Showing 18001 words to 21000 words out of 56867 words

Chapter 7 - YAR ZAMAN WANKA BOOK 3

27 Sep 2024

3836

ya zamana kamar goyo ya yi, sai ya zama kamar ƙadangare a jikin bango. Ƙafafunsa a sake amma kuma sai ya maƙalƙalo wuyan Imran, Imran kuwa tsabar ruɗewa ma bai san Shek ya ɗane bayansa ba shi dai kawai ya ji wuyansa a maƙalƙale sai ya yi tunanin micijin ne, aikuwa ƙafa me na ci ban baki ba, a haka yake ta sheƙa uban gudu a tsakar gidan.

Inna da ke can jikin bango tana hango su dariya kuwa cikinta kamar ya yi ciwo. Suna cikin gudun Imran ya kalli bayansa da wutsiyar ido, aikuwa ya hango Hassan na binsu hakan ne ya ankarar da shi cewar ba Hassan bane a wuyansa hannu ya kai bayansa aikuwa ya taɓo Shek da ke manne da shi kamar cingam haushi ne ya turnuƙe shi, yana mamakin ya aka yi ma bai ji nauyi ba sai ya danganta hakan da ruɗanin da yake ciki.

Wata mugunta ya yiwa Shek wani uban wujijjiga Shek Imran ɗin ya yi sai kuwa ga Shek yashe a ƙasa ya je da reran, miciji da je binsu da gudu yana zuwa sai ya bi ta kan ruwan cikin Shek, gabaɗaya Shek numfashinsa ya ɗauke lokacin da micijin ya bi ta kansa, bai ankara ba ya ji saukar wani fitsarin daga jikinsa. Imran kuwa wani tsalle ya yi ya koma gefe, micijin kamar an ce bi Inna kawai sai ya yi hanyar lungun murhu a mugun guje yana haɗawa da tsalle.

"Inna ce a nan lungun me maka ZAMAN WANKA" Cewar Inna cikin ruɗewa dan bata taɓa zaton zai zo inda take ba, ganin ya kusa ƙarasowa sai kawai ya saddaƙar ta yi wani uban tsalle ta faɗa cikin tukunyar da Imran ya fito.

Azaba da raɗaɗin ruwan ne da ya ɗau zafi ya ziyarce ta, kuka ta saki a zuciyarta tana cewa.

"Gwara na silsilge in yaso daga nan a kai ni maƙera su bani maganin wuta in ke shafawa a kan in bari ka sareni in mutu in barwa Tasalla Malam" Tana daga cikin tukunyar ta hangi micijin ya bar wajen, a sukwane ta fito ta ɗauki wani ruwa da ke cikin bukiti ta sheƙa tun daga kanta ta jiƙe jargaf.

"Kai Allah ka rabamu da wuta, ka haramtawa wuta cin naman mu duniya da lahira, yo ni da nake cewa sai na yiwa jikina ruwan zafi, saboda sanyin da na shaƙa a firinji ai yanzu na huta duk da sai cewa ruwan zafinsa ya wuce misali, oh duniya shi yasa ake cewa idan za ka gina ramin mugunta ginashi gajere gudun kar ka afka wata rana, gashi dai Imirana bai dahu ba ni na kusa dafewa lugugu ma ba luguf ba" Ta faɗa idanunta kafe a tsakar gisdan tana leƙawa dan ganin ƙwaƙwaf.

Shek da ganin miciji ya nufi lungun nan bai san lokacin da wani ƙarfi ya zo masa ba, da mugun gudu ya nufi bishi wani tsalle ya yi sai gashi ya ɗane bishiyar lokaci guda kamar wani biri, wani reshe ya samu ya hau ya zauna ya kama ya riƙe ƙam. Yana a saman nan, Sadiya da zuwa lokacin kawai ta daina kuka tana daga inda take tana ganin iko da ƙudurar da ta sauka a gidanta, micijin kuma yana dawo wa daga lungun sai ya daina gudu yake tafiya a hankali a hankali yana zuwa tsakiyar gidan sai kawai ya yi lifet kamar ya mutu, idanunsa ma a rufe ruf. A hankali Sadiya ta nufi wurinsa cikin sanyin jiki ta sanya hannu ta ɗan taɓa shi amma ko motsi bai yi ba.

