Showing 51001 words to 54000 words out of 60071 words
Beigon kasanni baka taba sani aiki na ketare saitiba kaduba irin aikn da kasamu akan mukashe kanwar Buf haka na Saida raina na aikata hakan
Sakamakon hakan kanaji aka kamamun yara cewa in banbayyanar da kainaba komai xai iya faruwa ciki ko harda kashe yarana da za ai
kai kasan ina ma aikin gsnganci dayawa wnd duk wanda kasa baya dawowa har abada
Ni koda nashigo kungiyar nan sbd alhj Bala nashigo sbd irin kuntata wa rayuwata dayayi ya kaskantar dani shiyasa nashiga kungiyarnan
naki shiga kananan kungiyoyi sbd tananne kadai xan iya jada Alhj Bala Dan Dana bincika suma kungiyar su tanada karfi dandai bata kai taka karfiba shiyasa nashigeta
Kuma kamun alkawari saika kamomin Alhj bala da hannunka innai maka wasu aiki tom namaka Amma har yaubaka kamomin Alhj balanba Alhalin ba kanada karfin kamashi kuma kasan inda yake
Tom wnn karon wlh xan iya komai akan yarana ciki harda salwantar da rayuwata ta hanyar Mika kaina asakinmun yarana suyi rayuwarsu
Dariya Begon yayi karya kake DIAMOND I swear to God karya kake
Shekarana nawa ina aiki da mutane Amma bantaba aiki da Wanda yake shigomun da kudi ba irinka DIAMOND acikin shekara kusan ashirin ina aiki da kai nayi gd da motocin da bantaba xaton xan mallesu ba rana daya baka isa kafitaba duk cikin yarana kaine nake bari kayi sallah saboda ynd naga kanasonyinta bantaba ganin lokacin sallah yawuce bakayi ta ba koda muna cikin operation ne Amma nabarka kanayi kai kadaine mai maidamun da magana inkyaleshiba ban fasa kanshi ba bana daukar yannaija a aikina Amma kai na daukeka duk dani dan naijane
barinka kungiyar mu tamkar mutuwar kungiyar muce
kaiba kudi bane agabanka Diamond nabaka dukiya maitsananin yawa wacce xaa lissafa ka a masu kudin naija kaki karba shiyasa nakejin dadin aikinka
yanxu kuma kace xaka fita baka isa bane
Abbun xuciyarshi tabashi shawara cewa yabashhi sai yagama yarda dashi ya bayyana mai dukka siriinshi tukunna komai xaifaru yafaru shidai yanxu yafara sanar dashi sirrikanshi sosai kadan yarage ya xartar da abun da ya kudurta aranshi
Buf wani irin bacci mai nauyi yakwasheshi yanata ajiyar xuciya da sauri da sauri
nasamu dakyar naban bare xuciyata kamar garwashi ashe bufa yanada wata mata Banda ummita
lalllai kam nikama wane irin ifti lai ne wannan
________________________
ABIN YABO BOOKSHOP
Kasuwar Rimi Kano
Tel: 07038339244
SANADIN SON BANZA
By:
Shamcsiyya Daheeru
(((27)))
Daki na koma ina tunanni me BUF yake nufi (mommy baxata yrd da aurenmu shin wanne aure yake nufi meye ma'anar hakan
kwakwalwata tashiga hargixa maganganun buf dole inne man ma kaina mafita
Daren da abun yafaru nashiga tsaka mai wuya tunani nashigayi kala da kala wato BUF baimasan da irin sonda nake mai ba kenan ni ke wahalar banxa ko meye banyi ba duk akan sonshi amma abanxa
Amma in Allah yayarda xannuna mai Banda mu dashiba xan fita sabgarshi kuma tsakanina dashi sai taimakon musulunci kamar yadda yake mana
ahaka dai nai barci ina wnn tunani
Washe gari yafito da sassafe da shirin tafiya saidai bansan kasar da xaije ba amma da katuwar jakannan ta baya agoye abayanshi yafito mom hanifa tace sai ina gashi nafito inma ka Dan abu mai ruwa ruwa inafa sane da kai jiya dana maka kotabawa bakayi ba haba Buf maiyasa kakeson ka dunga axabtar da kanka da yunwa bakasan cin abinci daga cornflakes sai peakmilk meye amfanin daukar Madam Aisha dammu ko ko Dan kai
ina xaunene dama muda mom hanifa ina koya mata karatun QURANI kamar yadda mukeyi duk asabar da lahadi inba school
