Showing 33001 words to 36000 words out of 72723 words
ba" murmushi tayi tace “da kinsani kin barta Ya Hajja nifa banga abinda zai zama fitina ba" murmushi Ya Hajja tayi tace bazaki gane ba Rafi'ah tashi kici abinci baason maijego da yunwa"
Irin kulawar da take samu a Maiduguri abin ya bala'in tsumata da tsaya mata a rai ta fahimci ashe mijin nata ɗan gatan danginsa ne satinta uku a Maiduguri yazo ganinsu dake kullum suna waya dashi ya cika da kewa da kulafucinta tunda ya kyalla idanu yaga yanda take ƙyalli sai wani glowing takeyi har wata ƙiba tayi ta kwanciyar hankali batada wata damuwa saidai taci ta kwanta.
Da dare tana kwance bacci ya fara daukarta taji an buɗe ƙofa ta buɗe idanunta duk da cewa bata ganin kowa ƙamshin turaren ya bayyana mata waye ta kuwa yi saurin gyara kwanciya tayi kamar bacci takeyi a cikin hakan gabanta na faɗuwar tsoro da firgicin abinda ya kawosa.
Ji tayi ya kwanta a bayanta tayi firgigit kamar zata tashi ya sanya hannu ya saƙalo cikinta yakai hannu yana shafa ɗinkinta yana busa mata iskar numfashinsa yace “Daƙyar uwar ɗakinki ta barni na shigo Noor hope na sameku your are fine?" Numfashi ta sauke tace “Abnoor babu announcing" kissing wuyanta yayi yace “Banida hayyacin yin announced ne Noor help me Please..." Yanda yayi maganar Saida taji wasu massun bala'i sun saukar mata tace “Akan me?" Ƙasa yayi sosai da muryarsa yace “wlh zan iya samun matsala yau idan banyi sex ba haƙuri na ya ƙare ke nake mugun feeling don Allah kar ki cemin a'a nasan yanzu ai kinji sauki 4 weeks Hisham har ya fara gane mutane"
A mugun sanyaye ta dago ta dubeshi duk da bata ganinsa sosai tasan yasan kallonsa takeyi yace “Yi magana mana" cikin kasala tace “Idan na rantse maka zaka yarda?" Shiru yayi tare da lumshe idanunta tace “Wlh tallahi billahillazi la'ilaha illahuwa AbNoor jinin haihuwa har yanzu bai daukemin ba" sakinta yayi yace “Ok na fahimta Noor na gane abinda kike nufi wato barin aikina da nayi na taho don in samu nutsuwa daga halali duk na banza nayi kike nufi ko? Shikenan kije na barki da haƙƙina" yana shirin ficewa tayi kukan kura ta rikoshi tace “Meyesa kakeson ka rinƙa barina da Allah ne AbNoor meye yasa kakemin irin wannan sabon ne kanason tsikar da zuciyata ne...." Angajeta yayi cikin fusata yace “Wlh idan kika kuma yimin magana saina ci mutumcinki..." Ta fusata sosai ta kuwa miƙe tace “Kai kullum bakayimin uzuri kullum baka neman haƙƙinka a wajena sai lokacin da kasan bazaka samu ba meye laifina ne gareka kawai don kaga inason ka...."
Rintse idanunta tayi saboda saukar hannunsa da taji a fuskarta ta dafe gurin da mugun mamaki ta ɗago tace “Saboda nace inasonka ka mareni?" Zare belt ɗinsa yayi yayo kanta ta rintse idanunta cikin mugun mamaki da jiran jin abinda yake shirin aikatawa bata gama Saita mamakinta ba taji belt ɗin ta naɗeta sosai taji shigar dukan ta sake rintse idanunta tare da dafe cikinta daidai aikinta ta buɗe idanunta da suka kaɗa sukayi jawur hawaye ya tsiyayo daga cikin ƙwayar idanunta ya kuma ɗaga belt ɗin zai zabga mata Ya Hajja dake shigowa ta riƙe belt ɗin ta zuba masa mari tare da angajeshi ya dafe wajen ya cije lips.
