Showing 48001 words to 51000 words out of 72723 words
na zama mijin kantace zaki tabbatar?"
_Share fisabilillah bonus page ne_
_*Oum Hairan*_
[11/17, 7:25 AM] OUM HAIRAN: _*24*_
Sunkuyar da kanta tayi tace “Amma AbNoor don Allah kayimin wata alfarma" bottle na ruwa ya ɗauko a freegde lokacin dasu Abdallah keyi musu sallama ya juyo yace “Ok Ina jinki fah" cikin son sanin meye a zuciyarsa tace “So nake ka amince nayi abortion na Fetus ɗinna...." Sakin bottle ɗin yayi da cup ɗin hannunsa suka tarwatse yace “Meyesa Noor?" Cikin murya me rauni tace “Nasha wahala wancan cikin AbNoor ina buƙatar hutu" girgiza mata kai yayi yace “Aa ki bari wannan karon bazakisha wahala ba Please kiyi shiru indai kuma ba so kike ki canzamin lissafin brain ɗina ba" yanda yayi kicin² abin har dariya yaso bata tadai maze ta kwanta ya gyara inda ya fasa glass ɗin ya fita bai jima ba ya dawo da cup na madara da cake ya tasheta zaune ya rinƙa bata a baki taci sosai sannan ya fice sai biyar ya dawo amma baya cika awa ɗaya sai ya kira ya tambayeta babu dai wata matsala ko? Takance masa eh saidai zuciyarta taƙi kwanciya da wannan kulawar da Abdulƙadir yake bata kamar zai maidata cikinsa.
Haka lokaci yaci gaba da tafiya wannan ciki yanashan gata ko motsi tayi saiya tambayeta meye take buƙata baya barin damuwa ko kaɗan ta shiga tsakaninsu yana ƙoƙarin sauke duk wani nauyi dake kansa nandanan ya mayar dasu jiƙaƙƙun ƴan gata kwanakin sukayita tafiya har cikinta ya fara ƙwari duk da tanashan laulayi amma haka ta rinƙa daurewa bata bari ya gane damuwarta.
Ashe ɓoye mata halinsa na zahiri yakeyi Abdulƙadir ya zama cikakken ɗan neman mata ta fara ganewa ne da yawan tsintar comdom da takeyi a kayansa tun ranar data tsinci na farko tashiga muguwar damuwa da tashin hankali da ta kasa jurewa yana dawowa ya fahimci akwai damuwa duk da tanata ƙoƙarin dannewa Saida ta gama haɗa masa abinci ta ɗauki wayarta tana dannawa ya karɓe wayar ya zubanta idanu kallon da yake saurin sanyata shiga hankalinta yace “Akwai damuwa ne?" Girgiza masa kai tayi yayi murmushi yace “Bazan yarda ba akwai damuwa Noor sanar dani meye yake faruwa?"
Dakewa tayi kawai garama ta nuna masa tasan komai karta barshi a duhu ya kasa gane kanta ya koma zarginta dayi masa rashin adalci, Saida ya kuma magantuwa sannan tace “Daddyn Hisham Billy tana garin nan ne?" Da sauri ya ajiye cokalin yana mata kallon nazari da kuma rashin gaskiya a haɗe yace “Aa wani abu ya faru ne?" Murmushi tayi daya sanya hawayen idanunta saukowa ta mike ta shiga dakinsa ta ɗebo comdom ɗin data tsinta har sau uku cikin aljihunsa ta zube masa kan dinning ɗin suka kama kallon kallo numfashinsa na neman rabuwa da gangar jikinsa yayi ta maza yace “Am kinga Rafi'ah...." Ɗaga masa hannu tayi tace “Don Allah karkace komai AbNoor cikin shekaru uku kan huɗu yakamata ace nasan abinda zaka iya dainawa da wanda ya riga ya shiga jininka AbNoor na yarda dakai lokacin da kacemin Billy ce farko saboda ta faɗa min zata rayu dakai ko ba aure nasan halin wasu matan akan namiji har shirka suna iya yi da Billy tayi nesa damu sai nayi tunanin shikenan ka daina AbNoor ina sama da ƙoƙarina wajen ganin na sama maka nutsuwa amma bana gamsar dakai kafi samun nutsuwa da matan waje ok Daddyn Hisham babu abinda zan iya akai komai kaje kayi Allah yanaji yana gani Insha Allahu bazan ƙara magana ba amma ka sani na gaji da gwamutsa halalina da ƙazanta"
Koda ta tashi bai dakatar da ita ba domin bashida wata karyar kare kansa da zai yi mata comdom a jikinsa kuma a cikin kayansa ai bai isa yace ba nasa bane, to waishi meye ma matsalarsa ne da neman mata meye baya samu a gurinta? Abincin da bai iyaci ba kenan ya tashi ya shiga ɗaki ya rinƙa zagayashi kalma ɗaya da zata faɗo masa da zai iya gamsar da ita ya rasa dole.
