Showing 54001 words to 57000 words out of 261814 words

Chapter 19 - AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE.txt

MAMUGEE   

07 Jul 2024

59003

Banka masa Dan haka sai yafara rikicewa ahankali ahankali sbd fushin Dad din da Kuma kansa da suke Neman juyar masa.

Siddeeq Daya fahimci yanayin Haroon din ya sauya sosai ya fara tsananta sosai daukesa yayi suka koma Nasarawa Koda lamarin zaiyi sauki idan Yana ganin Ameenatou wadda itama kullum take cikeda kewansa da damun su Babbah akan kada fa yaje ya auri wata acan Lagos yabarta anan ita tana jiransa.


Dawowansu Nasarawa ciwonsa tsananta yayi gashi basa ganin likita a bayyane a boye suke Gani sbd kada Yan jarida su ji Barr Haroon seelah magajin SEELAHs yana fama da matsalar data shafi damuwa da kwakwalwa.

Su Babbah Jin baida lafiya sosai suka shiga damuwa da tausaya masa sbd kaunar da suke masa ta wuce ta ogan Hafiz da Kuma Mai son Ameenatou.

Babbah da Yaya Abdul da kansu suka takurawa Haroon din da siddeeq suka Kaisa asibiti da kansu suna zuwa aka basa gado a dakin da Babu Wanda zaisan waye a asibitin.

Kwanciyarsa asibiti ya Sakasa sake tabbatarda bazai iya rayuwa Babu Ameenatou ba Dan kuwa kauna da kulawan da Bai taba tinanin ana samu daga ahali ba sune ya samu Dan kuwa Hafiz ne ma kusan yake kwana ya tashi dashi a asibitin babbah da Abdul ma kullum anan suke kusan wuni dadah da Heartbeat dinsa kuwa kullum sai sunzo da daddare su koma tareda su Babbah gaba dayansu.

Ameenatou duk narkewa tayi ganin yanda ciwon kwana biyu ya mayar dashi Dan haka tausayinsa ya Saka sonsa Data kasa ganewa da tantancewa cike dukkanin zuciyarta.

Kwanansa biyu aka sallamesa batareda ance musu komaiba kawai dai wai ciwon Kai da bp dinsa ne ya hau sbd damuwa da stress na aiki.

Bayan an sallamosa da kwana Daya Lagos ya tafi Dan sake dubo Dad dinsa Wanda har lokacin ko wayarsa Baya dauka.

Bayan isarsa Lagos Shima siddeeq gida ya koma Dan dubo umman fadila da yanzu Alhmdlh ta rungume kaddara tana rayuwarta cikin Kwanciyar hankali da Kuma kulawa me tsananin datake samu da kauna sosai daga siddeeq din Daya inganta rayuwarta sosai Babu abinda ta rasa saima Jin dadinta datakeyi.


******Tsayuwa Haroon yayi jikinsa na sanyi ganin Dad dinsa zaune a kan dining din cin abincinsu na dare bayan baiyi tsammanin ganinsa ba a gurin Dan kwata kwata ya Dena barin Yana ganinsa.

Mum Atee ce tayi saurin tasowa daga inda take zaune kusa da Dad din Yana washe Baki cikin kulawa da kauna sosai ta nufosa tana cewa

"Zo ka zauna yau tareda Dad Dinka zakaci abinci Inshallah duk komai ya wuce"

Kallan Dad din yayi Yana qarasowa jiki a Sanyaye zuciyarsa na sanyi hakama jikinsa na sake mutuwa sosai.

Mum Atee ce tayi saurin ja masa kujeran kusa da Dad tana cewa ya zauna ai Dad dinma yayi kewansa.

Zama yayi batareda ya dago ya Kalli Dad dinba Shima Dad din Bai kallesaba ba Saida gurin ya dauki shiru tsawon mintina kafin Haroon din ya dago ya Kalli Dad dinsa da idanuwansa dasukai wani irin ja da sanyi cikin sanyi da nutsuwa yace

"Dad barka da fitowa,
Yaya jikin?
Allah ya karo Maka afuwa da sauki."