"Shikenan ke ma Allah ya yanke miki wahala ɗiyar nan Hassan ya mutu kowa ya huta Husainin kaɗai ma ya isheki" Cewar Inna cikin sanyin murya tana tahowa wajen.

"Inna da ransa fa bai mutu ba da alama gajiya ya yi ko kuma bacci ne ya ɗauke shi.
" Cewar Sadiya tana kallon micijin da tausayawa a gefe ɗaya kuma tana haushi da zafin maganar da Inna ta faɗa na cewar Hassan ya mutu.Taɓe baki Inna ta yi tana wani kallon Hassan ɗin da ke kwance kamar babu rai a tare da shi.

Shek da ke maƙale saman bishiya ya musu ƙuri da ido, duk abin da suje a kan idonsa, ganin dai micijin kwance magashiyan sai ya fara tunanin durƙowa daga sama domin ya gudu. Ƙasa ya kalla daga saman bishiyar wani uban zurfi ya gani daga saman zuwa ƙasa.

"Allah da iko ashe dai wurin haka yake da zurfi amma lokaci guda na haye saman nan ko dan a tsorace nake" Ya faɗa yana jinjina irin namijin ƙoƙarin da ya yi wajen hawa bishiyar.

"Duk da haka dai sai na durƙo na gudu ya faɗa yana seta inda zai faɗo, aikuwa wara Bismillah da ya yi sai ji kake tik ya faɗo, a tsugunne ya faɗo, dan haka ko kallon su Inna da ke wajen micijin bai yi ba da Imran da shi ma yake tsaye ya kama tsantsa a wajen. A 360 Shek ya busawa rigarsa iska.

"Yaka liman zo karɓi yajin gayyata ka kaiwa matarka" Cewar Inna tana dariyar ganin yadda ya sanya gabansa hanyar ƙofar gida a guje ko waiwaye ba ya yi.

"La shakka laisal mushkila ku riƙe abinku" Cewar Shek lokacin da ya je ga ganshi ya buɗe ƙofar gida, shi ne ya ɓuga amsar da ya baiwa Inna.

Ƙo ƙofar bai rufe musu ba yana fita ya rinƙa zabga gudu kamar an biyo shi, mutane a hanya wanda basu san shi ba sai kallon mahaukaci suke masa waɗanda suka san shi kuwa sai kallon ba lafiya ba suke masa, a haka dai ya ƙaraso ƙofar gidansa yana haki. Wani uban bugu ya yiwa ƙofar gidan sai da ƙofar ta bugu da jikin bango, Barira da ke zaune tana tankaɗe garin tuwo jin buga ƙofar da aka yi a bango sai ta tsorata, bata tantance ba sai ganin Shek ta yi ya shigo jallabiya tattare a hannunsa ga hiraminsa ɗaure a ƙugunsa ko takalmi babu a ƙafarsa.

Ta san ba abu bane ƙarami kuma ba wani abu ne me sauƙi zai sa Shek wannan gudun famfalaƙin, tunaninta sai ya bata ko dai wani aka harba ko kuma bomb aka saka a wani wurin, ai tana ganin ya nufi ɗaki da gudu ita ma ta suri robar da take tankaɗe da kuma rariya a ciki dan ta san garin nan shi kaɗai garesu idan ya salwanta sai dai su kwana da yunwa. Tana shigowa falon nasu ta garƙame ƙofa ganin Shek ba ya falon sai ta bishi bedroom ɗin, a can ma sai sa ta sanya mukulli ta kulle ƙofar sannan ta ajiye garin da ke cikin roba ta kalli Shek da ya yi zaman ƴan bori a tsakar ɗaki, wata dariya ce ta ƙwace mata gani yadda farar jallabiyarsa ta jiƙe ga kuma ƙasa a jiki sannan kuma ga tumurin hirami a ƙugunsa sannan bakinsa sai mismis yake. Sai da ta yi dariyarta son ranta sannan ta kalleshi ganin ko kulata bai yi ba ta ce.

