Showing 81001 words to 84000 words out of 261814 words
Baki idan Bai bar gurinba Dan haka Dad dinne ya fice Kai tsaye ko gabansa Baya Gani sbd Shima jininsa yayi mugun hawan Daya wuce misali.
Daqyar yakai kansa cikin gida yayi samansa ya shige bedroom dinsa Dan har lokacin Babu kowa a gidan Yan biki suna gurin bikin.
Dad Lameenu ma BB ne ya taimaka masa ya fice.
BB ne ya dawo office din ya kama Haroon daya qanqame gabaki Daya Yana rawan jiki sosai yakaisa har palonsa ya dawo ya rufe office din ya fice daga Mansion din.
Haroon rarrafawa yafara yi idanuwansa na ganin duhu da haske yafara kokarin Kai kansa bedroom Amma ya kasa sbd wani kifewa da yayi akan console mirror dayake hanyar bedroom din ya fado masa ya fashe.
Bugawa kansa keyi sosai hakama hannuwansa rawarsu ta tsananta sosai har tayi muni hakanan ya sake dafawa ya tashi cikin glass din Yana dafa Bango ya Isa kofar dakinsa yana shiga ya zube qasa Yana buga kansa sosai a tiles idanuwansa Dake rufe suna sake birkicewa.
Siddeeq kaman yasan abinda yake faruwa a mansion din ya dawo daukan Haroon sbd acanma Haroon jikinsa ya rikice zazzabi Mai karfin gaske da Bai taba yin irinsa ba ya rufesa Wanda ya bawa siddeeq tsoro hakama mum datake Kiran yayan nata Babu me dauka siddeeq din ta kira tanajin Jamaal ba lafiya taji hankalinta ya tashi Amma Kuma wannan Karan rashin daukan wayar Haroon yafi daga hankalinta fiyeda ciwon Jamaal Dan haka tace siddeeq ya dubo mata mansion din zuciyarta takasa samun nutsuwa.
Koda siddeeq ya Isa halinda ya samu Haroon yayi mugun girgizasa Dan Bai taba ganinsa a irin wannan mugun halinba duk tsananin ciwonsa kuwa.
Da gudun gaske ya qaraso inda yake ya tallafosa sedai Haroon din yayiwa kansa mummunan rauni jini Tako ina Dan haka a haukace ya daukosu gaba Dayansa ya fito dashi Bai tsaya wata wata ya Saka mota sbd ba qaramin munu lamarin yayi ba ya fice dashi zuwa asibitin SEELAHs din da gudun gaske.
Yana Isa aka karbi Haroon din da gaggawa Dan tini ya fice hayyacinsa Wani jijjiga kawai yakeyi sosai kaman me wani ciwon daban.
Fadan tashin hankalin da siddeeq ya shiga a wannan lokacin bamai yiyu bane sbd ya shiga tsoro Mai girma wannan Karan da ciwon Haroon din ga Jamaal a kwance ba lafiyan Shima.
Haroon sosai ya wahala cikin azaban ciwonsa Babu uwa Babu Uba Babu wani nasa sai siddeeq Wanda ya tsayu akansa har Saida ya dawo daidai sbd cikin qanqanin lokaci Allah ya mayar dashi kaman ba shine angon da zaa daurawa gobe ba.
Duk karfin zuciyarsa siddeeq sai dayaji tausayin Haroon ya karyasa sbd bayan dawowansa daidai Hawaye ne masu tsananin zafi da radadin zuciyan gaske suke gangaro masa batareda yace komaiba.
Sallan magrib siddeeq yake yaji daga can ya koma hotel ua dubo yanayin Jamaal Wanda ya Riga ya miqe haryayi wanka yayi Sallah
Siddeeq din na zuwa ya sanarwa da Jamaal halinda Haroon yake ciki.
Karban key Jamaal yayi shi kadai ya nufi asibitin gurin Dan uwansa.