ganin yafito ne kuma da alamar tafiya shiyasa ma ta gane tafiya xai duk da indai zaitafiyar sai ya mata sallama
bai ce mata kala ba saidai ya sunkuyar da kanshi kasa yana sauraranta cikin ladabi
Yace mom xantafi xanyi kokari naga na gyara kimun addua tace yanxu me kaci yace nasha peak milk tace shixaimaka harkaje inda xaka yace karkidamu
yadago idanshi da suka Dan kada sukayi ja ya kalleni tsawon yn seconds nace ina kwana baicemun cikankiba kuma baidaina kallona ba can dai yafito da sauri sai karar tashin motoci muka ji alamar yabar Mansion din
Naji xafin abun da Buf yamun saidai banda yanda xanyi da shi inda sabo ya isa imma saba da ahalinshi
kwanan shi biyar da tafiya nayi wani mafarki daya gigitani wai gani ajikinshi kamar yadda yasaba rungumeni wai andaura mana aure dashi ashe nice matar da yake ta cewa mom baxa ta barshi da ni ba abun mamaki momynshi ce nahango tana miko mana fruits masu kyau da fararen kaya yatashi xaije ya amsa sai ga wata mata nan anrufemata fuska banga fuskar matarba ta tareshi kamar xata rungumeshi ashe wukace ahannunta tasoka mai takuma yo kaina xata soka mun momynshi tatare ta sokamata nikuma na gigice na nufeshi Amma fadi yake ki gudu Rukayya xata hallakaki bata da imani naki ingudu nayi saurin damkar matar muna ta kokowa inason ganin fuskarta waxan gani aunty xeee ce😳
Nan na sume ita kuma ta gudu
Tashi nayi afirgice ina kuka shabe shabe da hawaye naduba agogo naga karfe ukun da rabi da sauri nashiga bayi nayi alwala nafara nafila ina kuka ina rokan Allah karyasa mafarkina yaxama gsky
me yakawo aunty xee acikin mafarkina me hakan yake nufi gsky na shiga rudani meya hada momynshi da aunty zee wayyo ALLAH Buf ko ina yake oho
kasa fitowa nayi Saida nai shirin boko da yake yau Friday nafito gabadaya nashiga na gaida mom hanifa tace lpy naga idonki akumbure nacemata banda lpy tace mun to nasha magani nace mata eh tace abincinfa nace gashi can xan dauka akitchen nasan madam Aisha ta xuba mun a food fls dina tamun Allah kiyaye hanya nafito naxo kitchen na gaida ta nadauki abincina hartana yau da wuri haka baxa kitsay kiyi breakfast ba nace ah a wnn ma ya isheni
nafito banga motar jannifer ba saina xarce wajan yaya Yusuf natadda shi yana karya wa Alhmdllh gsky yaya Yusuf kafa taikyau yanxu yana takawa ko ina basai da sanda ba
na gaisheshi can kuma na fashe da kuka yayi shiru yana kallona baicemun kalaba har nagaji nayi shiru yace mun meya faru nace yaya Yusuf mafarki nayi
Nan na kwashe mafarkin tass nagaya mai shikanshi yadan tsorata da mafarkinnawa Amma sai yawani basar yace ke nifa ban son shiririta mafarki ai ba gsky bane aunty xee da tatafi tabarmu tun saddda abun xaifaru tun adaren takama kanta kokin manta
nace eh hakane
yace to yanxu ina muka ga wata aunty xee
dama can yar bariki ce suka hadu da Abbun ya aura takeamai kwantar bauna nace kaidai yaya Yusuf Dan dai jinin ku bai hadubane kawai katsane ta yace kekuma lokacin kina ganiyar haukanki na kuruciya shiyasa baxa ki gane ba yanxu dai wuce makaranta nima ranar Monday InShaaAllah xan koma aiki
nace ALLAH yataimaka yace kicigaba da addua kidaina kwanciya ba alwala harda shi ke kara sawa mutum na mugun mafarka mafarkai
na ce InShaaAllah xan kiyaye
natashi nafito balaifi nadanji damadama da yaya Yusuf yamun wann bayani
natadda Jennifer najira na nashiga na hau muka tafi
mun isa makarantar muka tadda Mrs Yusuf itama ansauketa waige waige take da alama nita ke neman ta inda aka sauke ni tunda duk sati motar kalakala ake kawoni wnn umurni Buf ne bansan me hakan ke nufi ba ga ko wacce mota da na urarta