Numfashi mata sauti Dan dumi Dad din ya sauke kafin ya amsa Kai tsaye Babu Jin dadi ko kadan a muryansa Dan kuwa ganin Haroon din kadai tafasa zuciyarsa yakeyi Dan gap yake da yafesa gwara yasan baida 'da ko Daya a gabansa Saiya fanjama mummunan aikinsa dakyau kawai ayi me yiyuwa.

Ayeesha Dake table din itama cikin kulawa ta gaida Dad din tana masa ya jiki ya amsa Yana gyada mata Kai kafin Suka fara cin abinci Babu me cewa komai.

Suna gama cin abincin mum Atee sai sake zuba masa juice din data hada masa da kanta takeyi cikin kulawa da tattalinsa kaman Dan data haifa.

Suna gama cin abincin kafin kowa ya tashi Dad sai lokacin ya dago ya Kalli Haroon cikin kamewa Babu sakewa ko kadan yace

"Ka hada komai na SSl project ka ajiye za'a rufesa gaba Daya Wanda kasan me Hakan ke nufi ai ko?"

Wani mugun zufa ne ya fara tsiyayowa daga cikin rigar Haroon ya dago idanuwansa ya Kalli Dad din cikin tsananin kwantar da Kai yace

"Dad Ina rokon ka karamin time na cike time din da aka dibarmin tin farko akan aikin nayi alkawarin zan cika Maka alkawarin dana dauka akan aikin,
Dad please Karkayi saurin rufe komai wlh Ina iya kokarina fiyeda yanda kake tsammani,
Ko yanzu rashin lfy nayi kwana biyun shiyasa aka fara samun durkushewa Amma wlh Dad nayi Maka alkawarin komai zaizo gabanka yanda kakeso....

Daga masa hannu Dad din yayi zuciyarsa na wani irin ciwo da radadi Dan har lokacin Jin yakeyi zuciyarsa Bata warkeba.

Jajir idanuwan Haroon din sukai kaman yanda na Dad din sukai jajir yanajin baisan me zai kama ba yabar Daya tsakanin 'dansa da dukiyarsu dasuke Neman rasawa.

Mum Atee datai shiru Dan muskutawa tayi tana rokon Dad din akan ya sake bawa Haroon din dama.

Ayeesha kuwa shiru tayi dukkanin jikinta yayi sanyi da tausayin Haroon Daya rasa komai akan Dad dinsa Amma Babu Wanda ya taba appreciating nasa ko kadan.

Shiru Haroon yayi zuciyarsa na nauyi me tsanani tareda nauyin Kai shima me tsananin Yana sauraran yanda mum Atee ke rokon Dad din kafin ya amince masa da sharadin ana samun matsala zai tattara ya koma Poland Shima gurin mahaifiyarsa.

Dagowa yayi da jajayen idanuwansa ya kalli Dad din tareda masa godiya kafin ya miqe jiki a mace yabar dining din Shima Dad miqewa yayi yabar dining din.

Koda ya koma dakinsa juyawa kansa yafara yi masa tin a palonsa ya zube Yana dafa Bango kaman ganinsa zai dauke Yana Jin kansa kaman zai tarwatse.

Daqyar yakai kansa dakinsa ya Isa gaban mirror Yana Neman maganinsa Amma Bai gansa ba.

Raffowa yayi Yana barin duk abinda ya fadawa harya Isa gefen gadonsa yafara janyo drawers hannuwansa na wata irin rawa Yana yamutsa kayan ciki gurin Neman maganinsa Amma kwata kwata ya kasa ganinsa.

Buga kansa yafara yi a jikin gadonsa Yana wata irin rawar jiki.

