Showing 42001 words to 45000 words out of 194226 words
Duka su ukun da sallama suka shiga falon anni,a lokacin ta nutsu tana amsa wayar jabir,sun fahimci waya take mai muhimmanci harda maimunatu dake baquwar gidan,sai suka samu waje kowa ya zauna,laila ce ta qarasa gaban tv ta dauka remote kafin takai ga zama ta canza channel sannan ta dawo itama ta sama waje ta zauna kamar su.
"Shikenan......amma ka zama cikin shirin kai jabiru,ba lallai sai ka sanar masa ba,ka rabu dashi kawai kaci gaba da sabgarka.....toh....Allah ya bamu alkhairi" shine maganar qarshe da annin tayi tana sauke wayar daga kunnenta tare da bin wayar da kallo,kana ta dauke idanunta tana maidowa kansu.
"Sannu tabawa,kun gama kenan?" Ta fadi tana murmushin jin dadin yadda taga maimunatun fuskarta ta sake fitowa fayau,sannan kuma tayi tarwai
"Eh hajiya anni,aikinma bamai yawa bane"
"Kedai sannunki da qoqari" anni ta fada tana sake kallon maimunatu
"Me zakici maimunatu?" Kanta a qasa ta girgiza kai,don har yanzu cikinta a cushe yake,tana jin daga nan har gobe da hantsi zata iya zama babu komai a cikin nata
"Bana jin yunwa anni"
"Badai a gidan nan ba,ke lailaa,shiga madafi,ki cewa lami ta zubo tuwon nan da aishatu ta kawo,cin mutum biyu ta kawo mana" ambatar sunan da anni tayi sai taji ya tsarga mata har cikin ranta,a duk sanda aka kirayi me irin sunan,babu abinda yake tuna mata face mahaifiyarta.
Sanda laila ta kawo tuwon zama tayi zataci,amma anni tace batasan wannan zance ba,ta koma can wajen uwarta taci
"Wallahi anni ke kadai ta yiwa tuwon nan duk gidan nan,ko abbi babu shi a ciki"
"A nan kuka fi kauri,wajen bada gudunmawar ci,da wani cikinku nace yayimin babu me katabus" ita dai laila bata damu ba,ta saka hannu a kwanon maimunatu ta fara cin abincinta tana sakowa maimunatu hira,abinda yasa anni fa sake qyale lailan kenan,saboda hakan da tayi tasan zai bawa maimunatu damar sakewa.
Ta kuwa dan sake din,tana tsakurar abincin,iyakarta da hirar laila uhmm ko um um,sai kuma murmushi wani lokacin,duka anni tana ankare da ita,tausayin maimunatu take ji sosai cikin ranta,gefe guda kuma tana sake shiga ranta,komai nata mai sanyi ne,cike kuma da nutsuwa a cikinsa.
A hankali a hankali 'yan mata matan gidan suka fara shigowa da daya da daya kamar yadda suke yawancin darare,suna shigowa anni su kuma dade wajenta,don ma fadanta yakan sanya wani lokaci suqi zama,amma idan suka sameta akan laushinta har kwana sukanyi.
Duk wadda ta shigo sai tabi maimunatu da kallo,wasu suce
"Ma sha Allah,anni baquwa mukayi?,ina kika samu balarabiya?"
"Yar uwarku ce" amsar da take basu kenan taci gaba da harkar gabanta,cikin girmamawa maimunatun take gaida duk wanda ga shigo,har suka dan cika a falon,sunata hirarrakinsu tana jinsu,koda sun sakota saidai tayi musu murmushi kawai,abinda ta lura dashi,su din mutane ne masu mutunci da girmama dan adam,hakanan suna da sauqin kai,duk da adan taqin zaman nasu ta fuskanci wani yafi wani sauqin kai a cikinsu,dama haka halittarmu take,kowa da dabi'a da kuma yanayin da Allah yayi masa.
Ranan kusan a nan duka suka sukaci abincin dare,maimunatu nata kallon banbancin rayuwa da kuma gaskiyar karin maganar nan ta bahaushe da yake cewa 'Allah daya gari bam bam' kowa yakanje ya diba zabinsa ne da abinda yakeson ci,ya kuma buda ma'ajiyar abunsha ya dauka kalar lemo da ruwan da yakeso,wasunsu kuma su sanya ma'aikatan gidan su kawo musu,babu kyara babu tsangwama,akwai alamun hadin kai da zaman lafiya bakin gwargwado tsakaninsu.
