Showing 9001 words to 12000 words out of 92896 words
Idris.
Da sauri yasaki hannun mutumin batare da yajira yakarasa fad'aba yajuya da sauri.
A can cikin gida kuwa da sauri Aunty Rafee'at tafito daga kichin in da suke rabon abincin ba'i d'akin Inna tanufa da sauri Jaleela tagani tsaye ga dukkan alamu abinda kunnuwar ta suka jiyar Mata suma shi sukaji. Inna kuwa sai tafa hannu take tana fad'in
"Amma ko mutanen nan sunsan abun da suka fad'a kuwa ya za'abasu d'auren auren Masa'udu su d'aura da maisunan Malan maza kirawo min Idris da Shu'aibu".
Tafad'a tana mika musu wayar
Aunty Rafee'at kam kasa karb'ar wayar tayi sabo da tsananin damuwar da tashiga Aunty Jaleela ce takarb'a takira numbern Abbu Yana fara ringing Tamika Mata Inna takara wayar a kunne dai-dai Nan Abbu yad'au wayar da sallama zatayi magana yayi saurin cewa "yihakuri Inna gamunan shigowa cikin gidan".
Batareda b'ata lokaciba su Abbu suka shigo cikin gidan direct d'akin Inna suka shige su Aunty Jaleela suka fita suka Basu guri
Aunty Rafee'at dai gabaki d'aya jikin ta yagama yin sanyi Bata iya komawa kichin in ba sai shigewa tayi d'akin *HAMDAH*.
Su Abbu suka Sami guri suka zauna tunkan su idda zaman Inna tafara fad'in
"menakeji haka ko kunyi mantuwar sunan ne kuka bada na Mai sunan Malan?".
Abbu ya ce "a'a Inna ba mantuwa mukayiba da shi *SALEEM* in aka d'aura auren".
Salati Inna tashiga yi tana tafa hannu ta ce "akan wani dalili zaku sauya daga kan Masa'udu ni dama nasan bason auren Nan kuke ba to kuyi duk Yan da kuke so".
Yunkurin mikewa Inna tashiga yi tana cigaba da fad'in "natara jama'a akan da Masa'udu za'ayi aure kuzo ku canza".
Girgiza Kai Abba yy tareda yin murmushi a b'oye ya ce "Inna kiyi hakuri ki sauraremu".
Abbu ya ce "Inna ke kikace kinason mijin da zai rike Miki *HAMDAH* Yakuma yihakuri da Jin bakin ta shiyasa mukayi nazari idan akace za'a had'a Masa'ud da *HAMDAH* aure to lallai bazaki Sami a binda kikeso ba Dan dukkanin su yarana Masa'ud shekarun sa 24 yanzu Kinga kuwa zaiyi wuya ya'iya rikon *HAMDAH* yanda kkso saboda karancin shekarun sa,shiyasa muka sauya daga kansa zuwa kan d'an uwansa
Kinga shi *SALEEM*
ya mallaki hankalin kansa shi zaifi riketa fiye da Masa'ud in".
Shiru Inna tayi a'lamar nazari zuwa can ta ce
"To wato da Mai sunan Malan in kenan? Amma dai zakuyi Masa kashedi a Nan ma kenan yake bugunta kamar jaka Ina Kuma ga taje gidansa".
"Bai Isa ya tab'a taba Ko da taje gidan nasa".
Cewar Abbu.
Gidan yafad'o baya ko kallon gaban sa tundaga tsakar gida yake kwallawa Inna Kira har ya'iso cikin parlour Bai fasa Kiran nataba yatura kofar d'akin ta yakusa kansa ciki Yana fad'in
"Inna nasan duk Shirin kine Wannan akan me za'a zantar da hukunci batare da saninaba ni nace Miki Ina bukatar karin aure ne to wlh bazai yuwuba!".
tsawan da Abbu yabuga masane yasashi tattaro nutsuwarsa yamai dashi kansa cikin d'aga murya Abbu ya ce "mahaifiyar tamu kk d'agawa murya Kai ka haifemu da har saimun nimi yar darka kafin muzantar da hukunci a kanka!".
