Showing 36001 words to 39000 words out of 44853 words

Chapter 13 - NAGA_RAYUWA_BOOK_1

Unknown   

02 Dec 2025

107

furta “na godewa Ubangiji da ya mallaka min kamilar mace, da nake jin In sha Allah nine nan d’an mukullin wancan abin da ake killacewa, I love you Ayshatu na….ina son ki fiye da son da nake wa ruhina, I wish to spend the rest of my life with you…” ya fa’da yana d’an jan hancina. “Na kusa cire kunyar nan gaba d’aya. Just 2 weeks za’a saka, a haka ma ni ba haka na so ba na so a ce 1week after Graduation kawai, amma ya zan yi Mommy ta kafe basu gama shirye shirye ba.”

Gani na yi kawai ya ja gefen hanya ya yi parking. Ya kwantar da kujerar yana kallona da wasu lumsassun idanunsa. Tsigar jikina ce take tashi kawai. Iya zallar kallon Ustaz yana canja min yanayi inaga ranar da zan ganni da ga ni sai shi a matsayin ma’aurata. “Say something AYSHA, ko da yau ka’dai ne kice Ustaz I love you na ji sanyi a raina…” Lumshe idona na yi, Karon farko na ji yau ina son shayar da Ustaz mamaki. Murya a sark’afe cikin wani irin sauti na furta “I… Love…You Ustaz with All my heart Ustazu na.” Jina kawai na yi a jikinsa yana bani wasu zafafan kiss. A kunne ya ra’da min “Me kika tanadar min a ranar da zamu tare?” Na runtse idona. “Kada ki ji kunya My Eesh ba kunya tsakanin Miji da Mata say it…. Kin tanadar min duka kan ki…” na d’aga kai na na ji ya bani sumbata a forehead d’ina da tsinin hancina. Ya saki ajiyar zuciya a hankali ya mayar da seat d’in yarda ta ke ya ja muka tafi.



Sanda muka isa gida, na hau sama Mami na tarar tana cika tana batsewa a cikin parlornta, idanunta sun ka’da jajur tana kallona kafin ta zauna ta rik’e kan nata. Jikina a sanyaye na yi hanyar da zata kai ni d’akina, na ji muryar Mami a kaurare ta ce “AYSHA! Zo nan!” Cak na tsaya kafin na juya a hankali na isa inda ta ke. Na zauna a gefenta. Ta nuna min cards… “Ga cards d’in bikinki nan, burinki da na iyayenki ya cika, ina muku murna, ba zan b’oye miki ba AYSHA sam bana farin ciki da aurenki, zan kuma amince da aurenki ne idan kika amince da wasu shara’di da zan baki…. As from today zaki dawo kwana a d’akina ba kuma naso ki gayawa kowa, sannan ban amince ko gayawa kowa wannan shara’din nawa ba, sannan ki sanar da shi daga yau ba waya tsakaninku sai mesaage…….



𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️
[8/5, 1:21 PM] Nazeefah Nashe: NA GA RAYUWA 17.



https://chat.whatsapp.com/HfGu1Pozgx9IxjCYqW7ZCZ


NA GA RAYUWA♥︎♥︎♥︎


𝒩𝒶𝓏ℯℯ𝒻𝒶𝒽 𝒩𝒶𝓈𝒽ℯ★✍️

Free Book.. MIKIYA WRITERS ASSOCIATION




Arewabooks @nazeefah

https://chat.whatsapp.com/HfGu1Pozgx9IxjCYqW7ZCZ


Wattpad@Nazeefah381

08033748387.

★★★★★ 𝒫𝒶ℊℯ 17.




Jikina na rawa na kauce fuskata daga sumbatar da yake kai min. “Ustaz shine ka min k’arya?” Na fa’da ina janye jikina daga nasa na zauna a kan kujera. Zaman dirshan ya yi a gabana ya zuba hannunsa a kan cinyata yana kallona cikin wani yanayi ya furta “AYSHA k’arya kuma? K’aryar me?”
Magana yake cikin wata irin murya da na kasa tantance a wani mahalli zan sakata.
“Kace min Khadija matarka ce.” Na fa’da ina yin k’asa da idona don bana jin zan iya jure wannan kallon da yake min. Wani murmushi ya saki da har ina iya juyo sautinsa da numfashin da ya sakar min ya ratsa fuskata. Yana dariyar ya furta “D’ago ki kalleni…” na k’i d’agowar da ba zan jure ba. Hannuna ya kama ya matse cikin nasa. A hankali ya furta “Ranar da kika ce ba kya so na, kin fasa aurena hankalina tashe na taho gida. Ni da kaina na tabbatar ikon Allah ne kawai ya kawo ni gida, Saboda tashin hankalin da zuciyata take ciki.

