Showing 33001 words to 36000 words out of 44853 words

Chapter 12 - NAGA_RAYUWA_BOOK_1

Unknown   

02 Dec 2025

102

na d’an turo bakina ina furta “Ba ga shi can har ta wuce ba, so take ta nuna min lallai ta fi ni iko da gidan ku.” Yatsa ya saka yana zagaye lab’b’ana. “Wato ashe bakin nan ya iya tsiwa? Amma da kike kasa sak’at idan kin ganni a wuri. Mu je na raka ki kin ji tunda ita ta nuna mana gidansu ne ta tafi ta barki.” Ya fita ya zaga ya bu’de min mota. Zai rik’e min hannuna na janye ina d’an duban hanya na furta “Ka bari mana, kada wani ya gan mu?” “And so what? Idan an gan mu Ai ba haramci muka aikata ba ko?” Ya fa’da yana tsotsar bakina ka’dan. Na lura lips d’ina suna burgeshi. “Ke halak d’ina ce Aysha, a yanzu ba wani shamaki tsakaninmu da ke, sai wancan karatun da Maminki ta kafe sai kin yi,
Wallahi ba ruwana duk ranar da ta wayi gari ta ganki da ciki….” Da sauri na waro ido jin abinda ya fa’da. Ya lumshe ido yana d’aga kai ya ce “Am serious Eesh baki san yarda nake ji akan ki ba…” ya fa’da yana jan hannuna.

Da sauri na janye hannun nawa ganin yarda mutane suka fara fitowa daga k’ofofi daban daban an ware ki’dan larabawa suka zagaye mu da Ustaz. Sai fa’dar Marhababuki lale suke. Kana ganinsu kaga jinsin larabawa don farare ne k’al da su. Ustaz d’an murmushi ya saki ya yi saurin zamewa ya bar ni da su. Matar mai kama da Ustaz kwabo da kwabo ita ta k’araso inda nake ta kama hannuna tana ha’dani da jikinsa tana fa’din “Marhababuki Ibnateey…” Wani irin sahihin k’amshi ne kawai yake fita ko ta ina a gidan. Suka ja hannuna zuwa cikin gidan. Kaina a k’asa k’irjina sai bugu yake, amma matar bata cika hannuna ba. Sai da muka isa cikin babban parlorn gidan. Tabbas gidan su Ustaz ba k’arya ya ha’du kana ganinsa ka san sun ci sun tada kai da naira, babu gami sam tsakaninsa da namu gidan. A kan kujera ta zaunar da ni, amma sai na zame na zauna a k’asa. Ina gaishesu a kunyace.

Kishiya ta ce tazo kusa da ni ta zauna. Tana kama hannuna na ji kamar ta zubar garwashin wuta a hannun, da sauri na janye sai na ji ta yi dariya ta furta “Am not his wife, he was just joking… ni k’anwarsa ce the only Sis da yake da ita….” Innalillahi na furta a hankali kunyar rashin mutuncin da na mata nake ji, dana sani ya shige ni sosai. Ta yi dariya sosai ta fara bawa mutanen parlorn labarin acting d’in da nake idan ta ce musu ni matar Ahmad ce. A raina na ji ba zan k’yale Ustaz ba sai na rama, wannan ai ba wasa ba ne. Dariya sosai mutanen parlorn suka fara. Mommy ce ta ce “Ahmad ba zai miki kishiya ba, ke ka’dai kin ishesa In sha Allah, Son da Ahmad yake miki ba a kwatancensa Allah ya baku zaman lafiya da zuri’a d’ayyiba.” Ta juya tana kallon k’ofa. Ta furta “Ibnateey maza kirawo min shi, a yi addu’a kafin a fara cin abinci..” Da sauri kuwa naga Habibteey ta mik’e ta nufi inda zata kira shi.


