Showing 6001 words to 9000 words out of 44853 words

Chapter 3 - NAGA_RAYUWA_BOOK_1

Unknown   

02 Dec 2025

97

ja bakinsa ya tsuke yana dariya.


Tun daga ranar ya zama na saba saka kayan hausawa, kuma ko aike na waje za’a yi Mami na bata bari na fita ba nik’ab har hakan ya zame min
Jiki. Sai dai a fuskar Umma
Wani lokacin ina kallon yanayinta kamar hakan baya mata da’di, sai dai ba yarda zata yi ne. Duk inda na je kuwa sha’awar shigata ake, don kowa ya ganni ya san d’iyar wacece? D’iyar mace mai mutunci wacce ta san ciwon kanta, kuma yake bawa y’arta tarbiyya, ba wacce da kanta take saka y’a’yanta shigar banza ba don kawai su kawo mata mazan aure ta dinga kuma zuga su da fa’din sun yi kyau.


Sanda na fara period kuwa, Mami hana aikena ta yi. Saboda wani irin kyau da na dinga zubawa, mak’erin y’an mata na ji suna cewa ya fara k’era ni. Don haka ta shiga taka tsantsan da ni. Idan Ya. Muhd ya yi magana ta hau masa masifa don haka ya gani ya zuba mata ido kamar yarda kowa ya yi.

Sanda maganar aurensu ta bujiro da y’ay’an abokin Abba Mami na jin iya secondary kawai suka gama. Ta dinga tab’e baki tana fa’din “Amma Sadik kun yi bak’ar dabara, yanzu meye riba a auren k’wailayen mata?” Ya Muhd don takaici kasa mata magana ya yi, Ya. SADIK MURMUSHI ya saki yana furta “Ai auren irinsu Mami ya fi riba, ko bakomai zasu bi duk wani tsari da aka shar’anta musu..” Ta ja tsaki ta furta “Mugunta zaku musu ba, ai shikkenan shi yasa duk bala’i ba zan yarda AYSHA ta yi aure daga gama secondary ba dole ko degree sai ta yi, idan ma bata yi masters ba…” Ya Muhd da yake tsaye ya tura hular sa goshi yana furta “A dai rage dogon buri, idan yarinya ta yi girma da yawa yanzu mazan ma gudun aurenta suke, don sun san tafi k’arfinsu…” Yana ji ta k’unduma wani zagi ya shige d’akinsu yana dariya.


Haka kuwa aka yi, bayan wani lokaci aka gudanar da bikin Ya. Muhd da Ya sadik. Muhd da Khadija, Yaya Sadik kuma da Nafisa a lokacin ina Js 3. Amma duk wata cika ta matantaka ta bayyana a surar jiki na.



★★★✍️


Ina SS 2… al’amarin ya faru. Mun taso daga Islamiyya ni da k’awata Asma’u, muna tafe muna hira a hankali cikin nutsuwa. Ranar ganin ba kowa a layin sai na ‘dage hijabi na. Asma’u ta kalleni da mamaki ta ce “Yau kuma Aysha? Lallai kina son idan Mami ta ji labari har ni ta ha’da ta ci mutunci na kenan?” Tab’e baki na yi, ina yamutsa na fuska na ce “Ai layin ba kowa….kuma ma waye bai sanni a layin nan ba?” Cigaba ta yi da bani labarin wani series da ake yi a Mbc bollywood wanda na yi missing ban kalla ba, sabida girki da Mami ta saka ni a daidai lokacin.


Murmushi kawai nake saki… Zuciyata ce ta wani irin bugawa daidai lokacin da muka ha’da ido da shi yana tsaye a gefen wani gida da ake gini ba’a k’arasa ba…” Da sauri na ja nik’ab d’ina na mayar ina jin yarda sautin bugun zuciyatta ya tsananta. Tabbas na san fuskarsa a sunna t.v matashin Malamine da yake tafseer a duk azimi. Ba wanda bai san Ustaz Ahmad ba. Saboda yarda yake d’an gayu komansa mai kyau ne yana kuma ji da tashen Naira. Asma’u ta furta k’asa k’asa “Ke AYSHA kamar Dr. Ahmad sulaiman ko?” Ban amsa mata ba, k’irjina dai ya cigaba da bugu. Sam zuciyata kasa cigaba ta yi da saurarar labarin da Asma take bani saboda wani yanayi da na fa’da mai girman gaske..