Sunnkuyar da kansa yy Dan baiyi zaton dasu Abbu a cikin d'akin ba.
fad'a sosai Abbu yashiga yi Masa Yakuma d'aura dafad'in "yau Kuma zata tare a gidan ka kaje kabud'e d'aya part in da ke gidan ka shine mallakin ta aciki zata zauna".
Abbu na kaiwa Nan yamike yafita Aunty Rafee'at da Aunty Jaleela yakwad'awa Kira suka fito da sauri, Abbu yadubesu ya ce "kuje yanzu direba yakaiku Bauchi gidan Yayan ku kuje kugyarawa *HAMDAH* d'akinta".
Suka amsa da "tom"
Sannan yakalli Goggo Hauwa ya ce
"Kibisu susaukeki a gida kuje kuyimata siyayyan kayan d'aki ".
Itama "tom"
Ta'amsa da shi, sannan yajuya yafita Yana Mai danna numbern Mamie tana d'agawa ya ce
"Kiyiwa Hajiya Fatima magana Hauwa zatazo sai kunimi wasu daga cikin Dan ginku kuje kuyiwa *HAMDAH* siyayyan kayan d'aki".
Mamie ta ce "to Amma Alhaji dawuri haka ai gara a Bari sai lokacin tarewan nata".
Abbu ya ce "yau zata tare a gidan *SALEEM* Dan dashi aka d'aura ko ba'a gama siyayyan yauba zata tare inyaso daga baya a Kai kauran".
Yasauke wayar a kunnen sa tareda katse kiran..........
_NAGA INGAN TACCEN COMMENTS DA SHARHI IN BA HAKABA NAKUMA D'AUKAR HUTU_
Mommyn Twins ce
*🌺HAMDAH🌺*
*NA*
*RASHEEDA S DIRECTOR*
_(Book one)_
*_________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association
*_________________________________*
MARUBUCIYAR👇🏻
*BA ABIN DA BAN GANI BA*
*INA SANE DA HAKA*
*ALFARMA*
*BAZAWARA CE ITA*
AND NOW👇🏻
*HAMDAH*
Free page
My no 08034690723
🅿️5
Har Abbu yafita *SALEEM* natsaye yakasa Ko da motsawa ne, Abba yamike ya dafa kafad'ar sa ya ce "jeka ai watar da a bin da a ka umur ceka".
Jiki a sab'ule yaja kafar sa yafita a d'akin,
Inna zatai magana Abba ya daddanne ta tahanyar ban hakuri.
Yana fita motarsa yashiga yy Mata ki yad'au hanyar bauchi, su Aunty Rafee'at ma tuni direba yy gaba da su sabo da gudun da yake kusan a tare suka shigo gari,
gidan su Abbu suka fara rasawa Dan sabo da su sauke Goggo Hauwa.
Yana dai-dai ta parking yafito yanufi ciki direct babban parlour yashiga Na'ima yagani tsaye da mayafi a kanta sai Kai kawo take a cikin parlourn yasan za'ayi haka Dan yanada tabbacin zuwa yanzu rahoto ya iso Mata.
Kokarin wuce wa yake
Da sauri ta iso in da yake Tasha gaban sa tazuba Masa idanuwan ta masu d'aukeda zunzurutun matsanan cin kishi ta ce
" *SALEEM* abin da zakamin kenan da irin Wannan mummunar sakayyar zaka sakamin! Amma wlh *SALEEM* kabani mamaki".
Jan yota yy jikin sa yatallafe fuskarta da tafukan hannun sa cikin irin yanayin sa yamosa laɓɓansa yasoma magana.
"bayin kaina bane yin mahai fanane".