Ya nemi guri ya zauna nesanta kansa da ita zai bashi damar yin tunani me kyau ko Allah zaisa ya samu mafita da wannan ya kwanta baccin ma a ranar baiyi ba da asuba ya tashi ya fita zuwa Masallaci bayan ya dawo ya kwanta wani feeling yakeji yana bijiro masa tun daga tsakiyar kansa har yatsun ƙafarsa zuciyarsa na raya masa kodai ya tashi yaje gareta ne tashi yayi ya fita zuwa ɗakinta ya buɗe zaune ya isheta saman sallaya tana karatun Alkur'ani mai tsarki duk ta jiƙe peper na Kur'anin da hawaye ya zauna kusa da ita tare da zare ƙur'anin ya rufe ya ɗago kanta ta Lumshe idanunta yace “Ina kwana Noor!" Sake rintse idanunta tayi ya janyota don shigar da ita jikinsa taƙi tama miƙe zata fice ya tashi da sauri yace “Ki bari Noor Ni me laifine kullum a wajenki zaki gyara ɓarna da ɓarna ne? Idan na kasance mazinaci in kika gujemin gyaruwa zanyi ko lalacewa?" Tureshi tayi tace “Ina ruwana da gyaruwarka Ni na cire tsammani da gyaruwarka ai kawai kaje kayi rayuwarka nima zanyi tawa"
Zuciyarsa bata cika ɗaukar turjiya ba dannewa yakeyi kawai don ba burinsa su samu matsala ba gyarawa yakeso suyi amma ta tubure masa nema take tasashi yayi abinda baiyi niyya ba cikin fusata Yace “To wai da kike wannan haukan Ni an faɗa Miki ana sani nayi abu da haka ne irin naki hukuncin kenan? Ki hanani halalina idan a baya babu ke cikin lalacewata yanzu fah kullum matar aure cikin binciken laifin mijinta take saboda ta samu dama ta azabtar dashi da haka karuwan da kike jin haushi in nayi mu'amala dasu fah? Rafi'ah kullum cikin tunanin me zasuyi su jiyar dakai daɗi suke duk wata manhaja ta jin daɗi ita suke Saita maka amma yanzu ke saboda kin kama comdom a aljihuna kin raba shimfiɗa dani na aje duk wani girma na biyoki don samun daidaito kin kuma tashi zakimin hauka to wlh tallahi kinji na rantse indai haka kika zaɓa Nima na zaɓi hakan zanje naci gaba da biya ana kashemin yunwata duk sanda naso"
Juyawa yayi ya fice a fusace bata saurareshi ba bare tabi ta kansa ta koma tayi kwanciyarta duk inda zashi ma yaje ta shiryawa hakan.
Tun daga wannan lokacin basu ƙara zaman farin ciki ba kullum cikin rigima suke har cikinta yakai watanni bakwai wata rana tana kwance a ɗakinta da dare taji tsayuwar motarsa dama bata shirya bi takansa ba tayi zamanta a ɗaki washegari ta tafi asibiti tun kafin ya fito ta fice daga gidan lokacin data dawo taga ƙofar a buɗe tayi tunanin ko shine a ciki ta shiga sai taga Billy ce da wata ƙawarta Cristiana ta tsaya a bakin ƙofa Billy na ganinta ta shiga hankalinta domin dukan da tayi mata wancan karon har yanzu da tabonsa a Jikinta.