shidai komai da na ura yake aiki kamar wani mara gsky ta hangoni taxo ta rungume ni tana murnar ganina
muka shiga makarantar akai assemble da mu muka shiga aji muka fara daukar lecture
mun fito break take mun tambayar banda lpy ne nace mata lpy lau nake danaga tadamu ne na gaya Mata mafarkina tayi shiru alamar tunani can tanisa tace mun me kika fahimta amafarkin nace oho nidai har yanxu banwani fahimci komai ba tunda meya hada aunty xee da ahalinn Buf GIANT
tace RUKAYYA KE MATAR BUF CE ANDAURA AURAN DA DADEWA
afirgice natashi tsaye nace me kike nufi matar yaya tace mun kwarai ni shaidace akan haka mijina yana cikin ss na farin kayan da mijinki Buf ke aiki da su
Nace Amma bakince mun Pharmacy bane tace kwarai kuwa nace to taya hakan takasance tace mijinkine yahadani dake akan inwayarmai dake sbd mijina da suke tare dashi abokaine
_______________________
ABIN YABO BOOKSHOP
Kasuwar Rimi Kano
Tel: 07038339244
SANADIN SON BANZA
By:
Shamsiyya Daheeru
(((28)))
Mijinki ya bude ma abban muhsin p harmacy a England dinnan shiya mun registration a makaranatar nan da harda dogon hijabi xaibiya kamar yadda yabiyamaki abban muhsin yace kudin xaiyi yawa ya barni da rolling namafi jin dadinshi
Rukayya auranki da Buf yasamo asaline alokacin da Buf yaje yana bin kididdiginku acikin jahar katsina kakanku na wajen uwa shiyayita rokon Buf da kar yace xai dau mataki akanku kamar yadda aka wa kanwarshi yana rokanshi da karya miki fyade yataimaka imma xai kashe ki ya kasheki cikin mutuncin ki wato aure
Buf da baiyi niyyar daukar maganar da muhimmanci ba amma ganin tsohonnan yatada hankalinshi yana ta rokwanshi akan karya lalata maki rayuwa shiyama kashe shi yabarku kuyi rayuwar ku yarane baku san duniyaba hajjo kuwa kakar taku ta wajen uwa kenan ciwonta na xuciya yaso yatashi
nanne Buf yatausaya masu yace tom xai kyaleku amma da sharadin sai abbunku ya mika wuya gareshi
Buf yajuya yai tafiyarshi bayan kwana biyu suka kara komawa garin katsina Dan suje kauyen su Abbun suyi bincike alokacin yana tare dasu abban muhsin
abban muhsin shima sojane Amma na farin kaya shi yakaranci fannin pharmacy ne idan baki mantaba lokacin da akakawoku mansion dinnan ai da sojoji biyu kuka shigo daya yana da magana dayan baida surutu ko tom mara maganar shine abban muhsin
Koda suka koma katsina dama da yaya Yusuf sukaje suka barshi acan tom sai yabiya saboda tsohonnan yabashi tausayi ga itama matar tana kwance kuma imbe mantaba yaji kamar ance ciwo xuciya gareta
cema dreban yayi yashiga anguwarsu umminku sukaje gdn suka tadda yan tsirarun mutane ga liman
Gaban buf ne yafadi karfa ace matar nan ta mutu ya fito asukwane yadoshi gun Amma abun mamaki saiyaga kudi da goro da alama kamar daurin aure ne ake shirinyi yawuce gurin baaba ALHJ
sukayi musabuha yace baaba lpy Yusuf yace lpy lau oga xamu daura ma Rukayya aurene Dan Allah kadubi darajar Allah kaxauna ayi daurin aurennan da kai jiyayi kanshi nasarawa yace Yusuf yaxa ayi rukky yar karamar yarinya kace xa a daura mata aure yace shine solution xamu barta ne taitaxama amansion tana budurwarta ai kaga hakan baidace ba duk da ina da yakinin kai mutum ne mai karamci mai adalci
yace to waxata aura yace kaidai oga xo ka xauna tsohonnan yataso ya yarungumshi yana kuka yace abun da xamuyi yaro shine mafita agaremu baki daya kuma shi xaisa IBRAHIM yabayyana aduk inda yake musamman yaga Rukayya da ciki alhalin yasan yarinayarshi bata da aure