Tabawa anni data jima da tashi a falon ta aiko kan maimunatu ta tafi ta kwanta,kusan dama ta gaji da zaman,don bata saba hira da mutane ba,duk sai zaman ya gundureta,amma ta rasa ta yadda zata tashi ta wuce dakin,don haka tabawa na idar da saqon ta miqe
"Balenjam" ta fada da tattausar muryarta,sai kuma ta danyi sak ganin yadda suka zubo mata idanu
"Sai da safenku" ta fada da harshen hausa,laila ce ta saki murmushi
"Allah ya tashemu lafiya fillo" murmushin tayi itama sannan ta juya zuwa ciki,tana mamakin yadda suna fulani amma basu damu da yin yaren a tsakaninsu ba,don tunda tazo da hausa taji suna hira har yanzun data tashi,wala'alla shi yasa suka bita da kallo sanda ta yaara musu.
"Gaskiya yarinyar nan kyakkyawa ce,tana da hankali da alama" salma data miqe dauke da.plate din data gama shan farfesun kayan ciki ta fada,dubanta laila tayi
"Sosai,tana da nutsuwa sosai,tana burgeni"
"Ni kaina haka" fa'iza ta amsa musu,daga haka laila bata ce musu komai ba,don tasan cewa ba wanda yasan komai kan zuwan maimunatu gidan,bai kuma kamata ita din ta fara cewa komai ba.
Sanda ta shiga dakin idanunta sun fara mata nauyi saboda bacci,qullin kayanta data hana tabawa dauka daxu ta janyo ta tasa kanta dasu,bayan tayi kwanciyarta qasan tiles ba tare da tayi gigin hawa gadon ba,babu jimawa wani nannauyan bacci mai dadi yayi awon gaba da ita.
*********Kyakkyawar macace wadda shekarunta na haihuwa suka kusa arba'in da bakwai,kana mata kallon farko zakasan cewa sanda take da qananun shekaru ba qaramin kasa maza dr marwan yayi a kanta ba,tana da siffa me kyau ko a yanzun ma,fara ce sosai kamar yadda akasan asalin farin bafullace,hakanan bata da tsaho can can,kamar yadda ba zaka kirata gajeriya ba,saidai alamun tsafta da qamshi da suka samu wajen zama a tattare da ita sun nuna kansu muraran.
Cikin nutsuwa kamewa da kuma sanin kimar kai take shigowa bangaren surukar tata,sanye cikin atamfa england me ruwan ganye,dinkin riga da plain zani,bayanta masu aikin gidan ne wadanda ke qarqashin bangarenta masu kula da bangaren kitchen dauke da trays,sai kuma salma dake riqe da wani warmer me kyau guda daya a hannunta,a shirye take tsaf da alama wani wajen zata wuce,tana daga gefan mahaifiyarta(Aishatu amma) suna magana ita da salma din.
Dakatawa masu aikin sukayi har zuwa sanda amma da salma sukayi sallama cikin qawataccen falon annin,wanda sam baiyi kama da falon tsohuwa ba,dai dai lokacin da DR marwan ke zaune gaban mahaifiyar tasa yana gaisheta,shima sanye da wata dakakkiyar shadda fara qal,kamar kusan ko yaushe kansa nannade da tattausan farin rawani na zallar auduga,da alama shima din fita zaiyi.
Jinin sarauta ce ita amma sam ba zaka dauka haka ba,saboda sauqin kai da take dashi da kuma sanyin hali,Gefan anni amma ta qarasa tana zama a qasa kamar yadda ta samu me gidanta,wannan din wata dabi'a ce tasu ita da dr marwan tun suna da jajayen sahunsu,dabi'ar data maida aishatu tauraruwa a zuciyar anni cikin kafatanin surukanta,ya sanya kuma wasu daga cikinsu suke kishin hakan,duk kuwa da cewa anni tana matuqar qoqarin boye hakan,saidai ko daga yadda ja'afar keda matsayi a wajen annin kadai ya isa ya fallasa maka wace aishatu a zuciyarta.