Buɗe baki yayi yace “Ya Hajja akan Rafi'ah kika mareni?" Nuna masa hanya tayi tace “Fita Abdulƙadir....." Sake gyara tsaiwarsa yayi yana ƙanƙantar da idanu ya motsa bakinsa yace “Zan koya miki hankali tunda nake da mahaifiyata bata taɓa cire yarda akaina ba sai a kanki tunda nake da ita bata taɓa tuhumata ba sai a kanki bazan iya tuna ranar da Hannun Ya Hajja ya sauka a jikina ba sai a kanki Rafi'ah akanki komai a kanki Ni meyesa kowa ya daina yarda dani akanki ɓatani kikeyi a wajensu ko wani abu nakeyi miki da suke gani wanda Ni bansanshi ba? Meye na rageki dashi dani kowa baya fahimtata akanki Abba ya kirani yana tambayata abinda yasa kika rame Daddynki ya kirani yacemin idan da wani abu da kike buƙata na sanar dashi kamar akwai abinda yake damunki sannan kullum Ya Hajja Gana Hajja cikin tuhumata suke akanki hatta Abdallah kullum hannunka me sanda Yakemin akanki waini meye nakeyi miki ne meyesa ba'a duba ke abinda kikemin yaushe rabonki da ki bani haƙƙina da kwanciyar hankali? Ok ni ba mutum bane kenan haka akeso na fahimta ko?"
Yana kaiwa nan ya juya ya fice a fusace Rafi'ah dake tsaye tayi zaman ƴan bori a gadon ta ɗora hannunta akanta tace “Innanillahi Allah ya Allah meye yake faruwa damune Ni me nakeyi masa ne ya tsaneni?" Zama Ya Hajja tayi cikin tsananin tausayin surukar tata ta dafata tace “Dama yana dukanki?" Saurin Girgiza kai tayi tace “Aa Ya Hajja kuma inma ya dakeni laifina ne yakai ya dakeni ni Indai dukan nawa zaisa ya samu nutsuwa Ya Hajja da kin barsa ya dakeni"
Murmushin takaici Ya Hajja tayi tace “Lallai dole ki lalace yarinya Namiji ba mutumin da zaki nunawa irin wannan soyayyar bane kinga ki rabu dashi da kansa zai kawo kansa har inda kike tsabar neman sanadi ne ma ya kawo shi" kwantar mata da hankali sosai Ya Hajja tayi sannan ta fita ta barta tana ganin ta fita ta ɗauki wayarta miscall ɗinsa ta gani har biyar kafin takai ga kira saƙonsa ya shigo ta buɗe saƙon yana share hawaye.
_“Meyesa zuciyata bata iya jure turjiyya daga gareki Noor wlh bandaina sonki ba har abada inasonki"_
Iya abinda ya rubuta kenan taja numfashi ta kashe wayar ta ajiye ta ɗaga rigarta abinka da farar fata har gurin ya shata ta shafa wajen hawayen fuskarta na gangarowa ta sauke idanunta kan Hisham dake baccinsa hankali kwance.
Washegari ta tashi da ciwon kai saboda kukan data kwana tanayi bata iya miƙewa ba sai goma tayi wanka ta gyara jikinta tasha kunun gyaɗa ta sake kwanciya tana ɗaukar wayarta taga alert na bankinta ta buɗe kuɗi ne masu nauyi har 2:5 millions daga asusun Abdulƙadir ta sake duba alert ɗin tun biyu na dare yayi mata shi ta cika da mamaki to kuɗin na meye ne?"
Kasa jurewa tayi ta ɗauki wayar ta tura masa saƙon gaisuwa tare da tambayarsa ko kuɗin na meye? Bai bata amsa ba taga kiransa tayi kamar karta ɗaga ta dai dake zuciyarta sukayi shiru na lokaci me tsayi kafin ya katse shirun da cewa “Ina kwana Mom Hisham" iska ta furzar tace “kudin na mene?" Cikin sanyin yanayi yace “Nakine ki kulamin da kanki ni na wucce Port Harcourt ɗazu da safe nazo Gana Hajja tace baki tashi ba"
“Uhmm!" Ta sauke iska tare da cewa “Na gode amma bana buƙatarsu jiya second Daddy ya samin 5 millions a acct ɗina meye zanyi da kuɗi ne AbNoor da kuketa nunamin su? Not Daddyn Hisham ni ba kuɗi nake buƙata ba kwanciyar hankali da fahimtar juna tsakaninmu yafimin duniya da abinda ke cikinta su zama mallakina inason naga ranar da rsyuwarmu zatafi wata bakwai da suka wucce a baya inganci yaushe hakan zai samu AbNoor?"
