Showing 93001 words to 96000 words out of 194226 words

Chapter 32 - GURBIN IDO COMPLETE HAUSA NOVEL

HUGUMA   

12 Dec 2024

26176

ba,baya ga dafi da zai barwa gangar jiki da zuciyarta kuma sai ya karanto sirrinta

"Nidai ban fada ba"
"Ni kuma na fada,with all these lapses ma cancanci a bani soyayya..... I don't know what to say...mafi qarancin abinda zance shine, thank you for opening my eyes and showing me the way, thank you for loving me" kalamansa sun mata dadi sosai,kuma ta sake tabbatar da cewa lallai mahaqurci mawadaci ne.

A daddafe take qarasowa cikin wata tafiya da tayi kama da takun isa ko yanga,wanda sam babu daya daga cikin abu biyun illa ciwon da takeji a dukka gabbanta,tun daga nesa idanunta ya sauka akan rolls Royce ghost din,tana da yaqinin ba motar hisham bace,ba kuma tasan me motar ba,don bata taba ganinta ba,don haka koda ta isa sai taja ta tsaya tana dan duba gefenta ko xata hangi motar hisham,wala'alla wanna motar ba ita tazo dauka ba.

Idanununsa ya bude a hankali daga dogon tunanin da ya tafi jin shuru har yanzu ba ita ba alamarta,kai tsaye a kanta suka sauka sanda take dube duben,sai ya sanya hannunsa saman hon na motar ya danneshi ba tare daya dauke dubansa daga gareta ba.

Wani irin firgewa tayi saboda yadda qarar ya saukar mata a bazata,baqaqen gilasai ne,bata tsammaci ma kwata kwata da mutum cikin motar ba,qafafunta ne gaba daya sukayi wani irin laushin da bazasu iya daukarta ba,tilas ta sulale a wajen tana dafe da kunnuwanta,jikinta na wani irin rawa.

A hankali ya bude murfin motar ya fito,ya fara takawa zuwa inda ta sulale din,tana tsugune a wajen ta cure waje guda,yaga yadda ta tsorata din ta cikin mudubin motar

"Get up" ya fada a taqaice yana duban ginin makarantar cikin yanayi na nazari,yayin da sautin muryarsa ya sake sanya maimunatun qara dimaucewa,tsoronsa ya sake shigarta.

Idanunsa ya sauke akanta jin bata motsa ba,bata kuma ce komai ba kamar bata wajen,sai ya lura da yadda jikinta yake rawa,da gasken tsoratar tayi sosai?,kafin ya sake cewa komai miss rebacca dake goye da jakarta ta iso wajen

"What's happening?,sir...kamar bata da lafiya sosai fa,ko jikin ne?" Ta fada tana qarasa kusa da maimunatu ta kama kafadarta tana tambayarta,sannan ta fara qoqarin dagota

"Sir....jikinta da zafi sosai,clinic sun rufe suma,saidai idan kun fita ku samu wani a waje a samo mata magani" ta fada cikin girmamawa bayan ta raka maimunatu cikin mota ta zaunar da ita

"Thank you" ya fada a taqaice,sannan ya taka zuwa motar ya shiga ya tada ita,saidai can deep inside him yana jin wani ba dadi a cikin ran nasa.

Tunda suka fara tafiya qwaqwqwaran motsi batayi ba cikin motar,sai ma sake takurewa da tayi saboda yadda uwar ac din daya balbalawa motar take barazanar hallakata,mugun sanyi takeji kamar me,ga na zazzabi ga na sanyin ac,abinda ya sake galabaitar da ita kenan,sanda take shirin ta bude murfin motar tana shirin fitowa wani zazzafan amai ya kubce mata,duk yadda taso kada tayishi cikin motar amma yaci qarfinta,take ta wanke jikinta zuwa qasan motar,sai ya zare seatbelt dinsa yana fitowa daga cikin motar.