Kawar da kanta tayi yayin da zuciyar ta ke kuna takuma Mai da duban ta kansa ta ce
"Meyasa ka Amin ce tun da bayin kan ka bane? wlh bazai tab'a yuwuwa ba Dan ban shirya zama da kishiyaba *SALEEM* Kai nawane ni kad'ai babu wata macen data Isa ta rab'eka kakoma kace musu bakaso".
Cire hannun sa yy daga fuskar ta yajuya yasoma tafiya Yana fad'in
"bazan iya zuwa nafad'a musu Wannan kalmarba yazama dole nayi musu biyayya kuma kema haka".
"Munafurcin banza da ma can kanaso in ba hakaba to kaki Amin cewa Mana wlh-wlh har idan yarinyar nan tatako gidannan masifa da bala'i yanzu yasoma!".
Tafad'a tana wani irin huci Mai d'auke da tsananin kishi.
Bai Kuma juyowa ba yashige cikin d'akin sa
ya Isa gefen gado yaja durowa yad'au makullin d'aya part in da Abbu ya ce yabud'e ta kofar part in San nabaya yafita batare da yabi ta babban parlour ba.
Na'ima kuwa ci gaba tayi da zuba ruwan bala'i da fad'an miyagun kalmomi gaba ki d'aya idanunta sun gama rufewa da sananin kishi.
Yana bud'e kofar part in motar su Aunty Rafee'at yashigo gidan wucesu yy yashige motarsa yabar gidan.
Suna shiga share-share da goge-goge suka sunkuyayi basuwani Sha wahalaba suka gama kasan cewar bawani datatti gurin yy ba Dan duk bayan wata d'aya uban gayyar yakan sa a bud'e part in a share a goge.
bayan la'asar wata jibgegiyar motar kamfanin da su Mamie sukayi odar kayan d'aki tafaka a farfajiyar gidan cikin han zari ma'ai katan kamfanin suka saussauko daga saman motan Nan suka fara sauke kayan Aunty Jaleela ce tafito tayimusu jagora zuwa ciki batare da b'ata lokaciba sukafara shirya kayan a duk in da yakamata yamma lis su Aunty Rafee'at suka koma Dass sukabar ma ai katan suna karasa sauran ai kin.
Da sauri Aunty Rafee'at tayi d'akin HAMDAH Dan tun d'azu take ta so tazo taga halin da take ciki Koda tashiga bb kowa cikin d'akin har tajuya zata fita taji motsin ruwa a bayi da Kuma magana had'e da dariya,
Komawa tayi cikin d'akin tazo jikin marfin bayin karar ruwa sosai takeji alamar dai wasa da shi take sai muryar ta da taji tana fad'in
"Tun da gube ba makaranta gudu zanyi Inna Bata sani ba naje lambun Baba na lambu irin ruwan lambun shi yafi dad'i".
Sai takuma sakin dariya.
Baki Aunty Rafee'at tabud'e tare da girgiza Kai "yarinta dangin hauka".
Tafad'a a fili
Bubbuga kofar bayin Aunty Rafee'at tayi ta ce "ke HAMDAH magana kk a cikin bayi to kiyi maza ki fito".
D'aukar boket in ruwan nayi najuye shi a kaina sannan naja zanina nad'aura nafito.
"La Aunty Rafee'at tun d'azu naketa dubaki ban gankiba"
Hannuna tariko tana fad'in "taho Nan kinje kin zauna cikin bayi kinata surutu maza sa kayanki".
Na ce "tom"
Saita saki hannuna tayi waje zuwa can ta dawo lokacin har nagama sa kayan Ina kokarin fita ta ce "yauwa harma kin shiryan nad'auka ai shiririta kk tsaya yi".
Tariko hannuna mukayi waje d'akin Inna muka shiga tana zaune a bakin gado tana ganina tamiko hannu tana fad'in "toho Nan takwara yau Zaki barni".