"Ya Shak wai duk wannan gudun bomb ɗin ne kamar wanda ke gudu ranar ƙiyama, ashe dai ku ma Malamai kuna tsoron mutuwa?"

Saurin wayancewa ya yi tare da ƙoƙarin seta kansa ya ce.

"Ba haka bane Barira, wato ainihin komai muƙaddari ne amma mutuwa ai dole ce in kin ga ana irin wannan wahala ake gudu bi ma'ana ceton rai kena" Ya faɗa cikin maganar Ustazai.

"Allahu akbar Kabiran, ni wallahi na ɗauka ma wani ne ya ɗora maka bakin bindiga a kan ka" Ta faɗa tana kallonsa.

"To kusan hakan ne, ko ma fiye da haka, wallahi arangama muka yi da zulƙululu"

"Me ye kuma zulƙululu?" Ta tambaya cikin rashin fahimta.

"Miciji" Ya faɗa yana kwashe komai ya faɗa mata. Dariya take tun ƙarfinta har da hawaye.

"Yo Ya Shek ai dama na faɗa maka amma ka ca wai zancenmu ne na mata wai mu mata mun saba gutsuri tsoma da yaɗa jita-jita, yanzu kuma ai idanunka sun gani"

"Ki bari kawai Barira ai yau na yi mugun gamon da zai daɗe yana zaune daram a ƙwalƙwalwata, ni dai ko hanyar gidan Imran na daina bi"

"Kai da abokin ka"

"An bar abotar, ko fitsarin da na yiwa jallabiyar nan ya fi a ƙirga, ita kanta na san sai ta ce Shek da fitsari a jikina kuma, carbina ma a can na barshi, ko dan wa ma yake ta carbi ana ta kai wa yake ta kaya" Ya faɗa yana since ƙullin hiramin ya fitar da takalmansa na dai suka sha dariyarsu, ya yi wanka ya canja kayansa.


A can gidan Imran kuwa Imran yana ganin Sadiya ta ɗauki micijin da sauri ya yi ɗaki dan shi abin ya wuce tunaninsa. Yana shiga bedroom ua nufi wardrobe ɗinsa zai canja kaya, yana buɗewa Mama da ke can ciki ta tsorata tare da maƙurewa a can ciki, Imran da bai lura da ita ba ya miƙa hannu zai ɗakko riga sai ya ɗora hannunsa a kan ƙafar Mama da sauri ta janye ƙafar tana zazzare ido, jin ya taɓa mutum ya miƙa kansa ya leƙo ciki aikuwa suka yi ido biyu da Mama, tuna abin da ya faru tsakaninsu ɗazunya sanya ya ji kunya, Mama ma kunyar ce ta rufe ta, cikin ƴar murya ta ce .

"Ashe Imran ne" Ta faɗa tana jin kunyarsa bayan abin da ya faru ɗazu yanzu kuma ya kamata a cikin lokarsa.

"Mama micijin nan fa ya yi bacci" Ya faɗa, jin hakan sai Mama ta ce.

"To, to, to" Ta faɗa tana zuro ƙafarta ta fito daga drower wata muguwar kunyar Imran na kama ta.

Hajiya da ke ƙasan gado jin Imran ya ce miciji ya yi bacci sai ta ɗan yunƙura za ta tashi amma ta ji ba hali.

"Imran, Imran, Imran" Ta shiga kiran ɗan nata.
Imran jin muryar Hajiya a ƙasan gado cikin sauri ya durƙusa ya kamo hannunta, jin ta maƙale a take ya, ya ɗage katifar ya fito da ita yana mata sannu.

"Kai yau mun ga ta kan mu, ko ma in ce na ga ta kaina, wallahi cinnaku ne a ƙasan gadon nan haka suka rinƙa safa da marwa a jikina babu yadda na iya, cizo kamar wani ƙudan cizo haka nake ji idan suka manne a jikin fatata" Ta faɗa kamar za ta yi kuka, sannun dai Imran ya cigaba da mata, ana haka sai ga Inna ta shigo, ganin Hajiya na karkaɗe jiki tana faɗar zaman uƙubar da ta yi a ƙasan gado sai ta shiga dariya, kowa kallonta yake da mamaki ta ce.