Zuwansa asibitin Haroon na ganinsa hawayen tsananin kaunar Dan uwansa daya tabbatarda duk duniya ko mum dinsa Kila Baya kaunarsa yanda Jamaal din yake sonsa ne suka ciko idanuwansa suna gangarowa.
Jamaal Daya kasa masa maganar abinda ya faru ayau din sbd ganin yanayinsa daukansa yayi suka baro asibitin Babu me magana shiru kowa da abinda yake tinanin Amma dai shi Haroon zuciyarsa da jikinsa gaba Daya a Sanyaye suke sbd rayuwarsa yasan daga yau ta dena moruwa ne sbd aurensa dayasan har abada Dad bazasu taba barin ayi aurenba,
Rasa Ameenatou garesa tamkar zare control na tabin kwakwalwansa ne kaman yanda su Dad suka fada Dan haka idan har tabbas gobe ya tabbata ya rasa Ameenatou to ya cire Rai daga komawa daidai,
Yasan Jamaal da mahaifiyarsu zasu shiga tsananin qunci da baqin ciki akan Hakan Amma Shima kansa a yanzu yasan ko da auren Ameenatou ko Babu tabbas tabin kwakwalwa ne a tattare dashi me tashi Kuma me tsananin gaske.
Rintse idanuwansa yayi ahankali maganganun Dad da fushinsa da Bai taba Ganin irinsaba suna dawo masa a kunnuwansa take yaji ciwonsa na Neman sake dawowa ya dago jajayen idanuwansa ya Kalli Jamaal dayake tuqi a natse Shima zuciya da kansa duka a jagule da lissafi kala kala.
Cikin wata murya me sanyin gaske data Saka zuciyar JAMAAL sanyi akan fushi da bacin ran dayake ciki akansa
yace
"Jamaal,
Kayi mun alkawarin ganin na auri macen danake so matiqar ba Allah yariga yayi cewan ba matata bace,
Ko ban auri AMEENATOU a gobe ba Kai inason ka sheda itace macen danake so fiyeda komai a duniya bayan Kai da mum,
Son AMEENATOU wata jarabtace da Allah ya jarabceni da ita,
AMEENATOU itace macen da zanso har karshen rayuwata Kuma itace mace Daya da bayan ita Babu macen da Nima zan iya so.
Ko ban auri AMEENATOU ba bazan iya rabuwa da ita ba Dan haka Dan Allah Jamaal Karka bari su dadi su hanani samun farin cikin aurenta,
Aurenta shine Abu na karshe da zanzo kafin rayuwata tabar duniya.......
Shiru Jamaal yayi masa har suka Isa mansion ya shigo dashi har cikin harabar gidan wannan Karan shine da kansa ya fito motan tareda Dan uwansa dukkanin securities din gidan da sauran Jamaar dasuka dawo event suna harabar gidan mutuwar tsaye sukai ganin su biyun a tare Kuma kusan kamannin Babu Wanda zai iya banbancewa bayan raunikan Dake fuskan Haroon sai Kuma haske da jamaal yafisa sosai.
Mam da lameenu wainda suka Fito masallaci sallan ishai daqyar sbd radadin da zuciyoyinsu suke ciki mutuwar tsaye sukai lokacinda suka kawo su Jamaal dinma sun kawo cak kowannensu ya tsaya Mam ganin 'yayan nasa a gabansa tare sai yaji zuciyarsa na narkewa da tsananin kauna da kewan kasancewa inuwa Daya dasu.
Lameenu kuwa kallo daya yayiwa jamaal yaji jininsa na son Hawa da sauri yai gaba
Shima Dad kafin kowannensu ya motsa ya gaidasa gaba yayi batareda ya waiwayosu ba ganin Haroon kawai Yana tafasa ransa.
Jamaal ajiye Haroon kawai yayi ya juya yabar gidan Kai tsaye gidan da zai Hadu da Dad Omar a daren ya wuce Yana kallan time.
