Showing 15001 words to 18000 words out of 56867 words
tana tuno yadda aka kwashe da soja da Hassan ranar nan.
Kamar wanda aka faɗawa micijin sau saurin barin wurin Imran ya yi ya tafi wurin Hajiya yana zuwa ya tsaya a gabanta. Ai da sauri ta gyara tsayuwarta tana ɗaga hannaye yadda Imran ya yi ra sanya su a gefen kanta yadda sojoji ke yi ta buɗe baki kuka na neman ƙwace mata sai dai tana tsoron sakin kukan dan kar micijin ya sareta ta ɗan ɗaga murya amma kuma ƙasa-ƙasa ta ce.
"Imran karanto min taken Nigeri'ar sai in ke faɗa idan ka faɗa ka san ni ba iyawa na yi ba, amma idan kana karantowa sai in ke bita, tun da gashi a gabana layi ya zo kaina" Hajiya ta faɗa idanunta a kan Imran da har lokacin bai saki hannayensa ba haka zalika ƙafafunsa na nan yadsa suke a haɗe, bakinsa kuwa sai jerawa Nigeri'a kirari yake, kamar wanda aka ce Nigeri'ar za ta watse idan ya dakata da yi.Sara ya fara a gabanta ko ƙaƙƙautawa babu, kuma babu alamar zai dakata, dan haka Hajiya sai ta fara kuka, kuka kawai take wiwi dan ta rasa ma yadda za ta yi. Cikin ikon Allah sai ya bar gabanta amma bata bar yin kukan ba, gaban Inna ya nufa yana zuwa ya tsaya. Kallon kallo suka fara da Inna wacce majina ta taru cikin tafukan hannayenta da ta rufe bakin da su, ganin micijin a gabanta sai ta ce a zuciyarta.
"Yau na tabbatar kai ba mutum bane, ɗan ruwa ne, in ba ɗan ruwa ba a ce jariri da kai amma har ka aan ka je gaban wannan ka je gaban wancan"
Ganin yana shirin kaiwa ƙasa sara sai Inna ta yi karaf ta fara masa waƙa.
"Haba Hasanunu, ɗan aljanna, haba hasanunu ƙaton kirki, haba Hasanuna ɗan Imirana, haba Hasanunu me sauya kala" Ta faɗa tana wani rausaya kai ita a dole ya bar gabanta, ai sai gani ta yi ya kai wani sara me ƙarfi.
"Lanjeriya ƙasar ƴan baiwa, lanjeriya ƙasar talakawa, lanjeriya ƙasar Bahari ɗan daura" Ta faɗa tana kuka hawaye shaɓe-shaɓe.
Wani saran ya kai wanda ya kusa samun ƙafarta ta janye da sauri, cikin kuka ta ce.
"Wallahi tallahi, ƙur'ani ban iya yaren nasaraba (Turanci) Dan Allah tun da dai Nigeri'a ƙasar hausawa ce ka barni hakan dan wallahi ban iya irin wanda Imirana da sojojo ke yi ba" Kamar wanda aka tsikara ya fara tahowa, gabaɗaya matan nan suka sha jinin jikinsu.
Kowacce ta shiga addu'a tana fatan kar ya zo wajenta, zagayasu ya yi sau ɗaya Mama da Hajiya da ke gefe, suka ƙara matsawa kusa da sauran kowa yana jin matsanancin tsoro.Gafe ɗaya ya koma ya tsaya yana ƙare musu kallo har Sadiya da ke tsugunne a wajen, Ashrof kwa hawaye sam basa tsayawa ga tausayin kanta da na ƴar uwarta da ma mahaifiyarta.
"Sahuuuu" Cewar Inna cikin tsoro, kowa da ido ya bita alamar tambaya.
"Yo jama'a ba dole na ce sahu ba tun da haka Allah ya ƙaddara mana yau, zama inuwa ɗaya da miciji, kuma miciji me son taken Nigeri'a to tun da Imirana ne ya fi iyawa sai mu bi ayari mu yi sahu, mu bi bayansa idan ya faɗa sai mu ke masa amshi da dai mu tsaya micijin nan ya mana ɗauki ɗai ɗai, dan ni kuma ban shirya mutuwa yanzu ba in barwa Tasalla Malam" Cewar Inna tana kuka abin tausayi abin dariya.