"Yo ni dama kowa ya ci tuwo da ni miya ya sha kuma sata a gidan ɓarawo wallahi rance ce, ba ni ka yi ta yiwa dariya ba ranar da na ƙarasa kwana a ƙasan gado ba yau na rama a kan uwaka dama ai ɗan kuka shi ke jawa uwarsa jifa" Cewar Inna tana dariya.

"Yau dai an yi kwaɗo, sirika a lokar siriki, hallaw sirika a ƙasan gadon sirika kuma duk jika ne ya haddasa hakan, sannu Amina, sannu Rakiya" Inna ta faɗa tana dariya. Babu wanda ya tanka ta dan su burinsu ma su bar gidan kawai.Haka suka fito suka bar Imran da ke shirin canja kaya, sai da ya canja ya fito daga ɗakin, sannan me ƙunshi ta buɗe kayan wankin da ke jibge a kanta ta fito. Tana fitowa ta zo za ta fita daga ɗakin kamar an ce ta duba mudubi ta hango wani baƙin aljani baƙiƙƙirin da shi ƙirji ta dafe tana ambaton Allah sai da ta yi gaba za ta fice daga ɗakin sai ta gane ashe ita ce, kawai baƙin lallan ya mayar da ita haka. Fuskarta ta tsaya ta ƙarewa kallo sai kawai ta rushe da kuka, a haka ta fito lokacin ƴan matan nan har sun fito daga maɓoyarsu sun tafi, sai Ashrof kaɗai, da kuka ta fito falon kowa yana kallonta Imran takaici ne yasa ya ɗauke kai Inna kuwa dariya kawai take tana cewa.

"Gobe ma ki ƙara yiwa tsoffi haka, ita ma yarinyar nan me ƙananun nono ta tafi wai ita nan mace ce ƙirji babu komai yo irinsu ne idan suka tarki saka rigar nono za ki ga rigar nonon da ban ƙirjin da ban"
Ba abin da ta ce a haka ta sanya mayafinta ta naɗe kamar niƙaf duk da haka ana iya ganinta amma hakan ya ɗan suturta ta dan idan bata rufe ba ta san duk inda ta fita gudunta za a ke.

Imran ɗaki ya koma ya ɗakko kayansa cikin jaka, ya fito. Mama da Ashrof sun tafi dan yau babu damar yin girki ko wani abu da gabaɗaya Ashrof a ruɗe take har lokacin tana zabura. Hajiya da ke yiwa Sadiya sallama ta kalli Imran da ya fito riƙi-riƙi da jaka. Kowa da mamaki yake kallonsa Hajiya ce ta yi ƙarfin halin cewa.

"Ina zaka da kaya haka Imran?"

"Tare za mu tafi"

"Tare za ku tafi da wa?"

"Da ke"

"Ina?"

"Gida mana , kawai tafiya zan yi can in zauna a tsohon ɗakina tun da ga Inna nan ta zo ZAMAN WANKA in ya so ta zauna ma har Sadiya ta yaye yaran" Ya faɗa yana sunkuyar da kai, dan kunyar Sadiya yake ji sun haifi ɗan amma yana so ya gudu, shi kuma har ga Allah so yake ya tafi dan ya gaji da darun gidan kuma dai ya ga alama Hassan ya ƙi dawo wa mutum.

" Ikon Allah wai na kwance ya faɗi, Taɓɗiiii, ashe kuwa za a yita a gidan nan, wane shegen ne zai zauna bayan kai ma uban micijin gudunsa kake, wato ga Inna kuka me daɗin hawa, wacce take so ta bar duniya a kwana kusa sai in zauna in maka ZAMAN WANKA, yo ai abin ma ya wuce ZAMAN WANKA ya koma reno wai har a yaye su in ya so idan micijin ma ya sareni baka da asara iyakarta idan na mutu a ZAMAN MAKOKI ka ce Allah jiƙan Inna, ana karɓar sadaka kana afa shinkafa kana kora lemo, haɗe da kunun zaƙi, to wallahi baka isa ba ko tsinke naka ba zai fita daga gidan nan ba" Cewar Inna da ta tashi ta kama tsantsa ta wani haƙiƙice ta rufe ido tana sababi..