Na Isa nazauna kusa da ita bakin zanin ta takama tana share 'yar guntuwar kwallar dake kasan idanunta cikin Jan hanci ta ce
"Kizauna lfy a gidan auren ki kiyi taka san-San da Mai sunan Malam in kk ce zakije kina nuna halin Nan naki dukan tsiya zakisha a hannun shi tun da ba imani yake da Shiba barema yaga bb idon kowa ai sai in da hali yy kawai, dole nakira ubanen ku nakuma jaddada musu Sam ban yar da ba, ban yar da da maganar dukaba".
Ido naware gaba d'aya a kan Inna Kamar Mai nazari nad'aura yatsa kan kumatuna Ina d'an girgiza kai na ce "Inna wa kk ce? Mai sunan Malam kk ce Ya SALEEM fakena".
ta ce "E 'yarnan ai na man ce ne ban sanar mikiba ai auren da shi aka d'aura ba da Masa'udu ba".
Huf na mike tsaye na ce
"Allah Inna ban yar da ba kice da Ya Masa'ud za'ayi Mana aure tukun yanzu kice da Ya SALEEM toma nidai wlh ban yardaba nafasa auren".
Nashiga bubbuga kafa a kasa,
Aunty Rafee'at ta kalleta tareda girgiza kai HAMDAH namatukar Bata tausayi idan tatuna cewa kan kishiya za'a kaita yarin yace Mai cikeda d'in bin kuruciya.
Aunty Jaleela ce tashigo d'akin dasauri rikeda waya a kunnen ta tana fad'in
"To Abbu".
sai tasauke wayar tadubi Aunty Rafee'at ta ce
"Wai mufito ga mota najiran mu inji Abbu".
Aunty Rafee'at tamike tsaye tare dafad'in "tom" takamo hannuna ta ce "toh Inna mudai mun tafi"
Inna ta ce "to HAMDAH kin daiji abin da nafad'a Miki kinutsu kizauna ban da rawan Kai Allah yabaku zaman lfy".
Na ce "cap Allah Inna sati d'aya zanyi nadawo tun da dai bamuyi haka da keba".
Inna dai cigaba da share d'an guntun kwallar ta tayi Bata Kuma cewa komai ba Dan har cikin ranta take Jin rabuwar da zasuyi da HAMDAH.
Muna fita cikin parlour Rabi na shigowa da sauri takaraso In da muke tsaye Aunty Rafee'at suna magana da wata cikin kasa da murya ta ce
"HAMDAH Ya Maheer yazo Kinga wayarsa yanzu naje na anso Masa a gun cj".
Da sauri na ce "haba zo muje d'akina mukalli soyayyar".
Nafad'a Ina kokarin janye hannuna dake rike a hannu Aunty Rafee'at".
Itako tadad'a rikeni gam tareda janyoni mukafita.
Tirjewa nayi na ce "Aunty Rafee'at kutafi kawai nikam kallo zamuyi".
"taho muje in kinje can d'in kyayi kallon".
Tafad'a tana turani cikin mota Baki natura a raina nake fad'in "yanzu shikenan kallon soyayyar Nan yashige ni? yanzu idan Ya Maheer yakoma kafin in dawo A'i na kuma zan sake kollon soyayyar oho, gashi kuma ba Ya Masa'ud bane aka Mana auren da shi bare muje muyi soyayyar".
Murmushi ne yasub'uce min lokacin da zuciyata takawo min wani tunani nakuma gyad'a kaina alamar gaskata a bin da zuciya ta bijiromin da shi "sai muyi da Ya SALEEM in kawai".
Sai kuma na kwab'e fuska Ina tantama akan a binda zuciyata keta sakawa da kwan cewa.
Jin karar tsayuwar motar ce yadawo Dani daga duniyar tunanin danatafi
Da mamaki nake kallon gidan wai yausheni muka taso da har mun iso duk da dai nasan sakanin Dass da Bauchi ba nisa Amma dai tafiyar tayimin sauri.
Motoci uku ne aka taho da su d'aya motar data d'auko mu sai wacce tad'auko 'yan'uwan Ummi da Mamie d'ayan Kuma 'yan'uwan Inna ne had'eda makota.