Ɗaure fuska tayi tamau tace “Ke ubanme kikeyi a gidannan?" Cikin tsoro tace “Yaya Audu ne yace na jirasa anan yana zuwa" a fusace tace “Ki jirashi anan yace Miki? Shi Daddyn Hisham ɗin to ki tashi ki ficemin ki nemeshi a inda kuka saba haɗuwa kuyi iskancinku in kuma kinƙi na rantse da girman Allah sai nasa an gwaleki nayi Miki kaciyar maza ƴar iska karuwar banza da wofi"
Sumsum Billy ta tashi taja ƙawarta suka fice tana shiga babu jimawa Mommy ta kirata take faɗa mata tana garinsu rokon Mommy ta rinƙayi harda kuka tana cewa ”Mommy baki taɓa kawomin ziyara ba dama don Allah kizo gidana ko sau ɗaya ne tak na ganki nima inna haihu zanzo ko Daddyn Hisham bai barni ba Mommy ina kewarku sosai"
Daƙyar Mommy ta amince zatazo gidan ɗiyar tata domin itama tanason ganinta zuwa yanzu tanason sake jan ƴarta a jiki don fahimtar zahiri ta nuna akwai jumurɗa cikin auren na Rafi'ah don dai tanada zurfin ciki ne. Hayar mota tayo har barikin Rafi'ah ce ta leka rasa Abdulkarim yaje ya taho da Mommy suka rungume juna suna farin cikin ganin juna bayan Rafi'ah ta bata abinci da sha ta taɓa kaɗan suka fara hira take faɗa mata dalilin zuwanta Port Harcourt ɗin suna tsaka da hira Abdulƙadir ya shigo kamar an jefoshi dukkansu hankalinsu ya koma kansa zubawa Mommy idanu yayi na ɗan lokaci ya mayar da kallonsa kan Rafi'ah yace “Ina Billy?" Ya faɗa da ƙaraji ta riga ta dake yau ta shiryawa duk abinda zai yi mata shiyasa tace masa.
“Tazo ta tafi" “Ta tafi ko kin koreta?" Ya faɗa ta ɗauke idanunta akansa ya sake daka mata tsawa yace “Uban waye ya bawa wannan watsattsiyar karuwar damar shigomin gid...." Bai rufe bakinsa ba ta sauke masa yatsunta cikin wata irin rawar jiki tace “Karka ƙara Abdulƙadir na rantse da Ubangijin dake da rayuwata a hannunsa ko zai zama sanadiyyar raina zan rabu dakai akan mahaifiyata baka isaba kaima ai ba akan daidai kake ba sai na uwata ne ya zama abin magana...." Batayi aune ba ya shaƙeta ya haɗata da bango ta fasa ƙara yayi watsi da ita ya bita yayi ball da ita Hisham ya rugo da gudu ya riƙeshi yana kuka yana cewa “Daddy Mommy is sick ka daina dukanta" bai saurari yaron ba ya kuma yin ball da ita ƙofae bayan dake saman benen ta buɗe bisa tsautsayi Rafi'ah ta daki kofar kawai tayo ƙasa gabaɗaya ya biyota yana huci Mommy da hankalinta ya tashi tayi ƙasa da mugun gudu tana cewa “Na shiga uku Ni Bara'ah Rafi'ah auren duka...." Bata rufe bakinta ba taji yace “Dama nasan wannan ranar zatazo tunda aka samu akasi ba tarbiyya ce ta raineki ba wlh ko baya ke babu wata mace na gama auren ƴar karuwa kije da uku wani me tsautsayin ya ɗauka ko kuma kiyi sana'ar uwarki"........
_*Oum Hairan*_
[11/17, 7:25 AM] OUM HAIRAN: _*AKWAI IRINSU*_
_*Oum Hairan*_
Yar uwa kina zaune Kullum da waya a hanunki amma bakisan ta yadda zakiyi business dashi kisamu kudiba Yakamata kizo kiji yadda zakiyi kina zaune acikin đakinki kimalake kuđi indai kinyi register da metar force bb abunda bazaki samuba nanda lokacin kadan kizama millioniers
Inaso don ALLAH kowa
yayi tambaya akan abunda yake son sani game d META FORCE
Kudena wasa d damarku😱
Abun nan abude yake kowa yasan gaskiya ne📌
Sannan kana d damar d zakayi research🔎 akansa (META FORCE)
META FORCE yana gaf dafin karfin talaka wlh
Daga lkcn d FORCE COINS wato coins din META FORCE yafita kasuwa labarin zai canja💃
ALLAH yagani mun fita hakkin ku mun faɗa muku iya gaskiyar mu📌💯
META FORCE ba wasan yara bane b abune d za'a dunga wasa dashi b awannan lokacin🧏♀️
Kowa mafita yake nema a rayuwar nan, ALLAH yakawo🤲 amman Arewa muna wasa d ita😔
Bayan muna gani kasashen d sukaci gabama sun rukeshi hannu bibbiyu, sai mu ne muke wasarere dashi🤦♀️
Duk abun mukeyi munayi ne don mugudu tare mutsira tare🫂
ALLAH y ganar d wanda yake kokwanto akan META FORCE
ALLAH yabamu SA'A🤲
Wanda yagane yahuta
Wanda begane ba Allah ya ganar dashi.