Zagayowa yayi,yayi tsaye a inda take aman yanayin fuskarsa na sauyawa

"Why J,why?" Ya samu kansa da tuhumar kansa da kansa,yadda take ta yunqurin aman ya isa gaya maka tana jin ba dadi sosai a dukka jikinta,baisan kuma yadda zai taimaka mata ba,sai ya dan tura mata murfin motar ta sake dafeshi kuwa sosai taci gaba da kelaya amanta.

Ruwan roba ya fidda a motar ya miqa mata sanda ta gama aman,a galabaice ta karba,sai data kusa minti biyu sannan ta iya kuskure bakinta ta zubar,yasa hannunsa ya rufe motar,sannan ga zagaya seat dinsa ya sake shiga ya tashi motar a hankali yana yiwa mai gadi hon ya dage masa qofar suka sake ficewa daga gidan ba tare da ko ciki sun shiga ba.

Ganin yadda take rawar sanyi sai yasa hannu ya kashe ac din,tuqi yake a hankali yana tunanin wanne asibiti zai kaita?,daga qarshe dai ya samu kansa da yiwa kansa jagora zuwa asibitin da marigayiya shaheeda ke ganin likita.

Sun dan sha fama kafin a gano file din nata,idanunsa akan sunan dake jikin file din,sai ya janyeshi gefe yana gayawa receptionist din,su maida wannan a bude sabo da wani sunan daban.

"Me sunan da za'a zaka?" Ya tambayeshi

"Maimun.....maimun ja'afar" bakinsa ya subuce kawai yaji ya furta hakan,sai ya maida kansa ga wayarsa yana juya sunan a cikin ransa.

Bayan likita ya gama ganinta dole yasa aka bata daki saboda yadda take sake galabaita,tana ta aman,yasa kuma aka jona mata ruwa bayan ya mata allurai,cikin lokaci qanqani bacci ya dauketa saman gadon.

Idanunsa yadan kai kanta,fuskarta har tadan yi fayau akan ganin da yayi mata dazun,wani abu me kama da tausayinta ya tsarga masa,yana ganin kamar hon din daya danqara mata shi yayi silar ta'azzarar ciwon,don likitan ya fada,akwai abinda kamar ya razanata,dubansa yakai ga hijabin dake wuyanta tun dazun,wanda dashi akasha gwagwarmayar aman,akwai buqatar a cire mata shi,to amma bazai iya tabata ba,agogo ya kalla,baisan yaushe zaa sallamesu ba,uwa uba ma likitan yace sai yadda yaga jikin nata,sannan shi kansa drip din kadan kadan yake diga,bazaiyiwu yayita zama ba yabar duk aikin dake gabansa,don haka ya fidda wayarsa ya soma duba number anni.

Har zai kirata ya fasa,ya duba number baba tabawa,Allah ya taimaka kuwa ya ganta,ya cilla mata kiran,ya kuma gaya mata driver ya daukota yanzu ya kawota asibitin,dai dai lokacin suna tare da anni tana hada mata kwadon zogale,sai ta dubeta

"Manya ne ya kirani,wai Doma,doma hospital" cikin mamaki anni ta kalleta

"Waye kuma ba lafiya?"

"Baice komai ba haj anni,kinsan hali dai"

"Ko shine?" Yadda annin tayi maganar cikin damuwa ma sai yadan baiwa baba tabawa dariya

"Kai haba dai,shi dinne bashi da lafiya zai kirani?,kamar ma kin manta halin mutuminki?,shi da ko sanda yana matashinsa ma saidai yayi ciwonsa a daki yagama ba wanda ya sani,saidai idan anga fuskarsa ta sauya?" Kai anni ta gyada,ta tuna mata kam abinda ta sha'afa

"Kamomin shi a wayar taki" bata musa ba ta koma kiran nass,dab da zata tsinke ya daga,kafin yace komai sallamar anni ta cika kunnansa

"Ka kira tabawa kace tazo asibiti,sannan kuma bakayi cikakken bayani ba,waye ne ba lafiya?" Shuru ya danyi kadan,yana rarraba hankalinsa kan sunan da zaya kirayeta dashi,a hankali ya furta.......