Ta ƙarashe maganar muryarta na fidda sautin kuka yayi saurin cewa “Shikenan ya isa haka Noor yanzu me kikeyi?" “Babu komi" ta furta masa yaja numfashi yace “Amma kina kwana arba'in zaki dawo ko?" Shiru tayi tana wasa da hannunta yace “ok na gane zanyi magana da Gana Hajja"
Tsakanin mace da miji sai Allah tuni duk abinda ya faru ya wucce sukaci gaba da rayuwarsu saiya kasance da dare bata samunsa a waya shima ya daina kira tayi uzuri wa aikinsa ne kawai duk da tasan shi ba wani abu yakeyi da dare ba yawanci amma dole in kanason zuciyarka ta kasance da nutsuwa saika rinƙa bawa mutane uzuri.
Satinsa biyu kuwa sai gashi yazo daukarsu wannan karon tattarata sukayi suka bashi matarsa suka tafi gidansu na nan Maidugurin wannan dare Rafi'ah ta karɓi madarar soyayya ta kuma karɓa a jikinta sai gashi kamar zai goyata sai nan nan yake yi da ita ita abinda yake bata mamaki duk wannan uwar rigimar da sukayi lokacin cikin Hisham ya manta wata ƙauna yake gwadawa yaron da ko ita albarka ƙuda wannan saidai ya shammaceshi ya taɓa masa ɗa.
Kwanansu huɗu suka wucce Port Harcourt tun parlourn farko ta rinƙa ganin abubuwan saɓanin yanda ta sansu wajen kaca² bayan tasan Abdulƙadir mutum ne me mugun tsafta to ya akayi wannan parlourn ya zama haka? Kafin takai ga tambayar yace “Au na manta ban faɗa miki ba Bilkisu ce ta dawo Gidannan da zama ta tafi makaranta ne"
_Paid book nrml 300 VIP 600 special 1k Email post 2k acct details 3184512451 Fauziyya Tasiu Umar first bank evidence 09013718241_
_**Oum Hairan*
[11/17, 7:25 AM] OUM HAIRAN: _*AKWAI IRINSU...17*_
BHUZUWA EMPIRE
BHUZUWA EMPIRE
BHUZUWA EMPIRE.
Assalamu alaikum Al'ummar musulmi baki daya.
Kamar yanda ku kasani nice *buxuwa empire* wanda nake kawo maku kalolin mallaka da dama ga duk wacce take da wata damuwa ko matsala da take ciki tana iya bina ta private ko ta kira ta waya ..... Aikin mu babu kauce hanya da sirrorin Alƙur'ani mai girma muke duk wani Ayyukan mu .
*AYYUKAN BUXUWA EMPIRE*
1.munayin aikin bakar mallaka wacce muke kira bita zai zai , amma sai mun yi istihara mun bin cika Zuciyar ki .
2. Munayin aikin haihuwa ga wacce bata samun haihuwa inshallah da kinzo taskar empire za'a haske da buwaya na mai sama'u .
3. Munayin aikin bakar firraku wacce duk wacce a kai mashi sun rabu kenan har abada.
4. Munayin aikin da idan mijinki na biye biyen mata kina iya kimasa mallakar gabansa ki gama dashi , shi da wata mace sai ido. Wannan mazinata ake yi mawa ,idan kin san kina da kishiya da cutarwa . Na iya wanda mazan su ke bin matan banza a waje ake mawa .
5. Munayin aikin dafa'i na zallar Ayar ALLAH .
6. Munayin aikin farin jini a duk inda kk ko kuma na samari .
7. Munayin mallakar wajen a aikinku ko na office wannan na ma'aikata ne .
8. Munayin aikin aljannu musanman wanda aljani ya takura masa ko ya hanashi aure ko samun samari ko saurayin da yazo yau gobe ba zai dawo ba. Ko ya hana zaman gidan Aure .
9. Munayin aikin budi akan kasuwanci .
10. Munayin aiki a kan miji idan baya maka kyauta ko baya kula da kai da yara tare da ɗaukar hidimar ka . Maza taho Taskar empire kisha mamaki .
Sannan duk macen da takeso a zautar mata da mijin ta a kanta a mallake mata shi sai yanda tayi to akwai wani aiki da nasomayinsa wanda nake aikawa da turaren gari garii idan ki kayi amfani dashi komai nashi sai kinsani haka kuma komeye kike so sai ya baki. Amma sai mun duba zuciyar ki idan babu cutarwa .