Sanda na isa gida ko ciki ban shiga ba kamar yarda na saba. Na shiga part d’ina na zauna hankalina a tashe. Duk na ji duniyar bata min da’di. Ashe Mommy taga shigowata ta camera ta aiko Khadija taga ko lafiya ban shigo ba kamar yarda na saba. Yanayin da Habibteey ta ganni ne ya sata zubewa cikin tashin hankali a gabana tana kama hannuna ta furta “Subhanallah Ya Ahmad lafiya kuwa?” Na ‘dago idona da suka yi jajir na zube a kanta sai kawai na ga ta ru’de ta fara magana “Ya Ahmad ka yi magana me ya sameka?” Ajiyar zuciya na saki cikin wani irin rauni na sanar da ita dukkan damuwata. Madadin naga ta cigaba da damuwar sai naga ta tuntsire da dariya ta furta “Ya Ahmad wallahi AYSHA na sanka, kawai dai akwai wani dalili da yake nema ya mata Katanga da son naka zai kuma iya togaceku daga aure idan baka yi gaggawar sakawa a d’aura muku aure ba ina tabbatar maka nan gaba zaka rasa AYSHA…” shiru na yi ina murza goshina kafin na ce “Khadija ta yaya kike zaton Iyayenta zasu yarda su aurar da ita a S.S 2.” Ta sake murmushi ta ce “Ka je musu da buk’atar auren kawai banda tariya idan yaso idan ta gama secondary school sai ku tare…” Shiru na yi ina nazarin zuciyata duk gwiwata ta yi sanyi don na san mawuyacin abu ne Abbanki ya yarda da abinda zan je masa, ni kaina ina tunanin yarda zan yi aure na kuma zuba miki ido bayan auren a zuwan sai an tare na kusanceki ko ba so akwai sha’awa balle ke da nake so nake kuma mafarki kullum
Akan wancan gwadaben sai na ji abin da kamar wuya. Gefe guda kuma ina jin tsoron ko kin daina so na don ba zan iya auren matar da bata so na ba, don haka kai tsaye na ce da Khadija “Idan kuma bata so na fa?” Dariya ta yi sosai, dariyar da ta dinga saka min wani irin d’aci a zuciya, a zafafe na ce “Khadija wai meye haka? Ya nazo miki da matsalata zaki saka ni a gaba kina dariya?” Dariyar ta sake yi kafin ta ce Tabbas Ya Ahmad na yarda kai sabon shiga ne a fagen soyayya, duk mutumin da zai Soka da farko ya dawo ya k’i ka da k’arshe to ba k’in ka yake ba sai dai idan akwai wani dalilin da zai saka ya janye soyayyar… ka bincika kuma zaka ce na gaya maka. Kana so ka gane tana sonka ko bata son ka?” Da sauri na ‘d’aga kai, don shi na fi buk’ata. Ta gya’da kai ta furta “zan baka hotona, ka kaiwa AYSHA a zuwan ni ce matar da zaka aura, idan har kaga ta shiga tashin hankali to tabbas tana son ka, idan kuwa kaga bata damu ba to gaskiya sonka bai je ko ina ba a zuciyarta.” “Good idea!” Na furta cikin jin da’di.