Next Chapter
Leave a comment

Post
Comments
11/24/22, 23:25 - Buhainat: Chapter 41
Shafi na arba'in

41


"Maimoon"
"Maimoon kuma?,maimunatu?" Anni ta fadi da yadda tafi ganewa a kirata

"Yeah eh" ya amsa mata a tausashe murya can qasa,don har ya qosa annin ta ajjiye waya,don yasan halinta yanzun zaa iya turkeshi da tambayoyin da wala'slla bashi da amsarsu

"Mene ya sameta?" Ta fadi cikin nuna damuwa

"I can't say" ya amsa mata a taqaice yana murza goshinsa da yatsun hannunsa

"Kaii,kayi ta kanka malam,idan zakamin fillanci ko hausa to kayi tun wuri bai qure maka ba"

"Ya salam" ya furta can qasan maqoshinsa yadda ba zata jishi ba sannan ya sake cewa

"Fever.....zazzabi da amai" ya sauya harshe don yasan yanzu zata kuma complain

"Ikon Allah,gata nan zuwa to" ta fada tana sauke wayar,wanda tuni ja'afar din ya rigata kashe wayar.

"Kodai qaruwa muka samu ne haj anni?" Tabawa ta fada cikin zumudi,fuskarta dauke taf da murmushi,tana latse wayar ta tabe baki sannan ta miqawa tabawa tana cewa

"Banjin haka gaskiya,jikina bai bani ba,amma.....koma meye ki shirya ki wuce,inason ki sakamin ido akan duk abinda yake faruwa,inason na sanin koma meye,sun doshi shekara,ya kamata zuwa yanzu musan me ake ciki,akwai ci gaba koko babu shi"

"To in sha Allahu" tabawa ta fada tana yunqurawa ta wuce dakinta ta shirya,driver ya dauketa,kafin ta wuce sai data biya wajen amma ta gaya mata abinda ke faruwan,irin tunanin da ya darsu a ranta shine ya darsu a ran amman,farinciki sosai taji ya.mamayeta,tana qaunar ja'afar can qasan ranta,tana kuma qaunar duk wani abu daya danganceshi,tana boyewa ne saboda 'yan uwansa da kuma idanun mutane,tana da kara da alkunya irin wanda asalin bafulatanin mutum ke dashi.

Sanda ta isa asibitin suna gaisawa ya fice a dakin,sai daya dan kalleta ta gefan idanu kafin fitar tashi,bacci take lakadan,sai ya taka a hankali yabar dakin,yana kiran waya yaji an kawo masa motar da yace a kawo masan.

Sai da baba tabawa ta fidda mata hijabin jikin nata ta sake gyara mata kwanciya yadda zataji dadi kana ta zauna dab da ita kamar me gadinta,itama tana cikin masoya maimunatu,wadda Allah ya dora mata qaunar yarinyar har cikin ranta.

Bayan la'asar kadan ya shiga gidan,main parlor din babu kowa,hakanan shuru yake sai na'urori daketa aikinsu,sama ya wuce kai tsaye,ya sanya key ya bude qofar dakin nasa kana ya tura yana furzar da iska daga bakinsa,da daya da daya yake duban dakin,yau dakin ya masa shirgi da yawa,baa kintse yake yadda yakeso ba,duk sai yaji ransa ya jagule,mutum ne shi da baya qaunar datti ko qanqani,don haka ya zare tie dinsa ya kuma soma fidda suit din jikinsa,ya zamana daga shi sai farar qal din singlet dinsa ta zallar auduga dake fidda wani sihirtaccen qamshi,a hankali ya fara picking duk abubuwan dake zube a qasa, yana kintsa dakin.