Buf yakamo hannun abban muhsin yace mai mudan xauna muga iya kar mutanenn nan mutumin da ke kulle shi xa adaurawa aure lallai mutanen
yanaji akace Ga Sadakin Rukayya IBRAHIM anbada lakadan ba ajalanba naira dubu hamsin ga waliyyin ango ga na amarya
waigowar da xaiyi yaga ai abban muhsin ake nunawa amatsayin wakilin ango ya juyo yakalleshi abban muhsin yamai murmushi y dage mai gira aka nuna wani mutum amatasyin waliyyin amarya wani yayan babanta ne wanda shikadai yake xuwa wajen su baaba ALHJ ko anji labarin Dan uwanshi ko yaranshi yana yawan xuwa gaskiya tunda shi asalima baya garin duk abun daya faru yana cirani saidaya dawo gd aka gaggaya mai abubuwa ynda suka kasance rasuwar babansu kadai yasani yatausayawa IBRAHIM yakuma sha alwashin Sai yanemar ma ibrahim hakkinshi akan abunda yan uwa suka mai
kafin ya ankare yaji ana ta daurin aure karshedai yaji ana ambatar shi kirkiri BILAL UMAR FARUK GIANT
ambakaa Rukayya amana Allah yatayaka riko
kanshi ya kulle amma yadake can kasan xuciyarshi yaji wani irin sanyin da baitaba jinshi ba arayuwarshi wanda shikanshi baxaice ga dalilin jin wnn sanyiba abu daya ne kawai ya yadda dashi rukkyn shi tatafi rukkyn shi tadawo
angama daurin aure mutane suka watse akabar buf dasu baaba ALHJ
yaya Yusuf yaxo kusa dashi yasadda kanshi kasa saiga baaba ALHJ nan shima yaxo xaiduka masa da sauri yarikoshi yatadashi tsaye ya kalli fuskarshi yaga kukama ashe yake
yaya Yusuf yace oga ka gafarce mu da abunda muka maka dama ko bakaxo ba xaadaura aurenka yau da rukky abisa shawarata danaba masu baaba ALHJ
Akwai dalilai masu karfi dayasa nayenke hukuncin haka
Dalilina nafarko shine Rukayya tana karkashinka baxan taba sowaba ace ka kusanceta bata hanyar aureba yakasance koda xaka mata fyaden yakasance matarka ce
Dalilina na biyyu xanso ace Rukkayya tasamu ciki cikin kuma naka ko banxa kagama da Abbun kahada jini dashi koda xai kara cutar da wani naka baxai iyaba sbd rukayya taxama ahalinku kodan rukayya baxai iya cutar da wani naka ba nasan Abbun yana mana sonda aduniya kafin asamu uban daya keson yayanshi kamar abbun sai anbincika
Dalilina na karshe kila ta sanadin hakan abbu ya Mika wuya kodan halaccin dakamana
Duka bayanan da yaya Yusuf yayi ma Buf ya fahimce hakan
Baaba ALHJ yace nikuma sbd halaccin da kai ma jikokina wanda cutar da mahaifinsu yamaka baka biyeshiba kadau fansa maimakon ka dunga axabtar dasu Amma kabisu da alkahiri shiyasa na mara bayan wannan aure sbd kai mutum ne adali mai gsky nasan INSHAAALLAH rukayya baxata taba danasaniba har abada aurenka alkhairine yarona ban gudanardashiba sai Dana kwana uku ina istihara nahango alkairai dayawa yarona Amma kayi hakuri mun maka katsalandan arayuwarka kuma munsan ahalinka baxasu taba yadda da wannan alamarin ba amma me nariga andaura aurennan xaka fuskanci kalubale dayawa saidai Alkhairan daxasu xo daga baya sunfi yawa yarona xakai alfahari da Rukayya domin jinin mamansu na arxikine
Buf dai yayi shiru yana bin baaba ALHJ da kallo da kyar dai yaciri baki yace tom kuyi tamana addua baaba na karbi auren Rukkayya ALLAH yasanya albarka
Yaya yusuf da baaba ALHJ har kuka sukayi nadadi hajjo ma dataji labarin tayi farinciki kamar me
yace alfarma daya nake nema Dan Allah kada kufadi ma Rukkayya aurennan sai komai ya kankama sannan kuma wani hanxari baguduba kwanannan momyna xata auramun wata yarinya dn gsky r magana imban auri yarinyar nan ba tofa xan iya samun matsala da ita
Baaba ALHJ yayi saurin cewa assha ai ba afatan haka kowanne da ai burinshi yagama da iyayenshi lpy kaje kawai bamatsala
😂😂😂su Hjy rukky ashema kune uwar gd😜