Tabbas tunda nake ban tab’a ganin mutumin da jallabiyya ta yiwa kyau kamar wannan mutumin ba. Ga wani azababben k’amshin turarensa da ya maye wajen gaba d’aya. A kallon da na masa sai naga ashe har ya fi kyau a fili. Yana da haske sai dai ba sosai ba. Idanunsa farare tas kuma mayalwata. Cikakkiyar gira ce da shi da gashin ido kamar yarda gashin kansa yake cikakke kuma bak’i si’dik. Duka wannan na gani ne a guntun kallon da na masa.


Asma tana shiga gida nima na fa’da gidanmu da sauri tunda mak’ota muke da su. Shi kuma Ustaz gidan da yazo gidan yana kallon gidanmu.


Ban bari kowa ya ji shigowata ba na haye sama da sauri na shiga d’akina. Haka kawai nake don sake ganinsa don na san windown d’akina yana kallon gidan da yazo. Ina d’aga labulan kuwa na hango shi yana tsaye still suna magana da Lawal da ya kasance d’an mak’otan mu. Idanunsa na ga ya juyo yana kallon gidan mu kamar mai nazarin wani abu… Daidai lokacin Mami ta shigo tana k’wala min kira. Da sauri na saki labulan windown alamar rashin gaskiya bayyane k’uru k’uru a cikin idanuna. Ba ta yi min magana ba sai takowa da ta yi zuwa gaban windown ta d’aga labulan tana furta “Uban me kike kallo anan d’in?” Idanunta ya sauka akan Ustaz da sauri ta juyo tana kallona baki sake ta furta “Namiji kike kallo Aysha? To Uban me ya ha’da ki da shi?”


Hantar cikina ta ka’da… bakina na rawa na furta “Babu komai Mami….




𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️


Wancan group d’in ya cika Wanda Bai samu Shiga group 1 ba ya Shiga 2. Amma don Allah idan kana group 1 kada ka Shiga 2 don duk Abu d’aya ne.


A shiga group, ba Zan juri posting a kowane group ba, ba kuma Zan juri a dinga cewa Na tura daga farko ta private ba. Hankalinka kwance ka shiga group kawai. Nagode[8/5, 1:21 PM] Nazeefah Nashe: NA GA RAYUWA♥︎♥︎♥︎


𝒩𝒶𝓏ℯℯ𝒻𝒶𝒽 𝒩𝒶𝓈𝒽ℯ★✍️

Free Book.. MIKIYA WRITERS ASSOCIATION




Arewabooks @nazeefah

Wattpad@Nazeefah381

08033748387.

★★★★★ 𝒫𝒶ℊℯ 5.



Mami ta zabga tsaki tana sakin labulan tana kallo na ta furta “Idan ma shi kike kallon, ki tsaya ki saurareni da kyau.” Ta fa’da tana jan kunnena “Koda wasa kada ki sake ki saka wani namiji a ranki, a yanzu dai kam don ko me zai faru ba zan bari a aurar da ke ba, sai na cika burina na kin zama wani abu a fannin ilimin boko.” D’aga kai na na yi, ina lumshe idona. Ta fice da sauri ina jin b’acin rai ma ya mantar da ita abinda ya kawo ta.

Bu’de idona na yi a hankali ina sakin ajiyar zuciya. Ba tare da damuwa ba na sake yaye labulan d’akin. Daidai lokacin da Ustaz ya d’ago yana sake kallon gidan mu, ban damu ba na tsaya na kalleshi sosai don na san ba zai ganni ba, glass d’in yana da duhu daga waje ba’a ganin wanda yake ciki.


Na saki ajiyar zuciya ina kallon sanda ya shiga motar sa yana sake bawa Lawal hannu suka yi misabiha. Ya ja motar ya bar wajen. “Allah ya yi halitta…” Na furta a hankali ina kai wa saman gado na zauna. Har a lokacin yanayin bugun zuciyata bai koma daidai ba.


Shikkenan na samu abin yi tun daga ranar da na gan shi, ban sake komawa daidai ba. Kullum cikin tunaninsa nake da burin sake ganinsa koda sau ‘d’aya ne a rayuwata.