Sam wannan ba rayuwarsa bace,dole ya koyeta,baya son kowa ya shigar masa daki,sai daya dauki good five thirty minutes sannan ya samu dakin ya masa yadda yakeso,bawai don ya gama qalqaleshi yadda ya kamata ba,yadda jikinsa yayi masa week yasa ya zame a gefan gadonsa ya kwanta,yana runtse idanunsa yana miqewa sambal,wanda tsahonsa gaba daya ya kusa cinye tsahon gadon,abinda zai tabbatar maka da baiwar tsahon da yake da ita kenan.

Yadda shuru ya ratsa dakin haka yaji kwanyarsa ta dauki shurun,a hankali abinda ya faru dazun ya gifta cikin idanunsa,yadda ta tsorata sosai sanda hon dinsa yakai kunnuwanta,idanunta suka fidda wani kalar tsoro da ya sanyata durqushewa a wajen

"Astagfirullah" ya fada yana maida folding hannayensa a qirjinsa,yana jin ba dadi har cikin ransa,tausayinta ya ratsashi,a sannan baisan zazzabi ne a tare da ita ba,da bai matsa mata hon din ba.

Tun asalinsa mutum ne mai tausayi da kuma son kyautatawa kowa,duk da zallar miskilancinsa ya boye hakan,mutane da dama suna masa kallon bahagon mutum mai zallar rashin son jama'a da mugun hali,musamman wadanda basu mu'amalanceshi na tsahon lokaci ba.

Haka yayiya kokawa da kwanyarsa da kuma tarin tunane tunanen da take saqa masa,tsahon wasu mintuna kafin a sannu a hankali bacci yazo yayi awon gaba dashi.

A hankali take takowa zuwa uwar dakin nasa,gabanta yana dukan uku uku,tana kuma warning daya yanka mata sati guda baya daya wuce,saidai zuciyarta ta kasa jurewa,bata samu komai daga gareshi ba sannan kuma ace ganinsa yana gagararta alhalin suna zaune a gida daya,amma idan batayi da gaske ba sai ta shafe sati bata sanyashi a idanunta ba.

Da wata nutsuwa data aro ta murza handle din sannan ta tura qofar dakin,idanunta ya sauka a kanshi sanda yake baccinsa very calmly kamar babu wani abu da yake damunsa cikin duniya,idanunta a kansa ba tare data iya daukewa ba taci gaba da takawa,duk takun da zatayi zuwa inda yake bugun zuciyarta ne yake daduwa,yayin da fuskarsan nan dake dauke da wani sassanyan kyau da kuma kwarjini na musamman wanda bai gushe ba koda ckin bacci ne take sake kusantowa gareta.

Dab dashi ta isa,sannan ta zauna gefan qafarsa a hankali idanunta na sauka kan sambala sambalan qafafunsa,kai kace baya taka qasa dash,fari qal sai lallausan gashin da ya yiwa yatsunsa ado,ya kuma kwanta luf a singalalin qafarsa,hannu takai kamar zata shafo sai kuma ta janye hannunta da sauri,ta maida dubanta ga fuskarsa,zaman da tayi yadan kare mata fuskar tasa,don haka sai ta sake miqewa tayi tsaye a kansa tana morewa kallonsa,kallon data tabbatar inda idanunsa biyu bata isa ta yishi ba,wani irin sonsa ke kwarara a ranta,takai hannuna hankali zata shafi kwantaccen sajen dake gefe da gefan fuskarsa

"Don't touch me" ya furta cikin kaushi cikin muryar mutumin dake bacci,sosai ta tsorata,ta janye hannunta da sauri tana fiddo idanu waje,dai dai lokacin da shima ya fara bude idanun nasa da kadan da kadan har ya zubesu fes kan fuskar unaisa.