Suma acan bangaren tin ana sallan ishai Yana fitowa masallaci Ahmed yayiwa Babbah abinda baisoba waton nuna masa power Kai tsaye sojoji ne suka daukesa daga kofar gidansa suka wuce dashi shi kuwa Haroon da Jamaal na ajiyesa ko zama baiyiba Shima ya fice gidan yayi gidansu Ameenatou Kai tsaye Yana Isa motar na wucewa da Babbah Dan haka ko gidan Bai shiga ba Shima yabi bayansu.
Sun isa da Babbah motar Jamaal ma na Isa Dan haka kusan da Ahmed din da Babbah dayake kallan Jamaal da dukkanin Idanuwansa da tsoro da shakka harma da fargaba tare suka shigo palon da Dad Omar din yake zaune.
Dayake bayason asan da Yana gurin ko makamancin Hakan ko securities Babu a gurin sbd guri ne da bazata taba tinanin samunsa agurin ba bare a biyosa.
Su kansu su BB Dake bibiyar Babbah ganin sojojine suka daukesa sai basuyi gangancin binsu ba sbd yanzu a ankare suke tinda Jamaal ya bayyana komai zai iya faruwa juyawa sukai Dan sanarda dasu Mam.
Haroon da Shima ya shigo da motarsa gurin yayi parking Yana ganin motar Dad Omar data Jamaal a gurin bayan Kuma yaga lokacinda sojojin suka ajiye babba suka fice take kirjinsa ya sake daukan nauyi Yana bugawa Dan haka Kai tsaye ya wuto ciki Shima.
Babba ne yafara maganarsa Kai tsaye da cewa
"Meyasa ka gayyato Haroon anan??
Kanason yasan ko Kai din wanene?
Kanason yasan kaine asalin mahaifin AMEENATOU wadda ka tsallake ka bari ranar da aka haifeta????
Cak Haroon ya tsaya bakin Kofar batareda ya qasara shigowa ba sbd gagaruman kalaman Babbah da suka shiga kunnuwansa.
#MAMUH
#DR JEEY SEELAH
#AMEENATOU SEELAH
#UNEXPECTED
#CRAXYLOVE
#ROMANCE
#DEEP
#LA HOT
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
52
Dip yaji jinsa Dan ganinsa na Neman daukewa sbd tsananin girgiza da rikewan abinda kunnuwansa suka ji.
Hannunsa Daya iya dagowa da kyar ya bubbuga kunnensa Dan Jinsa Daya dauke take ya dawo idanuwansa da Basu koma daidai ba suna sake rikidewa Dan Bai taba jinsa cikin mummunan tashin hankalin dayake Jin kansa a daidai wannan lokacin ba idan har AMEENATOU dinsa itace jinin Dad Omar din dasu Dad da shi kansa suka ringa dakon nema a tsawon shekarun Nan.
Babbah kuwa da zuciyarsa har lokacin radadin gaske takeyi kallan Omar din yayi Yana cigaba da cewa
"Me kace akan Ameenatou din?
Zaka Nisanta damu sbd Bata kariya
To meyasa ka dawo?
Shin ka manta irin masifar da kusancin naka da ita zai iya jawowa?
Sanyi muryansa tayi jikinsa da bakinsa na rawa cikin mutuwar jiki yace
"Ameenatou itace hasken zuciyata da idaniyata,
Ameenatou itace walwala da farin cikin rayuwata data iyalina,
Ameenatou ita kadaice jinin jinina Danake Gani,
Ameenatou itace nake kallan tawa Ameenatu din a cikinta meyasa zaka dawo Omar?
Meyasa zaka dawo daidai lokacinda take gap da samun farin cikin rayuwarta?
Omar na rokeka da Allah ka koma inda ka fito batareda kowa yasan alaqar da muke da ita dakai ba,
Ameenatou batasan tayaya zata fara karban cewan ga mahaifinta ba a tsaye gabanta wani ne ba ni ba....