Ranar da sati ya zagayo ranar wata lahadi still mun dawo Islamiyya da Asma’u kamar wancan lokacin. Asma ce take ta surutunta ni kuwa bakina shiru, don wani irin yanayi nake ji a zuciyata ga bugun zuciyartawa ya sauya. Muna doso layinmu na ji mayataccen k’amshin turarensa wanda ba zan tab’a mantawa ba. Da sauri na sauke Nik’ab d’in don kuwa na tabbatar shine duk da bayansa kawai na gani still sanye yake da jallabiya mai kyau brown kansa da hula tashi ka fiya nace mai tsadar. Muna doso ta inda suke zamu wuce don dole sai ta nan d’in na ji k’afafuna sun fara rawa kamar ba zasu d’aukeni ba. Duk da nik’ab ne a idanuna na ga ya ‘dago yana kallon inda muke sai kuma suka yi shiru da hirar da suke. Da k’yar na saita kaina na nutsu muka shige su. Sai da na shiga gate d’in gidanmu sannan na saki ajiyar zuciya a hankali ina furta “Ya rabbi! Me ke faruwa da ni ne?”



Bayan kwana biyu ina zaune a ajin mu ja Islamiyya. Aka aiko kirana. A matsayin da nake kai na shugabar makaranta na san ba wani abu bane don an aiko kirana d’in, amma wannan karan sai na ji zuciyata ta buga sosai. Ido na tsurawa mai kiran nawa. Har ya ji haushi ya furta “AYSHA magana fa nake.” Da sauri na amsa da “To gani nan.”


A Office d’in Headmaster na tsaya ina knocking a hankali. Muryar Malam d’in na ji yana furta “Bismillah Ayshatu…” Na yi sallama na shiga, k’amshin turarensa ya doso hancina har ban san sanda na ware ido ganin Ustaz a zaune ba idonsa akan wani littafi da ke hannunsa. Wallahi Allah ne ya yi ba zan fa’di ba, Saboda zallar rashin nutsuwa. Sunkuyar da kaina na yi ina wasa da yatsuna. Har Malam ya gama rubutunsa ya d’ago yana kallona “Gaisuwa fa Ayshatu?” Da sauri na juya na kalli Ustaz da ya yi kamar bai san da ni ba a wajen. “Ina yini?” Bai d’ago ba na ji dai ya masa murya a k’asa “Lafiya..” D’an tab’e bakina na yi duk da na ji haushinsa, na mayar da hankalina kan Malam. “Ki je maza ki sanar da duk ajujuwa akwai assembly idan an idar da sallah..” Na amsa da sauri don burina fita daga office d’in kafin halin da nake ciki ya bayyana…”



Haka kuwa aka yi, ana idar da sallah ba wanda ya tashi daga babban filin harabar makarantar. Kowa ya zauna ya kuma nutsu ana jiran fara assembly. Duka Malaman makarantar suna zaune sun kame akan kujerunsu. Mu kuma muna tsaye don lura da masu surutu. Wajen tsit baka jin saurin komai. Malam Kawu ne ya nuna ni da nufin nazo wajensa. Ina isa ya furta “Ki fara karatu, Yanzu Malam Babba zai zo.” Na mik’e na d’au speaker d’in ina fara karatu ya yi daidai da shigowarsu. K’asa kawai na yi da kai na na cigaba da karatuna kawai cikin muryar Shureim da na k’ware da karatu da ita. Ina kallo Ustaz kawai ya lumshe idonsa yana jijjiga k’afa a hankali.


Sai da nace sadak’allahul azeem sannan ya bu’de idon nasa ya sauke su a kaina. Ji na yi tsigar jikina ta tashi. Da k’yar na ja jiki na koma inda nake na zauna don kam ba zan juri tsayuwa ba.


Malam Ahmad ne ya fara jawabi da sanar da su babban cigaban da makaranta da ta samu na zuwan Ustaz Ahmad da son d’aukar wani darasi a makarantar…” Kabbara da ihu d’aliban suka saka cikin matuk’ar murna da farin ciki.



Bayan ajiye loudspeaker d’insa Malam Kawu ne ya d’auka ya ‘dan yi barkwancinsa sannan ya sanar da cewa ya barwa Ustaz abinda har zuwa sanda zai bar makarantar.” Ta cikin nik’ab na ware ido jin abinda ya ce don ajin Malam kawu nan ne ajin mu, gefe guda kuwa na zuciyata wani irin farin ciki ne mara misali a cikinta. Haka aka tashi zuciyar kowa cike da farin ciki. Ina ji y’an mata suna ta yaba Ustaz haka kawai sai na ji raina ya b’aci tsananin haushi ya shiga zuciyata, ban sani ba ashe wannan shine kishi.