Kafeta yayi da idanu wani zallar bacin rai yana saukar masa,wannan shine karo na kusan biyar da take masa hakan,kamar bazai motsa ba sai daga bisani ya miqe daga kwanciyar a hankali,cikin zuciyarsa yana karanto addu'a,saman gadon ya zauna sosai bayan ya zubo da qafafunsa qasan gadon

"Me kikemin a daki?" Ya tambayeta kai tsaye,sosai tayi qoqarin sanyawa kanta dakiya,duk da yadda jiki da kuma muryarta suke dan shaking kadan

"Zuwa nayi na duba dawowarka,ga abinci can a gama" shuru yayi na second uku

"How many times nake gaya miki ba kowanne jagwalgwalon masu aiki da sunan abinci nake ci ba?,take note please,kada ki sake shigomin daki ba tare da izini na ba" ranta ya sosu kamar kullum,ta kuma kasa hadiyewa

"Amma dai kasan ni matarka ce ko?,sannan kuma ko yaya ne ina da hakki a kanka" qas yayi da kansa,murmushi nason kubce masa amma kuma ya hana kansa faruwar hakan,don baya son raini,daga bisani ya kuma daga kan nasa ya dubeta kai tsaye

"I know,i already know, that's why na baki zabi ai tuntuni,a mutunce zan baki takardarki ki qara wuta,i assure you zaki samu dai dai dake" wani qullutun baqinciki ne ya tokare mata wuya,wanda ta kasa riqeshi,sai ta saki kuka kawai ta juya gudu gudu sauri sauri tabar dakin,yayin da shi kuma ya bi bayanta da wani kallo da tsarabar tsaki,kana ya miqe a hankali yana sanya hannunsa cikin sumarsa yana maidata baya saboda yadda ta cakude,bawai bashi da feelings ba,ko kuma feelings dinsa ya mutu ba,aah.....yana nan a yadda yake,lafiyayyen namiji,wanda wannan dalilin ya sanya ko a baya ya riga jabir aure,amma dai for now bayajin komai akan kowacce diya mace,musamman unaisar da sai a yanzu yake gano fuskarta ranar da qaddara ta fara hadasu da ita a wani club sanda yake aviation school,zuwansa club na farko kenan a rayuwarsa,shima baisan can zasuje ba,daga wajen cin abinci suke shida abokinsa kuma abokin karatunsa muslim,yace yazo ya rakashi wajen wani abokinsa,as'ad zubair,dan gida wani babbban qusan gwamnati a nijeria,acan ya gansu tare da ita,wanda shikam kallo daya ya yiwa fuskarta ya dauke kai,abinda yasa ya kasa shaida fuskarta kenan da wurwuri sai daga baya,duk da ba shigar banza ko wani abu yaga tana sha ba amma abun ya tsaye masa a rai,don yana da tabbacin cikakkiyar mace mai cikakkiyar kunya ilimin addini da tarbiyya ba zaa sameta a wannan wajen ba.

Ruwa mai dumi sosai ya sakarwa kansa,bayan ya gama yayi brush ya feshe bakinsa da turaren mouth mint mai qamshin strawberry,ya dauki babban towel yana tsane jikinsa daya jiqe da lema sosai saboda yawaj gargasar da yake da ita saman lafiyayyar fatarsa.

Cikin wasu lafiyayyun kaftan ya shirya kansa farare qal,duk motsin da zaiyi jikinsa na fidda wani irin qamshi mai taushi,ba kasafai ya fiya sanya hula ba,don haka ya riqeta a hannu bayan ya laluba key din motar da yake son fita da ita,ya kalli agogo yana duba lokaci,sai ya sanya wayoyinsa a aljihu bayan yayi kiran daya daga cikin drivers dinsa yaji yana kusa don qyuyar tuqi yakeji,har yanzu kasalar bata sakeshi ba,yayo waje cikin takunsan nan dake dauke da wani salo na dabam da zaka tsammaci tsabar jin kai ne ko izza.