Kar ki yarda ki yi irin zaman ban za ƴer uwa.ban
Kitashi ki yi abin arziqi sis🧏♀️
Akwai kuɗi 💰a META FORCE
Tashi ki diba💃💃 Dan Allah wadda tasan koh yasan dagske yake zai yi register toh yabini pc Wanda Kuma bai shirya ba Dan Allah kar mu batama juna lokaci nagode
07026020745/09131164861 me niman karin bayani ya tuntubeni ta wanna layi
https://chat.whatsapp.com/IxPjKawUjfX7IjrSrZL5vT
_*25*_
Duk da matsanancin yanayin da take ciki hakan baisa ta kasa jin saukar kalmar Rafi'ah na gama aurenki na sakeki saki uku....." Fuuu ya janye Hisham ya jefa yaron mota yaja ya fice daga harabar gidan da mugun gudu ya nufi gidan Abdullah hargowarsa ce ta sanya Abdallah daya shigo yanzu fitowa ɗaure da towel ganin yanda jikinsa yake rawa yasa Abdallah tsayawa turus ya tako ya iso gareshi ya sauke masa Hisham yace “Kar wani abu ya samu yaron nan kuma kada tsautsayi yasa nazo ɗaukar sa na ishe bayanan" daga haka ya fice yaron yanata kuka yana kiran Mommy Daddy idan mutum ya fado daga bene mutuwa yakeyi ka jefomin Mommy...."
Kasaƙe Abdallah yayi yana sauraron abinda yaron yake cewa kafin yayi kukan kura ya shiga mota ya fice ɗaure da towel har gidan Abdulƙadir yana zuwa masu gadi suka sanar dashi yanzu nan wata mata ta tafi da Madam cikin mawuyacin hali jini ma taketa zubarwa" hawaye ya share yace “meye ya faru?" Samuel ne yace “Sudai basusan komai ba sunga wata mata me kama da Madam tazo shima Oga ya dawo babu jimawa kuma sukaga ya cillota daga bene ya ɗauki Hisham ya fice babu ɓata lokaci ya dawo ya karɓi biro a wajensa ya rubuta wata takarda ya cilla mata ya fice wannan matar tana rokonsa ya taimaka ya kaita asibiti ita kaɗai ta mallaka matsayin ɗiya amma bai sauraresu ba ya shige gida ya rufe abinsa.
Wata irin suya zuciyar Mommy ta rinƙayi har zuwa lokacin da suka isa asibitin aka fara bata taimakon gaggawa dake magana ake ta kuɗaɗe kuma akwaisu babu ƙaryar ƙarya haka aka fara kula da Rafi'ah jinin kawai suka samu ya tsaya Mommy ta kira Daddy ta sanar dashi abinda ke faruwa ya kuwa bata umarnin duk inda suke su taho Kano saidai kafin tayi yunkurin neman wata hanya ta barin garin second Daddy yayiwa garin tsinke ta hanyar bin location ɗin wayar Mommy ya iso har asibitin idanunsa sun kaɗa sunyi jawur da farko bai damu ba lokacin da yaga saƙon Abdulƙadir a wayarsa ya rubuta masa.
_Duk da nasan cewa zan wahala da rashin Rafi'ah Daddy kayi haƙuri Ni Abdulƙadir Ibrahim Barzah na saki matata Rafi'ah saki uku...."_ Daddy bai wani damu ba domin yasan aure rai garesa amma da yaji irin wulaƙancin da yayiwa ɗiyar tasa saida ya girgiza don tashin farko iyayensa ya kira ya sanarwa Abba yace yaji komi a wajen Abdallah su haɗu a Port Harcourt ɗin second Daddy yace a'a zai tafi da ita Lagos ne" yana zuwa kuwa baije inda suke ba saida ya fara zuwa ya gama files na tafiya da ita sannan yaje yaganta a kwance kamar gawa sai ledar jini kawai dake Jikinta ya dubi Mommy yace “Kije kawai Bara'ah zan tafi da ita Lagos ne" taso tace a'a sai kuma ta tuna Abdulkarim tun da can ma baya magana biyu shine kawai yasata shiru tana kallo aka gungura Rafi'ah a gadon marasa lafiya aka sata a mota ta bisa da sauri tace “Zan iya zuwa nayi jinyar ɗiyata?" Jinjina mata kai yayi yace “Zaki iya" ya shiga motar suka dunguma sai airport wani katafaren asibitinsa aka kaita kulawa kam an ƙareta gabadaya anan cikin hukuncin ubangiji babu karaya a Jikinta ko ɗaya shine dalilin da yasa abin yazo da sauƙi.