Kashegari da wani irin ‘doki na yi shirin makaranta, karo na farko har da mutstsika Lipstick a lab’b’ana sai naga na yi kyau da sauri na saki nik’ab d’ina tun kafin Mami ta gan ni da jambaki ta min masifa.

Sai dai na makaro ina d’aga kai na hangota ta cikin mudubi fuskarta a ha’de take kallona. Ta iso inda nake zuciyata ce ta dinga harbawa da k’arfi. Saka hannu ta yi ta cire nik’ab d’in, ta kuma saka yatsa tana zagaye lab’b’ana tana sakin murmushi ta furta “Jambaki AYSHA? Jambaki kika saka zaki makaranta? Me kike son b’oye min ne?” Lumshe idona na yi ina jin zuciyata na bugu da mugun k’arfi. “Kada ki fara AYSHA, kada ki fara abinda zamu zo muna k’aramin yak’i da iyayenki a gidan nan. Goge shi tas idan baki yi wasa ba tsaf zan cireki daga Islamiyyar na samu Malamin da zai dinga koya miki…” Da sauri na rik’e hannunta “Don Allah Mami kiyi hak’uri kada ki raba ni da makarantata, In sha Allah ba zan sake sakawa ba. Kuma wallahi bana kula kowa ko Asma ki tambaya…” Murmushi kawai ta saki ta janye hannunta. “Zan bincika..” Daga haka ta fice bayan ta saka ni na goge jambakin dama ni ko kalli bana sakawa ina da kwallina daga indallahi. Na saki ajiyar zuciya ina fita daga d’akin.



Shiru makarantar da alama ni da Asma ne muka fara zuwa. Muna shiga aji Asma ta fice don itace da Duty ranar. Sai na zauna ni ka’dai na bu’de kur’ani na soma tilawa. Don dokar Tahfiz ce duk wanda ya fara zuwa shi yake fara karatu a lokacin….


K’amshin turarensa da sallamarsa ne ya saka ni yanke karatun cikin fa’duwar gaba. Na kuma kasa bu’de baki na amsa sallamar…


Tsaye ya yi yana kallona bai shigo ajin ba, ga shi nik’ab d’ina a d’age yake. Na saka hannu zan ja nik’ab d’in k’asa ya furta “Ba kya amsa sallama ne Malama…” Wallahi jin muryarsa ka’dai sai da ya razanar da zuciyata. Muryata na rawa na ce “Alaykassalam…” Murmushi ya d’an saki ya isa wajen zamansa. Sai da ya zauna ya furta “Ina sauran y’an ajin? Ni fa bana son makara, don haka dole a kiyaye…” shiru na masa don bani da nutuswar da zan iya cigaba da amsa masa. “Cigaba da karatunki…” Ji na yi kamar na zunduma ihu. Ta ina zan iya karatu wallahi ba zan iya karatu daga ni sai shi a yanayin da nake ciki ba… d’ago ido ya yi ya d’an kalleni ya sake furta “Cigaba na ce….” Ji na yi kamar na zunduma ihu. Allah ya taimake ni sai ga Asma ta ranga’da sallama cak ta tsaya ganin sabon Malamin. Gaisheshi ta yi ya amsa mata yana d’an tsuke fuska. “Kin makara ki juya…” Da sauri ta ce “Wallahi Malam ba makara na yi ba, na je duty ne ka tambayi AYSHA ma ka ji…” “AYSHA?” Muka ji ya fa’da, wanda yasa na yi saurin d’aga kai don a zatona kirana ya yi, sai naga kawai ya yi murmushi ya girgiza kai ya ce “Ku bu’de Manhajjul Muslim… A ina kuke?” Asma ce ta amsa ni kuwa sam hankalina baya wajen…

Tunda ya fara karatun bai ‘dago ya kallemu ba y’an aji kuma duk wacce tazo sai ya tsayar da ita ya ce ta makara… ga karatun da yake mana mai mugun saka kunya don karatu ne akan yarda ake wankan janaba da abinda yake sabbaba shi..