09030283375
[24/03, 5:14 AM] Mom Mashkur First class: *MAMAN AFRAH DATA SERVICES*

*BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*

*I selling MTN data with this cheap price*

*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===150
1GB@=====250
2GB@=====500
3GB@====850
5GB@====1,400

Dial *312*4*7*4# to check Data balance.
*Validity 1 month*

*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*

Act details FA'IZA ABUBAKAR unity bank 0020281885
Whatsapp OR
Call 09033283375




Wannan littafin kuɗi ne 300
Za a tura ta wannan accaunt ɗin Fa'iza Abubakar 0020281885 Unity bank shaidar biya ta wannan no 09030283375 idan katin waya ne mtn Ƴan Niger su tuntuɓi wannan no +22785885134



3️🅰️➡️🅱️




Kowa da kallo ya bi Inna ganin yadda ta haƙiƙice tana sababi kamar dai za ta hau Imran da duka.

"To kai Imran ban da abinka ya za a yi kana namiji kuma me gida ka ce za ka fice ka bar gida, ina ka taɓa ji an yi wannan sha'ani?" Hajiya ta faɗa tana kallonsa.

"Dan Allah Inna ki yi haƙuri kin san sha'anin yara sai a hankali amma babu inda zai je ma in sha Allah yana nan" Cewar Hajiya tana kallon Imran da ya tamke fuska ita dai Sadiya bata ce komai ba sannan ko a cikin ranta bata ji haushin Imran ba dan tana ganin kowa ma zai iya yin haka duk da kasancewarsa mahaifi a wajen Hassan bai kamata ya yi hakan ba amma dama ta san Hajiya ba za ta barshi ya bita ba ko ya bar gidan.

"Haba Amina ai duk da ba zan haɗa kaina da Imirana a wajen shekaru ba, to kuwa tabbas ba ƙaramin yaro bane, mutumin da yake da aure garsamemen ƙato da shi har da ƙaruwar ƴaƴa biyu duka maza duk da dai ɗayan miciji mutum ne, wato rabi da rabi, kuma ma ai yana saka ƙafa ya bar gidan nan ni ma jikata zan ɗauka da Husaini na aika miki Hassan ɗin in tafi da ita can wajena, ya za a yi ma ya mata ciki ta haife masa amma saboda yaro na da baiwar da yake sanya kowa a taitayinsa ya ce wani zai bar gidan" Ta faɗa tana galla masa wata hararar.

"Ki yi haƙuri Inna" Cewar Hajiya tana mamakin halin Inna da bata iya sakaya abu ita babu ruwanta da kowa duk abin da ta yi niyyar faɗa, to faɗa take ba ruwanta d me zai je ya zo ko kuma ya wanda aka faɗawa zai ji.

"Kar ma ki kai kan ki da nisa na haƙura ma ba dai ba zai tafi ba ai ni bani da ɓacin rai indai zai zauna ɓacin raina a ce ya tafi ya bar Sadiya da ni da Hassan shi ne kawai" Ta faɗa fuskarta fes da alamun dariya, tana ɗan yi tana kallon Imran da zuwa lokacin ya cika fam babu masakar tsinke, ji yake kamar ya hau Inna da duka amma babu hali, nasiha sosai Hajiya ta musu shi da Sadiya a kansu rungumi ƙaddara Inna tana gefe tana tattaɓe baki haka dai Hajiya ta musu sallama ta kama hanyarta ta tafi.


Inna da ke ƙunshe dariyarta ta kalli Imran da ya tashi ɗauke da jakarsa yana wani harare- harare ya yi cikin ɗaki. Dariya Inna ta kyalkyale da ita ta ce.

"Oh ni Azumi Imirana manyan ƙasa ina ga nan gaba duka za ka fara hawan mutane da shi yo Allah na tuba, wannan haloƙoƙon da kake na menene zama dai daram a gidan nan, kuma kai ma muna nan tare da kai"

Shi dai bai ce mata komai ba ya shige ɗaki wata ƴar dariyar ta yi ta ce

"Ni dai ban san ba harara sai ido ya faɗo" Ta faɗa tana kallon Sadiya da ke zaune kawai tana binta da ido.

"Sannu ƴar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login