Sai ga shi ya fito cikin wata jallabiya brown color yana shigowa da ni ya fara ha’da ido. Na d’an turo bakina ina masa hararar gefen ido, kafin na sake jan mayafi na rufe fuskata. “Ahmad kazo ka ciyar da matarka kamar yarda al’adarmu take at first day of marriage.” Wata mai kama da Mommyn ta fa’da tana sake janyo Ahmad zuwa inda nake. Zuciyata kawai bugu take ina tunanin ta yaya zai ciyar da ni? Daf da ni ta zaunar da shi har jikina yana ha’duwa da nasa. Ta kawo masa kayan abincin gabansa. Da kansa ya yi serving d’inmu. Kafin ya ‘dago yana kallon auntyn nasa, ta ‘d’aga masa kai “Oya ka fara mana, ina jira zan yi pic..” Hannunsa ya saka ya ‘d’aga mayafi na. Da sauri na runtse ido, ganin ya kai dabino guda baki na. A hankali ya furta bu’de bakin…” “Amma ka san ba haka muke ba ko?” Anty ta fa’da ranta a b’ace. Ina kallo ya d’an yi dariya, sai kuma ya mayar da dabinon bakinsa ya gutsira ka’dan ya tauna ban yi auneba na ji bakinsa cikin nawa yana zuba min taunannen dabinon. Jikina ne ya fara rawa da sauri na rik’e numfashina da yake son d’aukewa ganin still YUstaz bai cire bakinsa a cikin nawa ba sai juya harshensa yake cikin wani salo da lumsassun ido, sai da ya tabbatar na ha’diye sannan ya janye yana ‘dan murmushi. Ihu da Kabbara suke kawai a gidan. Aka dinga mana hotuna ni kuwa duk kunya ta saka jin jikina wani iri na sunkuyar da kaina kawai na kasa ha’da ido da kowa. Anty ce ta ce Khadija ta tafi da ni d’akinta sai a kai min abincin can tunda na kasa sakewa da su, su al’ada garinsu ce haka, ba abin kunya ba ce, rana ce mai mahimmanci a wajensu da ake wa saurayin da bai tab’a aure ba, don a ga yanayin da zai shiga a yi dariya idan an ga abinda zai yi a first deep kiss ‘d’insa. Ni dai tuni na bi bayan Khadija jikina na rawa muka isa ‘d’akinta.


Muna shiga ta janye mayafin fuskata tana dariya. “Bud’e fuskar Anty AYSHA na ganki da kyau, tunda dai nan daga ni sai ke..” Knocking muka ji. Khadeeja ta furta “Yes come in..” k’aninsu ne ya shigo yana d’an hararar Khadija ya furta “Mhmmn, I know kina nan kin saka ta a gaba da surutu kamar parrot…” ta wani waro ido tana furta “Ridwan am I play with you? Ni kake kira parrot iya get out from here…” Ya turo bakinsa ka’dan yana furta “Aiken Mommy ne, ta ce ki rakata part d’in Yaya Ahmad su ci abinci da shi tare…” Na wani irin waro ido, kamar na yi kuka nake kallon Khadija na ce “Ki gaya mata na k’oshi don Allah…” Khadija ta waro ido tana furta “Ban kai nan ba, idan ba so kike Ya Ahmad da Anty Danger su gididdiba ni ba..” tana jan hannuna amma na kasa ta shi. Sai kawai ta fita sai gata ta dawo da wacce na tabbatar ita suke cewa Anty Danger na ji ta ce “Anty Tasleem to gata nan, ki gaya mata da kan ki.” Murmushi ta saki tana jan hannuna ta furta “Ta so Inlaw, yau ranace mai muhimmanci ga duk mai son Ahmad, shima kuma yau rana ce da zai so ku kasance tare tunda dai ba yanzu za’a kai ki gidan sa ba. Muje ku ci abinci ku yi hira sosai.” A kunyace na mik’e na bi bayanta hannuna cikin nata, muka ratsa ta wata k’ofa, Khadija na bin mu a baya, sai da muka wuce wani fili mai kyau kafin mu dangana da wani d’an gini mai kyau duk da bai cika girma ba. Anty Danger ta saka hannu a k’ofar ta yi nocking sai ga shi kuwa ya bu’de ina ji Anty Danger ta furta “aka tabbatar ta ci ta k’oshi ka kuma bata gift mai tsadar gaske wanda ba zata manta ba, na san ka san me nake nufi ko?” Hannuna na ji cikin nasa kafin ya kalli Khadija ya furta “Ke bar nan..” Da sauri kuwa ta juya tana dariya ta furta “Su Ya.Ahmad da mata Ai sai Allah. Anty Danger ma ta juya ya ja hannuna zuwa cikin k’aramin parlorn mai masifar kyau na zata anan zamu tsaya sai naga ya shiga da ni wata k’ofa da ta kai mu ainahin wani babban bedroom d’insa… muna shiga naga ya jani jikinsa ya rungume sosai cikin wani irin sautin murya ya ra’da min “Bari na fara baki gift d’in da surikarki ta rok’a na baki…” k’ok’arin zame jikina nake Amma ina ji na yi kawai yana zame d’ankwalin kayana ya cusa hannunsa cikin gashin kaina a kunnena na ji yana furta “Alhamdulillah Eesh komanki is beautiful ina fatan cikinki yafi wajenki kyau….” Jikina rawa kawai yake shi kuma bai daina shinshina k’asan wuya na ba.. “AYSHA ina son ki sosai ke ce rayuwata ki amince min yau d’aya kawai….”


𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★✍️[8/5, 1:21 PM] Nazeefah Nashe: https://chat.whatsapp.com/HfGu1Pozgx9IxjCYqW7ZCZ


NA GA RAYUWA♥︎♥︎♥︎ 18.




𝒩𝒶𝓏ℯℯ𝒻𝒶𝒽 𝒩𝒶𝓈𝒽ℯ★✍️

Free Book.. MIKIYA WRITERS ASSOCIATION




Arewabooks @nazeefah

https://chat.whatsapp.com/HfGu1Pozgx9IxjCYqW7ZCZ


Wattpad@Nazeefah381

08033748387.

★★★★★ 𝒫𝒶ℊℯ 18.



‎Da sauri na kalleta kafin na girgiza kai na. Wasu hawaye na shirin zubo min, wanda bana komai ba ne sai na jin haushin tsanar da Mami na ta yiwa Ustaz, alhali shi yana sonta yana daraja ta, don kai tsaye zan iya cewa Ustaz kallon Uwa yake wa Mami. “Zaki amsa min, ko sai kin gama k’are min kallo? Na ce kin mik’a masa kanki ne?” Girgiza kaina na yi jin abinda Mamin ta ce. Sai naga ta saki wata ajiyar zuciya da har ta bayyana ta saman k’irjinta. Tana kallona ta furta “To wankan me kika yi? Ko da yake…” sai naga ta ‘dan cije leb’enta tana furta “Mhmn, ina ya kai ki bayan gidansu? Don naga da’dewar da kika yi ta yi yawa, kin saka na kasa barci fargaba ta d’aya kada ya mayar da ke cikakkiyar mace…•” K’asa na yi da kaina kurum. Na ce “Gidansu kawai ya kai ni, kuma na da’de ne saboda duk y’an uwansa suna gidan sun ‘dan ha’da Walima, wai su haka al’adarsu take, ranar da aka d’aura aure dole a yi Walima ta nuna godiya ga Allah…” Ta ‘dan tab’e baki. “Bayan walimar sai kuka zauna hira da mahaifiyarsa? A matsayinki na maras kunya ko?” Da sauri na girgiza kai na ce “Wallahi a’a Mameey, kawai dai ina zaune da sisters d’insa suna jana da hira…” na nuna mata kayan da suke kan gado na ce “Su suka bani.” Ko kallon kayan bata yi ba, ta fice da sauri daga ‘dakin tana furta “Ina ruwana da wasu kayansu, tunda dai bai kusanceki ba Ai shikkenan, ki gaya masa kuma fita an yi ta farko an yi k’arshe ba zai ya bu’dar miki da ido ba, ya zuba miki karatun da sam bana son ki fahimceshi a yanzu…” daga haka ta ja k’ofar da k’arfi ta bar ni da bu’dadden baki ina kallonta. Na saki ajiyar zuciya kafin na zura kayan sallah ta na tada sallahr isha’i da ban yi ba. Bayan na gama tunanin irin rigimar Mami, tabbas idan ka fahimci halinta tana da da’din zama amma kafin ka fuskanceta zaka saka ta a b’angaren mutane masu bau’dadden ra’ayi.

