Showing 144001 words to 147000 words out of 261814 words

Chapter 49 - AMEENATOU BOOK1&2 CMPLT BY MAMUHGEE.txt

MAMUGEE   

07 Jul 2024

59016

abubuwan rayuwa yanzu Kuma munzo kuce mana aa??
Dan Allah dai ku duba."

Ko kallansa basuyiba shi Kuma tini zuciyarsa ta fara harzika Dan haka ya kallesu zaiyi magana Babbah ya riqesa tareda kallansu ya Bude Baki yace

"Yaushe ne ranar dubiyan da kuke magana??

Batareda sun kallesa ba suka ce sai Wani sati.

Dan daure fuska yayi Shima zuciyarsa na 'daci da konuwa ya kallesu yace

"To zan Jira anan har Wani satin Dan wllah tallahi bazan tafi ba batareda naga 'yata ba"

Dadah Dake gefe matsowa tayi zata gwada nata rokon Wani security ya taso Yana hawansu da masifar data Saka ran Hafiz qarasa Baci take suka fara hayaniyar data Saka dole sauran securities din tasowa ana son kashe zancens amma babbah take ya fara son tara musu jamaa dan yayi rantsuwan bai tafiya koina sai yaga yarsa.

Kafin kace me tashin hankali yafara kokarin tashi a gurin sbd Babbah sarai yasan ba barinsu zasuyi shigar ba Amma idan Akai rigimar dole bazaa rasa wani babban daga ciki shiga zancen ba daganan sai a duba buqatansu.

Suma securities din basuda wani dogon mutunci Dan haka suka rufe idon bazasu ma duba maganar shigarsu ba Dan Haka lamarin yafara zama babba mutanen Dake shige da fice suka fara taruwa kallan fitinar.


Babbar sa'ar dasu Babbah suke tafe da ita itace ta taimakesu Allah ya kawo Dr Zakeer zai shiga asibitin motar dr ibrahim na bayansa Dan kusan tare suka iso Dan yau ne zasu tafi da Ameenatou asibitin matar Dr Charles wadda take private ce itace da kanta zata cire musu cikin batareda sani ko fatan samun matsalan komaiba su dawo da ita.

Fitinar da akeyi ce ta Saka Dr Zakeer Dake gaba tsayawa da motarsa batareda ya shige ba ya sauke glass Yana amsa gaisuwan securities din kafin ya Kalli su babbah dake tsaye Wanda kana kallan babbah kasan baida lafiya kwata kwata hakama Dadah Dake gefe kuka takeyi sosai Dan bata dauka ganin ameenatou zai musu wuya ba kenan babu maganar daukanta garesa zuwa gida kaman yanda sukazo da shirin hakan.

Dr Ibrahim ma sauke glass yayi Yana sauraron bayanin da security kewa Dr Zakeer akan hayaniyar.

Kallan Babbah Dr Zakeer yayi cikin girmamawa a matsayinsa na babba garesa yace

"Baba da alama bakada lafiya meyasa zakaita hayaniya
Zaka tayarwa da kanka ciwo ne ko qarawa
Yanzu dai hakuri zakayi baba ku tafi ku bari zuwa Nan da kwana uku ku dawo inshallah zaku samu ganin Wanda kukazo dubawa din"

Girgiza Kai Babbah yayi Yana Jin radadin ransa na karuwa Dan ma ciwone yasaka yake kasa Wani tashin hankalin Amma ai shi Kam bayajin zai matsa daga gate dinnan indai ba daukesa zaayi ba amma wlh Saiya ga Ameenatou yau ba sai gobe ba bare kwana ukun da likitan yake magana kaman yanda sukaji securities na Kiransa Dr kenan alaman shi din likita ne.