Su kansu sirikanta Babu ta yanda Rana tsaka a ranar daurin auren kawai ace musu wani ne mahaifinta ba Wanda suke tinanin sun karba auren a hannunsa ba,
Hakama sanar dasu Hakan dole muna buqatan yimusu qarin bayanin yanda Akai tabar hannun mahaifinta ta dawo nawa hannun,
A wannan gabar me zamu ce musu?
Me zamu sanar musu?
Cewa zamuyi anyiwa mahaifiyarta kisan gilla a gaban idanuwanmu aka yanka cikinta da cikin wata Tara a jikinta????
Ce musu zamuyi a hannuna jininta ya tsayaye Ina kallo ta sadaukar da rayuwarta ta haife cikin jikinta bayan yankan wuqar daya Huda cikinta da kirjinta???
Ce musu zamuyi a wannan ranar da aka haifeta ka tsallake ta ka barta duk akan ana bibiyar rayuwarka zaa hallaka ka??
Jamaal Da kusan Shima mutuwar tsayen yayi sbd shock da tarin mamaki da hada sauran bayanan dayaji a bakinsu Dad da bakinsu ayau din komai Yana haduwa acikin kansa Amma Jin irin kisan da Akaiwa Aminatu a bakin babban ya Sakasa rintse idanuwansa Yana Jin kaman jiri zai daukesa,
Meyake faruwa a duniyar Nan da suke ciki ne?
Wane irin buri ne da son duniya ya Saka su Dad shiga wannan mummunan qazamiyar kaddarar ta kashe kashe irin na zallan rashin Imani????
Bayan irin kisan da sukaiwa Aminatu matar Omar din mahaifiyar Ameenatoun ahakan suke sake bibiyan rayuwarta Baji ba Gani Dan su qarasa aikin da Basu qarasaba shekaru..... innalillahi wainna ilaihirrajiun,
Innalillahi wainna ilaihirrajiun?
Omar shiru yayiwa Babbahn idanuwansa jajir Yana Jin zantukansa na shigarsa suna dawo masa da komai tareda yanka zuciyarsa.
Ahmed ne ya katse babban cikin radadin zuciya da kasa dannewa da cewa
"Duk wannan abin da kake fada akan rabuwarsa da gujewansa tareda bawa Ameenatou kariyan da Kai da tasa sadaukarwan zasu tashi duka ne a banza Dan da hannuwanka gasunan zaka miqawa wainda ke bibiyan rayuwar tasa da tata ita a bainar jamaa gobe..
Da kanka zakai kirari ka dabawa kanka wuqa sbd su sirikan da kake magana sune jinin Omar din Kuma sune masu Neman jinin nasa.
Wani kallo Babbah ya juyo Yana yiwa Ahmed kafin ya mayar da kallansa kan Jamaal da Daya kasa kallan kowannensu Idanuwansa jajir Yana rintse su sbd kunyar abinda duk ake fada ana magana ne akan rashin Imani da Barnar mahaifin Daya haifesa.
Kan Omar Babbah ya mayar da kallansa Yana Jin zufa na tsiyayowa har ta cikin kansa da kunnuwansa Dan haka ya zare hular kansa yayi wurgi da ita Yana cewa
"Omar me nake ji?
Me yake faruwa?
Menene yake Kuma Shirin faruwa?
Shin balain ne ya dawo da masifar kokuwa wace balain ce take Shirin dawowa??
Meye hadinka da SEELAHs???
Kallansu yakeyi Daya bayan Daya a rude Yana Neman Karin bayani Dan kansa Neman Juyewa yakeyi da tashin hankali da tsoron abinda zai iya faruwa idan wani abu ya samu Ameenatou dinsa.
Omar ne ya dago tareda tashi tsaye Yana fuskantar babban idanuwansa jajir yace
"SEELAHs shine Nima nawa asalin sunan ba Jden ba?