Gabaɗaya kowa sai ya fahimci maganar Inna haka take dan suna ganin kamar micijin ya fi son national anthem dan haka sai suka fara yin lafi a bayan Imran banda Sadiya da ke tsugunne a tsakiyar wurin, Imran da har lokacin yake a ƙame bakinsa bao huta ba da taken Nigeri'a yana kaiwa ƙarshe sai ya dawo farko. Yana faɗa su ma suna faɗa duk da ba kowa ke faɗa daidai ba irin su Inna da su Mama su ma sauran matan tsoro ya mantar da su cewa sun iya national anthem sai suka dawo kamar wasu ƴan koyo dan suna ganin kamar Imran ne ya fi iya wanda micijin ke so.
Suna cikin yi sai micijin ganin sun tattaru a waje ɗaya sai kawai ya shiga zagaye su, a mugun guje yake zagaye su har wani tsalle-tsalle yake, ganin hakan ya sanya suka ƙara tsorata, cikin tsoro da ruɗewa suka dunƙule a waje ɗaya, kowa ƙoƙarinsa ya samu mafaka a jikin ɗan uwansa, dan gani suke kamar in kana kusa da wani micijin ba zai zo wurinka ba. Imran da Mama sun ƙanƙame juna cikin rashin sani dan ita bata san shi bane shi ma bai san ita bace an haka kowa ya ƙwamusu baka jin komai sai sautin koke -koke.
Sai da ya gaji dan kansa ya koma waje ɗaya ya tsaya, kowa ya ɗan fara sakin ajiyar zuciya, Mama da Imran sai lokacin suka ankare sa sauri suka saki juna Mama na saurin juyawa ta dafe haɓa tana zabga salati a ranta, idan ba larura ba ya za a yi a ce sun rungume juna ita da Imran mijin ƴarta Sadiya. Kafin kowa ya gama tantancewa micijin ya buga wani uban tsalle ya hau kan bishiyar da ke tsakar gidan gabaɗaya kallo ne ya koma sama, kowa na kallon micijin da mamaki har da Sadiya ma da ta rasa bakin magana sai kuka, jelar ya kanannaɗe a jikin reshien bishiyar ya zaro kan sa yana kallon kowa da kowa, ganin haka sai kowa ya fara neman inda zai fake idan an sakko micijin ya dawo mutum sa fito.
Imran da gudu ya nufi wajen tukunyar dafa ruwan wankan jego da ke ɗore a kan murhun sai dai ba a kunna wutar ba, a ka Inna ke barinta saboda wahalar ɗorawa sai dai wani lokacin ta kan bar ruwa kaɗan a ciki. Yana zuwa bai yi wata-wata ba ya gotar da murfin tukunyar da yake babbace sai ya samu ya shiga ba tare da ya cire murfin duka ba, yana shiga ya ringisa a ciki, ya miƙo hannu ɗaya ya ja murfin ya rufe kamar me rufe ƙofa.
Matan nan sai gasu suna tseren shiga kicin da Inna, Inna ce a kan gaba, tana shiga ra sauke idanunta a kan freezer da sauri ta ɗauke idanunta dan ko ƙaunar ganin freezer bata yi.
Wasu lokarsu ta ɗazu suka ƙara komawa bayan sun garƙamawa ƙofar kicin ɗin sakata. Me fulawa da Hajiya da Mama suka shige ɗaki Hajiya ta shiga ƙasan gado dakyar tana kukkujewa amma ba damuwarra bace hakan mafaka kawai take nema. Mama cikin wardrobe ɗin Imran ta shige ta rufe, tana kallon yadda ta zaune kayan sirikinta har da gajerunan wandunansa. Me ƙunshi kuwa kayan wankin da ta gani a ƙulle a zanen gado masu yawa su ta sunce cikin sauri ta kwasa ta libgawa kanta.Sai wani zarnin fitsari take ji a hancinta ashe wandon Imran ne da ya jabgawa fitsari ranar da Inna ta rufe shi a ɗaki a ranar farko da Hassan ya zama miciji. Amma bata damu da warinnba tun da ta samu mafaka.