Wayarsa Dake gefen gadon ajiye ce tafara ringing Amma Sam baima San meyake ji ba bare yaji Kiran.

Ameenatou Dake kiransa Dan Jin muryansa sake Saka Kiran Tayi tana matsuwa Daya dauka Dan haka kawai zuciyarta keson jinsa Dan yanzu zuciyarta ta gama yin naam da karban sonsa fiyeda yanda tayi tinanin tana son nasa.

Cigaba da Kiran datake masa ya Sakasa dago idanuwansa da sukai wani irin mugun jajir ya Kalli wayar.

HB ya Gani rubuce kan wayar yaga itace.

Hannuwansa Dake wata irin rawa ya dago suna jijjiga ya Dora akan wayar ya dauko tareda daga wayar ya Saka handsfree ya ajiye Yana Jinta acikin dadaddiyar muryanta me sanyi da nutsuwa tana magana.

Yana jinta Amma kwata kwata Baya iya magana saima Juyewan dayake Jin kaman kansa zeyi da azabbiyar ciwo da nauyi hakama jikinsa rawa yake qarawa sosai Yana hada zufan dayake sake tsatsafo masa Tako ina har cikin tafin hannuwansa da kansa.

Sunansa ta sake kira cikin damuwan jinsa shiru tana narke masa a wayan.

Wasu hawayen azabbiyar Sonta da tausayin kansa masu tsananin zafin gaske suka gangaro masa ya rufe idanuwansa harta gama magana yanaji ta kashe wayar batareda ta sake Kiran ba.

Kuka me zafi ne ya kufce masa Yana buga kansa a jikin gadonsa da karfi har lokacin jikinsa rawa yakeyi sosai musamman hannayensa.

Ya Dade acikin wannan azabar tsawon lokaci kafin ya Dan samu sassauci ya rarrafawa ya sake dudduba maganinsa ya gansa a Palo ya dauka da sauri hannuwansa na kakkarwa ya Bude roban ya zubo guda biyu ya jefa bakinsa tareda Isa inda ruwa suke da sauri ya dauka ya shanye maganin yana sake hada zufa me yawa kafin ya silale a palon ya zauna Yana rintse idanuwansa Yana jingina bayansa jikin bayan Daya daga cikin tsadaddun kujerun palon.

Yayi mintina sosai ahakan kafin ya dawo daidai ya sauke numfashi da ajiyan zuciya tareda miqewa tsaye ya nufi bedroom dinsa gurin wayarsa Kai tsaye ya nufa ya dauka Yana kallan time yasan zuwa lokacin Ameenatou tayi bacci Dan haka Hafiz ya kira ya tambayesa ya sanar mace tayi bacci.

Sallama sukai batareda ya kirata ba Dan kaman yanda su Babbah ke lallabata haka Shima yake lallabata kaman zuciyarsa Dan haka bazai iya tadata bacci da wayarsa ba.

Ajiye wayar yayi ya miqe ya nufi bathroom ya sakarwa kansa ruwa yayo wanka ya fito daure da towel ya shirya cikin kayan bacci marasa nauyi ya kwanta Yana rufe idanuwansa jikinsa har lokacin a Sanyaye.


Washe gari tinda safe breakfast kawai yayi dasu Dad yayi musu sallama suka nufi airport suka bar Lagos din shida siddeeq.

Bayan tafiyarsa Dad Lameenu ya Saka aka bisa Dan Saka masa ido sosai akan lamarinsa kowanne irin motsinsa da komai Dan shi Kam bazai yadda suna kallo su wayi gari basuda komaiba.
#MAMUH#
#JAMAAL JEEY
#HAROON SEELAH
#AMEENATOU
#IDENTICAL TWINS


*_ZAFAFA BIYAR_*

1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_

2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_

3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_

4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_

Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200

*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*

*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*

*_MTN/VTU 09134848107_*

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
36
Ameenatou na islamiya ya dawo Dan haka bayan yayi Sallah abinci yaci ya kwanta Dan samun baccin da tinda yake Lagos harya baro Bai wani samuba.
Shima siddeeq hutun ya kwanta ya samu kafin yamma.