*WhatsApp or call*
*08139762831*
Mata masu bukatar kaya da'a wato mgnn mata masu aiki da rubutu ko wanda ba mai aiki ba available maza ku garzayo gurin *Buxuwa empire* domin jin dadinku ma'aurata akan number ta dai wanda kuka sani gashi *08139762831*
Masu bukatar shuumin humra komai ya haɗa subhanallah wannan humra tayi wlh wlh wlh duk wacce tayi amfani da wannan humra mijinta wata ya mace ta burgesa an gama kuma , sannan da na farin jini mai kyaun gaske wanda ake haska tauraronki mata ku garxayo wajen *buxuwa empire* domin kuji dadin ku ku kuma godiya ga ALLAH
*BHUZUWA EMPIRE*
*08139762831*
Zubansa idanu tayi da matsanancin mamaki tayi kamar zatayi magana sai kuma ta fasa ta juya da nufin shigewa ɗakinta taji ya riƙo kugunta ya haɗata da jikinta ya saita bakinsa a kunnenta yace “Kamar bakiyi farin ciki da dawowa kiga Bilkisu a nan ba" ƙaƙalo murmushi tayi tace “Aa meye zai hanani farin ciki AbNoor kawai dai gajiya ce amma yaushe ta dawo?" Shafa kansa yayi yace “Batafi sati ba" ajiyar zuciya tayi ta shiga ciki tsayawa tayi turus ganin ɗakin kaca² gadon duk a hargitse pillows ɗin a ƙasa a warwatse ta rinƙa bin ɗakin da kallo wani wajen kaya ne a warwatse wani wajen harda pant da bra wani gurin ma kwalayen lemo ne da ledoji.
Rafi'ah ba macece me saurin fusata ba amma Saida wannan abu yasa mode ɗinta canzawa hakanan ta sanya zani ta goya Hisham ta fara gyaran ɗakin saida ta dawo dashi hayyaci sannan ta shiga bathroom ta fara yi masa wankin tsaf harda jini a ƙasan tiles ɗin duk wannan abinda take yi zuciyarta a jagule take tana turawa kanta tambayar “To babu wani dakin ne da aka saukar mata ita a ɗakinta?"
Kwantar da Hisham tayi ta shiga wanka ta gyara kanta ta fito domin shiga kitchen sukayi clear da Billy tana shigowa shi kuma gogan yana biye da ita a baya ta tsaya tare da ɗan ja da baya ganin yanda Billy ke ƙoƙarin bangajeta ta shige ciki kuma ɗakinta ta nufa gadan gadan, idanu ta zuba don ganin sarautar Allah har ta shige ciki baice mata ƙala ba ita abin sai ya zame mata baƙo kuma sabo ta juya zuciyarta taf da sake sake ta shige kitchen ɗin ta kunna gas ta ɗora abinci tana girkin ne ranta cike da sakar abubuwa da dama a cikinsa.
Har ta gama bataji motsin kowa a parlourn ba ta fito ta shirya a dinning ta sake gyara parlourn ta kunna masa turare ta nufi ɗakinta ta murɗa domin shiga tajishi a kulle ta tsaya da mugun mamakin wannan ƙarfa ƙarfa kamar karta ƙwanƙwasa saidai tunawa da tayi da ɗanta a ciki yasata ƙwanƙwasawa cikin masifa aka hayayyaƙo mata da cewa wai wanne banzan ne yake bugamin ƙofa yanzu"
Bata ɗauki wulaƙanci ba ko kaɗan hakan yasa ranta yayi baƙi tadai dake ta daure tace “Nice Bilkisu" tsaki tayi ta buɗe ƙofar ta tsaya a jiki ita kuma ta wucce ta shiga tare da juyowa da sauri tace “Bilkisu Ƙalau kike kuwa?" A wulaƙance tace “Da akayi me?" Cikin sanyin murya da yanayi tace “Haba Bilkisu Yaro jariri me kwana arba'in da Biyar zaki kwantar a dandagaryar tiles keko Meye yake damunki haka?" Tana maganar tana sunkuyawa ta ɗauki ɗanta zata ɗora a gadon.
Taji ta daka mata tsawa tana cewa “Haba Malama ya zaki kwantar min da wannan ƙazamin ɗan naki a gado dalla ki ɗaukeshi ki kaishi inda ya dace dashi" kallo ta bita dashi na mamaki tace “Gadonki kuma Bilkisu ya akayi ya zama naki?"
