Showing 48001 words to 51000 words out of 107151 words
lafiya shine Zainab ta koma Abuja ba bu abunda ya faru Ishaq yace na Fad'a miki kada ki kunyata sa agabanta yasan Halin ki baki da Tunani wani Lokacin kina jina ko..?
Idanuwa sun kawo ruwa ammh sai na maida su cikin Rawan murya nace"Eh..e..Naji"
Sannan ta saki kunnena tana fadin"Sannan ki yi wanka ki d'an gyara jikin ki in tazo ta ganki wannan yarkace yarkacen shi zai kunyata sannan yaran nan suma ki yi musu wanka ki sanya musu kaya masu kyau kina jina ko..?
Nan ma kai na gyada mata key din Shashen nasa ta ciro a jaka ta bani na saka Hannun Biyu na karba sannan ta kara da cewa"Zaki yi musu girken girken Tarba sosai yace tana son Sakwara da miyar agusi,Sannan ki yi mata kunun aya da Ferfesun kayan ciki,ki soya mata Naman kaza ki yi pepe dashi"
Kaina na kasa ban dago ba nace"kayan abincin mu duka ya kare shinkafa kadai garemu"
Bata Damu ba ta mike tana fadin"Daman ai kamar ya san zaki kawo korafin babu komai anjuma Jamal zai kawo miki Cefane..Wlh Tallahi Fa'iza in kika kuskuere mganata ki ka bamu kunya gaban Zainab sai kin Raina kanki ki kuma sani ki kara Sani matsayin ku ba D'aya ba Zainab yar gatace gaba da baya sannan yar boko ce mai kyau yar babban gida"
Har Haraban gidan na rakata tana kara ja min kunni da kara Jaddamin matsayina sai naji ban damu ba Domin ko bata fada ba ban isa na Hada kaina da wacce suke kira da Zainab ba,na ganta a hoto na kuma san ruwa ai ba'asan kwando ba ne.
Nayi kokarin yakice duk wani abu dake cikin raina Hankalina ya tafi kan Ahmad da Zazzabin jikinsa yayi zafi panadol na ruwa nake basa shima Sauran na Musty ne da yayi zazzabi kwanaki Ya Ishaq ya siyomin Hankalina duk ya tashi,ga shi yana ta zawo bani da pampers sai napkin nake yi mai kafin Safe ya bata kaya da yawa ina tashi da wankin na tashi,Sai da na gama tsabtace sa sannan na yi musu shirin Tafiya Hadda.
Saboda bani da masaniyar sanda Bakin da zasu iso,Bayan tafiyar su sai ga Jamal ya kawo min cefane nake tambayansa ashe bai koma ba..?
Sai yace min bai koma ba sai sati na sama shima ko zama bai yi ba yayi min sallama ya tafi.
Sai da na fara zagewa na gyara Shashensa,tas na turara turaren wuta mai kamshi sannan na gyara Falon da Sauran Dakunan daidai yadda zan iya sannan na Fad'a Kichen Hankalina ya kwanta Ganin jikin Ahmad yayi sauki har ya samu barci.
Cefane ne da yawa saboda bakuwa zata zo shiyasa aka siyo aka kawo har da Lemuka da ruwa kwai,Dankali Doya,Kayan lambu taliya macaroni da Buhun Shinkafa sai Couscouss,na Sauke komai a muhallinsa har da aya nagani Saboda ai Anty Binta tace Zainab nasan kunun aya.
Banji kyashi ko mugunta ba na zage na fara aiki kan jiki kan karfi miyar Sakwaran na fara yi sannan nayi ferfesun kayan cikin araina ina jin Dadin Dalilinta yara ma zasu samu chanjin abinci.
Na zuba a kololi na rufe naje nayi sallar azahar na zauna na Huta saboda ina Tunanin sai yammh zasu shigo,ashe ma sun zo garin gidan Mama suka fara sauka Badariya ta shiga makaranta sai ta Biyo ta iskeni ina makarda ayan a blander dina wacce Dakyar ma take yi tana yi ta na mutuwa ta tsufa duk taji jiki.
Tana ta fadamin uban kayan da Zainab din ta kawo ma su Mama har da ita an zo mata da abaya ni dai sai dai yake na kasa cewa komai.
Bata jima ba ban yi sakwara ba Ferfesun ta Diba taci sannan tayi sallah Tatafi jin sun iso yasa na mike na Cigaba da aikina kafin La'asar na gama komai hatta dakan sakwaran,nasha wahala sosai ga Ahmad a baya na ya tashi ya saka Rigima Dole na goyasa haka na yi ina yi ina Hutawa ina Haki,Kazan a karshe na Soyata kamar guda biyu ce ta Turawa sannan nayi pepe chicken na shirya komai na ijiye anan kichen din sannan naje nayi wanka na Sauya kaya na saka Atamfa ta riga da Sikat,ko Hoda ban shafa ba domin bani da ita,ban kuma ji ina son na Burge kowa ba sanin ko nayi bazan burge kowa ba.