Hafiz ne ya Dan matso cikin Sanyaya zuciyarsa da son rokon Alfarman yace

"Dan Allah Dr ku taimaka ku bari mu ganta,
Wlh kusan wata Tara mahaifin nata Yana jinya a kwance yake baisan waye akansa ba duka duka baifi sati uku da tashi ba ita kadai yakeson Gani sbd baisanma ta samu matsalan da aka kawota Nan din ba,. dukkaninmu bamu samu Daman ganinta ba tinda aka kawota..."

Dr Ibrahim Dake jinsu tinda Babbah ya ambaci sunan AMEENATOU acikin zancensa sai sunan ya tsaya masa Dan haka ya katse Hafiz daga cikin motarsa da cewa

"Menene sunan patient din taku??
Daga Ina kuke??
Cikakken sunanta?"

Suna Jin Hakan suka Maida hankalinsu gurin Dr Ibrahim din
Da sauri Babbah yace

"AMEENATOU NUHU BABBAH ko AMEENATOU OMAR JADEN........

gabaki Daya securities din gurin dasu dr ibrahim din juyowa sukai da sauri cikin tsananin mamaki me girma suka kallesa Baki sake.

Dr Zakeer ne ya Bude motarsa ya fito Yana kallan Dr Ibrahim Wanda Shima budewa yayi ya fito ya Kalli security Daya yace a Kori mutane da suka tsaya kallo.

Qarasawa sukai gaban Babbah Wanda yasan ba komai bane ya sakasu shiga mamakin face sunan Omar jeden daya ambata Dan ko ciwon haukan ne da 'yar Jaden sun San tafi karfin asibitin Nigeria bare shi da suke gani talaka yana tsaye da ciwo a jiki.

Dr Ibrahim ne ya sake jeho tambayarsa ga Hafiz sbd tinanin ko Babban baida cikakkiyar lafiyan Kai tsufa yafara cinye kan a natse cikin kokarin fahimtarsu ya Kalli Hafiz yace

"Daga Ina kuke?
"Menene cikakken sunan mara lafiyan taku?

Babu yanda zaayi su fada asalin inda suka koma a yanzu Dan haka Kai tsaye inda aka Sansu a Baya ya fada.

"Daga Nasarawa muke,
Wannan mahaifinmu ne,ga mahaifiyarmu Nan tsaye a gefe,
Ita wadda mukaxo Gani qanwata ce sunanta AMEENATOU OMAR kaman yanda ya fada"

Dr ibrahim zai sake jefa wata tambayar sbd kansa ya kasa dauka, shi ganin yake kaman Basu gane tambayarsa ba, dr Zakeer ne ya katsesa da sauri ta hanyar cewa su shiga ciki ayi maganar kawai.

Daman Hakan Dr Ibrahim Shima yakeda niyar yin Dan haka take aka shige dasu Babbah zuwa cikin asibitin aka bar securities da mamaki me girma da shakka sbd sunan daya fito daga bakin babban.

Kai tsaye office din md suke nufa Wanda yake asibitin tin sassafe sbd hankinsu duka yau din baa kwance ba da abinda zasu aikatawa Ameenatou,
A matsayinsu na likitoci sunsan illan abortion da hadarinsa musamman irin wannan da sune zasuyi sa da kansu,Barna ce akan Barna suke Neman aikatawa Dan rufe Barna da barnar,
Fatansa dai Allah yasa sunada Rabon rufe wannan Barnar batareda komai ya faru ba.

Shigowan su Dr Zakeer office dinsa ne ya Sakasa sauke ajiyan zuciya zaiyi magana su Hafiz suka kunno Kai.

Kallansu Dr Ibrahim yayi Yace su Jira waje tukuna.

Komawa sukai waje suna Jira Dr Zakeer ya rufe kofar ya dawo Yana cewa

"Dr ibrahim kana tinanin baban Nan Yana lafiya kuwa??