Ashrof kuwa bayi ta koma, ta banke ta aka bar Sadiya kawai a tsakar gidan tana kallon Hassan rataye a sama.
Inna da ke ƙasan wani dogon benci da da ake ɗora kayan abinci a kai ta rufa buhhuna kusan goma a kanta ta daddage ƙarfinta ta ce.
"Halima in ce dai kin samu mafaka, dan na ga Imirana tuni ya yi hanyar murhu, in kuwa tukunyar da nake dafa ruwa ya shiga dan na ji ƙaran murfin ina samun kaina wuta zan galgala masa sai na dafashi luguf ya dahu...
[24/03, 5:14 AM] Mom Mashkur First class: *MAMAN AFRAH DATA SERVICES*
*BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*
*I selling MTN data with this cheap price*
*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===150
1GB@=====250
2GB@=====500
3GB@====850
5GB@====1,400
Dial *312*4*7*4# to check Data balance.
*Validity 1 month*
*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Act details FA'IZA ABUBAKAR unity bank 0020281885
Whatsapp OR
Call 09033283375
Wannan littafin kuɗi ne 300
Za a tura ta wannan accaunt ɗin Fa'iza Abubakar 0020281885 Unity bank shaidar biya ta wannan no 09030283375 idan katin waya ne mtn Ƴan Niger su tuntuɓi wannan no +22785885134
2️⃣9️⃣➡️3️⃣0️⃣
Yadda Imran ya fito a firgice cikin kiɗemewa ko lura bai yi ba da Inna da ke tsaye, ƙaran dariyar da ta saki ne ya sanya ya dakata daga ƙoƙarin gudun da yake wanda shi kansa bai san ina ya nufa ba. Ganin Inna tana dariya har da nuna shi da yatsa sai ya dakata tare da haɗe rai kamar ba shi ne ya iyo gudun ceton rai ba daga cikin tukunya, sanadin zafin da ya ziyarceshi.
Kallon murhun ya yi ya ga yadda wuta ta kama take ci kamar wanda aka sanya fetur, ga sauran buhun nan wanda Inna ta saka bai gama ƙonewa ba.
"Lallai tsohuwar nan ta ga makwancina da yawa, yanzu ni ta balbalawa wuta? Dan na san dai ai ba za ta ce bata san ina cikin tukunyar ba, " Ya faɗa a zuciyarsa sai muzurai yake kamar zai hau Inna da duka.
"Imirana wai dama kai ne a cikin tukunyar wankan jegon matarka, soyayya ce ta sanya kakeso a dafa ka ta yi wankan da kai a memekon a dafa mata ruwa?" Cewar Inna tana ƙoƙarin danne dariyarta har da ƙwalla. Gefen leɓensa na ƙasa ya danne da haƙori ji yake kamar ya saki kuka dan takaici. Juyowa ya yi yana ƙoƙarin barin wurin dan dama wurin da murhun yake a ɗan lungu ne ba a sararin tsakar gidan yake ba.Sai da ya fito idanunsa suka sauka a kan Shek da ke ƙoƙarin raɓewa a bayan Sadiya ita kuma tana gocewa tana matsawa yana ƙara bin ta. A take maganar Inna da take cewa kwarto zai yi fyaɗe ta faɗo masa, ai ganin Shek kusa da matarsa ba ƙaramin fusata shi ya yi ba, in ba iskanci ba ya za a yi yake ɓuya a bayan matar aure, shin uban me ma zai shigo da shi cikin gidansa. Cikin jin haushi da fusata ya nufo wurin su dan gabaɗaya kishi ya rufe masa idanu har wani diri-diri yake gani, hakan ya mantar da shi ƙalubalen da yasa ya shiga cikin tukunya, dan gabaɗaya ya manta da batun miciji bare har ya yi tunanin shi ne dalilin da yasa Shek ɗin ɓuya a bayan matarsa. Idanunsa sun rufe ko lura da micijin da ke gaban su Sadiyar bai yi ba,a fusace ya nufo su, dan nufinsa yana zuwa wajen zai manta da mutunci da abokantakar da ke tsakaninsa da Shek ya shaƙe masa wuya sai an ƙwaceshi dakyar a hannunsa tun da shi ma bai ga mutunci da haƙƙin makotaka ba son zuciya ya rufe masa ido har ya zo yake neman yiwa matar aure fyaɗe.