Da k’yar na bari kashegari ta yi, kafin na kai kaina gidanku, sai dai me? Ina zuwa aka ce min kina gidan Yaya Muhammad. Wani farin ciki na ji. Na saka aka min kwatance sai gidan Muhammad. Sanda na baki hoton Khadija, lab’e wa na yi ba tafiya nayi ba, ina son naga reaction d’inki. Wani farin ciki ya mamaye ni ganin yarda kika nuna damuwa da hoton da kika gani. Ya Muhd shi ya sanar da ni komai da abinda ake ciki game da Maminki. Hakan shi ya bani k’warin gwiwar zuwa na tari Daddy na da zancen son zuwa a nema min aurenki. Da fari bai amince ba sai da na masa rantsuwar zan amince na barki ki yi karatu sannan ya yarda zai je nema min aurenki da shara’din idan Abbanki bai amince ba zan hak’ura. Na yarda da hakan.

Kashegari kuwa aka je nema min aurenki, abin mamaki take Abbanki ya ce ya amince banda ma yana tausayawa Maminki kada zafin ya mata yawa da yace na tare da matata kawai. Bokon me? Bokon Ai ba fa’dar Allah ba ce. Na ji da’din wannan labarin na tabbatar na auri y’ar babban gida irin matar da Manzon Allah ya kwa’daita mana mu aura. Muhd ne ya bani shawarar zai ‘d’auke ki ya kai ki gidansa har sai bayan an ‘d’aura auren don ya lura kamar damuwar da Mami take ciki ne yake neman tunzira zuciyarki. Ki bujirewa auren. Wannan shine abinda ya faru My Eeesh dafatan zaki yafe min?” Na lumshe idona kawai ina jin yarda yake murzar min hannuna a hankali. “Ana ahubbuki kaseer kaseer Eesh.” Murmushi kawai na saki ina janye hannuna na ce “Ustaz mu tafi gida kada dare ya yi.” Sumbata ya kaiwa hannun yana furta “wani gida kuma Aysha? Kina da gidan da ya wuce nan ne?” Idona na ne ya kawo ruwa na zare hannuna ina furta “Please Ustaz! Kada mu yi haka da kai mana..” Shiru ya yi yana sake matsar da hannuna saitin bakinsa idanunsa a lumshe yake sumbatar yatsun yana furta “Shshsh, idan kika cigaba da min magiya you will spend your night anan…” na waro ido. Jin abinda ya ce bai fasa kissing hannun nawa ba. Sai da ya gaji don kansa ya janye hannun yana sakin ajiyar zuciya ha’de da kallona da burkitattun idanunsa ya mik’e naga ya shiga wata k’ofa da na tabbatar toilet ne, bai wani jima ba naga ya fito da rigar wanka a jikinsa yana goge jikin. Da sauri na runtse idona na ji ya saki dariya mai k’aramin sauti ya furta “Idan baki wasa ba zaki shafa min mai….” Ai ban san sanda na isa bakin k’ofa ba, ina sakin haki na tsaya a bakin k’ofar da zata fitar da kai daga parlorn. Tsawon mintuna biyu sai ga shi ya fito sai zabga k’amshi yake fuskarsa very fresh. Ina ganinsa na yi saurin murza handle d’in k’ofar zan fita sai dai hakan bai samu ba don key ‘din na hannunsa ya k’araso daf da ni, kansa a saman wuya na ya rungumeni ta baya yana sakin ajiyar zuciya, a kunne ya ra’da min. “Kin saka ni wankan dole Ayshata…” wani irin runtse ido na yi na furta “Please Ustazu Ka Bari am too young fa..” naga ya d’an yi murmushi kawai ya kaiwa bakina sumbata ya furta “Mu je kafin Maminki ta k’arar da charging wayarki ta miki missed calls ya fi hamsin…” waro ido na yi ina kallon wayar da Ustaz yake mik’o min, a raina na furta shikkenan na ka’de yau har ganyena….

Da zan tafi Mommynsa da Aunty’s d’insa suka ha’da ni sha tara ta arziki. Tabbas a idanunsu na hango sun yi na’am da ni.

Sanda muka isa k’ofar gida, da sauri na kai hannu zan bu’de k’ofar sai na ji ta a kulle gam. Na juyo ina kallon Ustaz na ce ya haka?” D’an lumshe ido ya yi yana turo min lab’bansa “I need kiss AYSHA in dai kina son ki fita, ina son ki min abinda zan dinga tunawa da shi da zarar na rufe ido da niyyar barci…” “Allah Ustaz ba zan iya ba…” Ji na yi kawai ya yi baya da seat ‘d’insa ya janyo ni da k’arfi na zube jikinsa a hankali ya fara bani wani irin passionate Kiss. Mun d’au tsawon mintuna biyar a haka kafin ya sake ni. Ya danna lock motar ta bu’de “Sweet dream Ayshata, ki yi mafarki na pls…. I mean romantic mafarki…” Da sauri na fice daga motar. Don kamar lamarin Ustaz yana neman girman kwanyata.


