara zabura ta kwasa da gudu tana abbaton ya Khaliqu yini tayi ranar tana gudu babu ci babu sha ga cikinta inda akayi Mata aiki daketa azabar ciwo Amma Babu hankalin ta tsaya Abu daya da ya kasa mantuwa a ranta shine tasan idan taji danta ya motsa ta qara matsesa hankalin ta bashi abinci kuwa babu.
Ba ita ta samu ta daina ganin wutar ba saita ta wucce dambam ta shiga wani dajin shima shikuma ruwane yake binta da mugun gudu yanason cinyeta haka suka rinqa tsere da ruwan sai dare Allah ya kaita rugar wasu fulani da farko da suka ganta sun tsorata ita kuwa tana zuwa taga wata dattijuwa tana matsar nonon saniya sun hadawa shanu wutar jin dumi aikuwa sai ta nufi dattijuwar nan ta tsaya akanta matar ta miqe da sauri a tsorace ganin mutum a kanta murmushi tayi kamar me hankali sai ta yaye hijjab dinta ta budewa Mahir fuska ta miqawa dattijuwar ta bude baki zatayi mgn abin mamaki sai bakin ha harde ta kasa mgn.
Tayi tayi tayi mgn ta kasa kawai sai hawaye ya wanke mata fuska ta zube a gurin tanata kakari a dole mgn takeson yi ta kasa Abu daya da idan ta dage take iya fada shine Mahir Ya Khaliqu bayan wannan komai ta kasa furtawa, nan fah gurin ya cika taf da mutanen rugar daidai lkcn da wata arniyar mota ta parkar a bayansu kadan an jima baa fito ba can aka bude aka fito wani kyakkyawan matashin attajiri ne a qallah zaiyi shekaru arba'in da biyar ya nufo rugar dauke da wata jarka a Hannunsa mamaki ya cikashi na ganin yanda mutanen rugar suka kewaye guri guda,
Hakan yasashi saurin qarasawa idonsa ya sauka akan Rafi'ah da ta hada uban tagumi tanata gunjin kuka so takeyi tayi mgn ta kasa hakan yasata dole ta Kama kuka tsayawa yayi daga baya kadan ya zuba Mata idanunsa a mamakance ya juya ya kalli wani mutum yace “Moddibo wannan fah daga Ina?" Dagowa Moddibo yayi yace “wlh bamu sani ba kawai yanzun nan tazo ta miqawa Gwaggo Hinde jaririn can tanata qoqarin mgn Kuma ta kasa" sake kafeta yayi da ido ya matsa gabanta ya tsugunna yasa hannu ya dago kanta Saida gabansa ya fadi ganin irin kyawunta da quruciyarta kawai sai ta fada jikinsa ta sake sakin wani kuka tana shan zuciya tuni zuciyarsa ta karya ya cika da tausayin baiwar Allan tabbas yanayinta ya nuna ba daga qaramin ahli ta fito ba, haskata yayi sosai da fitilar wayarsa tana kwance a jikinsa ya dago ya kalli Gwaggo Hinde yace “Ina tunanin Jaririn nan dantane kijata ki kaita dakinki ki bata abinci da ruwa tayi wanka amma ta fara shayar da jaririn Nan akwai wani boyayyen qulli cikin lamarin yarinyar nan idan ta huta zuwa safiya zanzo zan dauketa na tafi da ita Gombe"
Tsalle Hinde tayi taja baya tace “Oye aradun Allah banni samkarta Niko shedai ka tahi da itan tun yau hakanan abuda munaji a gari ana yanke kawunan mutane nasani ko aikota akayi ta yanke kaina don anga zayayi tsada....” saurin kallonta yayi yace “haba Gwaggo da ganin yarinyar nan kinsan badaga qaramin gida takeba Kuma tana buqatar taimako idan kika taimaka Mata kema Allah zai taimakeki Kuma bakisan abinda Allah ke nufi ba ya kawota nan rugage nawa ta tsallake bata tsaya ba sai anan"
Sake ja tayi da baya tare da miqa masa jaririn tace “kaidai da kaji kana iyawa ka dauka nikam bani iyawa...." Alh Hashim irin mutanen nan ne masu zuciya kawai saiya Kama hannun Rafi'ah ya miqar da ita yace “ok ki zubamin danyar madara a kawomin mota Amma ki taimaki yaron nan ki bashi ko danyan nono ne dafaffe yasha akwai alamun bata Sami hayyacin bashi abincinsa ba" shima Hinde taso ta musa Saida Moddibo ya shiga mgnr sannan ta yarda ta dauko qaramin Kofi ta tsiyayo dafaffiyar madarar shanu Moddibo ya kawo Zuma akasa a ciki akayi kwakkwaro da ganyan ayaba