Yadda ya taho a fusace kamar kumurcin miciji za ka ɗauka yana zuwa zai ɗauki hukuncin da ba zai yiwa kowa daɗi ba, amma me sai da ya zo dab da su idanunsa suka sauka a kan Hassan da ya yi wata alkafira, kansa ya cake a ƙasa sai jelar ta zama a sama sai wani wulwula ta yake kamar fanka. Wani uban birki Imran ya ja, tare da haɗiye wani yawu muƙuuut, ajiyar zuciyar ya fara saki a jere- a jere kamar wanda ya ƙwaci kansa daga hannun ƴan fashi. Cikin sauri ya fara kalle-kalle yana so ya ga ta inda zai tsere, yana waiwayawa bayansa sai suka haɗa ido da Inna da ke dariya marar sauti, ganin abin da ke faruwa dan dama ta gama karantar cewa Imran kishi ne ya rufe masa ido ya tafi ba tare da ya lura da micijin da ke juya jekarsa kamar an ƙurewa fanka gudu ba. Ita ma Inna a tsoracen take dan abubuwan da Hassan ke yi yau sun girmi tunaninsu, amma kuma ganin Imran ya taka birki ƙiiii kamar wanda ya kusa faɗawa kwalbati ya lura da ramin gabansa, hakan ya yi lolacin da ya yi ido huɗu da micijin.
"Dole ka nemi mafaka Shek ba lefinka bane, tabbas na daina ganin lefinka ko ni na na shiga gidan matar aure tuni zan manta da igiyar aurenta, in har a irin wannan bala'in ne ko a cikin ɗan kamfai (Pant) Ɗinta sai mutum ya totsu ya yi mafaka" Cewar Imran a ransa, fuskarsa kamar ya saki kuka, ga ruwan tukunyar da ya jiƙa masa jiki sai tsiyaya yake daga jikinsa, kallon Shek ya yi da gabaɗaya gumi ya gama wanke masa fuska sai tsiyayowa gumin ke yi ta jikin gemunsa yana ɗisa a ƙasa, ga yadda ya jiƙe da fitsari da alama ya yi fitsarin sama da kifi uku.
"Wayyo maƙocina, ashe kana cikin gidan nan, wallahi Sadiya ta ce min baka nan da tuni kai zan nema amma ganin baka nan ya sa nake nema ya rungumi wuta da hannu na, yo wuta mana duk inda na rafki matar aure da hannu na ai na san na kama wutar jahannama" Shek ya faɗa yana kallon Imran da ke kalle-kalle dan shi gabaɗaya ya kasa tantance a raye yake ko a mace ko mafarki yake da yake ta haɗuwa da wannan iftila'in.
"Imirana wai ya ka toge abokinka yana maka magana, amma ka ƙeƙashe ƙasa ka tsaya kamar wani gini, kar fa Allah ya kama ka a kan haƙƙin maƙotaka maƙocinka na cikin wani hali amma ka kasa kai masa taimakon gaggawa" Cewar Inna tana kallon Imran tare da danne dariyarta dan wata uwar harara ya aika mata kamar dai ta ce ya damƙi wuta.
"Allah dai ya miki albarka tsohuwa, nagode ƙwarai da gaske da kika ƙara fahimtar da shi" Cewar Shek yana kallon Inna da ke tsaye can hanyar murhu, so yake ya gudu bayan Imran amma yana tsoron abin da zai je ya zo domun kuwa ya ga micijin zai iya wartoshi lokaci guda , a gefe ɗaya kuma ga Imran ɗin ma kamar a tsorace yake, duk da kasancewarsa uba ga micijin.