Sa’daf Sad’af na shige bedroom ‘dina. Don bana son na yi k’wak’wkwaran motsin da Mami zata ji ni. Ina shiga d’akin kuwa kayan jikina na cire da duk suke k’amshin turaren Ustazu, idan ba hanci na bane ya ji ba daidai ba, sai na ji kamar jikina ma k’amshinsa yake. Da sauri na fa’da toilet don a jikina nake jin ya wajaba na yi wanka.


Ina wankan na dinga jin ana buga k’ofar toilet d’in da k’arfi gabana na wani irin fa’duwa na fito. Ina fitowa kuwa idanuna suka sark’e da na Mami da yake wurga min wani irin kallo mai nuni da zallar jin haushi. Idanunta a burkice banda bata shaye shaye sai na ce ma a buge take… cikin rawar murya na furta “Sannu…sannu Mami, ke ce?” Ta sake wurga min kallon tana mik’ewa ta iso daf da ni. Kallon sama da k’asa take min kafin ta saka hannunta cikin sumar gashi na ta furta “Wanka AYSHA? Wankan me kika yi na ji gashinki a jik’e don’t tell me kin mik’awa wancan wawan kan ki?”





★✍️ 𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢
[8/5, 1:21 PM] Nazeefah Nashe: NA GA RAYUWA♥︎♥︎♥︎ 19.


𝒩𝒶𝓏ℯℯ𝒻𝒶𝒽 𝒩𝒶𝓈𝒽ℯ★✍️

Free Book.. MIKIYA WRITERS ASSOCIATION




Arewabooks @nazeefah

https://chat.whatsapp.com/HfGu1Pozgx9IxjCYqW7ZCZ


Wattpad@Nazeefah381

08033748387.

★★★★★ 𝒫𝒶ℊℯ 19.



19.



Wani iri na ji kaina ya yi, na kasa d’aga ko ido na kalli Mami jin yarda nake jin wani irin d’aci a mak’ogwaro na, na tabbatar b’acin rai ne ya haddasa min haka. Bata jira jin abinda zan ce naga ta mik’e ta shige bedroom d’inta hakan ya tabbatar min bata buk’atar yarda ta ko rashin yarda, umarni ne kai tsaye ta bani da take tunanin tilas ne na bi shi. Hawaye naji suna zubo min masu d’imin gaske wanda suke narkar da duk wata damuwata da take k’asan zuciyata. Jikina a salub’e na shige d’aki, Ina ji lokaci ya yi da ya kamata na nunawa Mami nima y’ar Zamani ce, zan iya jurar komai banda rashin waya da Ustaz, ya Riga ya saba narkar da zuciyata da kalamai masu narkar da zuciya. Furucinta kam tamkar d’igar dalma ne cikin zuciyata gwara ta min komai banda hana ni jin muryar ustaz wallahi.


Bayan Isha, still Ustaz yazo gidan mu. Kamar yarda ya saba wannan karan ma da shi aka ci abincin dare. Ya kalleni bayan ya mik’e bai ji kunyar Abba ba balle su Mami ya furta “AYSHA, zo mota ki amshi sak’o.” Ta gefen ido nake kallon Mami da take zuba masa banzan kallo. Na mik’e jikina a salub’e na bi bayansa. Har ya shiga cikin mota. Hakan yasa na masa knocking glass. Bu’de motar ya yi ya furta “Shigo mu fara tsara yarda shirin bikin zai kasance, bana son hira a saman Mami, I can’t feel comfortable…” Na shiga Motar jikina a sanyaye. Ya janyo paper da biro ya mik’o min. “Lissafo min abinda duk kike so a yi a bikin, da duk abinda za’a kashe.” Ya furta yana kallona. Kafin ya d’an tab’e baki ya ce “Why are you so quiet yau ne? Ko har kin fara tunanin aure ne?” Lumshe idona na yi ina girgiza kai. Na furta “Bakomai fa, kawai stress d’in exams ne yake tambaya ta.” Ya girgiza kai yana jan hab’ata ya furta “Oh I see, am so sorry dana sani ban zo yau ba. Jeki gida zan shigo gobe ko jibi, ina hoping by that time kin wartsake stress mu samu mu shirya bikin sosai, duk da bana son event da za’a ha’da maza da mata please ko hoto mace nake so.” Na d’aga kai. Ya ja hannuna ya yi kissing kafin ya mik’a min ledar hannunsa. Mai kyan gaske tun kafin na bu’de na san turare ne a ciki saboda wani k’amshi na fitar hankali da naji yana fita a ciki. “Sweet dream…” Ya furta a hankali cikin
Wata husky voice mai dashewa. Na amsa ta hanyar d’aga kai. Na fita daga mota.