Turo kofa yayi ya shigo tana ganinsa ta fashe da kuka tana cewa “Dama Saida nace bazanzo gidanka ba Yaya Audu kace sai na dawo yanzu gashi daga dawowar matarka ta mareni tayimin gori har tana cewa sai nabar mata gidan mijinta...."
Babu zato babu tsammani taji ya rufeta da duka da gaske tun Rafi'ah na ƙoƙarin ƙwatar kanta har ta saduda yau kasheta Abdulƙadir zaiyi, Saida ya daki me isarsa sannan yasa hannu ya debeta ya watsa parlour ya nuna ta da yatsa yace “Idan har ke kinajin nan gidan mijinki ne to ita kuma da take ƙanwa a gurin mijin naki ya zataji da har kike da baƙin yi mata gori Rafi'ah zan shayar dake mamaki akan wannan mugun halin naki Ni na lura dama ke bakya ƙaunar Bilkisu tun zuwanki cikinmu banza shashasha mara tarbiyya"
Banko ƙofar ɗakinsa yayi daƙyar taja jikinta ta matsa jikin kujera ta haɗe kai da gwiwa kukan da bata taɓayi ba a rayuwarta yau shi tayi karon farko a rayuwarta da aka taɓayi mata duka kenan bata taɓa tunanin akwai rana da lokacin da zaizo wani ya samu damar da zai fitar da jini a jikinta ba.
Tayi kuka kamar ranta zai fita kukan Hisham ne yasata sake rushewa da kuka ga nononta duk ya cicciko da alama yaron yunwa yakeji.
Jin kukan takeyi a tsakiyar ruhinta ga rashin mafita tashi tayi tsam ta buɗe ƙofar parlourn ta fice daga cikinsa domin ranta bazai iya ɗaukar mata kukan yaron ba gara kunnenta baiji ba, bayan ginin gidan ta zagaya ta samu wani ɗan guri ta rakuɓe ga sanyi ga tsamin jiki ga kukan ɗanta yana taɓa mata zuciya gashi batada wani abinyi haka ta wanzu a wajen tsayin lokacin da ita kanta bazata iya tantancewa ba kafin hancinta ya fara jiyo mata ƙamshin turaren Abdulƙadir tayi ƙarfin halin ɗagowa idanunta ya shiga cikin nasa tayi saurin ɗauke idanunta tare da janyewa cikin tsoro ta miƙe jikinta duk rawa yakeyi ga shatin belt ɗinsa nan ruɗu ruɗu duk a jikinta.
Miƙa mata yaron yayi zuciyar ɗa da mahaifiya duk da tsoron da ya dasa mata a zuciyarta hakan baisa ta kasa matsawa ta karɓi ɗanta ta nemi guri ta zauna ta sanya masa nono ya kama da sauri suka sauke ajiyar zuciya tare ita da yaron hawayen ta ya ɗiga kan fuskarsa abinda ya sanyashi buɗe idanunsa ya zubashi a kan fuskarta.
Zamewa tayi daga kan ɗan ginin da take zaune ta kuma rushewa da kuka har cikin ranta takejin tausayin kanta a wannan halin da ta kuma ruftawa ciki a fili tace “Allah kasan komai kuma kai ka nufeni da faɗawa kowanne irin ƙunci a cikin sunnar ka da na zaɓa dan kiyaye dokar Shari'ar addininka Allah bansan meyesa jarrabawata ta tsananta ba duk da na kasance me rauni saidai nasan kai kasan dalilin da yasa ka jarabceni da hakan Ubangiji ka agazamin na rantse da girman zatinka da buwayarka bazan iya jurewa wulaƙanci duka da tozarci a gurin wannan bawan naka dana zaɓa na tura maka zaɓi akansa kuma kaima ka zaɓamin ba Allah bazai zamemin bango ba katangar da zan jingina na samu sauƙi ba meye yasa ka zaɓamin shi...."
Ji tayi ya dafata ta bige hannunsa cikin mugun matsanancin fushi da kuka me cin zuciya tace “Karka ƙara taɓani Abdulƙadir na tsane....." Rufe mata baki yayi da mugun sauri ya fincikota jikinsa ya ƙanƙamesu zuciyarsa na bugawa da ƙarfi yace “Aa Noor baki tsaneni ba wlh bazaki taɓa tsanata ba har abada" tureshi tayi tana kuka me taɓa zuciya ta