A hankali Shek ya fara lallaɓawa sai da ya tsugunna daga tsayen da yake, cikin sanɗa ya fara rarrafawa ya nufi wajen da Imran yake, sai dai a matuƙar tsorace yake dan kar micijin ya biyo shi. Imran kuwa kafe Shek ya yi da ido ganin ya tunkaroshi zai je ya goga masa kashin kaji, dan idan da micijin zai masa kara saboda kasancewarsa uab a gareshi amma yanzu ganin Shek zai sa ya canja shawara, wani kallo ya yiwa Shek ɗin, yana kallon wannan hiramin da ya ci tumuri da shi a tsantsarsa. Shek kuwa ya raba hankalinsa biyu, ɗaya yana ƙoƙarin ya kai wajen Imran ɗayan kuma a kan micijin da ya ga duk wulwula jelar da yake amma kuma idanunsa a kan Shek ɗin suke. Har ya yi kamar zai dakata sai dai ya cigaba da rarrafen, sai da ya je daf da Imran micijin ya sauke jelarsa ƙasa, cikin kiɗima Shek ya dakata da rarrafe, bai san lokacin da ya tashi ba sai ganin kansa ya yi a tsaye cankarkar sai dai ya kasa tsayuwa dai dai sakamakon karkarwar da ƙafafunsa ke yi.
Inna kallonsu kawai take tana so ta ga ta yadda wasan zai fara dan ta san babu yadda za a yi a kwashe lafiya. Tun da Hassan ya ajiye jelarsa a ƙasa sai ya juyo ya maida hankalinsa ka su ya fasa kansa yana kallonsu, Shek ganin ya ƙura musu idanu sai ya sha jinin jikinsa cikin sauri ya buɗe baki ya ce.
"Ka masa magana mana Imran kai da ɗanka, ka yi saurin bashi umarni ya koma ɗaki ni in samu in bar gidan ma dan na rasa wane tsautsayi ne ya kawo ni" Ya faɗa yana kallon Imran da ke jifansa da wata muguwar harara.
"Da yana jin umarnin ai da baka zo ka tarar da abin da ka tarar ba hatta uwata tana cikin gidan nan ban san ma a ina ta ɓoye ba, kuma da ya san cewa ni ubansa ne ai ba sai na bashi umarni ba zai yi abu, ɗazu a gabana ya tsaya yana kai sara" Ya faɗa kamar zai saki kuka.
"Ka manta baka faɗa masa cewa har ƙwaƙumar Rakiya ka yi ba cikin rashin sani" Cewar Inna tana dariya tare da tuno lokacin da ta hangi Imran da Mama sun rungume juna kamar za su koma cikin juna saboda tsoro. Banza Imran ya mata dan shi yanzu kawai so yake ya fice daga gidan dan ya gaji da wannan wasan kwaikwayon. Yana tunanin mafita sai ganin micijin suka yi ya fara zulalowa a hankali kamar baya so, sai da ya zo tsakaninsu inda suke tsaye Imran da Shek ya ja ya tsaya, Shek na ƙoƙarin matsawa ya ɓuya a bayan Imran sai Imran ya ce.
"Kar ka kuskura ka motsa dan wallahi idan ya sareka ba ruwana"
Wani yawu Shek ya haɗiye yana kallon micijin kamar ya fasa ihu saboda yadda ya ganshi dab dashi abin ya matuƙar ƙara firgita shi amma ba yadda ya iya haka ya daure ya tsaya a inda yake. Zagayesu ya fara yi amma bai yi yinƙurin yin komai ba, ganin hakan ba ƙaramin ruɗewa Shek ya yi ba, amma kuma Imran ya hanashi motsi kamar yadda shi ma Imran ɗin bai motsa ba.
Wani tsalle da micijin ya yi shi yasa Shek da Imran rungume juna, yana komawa can gefe sai suka saki juna suna maida numfashi, kowa neman hanyar gudu yake, fara zagaya su ya fara yi cikin kuskure sai Imran ya ɗan motsa aikuwa Shek ma ya matsa wurinsa, miciji kwa ya ce da wa Allah ya haɗa shi in ba da su ba, haka suka shiga tsere, Imran a gaba Shek a bayansa, sai miciji a bayan Shek suna cikin zagaye Shek da ya ga micijin a bayansa yake kuma yana neman kai masa cafka sai kawai ya yi tsalle sai gashi ya ɗane bayan Imran, da yake jallabiyar ce a cikinsa kuma da zai haye bayan Imran be tattare ta ba sai ya zamana ya kasa ware ƙafafunsa