“Yanzu kun gane yarda ake wankan ko? Da kuma sabbabinsa?” Asma ce kawai ta ‘d’aga kai, ya juya yana d’an kallo na.. “AYSHA kin gane menene janaba, sababinta da kuma yarda ake wankanta?” Runtse idona na yi jikina har ya fara rawa musamman idanunsa duka ya zubesu a kaina. “Ba kya ji ne? D’auke wannan bak’in k’yallen ki min cikakken bayani….” “Ya ilahi na furta ina jin kamar na zunduma ihu ta ina zan fara wannan abin kunyar…. “Ke samo min ruwa a office mai sanyi, ke kuma ina jin ki?” Ina kallo Asma ta fice tana dariya k’asa-k’asa. Ji na yi kamar na ruga na gudu musamman da ya jawo kujerarsa daf da ni, ina sake shak’ar Mayen turarensa… “AYSHA” ya fa’da cikin wata irin husky voice “D’ago ki kalleni..” Da k’yar na d’ago sai dai na kasa kallon nasa. Kallona yake shi kuwa kamar ya samu Tv fuskarsa d’auke da murmushi ya furta “Answer my question before na ha’da duk makarantar nan ki musu lecture akan haka…. menene janaba? Hukuncin ta a musulunci da yarda ake wankanta?”



𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️



Albishirinku! Albishirinku!!


Yau ne fa! Yau ne litattafan Bright pens za su fara zuwa muku da izinin Ubangiji….


1.K’arfe a wuta. AYSHA cool marubuciyar k’anwar maza.


Hadarin gabas Nazeefa Sabo Nashe. marubuciyar Me Zan Yi da ita?


Mutallab daga harzik’ar marubuciya Nimcyluv


Zaytoon zai zo daga Alk’alamin Malamar Adabi Zee kumurya.


Za’a fara sakar muku K’arfe a wuta kafin zuwan sauran In sha Allah.

Don samunsa a sauk’ak’e ku yi joining wannan link d’in…



‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/FTFuiA4woYJCgNQrcBYGX4
[8/5, 1:21 PM] Nazeefah Nashe: NA GA RAYUWA♥︎♥︎♥︎


𝒩𝒶𝓏ℯℯ𝒻𝒶𝒽 𝒩𝒶𝓈𝒽ℯ★✍️

Free Book.. MIKIYA WRITERS ASSOCIATION

Page d’in kacokam naki ne k’anwata Nimcyluv hope na goge lefina Masoyiya 🤣


Arewabooks @nazeefah

Wattpad@Nazeefah381

08033748387.

★★★★★ 𝒫𝒶ℊℯ 6



‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/LSB89Dp71pHETB3hpaWohR


Ji na yi zuciyata ta cigaba da bugu, na kasa amsa masa tambayar ya bi kuma ya tsare ni da ido. Hannayena kawai nake matsawa don ban san me zan ce masa ba. “Ba ki ji ba? D’age wannan bak’in k’yallen don ban sani ba ko hararara kike..” K’iris ya rage na fashe da kuka saboda yanayin da ya saka ni, ga mayen turarensa ya bi ya hana ni sukuni… “ki d’aga na ce, Are you dumb?” Hannuna na rawa na saka na d’age nik’ab d’in. Na runtse idona saboda har ga Allah ba zan iya cigaba da kallonsa ba… ina ji ya sauke ajiyar zuciya yana furta “Kin yi passing wannan Oya tashi ki fita sallah…” Tun kafin ya kai k’arshe na mik’e da sauri ban san yarda aka yi na isa bakin k’ofa ba, ni dai na gan ni a waje. Na tsaya ina sauke numfashi hannuna dafe da k’irjina da take matsanancin bugu… Ina jin k’amshin turarensa alamar nan yake tahowa na zuba sauri har da ‘dan gudu don kada ya riskeni a wajen…


Yanayin tsarin karatun nasa ya saka y’an aji aka daina makara saboda ana son karatun nasa sosai. Na san wasu y’an matan da yawa ba don Allah suke zuwa da wuri ba. Ga shi su cab’o Uban kwalliya a fuska a baza k’amshin turare ana yi ana zuba iyayi duk don Ustaz ya yaba. Shi kuwa sam baya kulasu idan zai shigo ma bak’in glass yake sakawa ya rufe idonsa…


Wata rana da ta kasance ranar Talata ce. Sam kasa yarda na yi na je makarantar saboda da na duba maddar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login