Sanda na kwanta kuwa kiran wayar Ustaz ne ya isheni, kunyarsa da nake ji na abubuwan da suka wakana a tsakaninmu ne ya hana ni d’aga wayar, sai da ya yi kira ya kai biyar sannan na saka wayar a kunnena. Wata ajiyar zuciya ya saki. Yana furta “Na kasa barci Eeesh, kina ta yi min gizo duka surar jikinki ta baibaye tunani na, da na san haka ne da ban fara janyowa kaina ba….wani feeling nake ji mai zafin gaske AYSHA, na kasa controlling kaina na samu barci… please ki amince min even once… na kusanci halak d’ina..” K’it na kashe wayar ina mayar da numfashi. Lamarin Ystaz yana neman ya girmi kaina. Kiran duniya ban amsa ba. K’arshe ya turo min msg. “Shikkenan tunda ba zaki amsa ba, I really missed your cutable lips…. And…boo….” Sai ya yi alamar murmushi bai k’arasa ba. Wani irin waro ido na yi a fili na furta “Na shiga uku me yasa Ustaz sam bai da kunya, amma idan ka ganshi a fili ba zaka zaci zai aikata haka ba. A lumshe idona yake Amma duk wasu feeling ina jinsa nima kamar Ustaz d’in kawai daurewa nake don ban san ya zan yi ba idan ba dauriyar ba, na san ko giyar waje na sha ba zan amincewa buk’atar Ustaz ba, idan ba so nake Mami ta yi yaga yaga da nama na ba.


Da safe sanda na isa makaranta ashe labari tuni ya baza makarantar kunya ta dinga isata jin ana ta min Allah ya sanya alheri. A islamiyya ma kasa katab’us na yi duk da dai da nik’ab a fuskata.


Tunda aka d’aura aure sai gidanmu ya zama nasu Ustaz, don in dai yana gari baya jure rashin iya zuwa. Mami kuma ta kasa ta tsare don k’iri k’iri wani lokaci da ya tambayeta zan raka shi unguwa ta ce “Ahmad, ka saurareni da kyau ba zan amince ka dinga fita da AYSHA bata tare ba.” Ya ‘dan ware ido yana kallonta ita kuwa ba abinda ya dameta ta mik’e ta shige bedroom d’inta. Ustaz ya ‘dan dubeni yana sakin ajiyar zuciya. Na mik’a masa lemon da na ha’da masa, don anan saman Mamin muke zance da kanta Kuma ta buk’aci hakan. Ranar da yazo bayan d’aurin aure da kwana biyu zan fita sitroom ta ce “AYSHA hau da shi sama na, ai ya zama d’an gida, bai kyautu a dinga barinsa a parlorn waje ba, sai kace wanda yazo zance.” Gaba ‘d’aya wajen ba wanda bai d’ago ya kalleta ba, hatta Abba sai da zancen ya bashi mamaki. Ita kuwa ta maze tana murmushi ta ce “Da ne nake adawa da auren AYSHA, banda yanzu da k’addara ta Riga ta tabbatar da hakan. Allah ya sanya musu albarka a auren.” Abba murmushinsa ya kasa b’oyuwa kamar yarda bakin Umma ya kasa rufuwa.

Shikkenan tun daga ranar Ustaz ya samu sake, mafi yawan lokuta ma tare ake zama a ci abincin dare da shi. Ya d’auki iyayena kamar nasa kamar yarda nima kullum muke gaisawa da Mommynsa a waya idan har na sha’afa ban kira ba, da kanta take kira na. Khadija kuwa ta zama uwa k’awata tsabar shak’uwar da muka yi, duk da ta girme min.

Gefe guda al’amarin Mami na bani mamaki a zahiri a gaban kowa ta hak’ura amma a ba’dini ni ka’dai na san yarda muke zaune da ita, musamman duk ranar da Ustaz zai zo ta dinga ha’de rai kenan tana min masifa komai na yi kuma laifi yake zama a wajenta. Ban gayawa kowa ba, don bana son kowa ya sani balle a ji haushinta. Mafi yawan lokuta idan Umma ta fara mata zancen da ya rage na watannin tariyata tsam take mik’ewa ta bar wajen.