A tare mukashiga ciki kowa sai San barka yake da tsaruwan part in, duk da ai kin Rabin wuni ne amma Bai Hana part in tsaruwa da d'aukar Ido ba, Dan kwararrun ma ai katane sukayi ai kin cikin kuma kan kanin lokaci suka gama Dan ai kine bana mutun d'aya ko biyuba surai wajan goma ne.
Ko zama mutane basuyi ba diraibobin sukace 'yan Dass sufito sumai dasu a cikin Daren suka juya dasu 'Yan cikin gari ma kowa takama gaban ta mukarage dagani sai Aunty Rafee'at da Aunty Jaleela.
Wanka Aunty Rafee'at tasani naje nayi Ina fitowa Tamika min Mai nashafa sannan na d'au kayan bacci da ta cire min shi nasaka suna zaune nagama kimsawa tsaf.
Duba a gogo tayi "ta ce Jaleela inaga mukwana kawai kin ga yanzufa karfe 12 ko munfita ma ba lailai bane musami a bin hawa gashi Kuma diraiba yatafi".
Aunty Jaleela ta ce "to shikenan".
Nidai gado nahaye ba jimawa bacci yad'au keni.
Washegari Ina salla nakuma komawa gado su Aunty Rafee'at fita sukayi sukaje suka kikkim sa Mata cikin parlour zuwa kichin da bayin parlour duk da dai baiwani yi datti sosai ba zuwan ba'in jiyane gurin yad'an hargitse
Sannan suka had'a breakfast mafi sauki suna gamawa suka komo d'akin Aunty Jaleela tamaso bakin gadon tad'aka Mata duka.
Firgigit nafarka tareda mikewa zaune Ina shafa inda tabugan,
Baki naturo na ce "Toni menaki?".
Ta ce "banza kin kwanta sai sharar bacci kk kin d'auka Nan d'in gidan Inna ne to Nan bb Mai yimiki Dole ke Zakiyi Koda cewa akwai Mai aiki a gidan yazama dole wani abun kezakiyi".
Aunty Rafee'at ta ce
"kyaleta Jaleela tashi kije kiyi wanka kizo kiyi break".
Namike Ina kunkuni nashige bayi.
Bayan nayi wanka nasa kaya nazauna gefen Aunty Rafee'at nasoma cin breakfast in da ta had'amin Ina gamawa ta ce min nakwashe plt in nakaisu kichin nakwashe nakai Koda nadawo ganin su nayi sanye da mayafi nakaraso in da suke Ina fad'in "Ina Kuma zaku?".
"Zo zaunan Nan".
Aunty Rafee'at tafad'a tana nunamin gefen ta,
Nazauna tadubeni ta ce
"To mu zamu tafi sai in an kwana biyu zamu zo muduba ki HAMDAH".
takuma Kiran sunana na ce "na'am". Ta ce "HAMDAH kirage kiuya idan tayi yawa itake janyo kazan ta da safe kina sallah kada kikoma ki kwanta harsai kin share part inki kin gogeshi kin samasa turare, idan Ya SALEEM anan yake to kitabbata sai kin had'a Masa breakfast tukun idan Zaki kwantan nema saiki kwanta,
Kinsan Ya SALEEM yanada son Shan tea in dare to kidage zan kawo Miki kayan kamshi wad'an da ake girka shayi dasu sai kirika girka Masa dasu".
Shuru nayi Ina kallon ta ni duk tunanina ma yatafi kan shara da goge-gogen data fad'a
"Na ce "Kai Aunty Rafee'at duk ni kad'ai zan Rika sharewa da gogewan tap yaushe zan iya".
"Waye da kk tunanin zaizo yamiki to kada Allah yasa ki'iya Aunty Rafee'at kyaleta kada tayi tasan halin Ya SALEEM ai Sarai Allah yasa kullum yarika nakad'a Miki duka tunda ke idan aka fad'a Miki magana bakyaji tashi mutafi Aunty Rafee'at kada tayi".