Sanda na shiga gida duk sun watse daga tsakargida, na hau saman Mami bayan na lek’a na yiwa Umma sallama. Mamin bata parlor na shiga d’akina.


Kyaututtukan da na samu na dinga bu’dewa ina binsu da kallo. Sai daga k’arshe na bu’de ledar Ustaz wani rantsatstsen turarena da charbi da sallaya da aka saka sunana a jiki da haruffan larabci “Zaujaty Ayshatu…” Murmushi na yi ina rungume d’an zoben gold d’in a k’irjina bayan na fesa turaren mai k’amshin na Ustaz sak sai dai shi wannan na mata ne k’amshin bai kai na Ustaz k’arfi ba. Lumshe idona na yi. Sai jin tafi na yi a kai na. Da sauri na ware idona ganin Mami a tsaye idonta a kaina. Ta furta “Weldone Aysha, kin kuma burge ni.” A daburce na furta “Mami me na yi?”


Ta tako zuwa inda nake, ta saka k’afarta d’aya ta tokare a saman gado tana kallona ta furta “Me kuwa kika yi AYSHA? Ba abinda kika yi illa kina so ki nuna min ke ma kin girma. Ahmad ya fara shayar da ke da’di da zumar da ke cikin aure, tunda ga shi har kin san ki rungume kyautar sa a jikinsa, alamu ya nuna kin fara sanin soyayya kin kuna san menene sha’awa, tabbas lokaci ya zo…” Ta fa’da tana lasar leb’enta “Uban me kika tuno da yasa ki lumshe ido da murmushi? Kin hango yarda yake rungumeki ko? Ke a tunaninki wai na amince da aurenki ne? Ko ka’dan har yanzu zuciyata bata so ina kuma adawa da haka. Na k’i jinin tarayyarki da wannan mutumin da yazo ya wargaza min duk wani tanadi na a kan ki….


Sak na yi ina jin furucin Mamin kamar d’igar dalma a cikin k’irjina. Ji nake kamar ana soya zuciyata saboda tsananin hucin da nake ji a k’asan raina.


“Mik’o min turaren.” Ta yi furucin cikin b’acin rai. Na saka hannu na mik’a mata turaren. Ta fice da shi tana furta “Kin bar amfani da duk wani abu da zai baki, musamman turare waya sani ma ko asiri ya miki a cikinsa. Shegen mutum mai azababben naci..” Ta gama zaginsa ta fice daga d’akin sai sannan naji wani kuka mai tafe da takaici ya zo min, ba shiri na saka kukan kuwa sosai. Raina ya b’aci sosai don haka bayan na yi wanka na shirya nan je ‘dakin nata ba kamar yarda ta min umarni na yi zama na a ‘d’aki.


Wajen sha biyun dare ta shigo d’akin cikin shigar wasu silk kayan barci sai baza k’amshin gabbasa take. Ina kwancen ta zauna a gefen gadon. Da sauri na lumshe idona don ko ganin Mamin naji bana son yi. Sunkuyo da kanta ta yi saman fuskata ta bani kyakykyawan kiss a gefen kumatu. A kunne ta ra’da min “Tashi Babyn Mameey, don’t tell me fushi kike da ni, na san dai idonki biyu.” K’in motsa wa na yi. “Ba zaki tashi ba?” Ta sake

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login