A ranar Saida iyayensa sukazo Lagos dukkansu babu wanda ya iya cewa komai banda tur da suke da baƙar zuciyarsa da tambayar dalilin sakin Mommy ce tace to itadai ta fahimci kamar rigimar akan wata Billy ne amma batasan meye abinda ya kawo rigimar ba jinjina kai Ya Hajja tayi tace “Ai shikenan yayiwa kansa Rafi'ah Allah ya baki wanda yafishi amma Audu ka cuci kanka munyi rashin suruka ta ƙwarai"
Kwananta ɗaya ta farka daga doguwar sumar da tayi sunansa ne kawai ya fara zuwa bakinta bayan salatin Annabi sannan ta fara kallon kowa daidai second Daddy first Daddy Mommy da Abba Lumshe idanunta tayi Amon muryarsa na tashi a kunnenta “Ko ke kaɗai kikayi saura mace na gama zama dake tunda dama ba irin tarbiyya bace akanme zan damu sai kinyi aikin masu tarbiyya kije da uku wani me tsautsayin ya ɗauka.....
Wata ƙara ta saki ta diro daga gadon Daddy da Abba sukayo kanta ta riƙe Daddy tace “Ƙarya kunnena yakeyi bai sakeni ba ko Daddy? Abba ina Daddyn Hisham na yarda na karɓi laifin nayi kuskure dana kori karuwarsa a gida yaci gaba da kawota...."
Rufe mata baki Abba yayi zuciyarsa ta karye kullum Suka samu matsala shine me laifi wannan auren Gara ma da ya mutu kowa ya hutu shekara huɗu tunda akayi ba'a huta ba rigimar yau daban ta gobe daban.
Daƙyar da kalami suka samu ta nutsu amma bata daina kukan rashin masoyi ba taci gaba da samun kulawa gurin likitocin asibitin Daddyn nata Saida ta haihu sannan suka koma gida ta haifi ɗiyarta mace yarinyar kyakkyawa kama take da ita saidai yanayin fatarta na ubanta ne batada haske sosai.
Kiran Mahaifinsa akayi aka sanar dashi haihuwar yayiwa Allah godiya shi kuma second Daddy lokacin zai tafi Indonesia don haka yayi mata siyayyar ban mamaki ya basu damar tafiya Kano da ita dake yamma ce akayi haihuwa washegari bata tashi ba Iya Lami ta shigo tace tanada baƙo ta yunƙura ta tashi tace “Koma waye bananan" da sauri Iya Lami tace “Hajiya Mommy ce tace a faɗa Miki inji Daddynki ne yace a faɗa miki kinada baƙo" jin an ambaci Daddy ne yasata cewa ok koma waye ki shigo dashi parlou"
Fita Iya Lami tayi ta tashi ta shirya ta sanya hijjab ta fito a ƙofar dakin taci birki ganinsa tsaye yana zagaya ɗakin taji wata faɗuwa gaba ta dirar mata ta daidai lokacin da Daddy ya iso ya karɓi yarinyar yace “Ka zauna mana ka tsaya Audu" ajiyar zuciya ya sauke idanunsa kan Rafi'ah da takeyi masa wani mugun kallo da yakasa Fuskantar ina ya dosa yana shirin zama yaji ta datso ƙofar ɗakinta sosai baiji daɗin irin tarɓar daya samu a wajenta da wajen mahaifiyarta ba duk da cewa yasan shi ɗin cikakken me laifi ne a gurinsu amma ya kamata su saurari dame yazo inda hanyar da zaabi ayi amfani da ita wajen gyara wannan kuskuren daya aikata.
Duban Daddy yayi yace “Daddy inason magana da Noor" nuna masa ƙofar yayi yace “Ka shiga mana tana ciki" kallon babyn yayi ya miƙe ya nufi ɗakin ya tura ƙofar ya shiga tana zaune gefen gado ta zabga tagumi ya matsa kusa da ita ya zauna kan Bedside drower ya kira sunanta sai a lokacin tasan ya shigo ɗakin ta ɗago da sauri tare