Karfe Biyar da mintina ya tashi daga babbacin na awa Daya da Yan mintina San Saida yayi laasar ya kwanta.

Wanka kawai yayi ya shirya ya karbi ke din mota daga hannun siddeeq da kansa yaja ya nufi makarantarsu Ameenatou Kai tsaye.

Yana Isa ana tayar dasu Kuma Hafiz ma Yana Isa daukota Dan haka Koda ta fito cikin doguwar hijabinta akansa idanuwanta suka fara sauka Yana tsaye jikin motarsa Yana waya ahankali kaman mara lafiya kyakkyawar fuskansa ta fada kadan gaba Daya ya juyo hankali da idanuwan duk Wanda ya fito makarantar dama masu wucewa akansa sbd ganin bature tsaye bakin makarantar tasu.

Waya yakeyi Amma Shima tinda ta fito idanuwansa na kanta yanajin jikinsa na mutuwa zuciyarsama sanyi tayi Dan baisan wane irin so ne yakewa Ameenatun ba.

Ganinsa itama ya Sakata sakin kyakkyawar murmushi tana Dan dauke idanuwanta daga kansa Dan kuwa Jin tayi ganinsa ma gaba Daya ya Sakata Jin wani farin ciki me yawa gashi tana son tayi murna sosai a fili Amma batason Yan makarantar Susan shi zata aura su fara kalle mata shi Dan gulmansu.

Nufosu tayi zata Bude Baki tayi magana Hafiz ya jefa mata wani kallan Daya sakata nutsuwa tana hadiye zancen Daya fadawa Haroon na kewan datai masa me tsanani.

Kashe wayarsa yayi Yana kallanta fuskansa daukeda murmushi Mai bayyanarda farin ciki yace

"Barka da fitowa Budurwan Babbah"

Wani sabon farin ciki taji ya rufeta sedai narke fuska tayi tana qasa qasa da murya kada Hafiz yaji tace masa

"Yanzu ba budurwan Babbah bace ai na sauya suna"

Mota ya Bude mata ya shiga ya rufe mata Saida ya zagaya ya shiga ya zauna Hafiz ma ya shigo kafin ya kalleta Yana tayar da motan yace

"Yanzu yar budurwan Barrister ce ko??

Wani sabon dadin taji Yana hararan Hafiz da Shima ita yaketa harara kaman idanuwansa zasu fado Amma taqi kallansa bare taga kwabar dayake mata ya ido sbd sakarcin Data Saba yi musu hadda Haroon din kada tayi a gaban makarantar cikin bainar jamaa.

A hanya kafin su Isa gida guri uku tana sakawa ana biyawa sbd siyan wani littafinta na islamiya da zata dashi gobe kafin suka Isa gida anata kokarin shiga sallan magrib Dan haka Haroon din Bai shiga ba alwala kawai sukai a waje suka wuce masallaci ita Kuma ta shige gida.

Saida sukai ishai suka shigo gidan anan Haroon yaci abincin Dare tareda su Babbah na tambayar yanda ya baro mutanen gida.

Irin son dayake mata itama take masa basa buqatan ma wai saisun kebe sbd a jininsu suke jinsa shiyasa duk firar da sukeyi anan dai tareda kowa tsakar gida ake yinta Kuma ahakan suke soyewansu a gaban su Babbah Dan shi Kam idanuwansa ne basa iya kaucewa daga kallanta matiqar tana gurinda yake ita kanta kallansa shine ke sake sakawa duk tana sake shagwabe masa ko agaban su Babbah ne kuwa sai idan Hafiz ya gaji da sakarcin ya dinga fada kenan Yana hararta idan Haroon din ya tafi.