Numfashi Dr Ibrahim ya sauke Yana fara jerowa md bayanin komai kafin ya Dora da cewa

"Lafiyansa kalau ga dukkanin alama,
Kuma idan na Tina duka bayanin Ameenatou dayake rubuce a file nata itace Ameenatou Omar Kuma address nata Nasarawa ne kadai a jiki,sedai abin mamakin anan shine wannan din yace shine mahaifinta sannan Kuma ya ambaceta da Ameenatou Omar Jaden a sanina Kuma Omar Jaden Daya muka sani Babu wani"

Qara karfin AC md yayi sbd zufan Daya fara jiqasa hankalinsa na tashi kansa na daukan zafi kaman yanda Dr Zakeer Shima ya rude.

Wata masifar ce da alama take Neman Hawa akan masifar da suke ciki.

Meya hadasu da 'yar Jaden Kuma??
Yar Jaden anmata ciki a asibitinsu ai qiyamarsu ta tsayu,
Suna baqatan bayani dai cikakke,
Idan dai yar babban ce su bincika kawai asirinsu rufe su Bata sallamarta ya tafi da ita batareda sanin cikin ba Dan tana tafiya record dinta clean zaa rubutasa Babu komai Babu matsala Dan ko zancen cikin ya bulla Babu ruwan asibitinsu lafiya kalau suka badata.

Wannan shawarar Dr Zakeer ya bada Amma suka kasa Naam da Hakan sbd tsaro Dan haka Dr ibrahim ya kirawo su Babbah suka shigo.

File dinta Dake office din md tin jiya
md din ya miqawa Dr ibrahim ya Bude Yana fara karanta informations nata Daya bayan Daya da abinda aka rubuta ya kawota asibitin da duka bayanai akan ciwonta da komai.
#MAMUH#



*_ZAFAFA BIYAR_*

1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_

2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_

3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_

4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_

Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200

*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*

*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*

*_MTN/VTU 09134848107_*

_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
#ZafafaBiyar
89

*_AISHA's COLLECTION_*
Hajiyata Kinason kiyi kasuwanci amma bakida jari?
Ko kuma kinada jarin amma bakisan maiya kamata ki fara saidawa ba?
Tou hajiya nesa tazo kusa ga sauki yazo na kawo muku inda zaku samu kaya a cikin farashin sari,muna saida kaya kala-kala inda zaki samu a cikin sauqi da rahusa.Akwai varieties of women accessories ranging from Atamfa, Laces and shoes at both wholesale and retail..
Hajiya da kayan da kika sani da Wanda Baki saniba harma da Wanda Baki taba Gani ba na kayan alfarma da burgewa da asalin kyau na quality kizo karki bari ayi Babu ke,
ko kasuwaci ko sanyawa,ko ankon biki,lefen alfarma,kayan sallah..komaima namu inshallah na musamman ne da zakiji dadin kasancewa a cikin kasuwanci damu...
Join our group to see lot of our amazing products 👇

Location: LAGOS
We deliver nationwide

09013833502

https://chat.whatsapp.com/JRkPEIt0xVj2vuE8HAGRUL

************
Numfashi me zafi Dr Ibrahim ya sauke tareda dagowa ya Kalli Babbah dasuke zaune gefe cikin bada nutsuwarsa ga abinda zai tambaya da amsar zaa basa yace

"Baba kace cikakkiyar sunan 'yarka Ameenatou Omar??

"Eh hakane sunanta" Babbah ya fada cikin nutsuwa Shima.

"Kaine ka haifeta?
Menene cikakken naka sunan?

"Sunana Nuhu babbah,
Ba nine na haifeta ba Amma a hannuna aka haifeta Dani da mahaifiyarta uwarmu Daya ubanmu Daya nine Uba Kuma uwar mahaifiyarta hakama itama nine ubanta nine gatanta Dan har ayau batasan ba nine na haifetaba.

Shiru sukai dukkaninsu na seconds kafin Dr Zakeer yace ko zamu iya sheda Hakan??

Da sauri Hafiz yace "eh" Yana ciro wallet dinsa daga aljihunsa ya Ciro id cards dinta guda uku duka masu hotonta da sunanta Ameenatou Nuhu babbah ya miqa musu.