Sai data fara gaida anni sannan ta waiwaya ga me gidanta shima ta gaidashi,duk da cewa sun gaisa a ciki kafin ya fito,ya amsa mata cikin kulawa kamar ko yaushe,salma ta matsa kadan ta gaida dr sannan ta maida dubanta ga anni,murya qasa qasa tace
"Ranki ya dade hajjaju anni" wani kallo ta jefi salman dashi,tasan duk me salman take wa
"Allah ya baki haquri anni ina kwana"
"Lafiya sumul natashi 'yar nema,duk take takeki kar nake kallonki,gwara kiyi ta kanki 'yar nan" wuri wuri salma tayi,da alama tonin silili anni keson yi mata a gaban wadanda take gudun yin maganar a gabansu,bata gama tunanin ba kuwa maganar annin tayi mata saukar aradu
"Wai marwanu.....ita wannan kazar mayun har yanzu bata isa ayi maganar aurenta bane?" Ji salma tayi kamar qasa ta tsage ta shige,maganar da tayin tana nuna kuma yasa dr maida idanunsa kan salma
"Me ya faru anni?" Gyara zamanta tayi
"Yo ni na gaji da hada kafada dasu idan ku baku gaji ba,ina buqatar ganin wasu 'yan dagwai dagwai din,ko ka aurar dasu ko ka auro,zuri'a nake da buqatar gani me tarin yawa......yawwa......duk gidan nan billhillazi babu yaron da bai isa aure ba,ramatu ce kawai za'a iya dagawa qafa,amma ace babu me aure?,baga mazan ba baga matan ba?,to idan baqinjini garesu zan buga gangar bada sadakarsu mazansu da matansu" kafin ta diga aya salma ta kwashi takalmanta a hannu tayi waje,don taga alama yau annin me manya manya take barota.
"Ayi haquri anni" abinda dr yake fada kenan,don yasan da biyu take wannan fadan,tana tunanin kamar shike qin bada auren yaran nasa,bayan kuma yaran da kansu suke sha'awar karatu shi yasa ya qyale kowacce da zabinsa,uwa uba ma duka duka salma hafsat da laila ne a makarantun gaba da secondary,samma hafsa nadiya fa'iza da khadija sune 'yan candyn bana,zahra'u na ss one,sai rahama dake j.s,mazan kuwa dukkansu ba wanda ya gama jami'a banda ja'afar da haisam,sai Mahmoud dake ajin qarshe
"Yanzu fisabillahi....salma zaman me take?,shi karatun da take cewa akayi bashi yuwuwa ta qarasashi cikin dakinta?"
"Ta fiddo wanda takeso anni,ai baza'a qi aurar da ita ba"
"To ta fitar kuma shi take ta raragefan gaya maka kai da uwar tata" qas amma tayi da kanta,wal'alla ta gayawa anni sunyi zancan da ita kenan
"To ba damuwa anni,zanyi magana da umar(qaninsa kenan me bi masa),saita turashi can yaje ya gaidasu"
"To ba laifi" annin ta fada tana sassautan fadan,dai dai sanda salma tayi dake labe daga waje tayi tsallen dadi,anni tasu,anni ta wajensu,ayi tsiya ayi dadi,ga tsiya ga aiki,lallai yau dole ta yiwa annin wani tagomashi,saita juya cikin jin dadi zuwa ma'ajiyar motocin gidan,inda driver yake jiranta,ranta fari qal.
Daga can falo kuwa duban dr anni ta sakeyi
"Shi kuma jabiru da ja'afar fa?,da aka barsu suke zaune a wata uwa duniya,ga wancan qaton tuzurun haisam?" Miqewa amma tayi saboda kara da yakana irin tata,tana ganin ya kamata ta basu waje suyi maganrsu sosai
"Ina kuma zuwa?" Anni ta fada tana binta da kallo
"Zan duba meye baku dashi a kitchen"
"Idan kin shiga,kiyi waya can gidansu marigayiya,ya kamata a dawo da amna,jimawar da tayi a can wannan karon tayi yawa"
"To anni" ta amsa mata cikin girmamawa tayi ciki,dawo da dubanta tayi ga dr marwan tana tattara hankalinta sosai a kansa sanda ya fara mata bayani
"Maganar da nakeso muyi kenan.....a jiya da kika sameni da baqi kamar yadda na gaya miki ministern ilimi ne na qasa ya kawomin ziyara,bayan mun gama tattaunawa kan batutuwa irin namu,sai kuma ya jefomin maganar diyarsa unaisa,ya yimin tayin aurenta da ja'afar kamar sanda ya taba yimin a baya ban karba ba,lokacin ja'afar din yana aviation school,magana kuma tayi nisa tsakaninsa da marigayiya,to a yanzun inajin nauyi na sake qin karba din,kada yaga kamar banason hada zuri'a ne dashi ko kuma wani abu makamancin haka,na amsa masa ne duba da cewa gaba dayanmu dama muna laluben masa abokiyar zaman da zata iya zama dashi bisa juriya da kuma haquri kan sauyin hali da dabi'arsa,na kuma tabbatar kema idan kikaji hakan zaki farinciki,tunda burinmu kenan gaba daya"
Shuru anni tayi tana duban dr marwan,bawai don yayi kuskure ko kuma maganganunsa ba'a kan hanya suke ba,a'a......saidai tana tunanin wace unaisa?,akwai yiwuwar samun dacewar zama tsakaninta da ja'afar din?,uwa uba kuma ga batun maimunatu da take tafe dashi,sai takega kamar akwai matsala.