Washe gari ne zaa tafi da Ameenatou Abuja gurin rubuta jamb nata Daman hadda shi ne ya Saka Haroon din dawowa da wuri Kuma kaman yanda yaso university na Lagos aka cika Mata Dan haka tin 6 da mintina ya iso gidan da motarsa Daman Abdul tini ya shirya itama duk rigimarta Saida aka lallabata tayi wanka tin asuba ta shirya dadah ta shirya mata abincin karyawa da wuri Babbah ma sai addua yake binta da ita Yana cewa saita cinye har marking din Daya wuce Wanda akeso.

Abuja zatai jamb din Dan haka Babu Bata time suka fito itada Yaya Abdul da Haroon din suka kama hanyar Abuja idanuwan Haroon na cikin mirror Yana kallanta itama shi take kalla suna jifan juna da murmushi tana masa magana kadan kadan kaja Yaya Abdul din yaji Mai take fada masa batasan Yana ganinta ba yayi mata banza sbd yasan ma maganar idan yayi Bata bakinsa zaiyi Dan haka yayi kaman ma baisan me sukeyi ba fatansu dai kar Haroon din ya jefar dasu gurin wannan mayen kallan nasa da kullum sai Babbah yace tsoron yakeyi Haroon din ya cinye masa ita da ido ta rame kafin a tashi auren.

Sai 3 suka dawo gida a gajiye budurwan gidan ta dawo harma da zazzabi sbd kaf rayuwarta Bata taba Shan wahalan tafiya ko wata yar gwagwarmayar ba sai yau duk da komai na gata Akai mata Dan kuwa ko Rana Haroon dinta Bai bari ta shiga ba Saida zata shiga exams din ta fito mota hakama bayan fitowanta lafiyayyar tsadaddiyar restaurant yakaisu sukaci abinci Amma Sam Bata iya cin wani abincin ba sbd gajiya gida kawai takeso karshe ma haka suka koma daga shi har Abdul din suna lallabata har aka iso gidan.

Haroon ajiyesu kawai yayi ya wuce Shima Dan haka wanka dadah ta taimaka mata Tayo ta zo ta kwanta take bacci ya dauketa sedai Koda yamma tayi zazzabi sosaine ya rufeta Dan haka hankalin dadah ya Dan tashi zuwa dare Saida aka Kaita chemist kafin su dawo zazzabin ya Dan saketa Se zuwa dare ya sake dawowa.

Koda gari ya waye Haroon Bai Isa gurin aikinsa ba Jin rashin lafiyanta Kai tsaye gidan ya taho karshe dai asibiti aka kwasa aka Kaita duk da narkewanta ne yake Saka ciwon zama wani babba.

Suna zuwa haka aka kwantar da ita sbd ganin yanda hankalin duka ahalin ya tashi hakama Haroon seelah din.

Kwananta Daya a asibitin aka sallameta bayan Haroon yagama lalacewa akanta tareda mantawa da aikin dayake gabansa Wanda duk iya kokari da sadaukarwan siddeeq gurin ganin project din ya tafi daidai ko kadan ne Hakan Bai faru ba Dan haka yake cikin tashin hankali da rashin nutsuwa.

Aikuwa Haroon na dawowa hayyacinsa ya nutsu ya fahimci gagarumar tashin hankalin Dake gabansa take ya shiga firgici Shima Dan tini ma sbd sakacinsu aka sace plans da komai da komai na project din.

Wannan mummunan tashin hankalin ya kusan Sakasa zaucewa Dan kuwa Yanke jiki yayi ya Fadi Saida siddeeq da sauran ma'aikatan suka taresa sedai gaba Daya Jin yayi Yana fita hayyacinsa kansa na Neman Juyewa hannuwansa na rawa.