Voters card dinta ne,sai national id card,sai Kuma na exams dinta na waec datai duka suna hannunsa Daman shine ko Yaya Abdul suke ajiyewa.

Address dinsu ya tambaya suka karanto masa Ya duba na jikin id cards nata shikuma Dr ibrahim ya duba na jikin file yaga Abu Daya ne Dan komai nata Babu Wanda JEEY ya saka na Seelahs ko na Jaden duka na Nasarawa ya Saka sbd tsaro Kar asan ita wacece din nuhu babban ne kadai bai saka a sunan mahaifinta ba ya saka omar sbd bai san sunan babbah na asalinba babbah kadai yasan suna ambatarsa hakama da sunan asalin mahaifinta aka daura masa aure da ita shiyasa Kai tsaye ya Saka mata Ameenatou Omar kawai batareda ya Saka Jaden din ba.

Md Daya matsu yaji inda sunan jden ya Hadu Da wannan maganar gabaki dayanta ya jeho tasa tambayar d cewa

"Menene cikakken sunan asalin mahaifinta?
Yana raye ko ya rasu ne?

Shiru Babbah ya Dan yi kafin ya Bude Baki Kai tsaye ba shakkar komai yace

"Omar Jaden seelah ne asalin mahaifinta"

Tsit suka sake yi md yana sake goge zufan goshinsa,
Kenan Dr JEEY yar uwarsa ce shine Bai taba nunawa ba koda wasa bazaka taba cewa ma ya Santa ba bare hada family,
Duk kulawan dayake Dan nuna mata da karban case dinta da yayi duk Yana sane,
Innalillahi wainna ilaihirrajiun.

Zufa kowannensu ya sake sharewa hankali na tashi.

Dr Ibrahim ne yayi karfin halin tambayar Babbah dalilin kamuwa da ciwonta da abinda yasa duk tsawon wannan lokacin Basu taho sunzo gurinta ba.

Ahankali Babbah ya zayyano labarin da kusan kowa ya sansa A ranar daurin auren 'dan Mam Seelah yayi taccident ya rasu tareda mahaifin matarsa da uncle dinsa Alh Omar jden wanda tin da Akai accident din Babu Wanda ya sake Ji daga Omar din da ahalinsa.

Iya daga Nan labarin yake tsayawa koina batareda an Dora da sanin Ina amaryar take ba bare danginta tinda su talakawa ne baa sake tada nasu zancen ba.

Shiru kowa yayi tsit na tsawon mintina kafin md ya Kalli Babbah cikin qarfin halin da kulawa yace

"Duka bayanai gasunan munji Kuma mun fahimta sosai Amma duk da Hakan sbd tabbatarwa da gudun matsala tareda cike doka zamu baka hakuri yanzu ka tafi zuwa Nan Da kwana biyu saika dawo inshallah zamu baka damar ganinta harma fiyeda Hakan idan ka buqata"

Shiru Babbah yayi cikin nazari da tinani kafin ya dago yace

"Ba iya ganinta nazo yi ba,sallama muke so mu tafi da ita gida insha Allah zamu nema saukin daga Allah acan"

Daga md har su Dr Zakeer ajiyan zuciya me karfin gaske suka sauke a boye ta dr ibrahim CE ta fito fili sbd anzo inda yanzu Kam sukeson Azo Dan kuwa Babu Wanda ba tsoro da tashin hankali ne a ransa ba Dan alamun dai suna nunawa da gaske ita yar Jaden din ce tinawa da labaran rasuwar matarsa Da aka ringa yi a lokacin da Akai gobaran.

Wannan masifar da balain ko waye yayiwa yarinyar Nan ciki Allah ya Isa a tsakaninsu,
Dole ma suyi gaggawan binciken komai kafin jibi Babbah yazo su miqa masa yarsa su tafi tin kafin cikin Nan Daya fara fitowa ya bayyana su shiga masifar d batada kofar fita a hannun Omar Seelah.