Aunty Jaleela tafad'a tana mikewa tsaye,
Murmushi Aunty Rafee'at tayi Dan tasan garunsu baya hawa akwai 'yar tsama na sako da sako sakanin su duk da cewa Jaleela tabaiwa HAMDAH tazaran shekaru dad'an dama.
Aunty Rafee'at Bata Bari sun bar gidan ba harsai Dana Mata alkawarin zanyi duk abin da tasani hardama wad'anda takara d'auramin su akarshe, har bakin get narakasu dafari nace ni zanbisu Aunty Rafee'at tace nazauna ita zatazo gobe Ina tsaye harsai da naga sun shiga nape kafin najuya nakoma ciki, nasa kaina zan shiga parlour sai ganin Aunty Na'ima nayi tsaye cikin parlourn rikeda wuka a hannun ta tana ganina tayi kaina..............
HHHHHH🤔 uhum Bari nayi shiru nafece🏃🏻♀️
Mommyn Twins ce
*🌺HAMDAH🌺*
*NA*
*RASHEEDA S DIRECTOR*
_(Book one)_
*_________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association
*_________________________________*
MARUBUCIYAR👇🏻
*BA ABIN DA BAN GANI BA*
*INA SANE DA HAKA*
*ALFARMA*
*BAZAWARA CE ITA*
AND NOW👇🏻
*HAMDAH*
*Free page*
My no 08034690723
🅿️6
Kara nakwalla ganin tayi kaina tana juya wukar,
kafin nayi yunkurin gudu harta isoni tashako kwalata tad'aga wukar takawoshi daf da fuskata,
tana cigaba da juyashi,
tsananin tsoro had'eda firgici su suka dirarmun kad'an yarage nasaki fisari a jikina, duk wani barazanar da Inna takeyimin nazata yankani Bata tab'a d'aukar wukan har takawoshi kusadani irin hakaba.
Wani gigitaccen Kara nasake Mai cike da tsananin tsoro nadaddage narike hannunta data da ta shako wuyata da shi, da ƙyar na iya sun kuyar da kaina na yanka mata cizo a hannun, da sauri tasaki wuyana najuya da mugun gudu nashige d'aki, namai da kofa narufe da karfe namurza key, najin ginu da jikin kofar tareda dafe kirjina da ke dukan uku-uku, sai sauke numfashi nake kamar wacce tayi tsere,
zamewa nayi kasa nazauna har lokacin hannuna nadafe a kirjina.
"Nashigesu yaushe Aunty Na'ima tahaukace?".
Nayiwa kaina tanbayar.
Jin tana dukan kofar yasani mikewa zunbur, sosai take dukan kofar tanafad'in
"Wlh da kin tsaya da sai dai yau uwarki tahaifi wata shegiya munafuka ai ni tun sanda nafara ganin ki nasan bakaramar hatsabibiya za'ayi anan ba, ina zama da mijina kk zab'a to kuwa kin zab'i tarwatsewar rayuwarki!".
Tajuya fuuu tafice.
lekawa nayi tajikin kofar na hangi bayanta tana ficewa daga parlourn, da sauri na Isa bakin gado nazauna Kuma dafe kirjina nayi
"dama ashe Aunty Na'ima tahaukace shine Inna tasa aka kawoni gidan Nan Allah bazan zauna ba ko sati d'ayan ma nafasayi".
Ta babban parlour Na'ima tabi tana shiga Ya SALEEM nafitowa da ga part insa, da sauri taja tatsaya tamai da hannunta dake rike da wukar tabaya,
A sannu yakaraso in da take yatsaya daf da ita, kirjin tane yafara dukan uku-uku tabbas idan yasan a bin da taso ai katawa yau kashin ta yabushe,
Dan tana da tabbacin yaga ta in da tafito, ji tayi zuciyarta tama bushe tashirya
d'aukar koma menene zama da