Mamman seelah, Lameenu seelah, Omar seelah da Yan uwanmu biyu da suka rasu kasim da jamilu seelah Yan uwan jini muke,
Dukiya itace ta lalata jinin dayake yawo a jikin kowannenmu na alkawarin tsira tare mu mutu tare,
jinin yan uwanmu ne Daya zuba akan dukiyar ya gurbata dukiyar ta Saka mu samun Kanmu a mummunan halinda muke ciki a yanzu na bibiyan rayuwar Yan uwanmu Amma ka sani har abada bazan iya rabuwa da yata ba a yanzu kaman yanda nayi alkawarin Bata kariyar da ban samu bawa mahaifiyarta ba,
Ameenatou a yanzu itace babban abinda duk wani maqiyana yake Neman samu,
Ameenatou itace mukullin dayake riqe da duk wani abinda Dana mallaka,
Ameenatou itace mamallakiyar dukkanin tarin dukiyar Jden a rubuce Dan haka samunta a shine mafi farin cikin cikan burinsu,
Sanin wacece Ameenatou shine babbar hatsari da tashin hankalin da dukkaninmu zamu fuskanta Dan haka Babu maganar aurenta a goben Dan har abada bazasu taba Dena Neman ba har sai ranarda suka samu sanin waye magajin dukiyar jdens gaba dayanta.
A rubuce dukkanin dukiyata da abinda na mallaka nata ne,
Ahmed ya sani ayau Kai da Jamaal inason Kuma ku sheda Hakan sedai ku sani barin asan wacece ita shine karshen komai.
Kallan babbah Daya gama jiqewa da zufan gaske hankali tashi yayi kafin ya Kalli Ahmed ya zaune dashi ahankali ya fara zayyano masa asalin tarihinsu da komai tin daga barowansu gaban iyayensu har zuwa yanzu da suke maganar.
Kuka wiwiwi Babbah keyi dukkanin jikinsa na rawa sbd shiga tashin hankali da tsoron rayuwar dasuka samu kansu dumi dumi aciki ta masifar da Bai taba ji ba...
Jamaal ma kusan silalewa yayi kan kujera wannan Karan da hannuwansa biyu ya Saka Yana rintse idanuwansa sbd kansa Dake Neman bugawa tareda zuciyarsa....
Ahmed ma da tinda yake da Omar din baisan asalin asalin mafarin komaiba sai yau din sbd kaf duniya yanzu Babu Wanda yasan ba uwa Daya Uba Daya SEELAHs suke ba sai yau din,
Ko Jamaal da Haroon dasuke yayan cikinsu da matayensu Basu taba sanin wannan sirrin ba sai yau din da Omar yake fada musu da bakinsa cewan ba uwa Daya Uba Daya suke ba...
Dukkaninsu Dake palon silalewa sukai qasa kowa kafafunsu na kasa daukansu,
Duk tsananin jarumta da karfin halin Jamaal Hawaye ne suka ciko jajayen idanuwansa yanajin wani abu me nauyin gaske ya tsaya ya tokare kirjinsa sbd baqin ciki da radadi tareda kunyar abinda ake fada mahaifinsa na ciki,
Makashi ne ya haifesa?
Makashin Yan uwansa da wainda Basu da hakkinsu na komai shine mahaifin Daya haifesa,
Mahaifinsa shine makashin kakanninsa da macen da harya mutu bazai taba Dena Sonta ba.....