_To masu karatu,muje zuwa,shin al'amarin zai yiwu?,duk da bamusan wacece unaisa ba,abbi baisan wace maimunatu ba,kamar yadda wanda aketa abun a kansa baisan wainar da ake toyawa bama_
10/20/22, 08:13 - Buhainat: *17*
"Ni ai tuni na samarwa ja'afar matar aure"anni ta fada kanta tsaye,ba tare data jira komai ba ta dora
"Ire irensu unaisa ba daya ba ba biyu ba......amma sun kasa jumuri da juriya da kuma samar mana da abinda mukeso" anni ta fada cikin cikakkiyar nutsuwa da bawa zancan muhimmanci,har yanzu ita dr marwan yake kalla,ganin haka ya sanyata ta dora
"Eh,hakan yasa na sauya shawara bisa hasashen ramatu" nan ta ware masa komai kan hasashen yuuma,da yadda ta gamsu da maganarta,da kuma yadda ya zamana tashin farko maimunatu ce ta fara zuwa mata zuciya da ranta,mizani da ma'aunai masu yawa da maimunatun ta hau taga kuma tabbas ta dave da matsayin matar ja'afar.
Cikin nuna gamsuwa dr marwan yake gyada kai,dukka hasashen annin dama abinda ta aikata yayi dai dai da nasa ra'ayin
"Saidai duk wanda keson naka yakeson hada jini da kai ba qaramin masoyinki bane,sa'an nan wannan ba shine karon farko da ya nuna sha'awarsa kan hakan ba,to bai kamata mu watsa masa qasa a ido ba,kuma namiji mijin mace hudu ne ai,fatanmu shine Allah yasa a dace,yasa qarshen matsalar kenan" kai abbi ya gyada
"Gaskiya ne anni,Allah ya saka da alkhairi,ya qara girma"
"Banga abun godiya ba marwan,wajibi na nayi,babu abinda bazanyi ba saboda rayuwar ahalina matuqar bai sabawa shari'a ba,yanzu abu daya ya rage,ja'afar ya dawo cikinmu,koda zai koma sai komai ya dai daita,don ban gamsu mu bashi yaran mutane ya tafi dasu har wata uwa duniya ba"
"Gaskiya ne anni,hakan yayi"
"Shikenan,zan sa a kiramin jabirun ko zuwa anjima ne".
Dai dai lokacin maimunatu ke fitowa daga dakinta zuwa falon,tayi wankanta ta shirya tsaf bayan baba tabawa ta leqa da safen sun gaisa,ta kuma umarceta da yin wankan,mamaki ne yaketa kasheta,duka duka yaushe tayi wankan jiya?awa nawa ne a tsakani?,duk da hakan bata musa ba tayi kamar yadda baba tabawa ta umarceta,ta kuma shirya kamar jiya,saidai yau din haskenta ya sake fitowa fiye da jiya.
Da murmushi anni ke kallonta sanda take isowa wajen,daga nesa dasu ta zube har qasa tana gaidasu,abbi baisan wace ba,amma ya amsa mata cikin kulawa kafin ya maida kansa ga labaran qasa da ake gabatarwa a tashar NTA da ya dauki hankalinsa.