Cikin girmamawa suka bawa Babbah tabbacin inshallah zuwa Nan da jibi yazo zasu duba su sallametan su basa ita din.

Farin ciki ne me tsananin gaske ya rufesu babban yai godiya sosai suka fito.

Suna ficewa md ya miqe Ya dauko ruwan hannuwansa na Dan rawa yakai bakinsa yasha Yana Jin zafi Tako ina,

Yau da ace sunje zubar da cikin Nan Wani abin ya biyo Baya Yaya kenan zasuyi da seelahs?
Cabdijam,
Jin yayi kwata kwata Babu abinda yakeso yanzu kaman Ameenatou tabar asibitinsu kota halin Yaya ne.

Kusan Suma su Dr Zakeer tinanin ne a ransu Dan haka take aka kira Dr Charles aka sanar dashi komai ya sauya,
Shi kansa Yana Jin Hakan ya ringa godewa Allah da matarsa Bata taba lafiyan Ameenatou din ba dan haka shi tin a cikin Daren ma ya fara tinanin Neman sauyin asibiti kawai Yama barta gaba Daya incase idan gaba tsautsayi yasa zancen ya dawo Baya.

Dr Zakeer ma fara neman yanda zaa sauya masa asibitin yayi Dan hankalinsa Kuma ya tashi akan lamarin,
Bawa Babbah ita shine rufin asirinsu  ayanzu to Amma Kuma dawowan Dr JEEY shikuma wani tashin hankalin ne daban duk da kaman yanda md ya fada bai nuna musu yar uwarsa bace koya dawo suma bazasu nuna sun saniba magana Daya iyayenta sunzo an sallameta.

Cikin farin ciki su Babbah suke sukam Dan haka a masaukinsu da suka sauka na Wani hotel suka koma a shirye tsaf da Shirin tafiya kowanne lokaci.

******Sister Ashley Dake kallan Street din gabansu tana sanarwa me taxi din idan sun samu mutane a kusa pls suyi tambaya Dan batasan gidan datazo din ba itama.

Wayarta ce tafara ringing ta Kalli Jakarta Dake kan jikinta ta Bude tareda Saka hannu ciki tana Neman wayar.

Katsewa wayar tayi Wani kirin ya sake shigowa ta fito da wayar tana kallan screen din

Bazata iya Tina lokaci mafi farin ciki a rayuwarta ba kaman yanzu da wani sanyi da farin ciki me tsananin gaske Daya cike zuciyarta ba ganin sunan Dr JAMAAL akan wayarta.

Hannunta har Wani rawa sukeyi ta dauka da sauri tana hamdala farin cikinta da mutuwar jikinta duka a bayyane.

Tana dagawa kafin tayi magana muryansa tafara Ji cikin tsananin sanyi da nutsuwa yace

"Aslm alailkm."

Amsawa tayi cikin girmamawa jikinta na sanyi da yanayinsa sedai Bata karayaba ta gaidasa.

Amsawa yayi da murya me kama da yanayi na rashin lafiya kafin da kasala yace

"I'm sorry,bazan iya magana ba ita kadai nakeson Ji,Inason Jinta,pls can you.........

Katsesa Ashley tayi da cewa

"Dr JEEY kayi hakuri Amma kana buqatan Jina tukuna,
Ameenatou na dauke d........"""dip Kiran ya katse.

Wani mummunan accident ne ya faru sakamakon motar data dakesu batareda sun San da zuwanta ba ta gefensu Wanda ya Sakasu mugun bugawa da transformer Dake gurin wuta tafara Watsi tana kokarin tashi.

Motar su BB da suka cirewa number tini tayi Baya duk da ta bugu sosai ta fashe ta gaba sbd yanda suka daki motar su Ashely din.

Reverse sukai suka bar gurin da mugun gudu goshin BB na zubar da jini sosai na buguwa Shima bullet hancinsa jinin yake zubarwa kansa na juyawa Amma haka suka tsere sedai basuyi tafiya me nisa ba suka parker motar Wani gurin da Babu mutane suka fito tareda cire komai nasu suka bankawa motar wuta sbd bazasuyi wata tafiya me tsayi ba zaa kamosu hakama sun bugu sosai Suma komai zai iya faruwa.