Daya tashi yaxube masu kudi masu yawa yace xaije cikin kauyensu Abbun shine sukatafi da wanna Dan uwan Abbun mai suna Ahmad yamai jagora suna tafiyane ma yajuyo ya kalli abban muhsin yace ya akayi hakan takasance harda bada sadakinka da mun walittaka yace lokacin da akema bayani muka kebe da baaba ALHJ yake gaya mun xaa daura maka aure da rukky ya nake ganin ba matsala nayi wani tunani naga tunda muke da kai baka taba kawo wata mace a mansion ba har tashiga palace sai ita ko yan uwanka imba rukky marigayiyaba bantaba ganin kayi saving din wata maceba bayan ita ko su ummita danaga anayawan xuwa dasu bakayi saving dain sunan su akwanfuta ba sai ita nikuma tsakanina ga ALLAH hadinkawai naji yamun nakuma lura da yadda ka ke yawan saima yarinyar nan kaya kuma kayanma jallabiya duk inda mukaje wani aiki saika saimata abu innai magana kace sadaka kake bata sbd taci sunan marigayiya
gsky akwai boyayye n alamari wnd da ga kai sai Allah kuka sani yakarashe maganar yana dariya Buf yayi murmushi ya basar da maganar yace banxa Dan sa ido
Sun isa kauyen su abbun sun tarda gidan yakara cika da batsewa da yaya
sukayi sallama akamasu iso aka budemasu wani daki aka shimfida masu tabarma aka kawo masu ruwa da abinci
Karramasu ake bil hakki da gsky musamman da aka ga motocin da suka xo dasu ga kuma suna tare da Amadu
Amadu yashiga sasan babbn yayansu yamai bayani bakine daga cikin gari sunxo kan maganar ibrahim gsky yaya iliya ka fadi masu gsky kuma Banda sharri Dan nasan halinka musamman kaga kudi
Yaya iliya yace to Dan banxa baxa afadi gskyr ba fashidai uban kowa yasan ibrahima Dan fashine har ajarida ana bugashi to meye kuma na boye boye
Amadu dai yace adai ji tsoron Allah yace waikai amadu wanne irin raini ne ketsakanina da kai tunda kadawo ciraninnan kanka yakarawayewa kake kawao mana rainin wayau matarka fa da ka aura abirni haryanxu kaki ka kawota ta gaidamu Wai saita haihu sa boda tsabar raini Allah mayasa andaura auran
Amadu yace eh koma dai meye naji muje dai
Haka iliya ya iso Sai sa babi yake kamar mahaukaci
yana xuwa yayi sallama ai yana hada ido da Buf yanatsu harda dukawa Wai xai gaisheshi sbd tsabar rudewa da kuma kwarjini daya mai
nan dai yadakatar dashi tahanyar daga mai hannu
yace bashi yakawoniba nan dai yadan daidata kanshi yanda xaiji dadinmai wayo irin na jamian tsaro yace malam iliya yakuke da ibrahim aikafin ya ida yacea ai ibrahim mundade da cireshi daga cikin jerin yan gidannan
Yace mai
Meye dalili nan yashiga raftakomai karya da gsky game da Abbun harda cewa tun yana karami yake sata sharri dai kalakala yama Abbun Wanda yasa Ahmed harda kukanshi najin irin kaxafin dayaya iliya yawa Abbun
Shima Buf naxarinshi yayi tukunna yacigaba da rubutu wani abun arubuta wani kuma saidai akyale Dan dagaji sharrine hakandai suka gama sukaxo tafiya amadu yace Dan Allah oga kar kayadda da maganar yaya iliya walh harda sharri buf dai murmushi yayi yace kar kadamu ita hukuma ai bamahaukaciya bace
nan dai yamusu gdy tare da kara bashi hakurin auren da aka daura bada izinin shiba wani murmushi yakuma yiwa amadun wanda baxakataba sanin meye maanrshiba sai shidayayi
hakan sukadawo Amma bai biyu ta wajen su baaba ALHJ yawuce yola ba adade ba aka daura mai aure da ummita kwana daya da bikin yayi tafiyarshi Dan ko events kodaya baitsayaba
Wannan shinelabarin aurenki da Buf kamar yadda abban muhsin yabani labari gashiyau nayi katsalandan na fadi maki
ina fata xaki cigaba da boye wa kamar baki saniba
hawaye ne dankare afuskana narasa na meye ne