innalillahi wainna ilaihirrajiun,
Innalillahi wainna ilaihirrajiun
Babbah kuka yakeyi sosai hankalinsa da gashin jikinsa duka suna tashi,
Shi kansa Omar da sai yaune ya Bude Baki ya iya furta abinda yake ransa qunshe tsawon shekarun Nan Bai taba maganar dayake cin zuciyarsa Yana saukar masa da radadi mafi ciwo na yanda shi da Yan uwansa suka kasance,
Tin suna Shan nonon iyayensu suke tareda juna a guri Daya aka haifesu suka taso tare batareda ko a takalman sakawa iyayensu sun banbantasu sbd kauna junan datake yawo a jininsu tin
A iyayensu take acan ta samo asalinta har a nasu jinin,
Sun tashi da kauna me karfin gaske a tsakaninsu Amma yau rayuwar junansu suke nema,
Wannan abin ne yake Saka Omar baqin cikin Daya zauna zuciyarsa yake cinsa akowace daqiqan rayuwarsa Dan haka yau Daya samu furta sirrinsu hawayen ne suka gangaro masa a Karan farko sbd a yanzu bayan su ukun dasuke gabansa Babu Wanda ya yadda dashi Akan yarsa,
Su uku sune wainda yasan zasu tayasa bata kariya da rayuwarsu Dan haka ya juyo da idanuwansa akan Jamaal Wanda shi kadai ne Seelah Daya dayake Jinsa har cikin ransa Kuma ya yadda dashi fiyeda rayuwarsa kaman Ahmed a Sanyaye yace
"My son Ina tsananin baqin cikin hanawa Dan uwansa wannan auren sbd ba Kai bane,
Kai kadai ne namijin dana yarda na bawa aurenta na jefata cikin SEELAHs batareda naji shakka ko tsoron Hakan ba,
Kaine Wanda zan bawa amanarta ko Bada aure ba Amma kwata kwata zuciyata Bazata taba samun nutsuwa ko Kwanciyar hankalin bawa Haroon aurenta ba Badan komai sai Dan rauninsa ga mahaifinsa Wanda ba ita kadaina akanta shi kansa tasa rayuwar a hadari take.....
Dago jajayen idanuwansa Jamaal yayi ya zubawa Dad Omar din tareda girgiza masa Kai bakinsa na sake daukan nauyi sbd tsananin son da Dan uwansa yakewa Ameenatou din idan aka rabasa da ita matsalar ciwonsa zata iya Maidasa cikakken mahaukacin dayake tsananin tsoron ya koma,
Bazai iya kallan Rabin jikinsa Haroon din ya koma Hakan ba,
Zai iya sadaukar da rayuwarsa akan lafiyan Haroon da Kuma samar masa macen dayake so fiyeda nasa ran Dan haka ya Bude Baki bakin cikin muryansa Daya shaqe sbd tsananin tashin hankali da baqin ciki harma da shock yace
"Dad Dan Allah Karka Hana Haroon auren Ameenatou,
Ameenatou itace farin Daya Kuma nutsuwa Daya rak Datake riqe da rayuwar Haroon,
Hana masa aurenta tamkar rabasa da lafiyarsa ne gaba Daya,.
Haroon Yana yimata tsananin son da bazai taba barin komai ya faru da ita ba Koda hakan na nufin zai gitta tasa rayuwar".
Kuka Babbah ya sake fashewa dashi sbd gano gaba Daya su rayuwarsu acikin seelahs din da aurenma gaba Daya a duhu suke Babu Abu Daya dayake gaskia sai soyayyar da Ameenatou dinsa takewa Haroon sbd Jamaal da Haroon dai mutum biyu n mabambamta da suka ringa wasa da zuciyar Ameenatoun,
Tayaya zai bari Ameenatou tayi aure a cikin wainnan mutanen da yanzu ma tsoro suke tsananin basa bayan Omar din da Ahmed sai Jamaal din Wanda yaji yamafi samun nutsuwa dashi.
"Bazan taba bawa Haroon ko Daya daga cikin zuriar seelahs din auren Ameenatou ba gaba Daya har abada" babban ya fada Yana dagowa jajayen idanuwansa Yana kasa kallan Jamaal Daya cike masa ido har lokacin Hawaye ne ke zubowa daga idanuwansa.....
#MAMUH#
#THE SEELAHS
#THE JDENS
#LOVERS
#MARRIAGE
#AMEENATOU JDEN SEELAH
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_AMEENATOUH_*
_Mamuhgee_
#Arewabooks@Mamuhgee
#ZafafaBiyar
#BestLove
53
Maimaicin fasa aura masa Ameenatou da akeyi ne ya Saka kansa kasa dauka hannuwansa suka fara rawa hakama