Mutane cikin gaggawa suka Dan taru sbd anguwan ba mutane sosai can JAMAAL ya siyawa umman gida,

Cikin gaggawa mutanen da aka samu sun shigo street din suka rufu aka motar dan taimaka musu.

Cikin yardar Allah daga Ashley har drivern Babu Wanda ya rasa ransa amma Ashley ta bugu sosai hakama bleeding takeyi sosai daga cikinta Wanda ya Saka wata nurse Dake gurin itama cewa tana tinanin cikine a jikinta Kuma Kila fita zaiyi.

Da gaggawa aka kwashesu zuwa asibiti sbd cetan ranta da abinda yake cikinta idan da akwai Rabon ya rayu.


JEEY kuwa tashi yayi daga kwancen dayake tareda zare roban drip Dake hannunsa ya tashi da kyau Yana sake Saka Kiran wayarta.

Cikin ikon Allah wayar Bata mutu ba Amma Kuma baa daga ba haka ta ringa ringing Amma baa dauka.

Siddeeq ne da isowarsa kenan Poland din tareda Mam ya shigo dakin asibitin Yana kallan JAMAAL daya Dan fada yayi haske sosai idanuwansa sun qara haske ya dago idanuwan ya kallesu.

Ganin Dad dinsa a tareda siddeeq din Wanda suka sauka kasar tare ya sakashi Dan dauke Kai Yana cigaba da Saka Kiran Ashley.

Tsakiyar dakin Mam ya iso ya tsaya akansa Shima kallansa yakeyi Yana auna irin hawan da jininsa yayi fiyeda a kirga sbd Jin JAMAAL din ciwon ciki me qarfi da zazzabi tareda tsananin damuwan ciwon Mum dinsa daya kwantar da shi ba tsammani.

Bai taba tinanin sake zuwa qasar ba Amma bazai iya riqe kansa ba ko kadan ga zuwa ganin 'dansa Dan bazai iya komawa Nigeria dinbama da tinanin JAMAAL din ba lafiya.

Shiru ne ya ratsa gurin batareda kowa yace komaiba,

Mam yaqi magana ne tareda zubawa JAMAAL din idanuwa Dan kuwa yasan komai lalacewansa tinda ya Riga ya zama ubansa ya haifesa to ya gama da duk wani zafin kansa,

Shikuwa JAMAAL din da zafin kan nasa da radadin uba Daya kasance irin nasa yake yakicewa kafin ya juyo a hankali cikin kamewa da fuskewa ya Kalli Mam din Kai tsaye ya gaidasa Yana komawa da bayansa ya kwantar tareda Maida idanuwansa akan Siddeeq da baida ikon magana duk yansa ya so batareda Mam da Jeey din sunyi magana ba duk kuwa da yanda ya matsu ya iso yaga jikin JEEY din Dan ba qaramin tashin hankali suka shiga ba da ciwon nasa daya bawa har doctors dinsa tsoro.

Cikin Kulawa da tsananin kaunar da kulawan dayakewa jeey din a bayyane yace

"Yaya jikin Dr?"

Gyada Kai yayi a natse tareda kallan wayar hannunsa da idanuwansa Yana cewa

"Kira Ashley yanzu inason magana dasu"

Magana ya qarasa gurinsa yayi masa a natse kafin ya juya ya fice Yan daga wayarsa Dan Kiran Ashley yabarsu su biyu a dakin.

Wayar ya ringa Kira Amma shi ko shiga Batayi kwata kwata Amma Bai kawo tinanin komaiba yaci gaba da sake gwada kiranta Dan Shima yanason magana dasu din kwana biyu Bai samu Daman waya da kowaba kansa ya cake da zafin ayyuka acan Greece sunyi yawa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login