Gaggawan mayar dashi hotel siddeeq yayi Shima nasa hankalin baa kwance ba Dan kuwa yasan ko Dad yaji wannan zancen sake samun hawan jini zeyi gashi Babu ya yanda zata yiyu cikin qanqanin lokaci su hada sabuwar plan din dazata sakasu Kai labarin wannan project da aka fara.

Haroon Neman zaucewa yafara yi zuciyarta na tsananta bugun Daya wuce misali hakama baisan ta inda zai fara ba.

******Dad Lameenu Dake zaune tareda Mam a palonsu na office suna magana wayarsa ce tayi ringing Ya juya ahankali ya Kalli sunan me Kiran yaga BB ne Dan haka Kai tsaye ya dauka tareda Kai wayar kunnensa Yana cewa

"Yes BB"

Bayanin komai daki daki BB ya fara korowa tin daga kan sunayen ahalin gidan Babbah da Kuma yanda Haroon gaba Daya rayuwarsa ta mace akan yarinyar gidan da Baya gane komai ba a yanzu idan ba abinda ya shafeta ba harma da bautawan dayake musu da gagarumar tsautsayi da aka samu akan project din....

Dad Lameenu Bai gama Jin karshen zancen ba wata mummunan zufa ta tsinke masa Yana cewa

"What???
Yaushe wannan babban balain ya samu??
Ina Haroon din yake yanzu??

Mam na Jin Hakan ya ajiye wayar hannunsa Daya karanta wani article da aka rubuta gameda rushewan da SEELAHs keyi a boye batareda sun bari duniya ta saniba.

Ajiye wayar yayi Yana Dan rintse idanuwansa da suka fara sauyawa Dan kuwa Yana fatan ba abinda zuciyarsa ke Saka masa bane zaiji daga Lameenun.

Cikin tashin hankali lameenu ya buqaci ganin BB yanzu yanzu Dan zuciyarsa bugawa zatai idan Yana sauraron wannan mummunan tashin hankalin ta waya.

Kashe wayar yayi Yana kasa kallan Mam da shima ya kasa tambayar Lameenun komai BB din yake Jira yaji komai Dalla dalla daga bakinsa.

Kafin BB ya iso daga Mam har lameenu da jininsa ya Dade da Hawa Dan tini aka kirawo likita Yana cikin auna BP dinsa BB ya iso take ya sallami likitan akan saisun gama magana.

iPad din hannun BB ya fara kamo hotunansu Hafiz da Yan gidan kaf ya ajiye ipad din gabansu bayan ya kamo hoton Ameenatou datake sanye cikin hijab dinta na islamiya tana murmushi asalin kyanta da kuruciyarta a bayyane tana kallan gefe Dan kuwa batasan ana daukanta hoton bama.

Bayani Daya bayan Daya a tsanake BB yafara jerowa Wanda yayi mugun girgiza su musamman Mam Dan kuwa Bai taba tinanin Shima Haroon zai fada irin kaddarar Dan uwansa ba ta yiwa mace son da Bai kamata ba adaidai lokacinda suke buqatan nutsuwansa da hankalinsa tareda sadaukarwansa fiyeda komai a duniya yanzu.

Ameenatou dukkaninsu suka zubawa idanuwansu da sukai jajir,

Tayaya Haroon zai bari zuciyarsa ta mutu akan mace bayan yasan Menene a gabansu,
Tayaya Haroon zai bari mace ta shiga zuciyarsa,
Tayaya zasu iya samun yanda suke so daga zuciyar Daya mutu akan mace.

Kenan shi tasa mummunan kaddarar akan matan da yayansa suke so ne ko me?
Shima Haroon macen ce zata shiga tsakaninsa da ita?
Ta Ina zai fara karban wannan kaddarar ta Haroon bayan haryanxu Bai fito daga baqin ciki da radadin ta Jamaal ba.

Wani nauyi kirjinsa yayi Yana tafasa da wani irin zafi da radadin da baisan mezaiyiba akan Haroon din

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login