Wannan abu yana tab’a min ruhina har na ji sam ban ji da’din abinda take yi d’in ba. In dai batun karatu ne, da bakin Ustaz ya mata alk’awarin sai nayi karatu a gidansa har sai nace ya isheni, tunda shima ta wani fannin d’an boko ne da ake damawa da shi a bokon.


June-july, shine watannin da muke saka ran zamu gama makaranta. Kwanci tashi sai ga shi lokacin har yazo. Ina ji ko mu da zamu zana jarrabawar bamu kai Ustaz lissafa kwanakin ranar graduation d’in mu ba. Wata rana muna waya. Ya ce “AYSHA, na k’agu ki gama wannan makarantar na sauke buk’atar da ta min cunkoso a jikina….” Waro ido na yi kafin na furta “Wace buk’ata kuma?” Sai da busar da iskar da take bakinsa, har na ji sautin ta ta cikin waya sai na ji ya ce “Kashe mu yi vedio call, zan gaya miki buk’atar…” “Ni dai A’a, na yafe.” Na fa’da a shagwab’e. Ya saki murmushi kafin ya furta “Ashe kin san buk’atar tunda kina jin kunyar na gaya miki, bari na miki ta Malam bahaushe, wallahi AYSHA na gaji, gangar jikina tana buk’atar maha’dinta, ina son jin d’umin Aysha zahirinta ba tare da shamakin tufafi ba…” da sauri na kashe wayar ina mayar da ajiyar zuciya. Ni da kaina na san Ustaz ya yi hak’uri gashi yanzu ko rungumar baya samu ya yi min Mami ta kasa ta tsare, sau tari sai muna zance sai ta shigo parlorn da niyyar d’aukar wani abin. Wani lokacin Ustaz kasa sakin jiki yake yi. Shi yasa yace min sau da yawa shi yasa baya zaman Nigeria yake tafiyarsa wata k’asar ya kwana biyu.



Burina kawai na fito da A1 a duka subject d’in da nake, don haka na dage da karatu Ka’in da na’in. Ustaz ma a wannan lokacin ya mugun d’aga min k’afa sai dai ya kira ni a waya. Har rama na yi saboda bani da isashshen lokacin kaina ko waya a gaggauce nake amsa masa, sau tari sai ya nuna fushin sa sannan nake bashi lokaci na.


Ranar da muka gama makaranta, rana ce mai matuk’ar mahimmanci a wajena. Duk da Ustaz ya hana ni ko saka kwalli a ranar, hakan bai hana ni zuba wani Uban kyau ba na kwatance. Wata doguwar Riga mai masifar kyau na saka wacce Mommyn Ustaz ta kawo min. Da takalmi half cover wanda zai matching da adon rigar golden brown. Na yi rolling kaina. Sanda Ustaz yazo zamu tafi hararata ya dinga yi yana tsaki k’asa k’asa. Muna isa wajen ya kulle motar yana zuban narkakkun idanunsa. Kafin ya kaiwa bakina sumbata ya furta “Me yasa? Me yasa ko baki kwalliya ba sai kin yi attracting idon mutane..” Murmushi kawai na masa. Sai naga ya bu’de dashboard ya ciro nik’ab Sabo fil a leda da kansa ya saka min nik’ab d’in yana furta “fuskar Matata haramun ce ga dandazon maza.”


Ustaz ya kasa ya tsare ta dole ya nunawa mutane ni matarsa ce, don bai ji kunyar ko su Abba ba sanda za a bani kyauta ya rik’e hannuna muka hau kan step. Shi ya karb’i kyautar da Mataimakin governor ya bani sab’anin sauran matan da suka dinga amsa da kansu. Tafi aka dinga yi da wani irin ihu.


Da aka tashi bai barni na yi hotuna ba, ya saka ni a mota yana furta “Is enough kuma, idan ba so ake Ustaz zuciyarsa ta yi bombing ba..” ya tada Motar yana jan hannuna da yake saman cinyata yana murzawa a hankali ya furta “Saura 2 weeks na mallaki komai da komai na jikinki Ayshatu na, har nan ko?” Inda hannunsa ya sauka ne ya saka ni ware ido ina runtse su da sauri da k’arfi. Sai naga ya daki sitiyari yana murmushi ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login