Cikin kulawa anni itama ta amsa
"Ya kwanan baqunta?" Ta tambayeta cikin salon jan mutum a jiki da kuma son ya sake,murmushi kawai tayi mata tana sad da kanta qasa
"Kinsan kitchen ai,leqa kice aishatu tazo,ta taho da qarin plates"
"Toh" maimunatun ta amsa tana miqewa a nutse tayi kitchen din.
Kafin ta qarasa tadan dinga jiyo hirarraki da alama akwai mutane a kitchen din,ta saka kanta a hankali bakinta dauke da sallama,abinda yaja hankalin amma dake tsaye suna magana da baaba tabawa,hannunta dauke da wata roba tana duba rubutun jiki.
Waiwayowa tayi,sai suka hada idanu da maimunatu,dan zubawa maimunatun idanu tayi,tana mamakin jin irin muryar data sani daga gareta,amma kuma batasan fuskar ba,bata taba ganinta ba.
Gaisuwar da take mata ta amsa cikin kulawa,sannan ta maida dubanta ga robar hannun nata,saidai kuma hankalinta naga muryar tata sanda take gayawa baaba tabawa anni ce ta aikota ta kira wata,kasa fadar sunan tayi kai tsaye,saboda suna ne dake da girma da kima a idanunta
"Yanzun bansan wa anni ke nema cikin madafa ba,kin kuma kasa fadi,hala sunan yana da nauyi a wajenki maimunatu" murmushi tayi a takure gami da jin nauyinsu su duka,musamman amma da hakanan taji tayi mata kwarjini.
Murmushi amma tayi
"Falon zan koma,muje naji wanda ake kira....tabawa qarasa aikinki,idan kin gama ki sameni keda bara'atu a sassana,zaku yimin gyaran wardrobe"
"To in sha Allah" haka suka jero,amma tana gaba maimunatu tana binta a baya,har suka qaraso falon
"Baquwar taki ta kasa faden wanda kk nema anni" amma ta fada tana zama daura da dr cikin shirin serving dinsu abincin data kawo musun,murmushi anni tayi
"Ke na aika ta kiramin,hala kasa fadin sunan tayi" gyada kai amma tayi
"Eh wallahi,anni ina kika samo mana bafullatar usul"
"Daga garinsu ramatu,gata nan don Allah aishatu,inaso a kulamin da ita da kyau,so nake ta zama 'yar gida tamkar su salma"
"In sha Allah"amma ta fada tana dan sake kallon maimunatu kadan,wadda kanta yake qasa har lokacin,sai kuma ta miqe,don a takure take,ba zata iya zama cikinsu ba.
Anni na shirin tsaidata don taci abinci a cikinsu tabawa ta fito ta kirayeta zuwa kitchen,abinda yasa anni ta qyalesu,ta maida kanta ga surukuwarta da danta.
Cikin yanayi na shaquwa da kuma fahimtar juna suke cin abincin,suna kuma tattaunawa kan lamuran rayuwa wanda suka shafesu,amma na gefe ba tare data sanya musu baki ba,wannan daha daga cikin halayyarta kenan.
Gab da zasu gama akayi sallama cikin falon,kyakkyawan matashine,yana da white skin hakanan giant ne shi sosai,kamanninsa na zahiri shi da dr Marwan sun bayyana.
Yayi dressing very neat cike da tsafta kamun kai nutsuwa gami da zallar ilimi,hannunsa daya riqe da lab coat dake bayyana cewa shi din tabbas likita ne,a nutsensa sannan cikin girmamawa ya tube takalman qafarsa ya qaraso falon,ya duqa ya fara gaida anni sannan dr sai amma.
Kansa yadan shafa kadan da yasha saisaye me kyau
"Anni,zan samu sauran abinci kuwa?" Kai tsaye anni ta kalla amma
"Bakuyi girki ba yau aishatu?"
"Munyi anni,sanda zan fito ma na leqasu suna gab da gamawa,zuwa yanzu nasan sun gama" qaramin tsaki taja
"Shine wannan qaton gardin zaizo ya sani gaba da tambayar abinci?....kaga idan zaka wuce gwara ka wuce,kuci a waje kamar yadda kuka saba,tunda haka kuka zabarwa kanku" dama yasan za'a rina,tsautsayi yasa yayi mata maganar,tun kafin ta tafi adamawa dama taketa rikici dasu,aure kawai takeso wai kowannensu yayi,wani lokaci sai yaji gwara ma