Sai da suka tsaya sukayi sallar magariba da isha'i a hanya sannan suka qarasa a asibitin,a sannan har yayi waya an musu take away na abinci awa daya kafin ya isa,qarfe takwas da wasu motsi,driver yayi parking motar tasu,ya balle murfin motar ya ficw cikin nutsuwa,iskar asibitin tana kadashi,tana kuma tuna masa wasu abubuwa sa suka shude cikin rayuwarsa.

Babu yawan jama'a sosai a asibitin,hakan ya bashi damar isa qofar dakin kai tsaye,tun bai shiga ba ya tabbatar akwai mutane a ciki,sai ya tura qofan a nutse da sallama.

su hudu ne 'yammatan gidan nasu,sai baba tabawa ta biyar dinsu,sallamarsa ta sanya su duka yin dif,yayin da wuta ta daukewa maimunatu dake zaune ta jingine bayanta da filo tana sauraren hirar tasu,sanye take da doguwar rigar atamfa wadda ta zauna mata sosai a madaidaicin jikinta,ta kuma fidda mata shape dinta saboda yadda breast curve din aka yishi cif da cif,ya kuma zauna mata sosai,dogon hannu aka yiwa dinkin saidai an yayyanka shi ya koma kamar spaghetti sleeve,tayi tayi sanda ta sanya kayan a bata baby hijab dinta data saba sakawa amma fa'iza tace a'ah,su da su waye a dakin da sai ta sanya hijab,baba tabawa ma tace

"Ki barshi kawai maimunatu,kada kije ya dameki ma ya gotar miki da canola din" kasancewar sun cire mata ruwan da ake qara matan don ta huta.

A ladabce suka gaidashi bayan baba tabawa ta miqe ta bashi kujerar da take kai ta matsar da ita gaban gadon maimunatu,maimunatun da tunda ya shigo tayi qas da kanta,ko sau daya bata dago ba,idanunta nakan Canola din hannunta.

Takalmanta baba tabawa ta jawo tana sanyawa,dai dai sanda anni ke fitowa daga bandaki

"Yaushe ka shigo?" Da hannu ya nuna mata yanzu yanzu

"Zamu wuce,dama shirin tafiya muke"

"Akwai driver?" Ya tambaya a taqaice da muryarsan nan me cike da ginshira

"A'ah a'ah,salma ta tuqomu,gani nayi tafiyar babu yawa" cikin salma ya duri ruwa,ita anni me yasa ba'a sirri da ita?,kawai tace masa eh driver dinne,na meye saita bashi labari?.

Qarasa dibibicewa tayi sanda ya watsa mata wani kallo na gargadin kinyi na farko kinyi na qarshe,baa baau mota su tuqa a gidan,saidai idan kinyi aure mijinki ya baki,suk inda zasu driver ke kaisu

Da daya da daya suka fice a dakin suna yima maimunatu sallama tare da cewa zai gobe,murya can qasa take amsa musu,gabanta na wani irin faduwa,tana jin kamar tabi bayansu sanda suka fita,dakin ya rage daga ita saishi daya sanya waya a gaba yana dannawa
11/24/22, 23:25 - Buhainat: GURBIN IDO....
View: 262
Words: 1.7K
GURBIN IDO
Chapter 42
Shafi na arba'in da daya
42
'"Ina yini" sassanyar muryarta da 'yammatanci suka fara cikata a maimakon quruciya ta daki kunnensa,sai ya zame wayar daga fuskarsa a hankali,karon farko da yaji muryarta a nutse kuma a wajen da babu kowa saisu,a kanta idanunsa suka sauka,kanta yana qasa bata ko qwaqwqwaran motsi,sai yaga kamar a tsorace take dashi har yanzun
"Lafiya,ya jikin?" Ya amsata a taqaice
"Da saugi" ta amsa masa tana jin yadda muryarsan ta saka mata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login