Karfe hudu daman nace Haruna yaje ya Dauko min su Amir,Shima din yana da Hakuri da Darajan makota wajen wata biyu Ya ishaq bai basa kudin sa,ina Tunanin ranar da yagaji ya daina kai su sai dai na kai su a kafa kuma akwai tazara mai yawa Tsakanin gidanmu da makarantar tasu.
Suna Dawo na taya su suka cire kayan makaranta ko alama ban gaya musu Babansu zai dawo ba Na riga daman na Dibar musu sakwaran ni dai ko ban ci ba,su dai su samu su ci,daki na jasu sukaci achan kada su ci afalo su lalata Su shigo fada'n komai ya Dawo kaina na shiga uku.
Bayan sun gama Daman sun yi sallar su a makaranta,Sai na saka musu Sabbin kayan su Anum nata Murna Amir ne yace"Umma anguwa zamu?
Sai nayi masa shuru ban ce komai ba sai na Tuna naji wani malami yana mgana kan tarbiya yara yace kada yaro ya jefa miki tambaya ki yi shuru to a ransa zai saka wani abu.
Sai nayi saurin cewa"Sabuwar Umman ku ne zata zo Amir"
Dukkansu suka bini da kallo ban damu ba na cigaba da fadin"Tare da Daadan ku zasu zo in kuka ganta ku je ku gaisheta itama Umman ku ce"
Anum da Amir suka Dagamin kai Musty na chan na wasa da kwalliyar jikin Yan kantin da na sakamai riga da wando.
Hatta Ahmad da bai jin Dadi na sakamai yan kati riga da wando,nayi mai Napkin duk da zawon yayi sauki ba kamar jiya ba na goyasa Tunda baya jin dadin jikinsa har alokacin.
Su dai yaran suna ta Tsalle tsalen wasan su ni kuma ina zaune nayi jugum ina Tunanin wani irin Tarba amaryan Ishaaq zatayi min..?
Sannan wani zama zamu yi da ita acikin gidan nan..?
Nayi zurfi cikin Tunanina naji Amir a saman kaina yana fadin"Umma wayarki umma."
Nayi firgigit na kallesa wayatace a Hannunsa ana ta kira ya mika na karba sai da gabana ya fadi da naga Sunan Ya Ishaq na kirana cikin Rawan jiki na Daga kiran tun kafin nayi sallama naji muryansa cikin Kaushi yana fadin"Ina kika kuma jefar da wayar ina ta kiran ki baki D'auka ba..?
Cikin yanayina nace"Ban ji ba ne.."
Karamin tsaki yaja kafin yace"Ina fatan kin gyara ko'ina..?
Yanzu zamu baro gidan Mama"
Kamar yana ganina na gyada kai sannan nace Allah ya kawo ku lafiya
Bai ko amsamin ba ya katse kiran ya barni da waya a hannu ina Tunanin mafita da farko wlh jikina bai saki ba sai da ya kirani yace gasunan zuwa naji gabbaina sun saki jikina ya fara rawa ina nan zaune ina fama da Faduwar gaba naji kamar ana taba Kofar falo ko Hon dinsa banji ba ballatana Shigowar Mota,to ina ma nake da karfin jin ballatana,yadda hankalina ya bar jikina raunannun kunnuwan nawa ba su saka naji ko motsin shigowarsu ba.
Sai da naji Sallamarsa da mganarsa Su Amir na dago na kalla basu bi ta kaina ba suka fice da gudu suna kiran sunansa Daada kamar yadda suke kiransa.
Ni kuma ina zaune na kasa tashi Jikina gab gab yake yi kamar mazari gabana ya fara Dif Dif kamar an sakamin Wutar lantarki ji na nayi na kasa motsi sai yanzu nake jin yanayi na ba Dad'i ina Tunanin da wani irin kallo Amaryan tasa zata karbeni,?Kamar acikin kaina naji yana Kiran sunana a kausashe kamar yadda ya Saba.
Sai na zabura na mike da Hanzari Daidai Anum na shigowa Dakin ta fara jan Hannuna tana fadin"Umma Daada na kiran ki"
Kamar rakuma da akala haka Anum ta rika jan Hannuna har Tsakiyar Falo inda Ishaq da amaryan suka samu mazauni saman kujera mai zaman mutun biyu Amir na jikin Babansa Musty na Dauke ajikin wata Farar mace Doguwa Lalle tsarki ya tabbata ga Allah shugaban Hallitun Duniya.
Lalle gaskiyan su Anty Binta ne kada na Had'a kaina da zainab,tazaran kamar sama da kasa ne a wajen nisa ashe a Hoto ma an rage mata kyau da Haske kamar balarabiya tana sanye da Wani leshi daga ganinsa mai Tsada ne doguwar riga taci Daurinta gashinta ya zubo har gadon baya Fuskata Dauke da kwalliya mai kyatarwa kafafunta da Hannayenta Sun ci kunshi Lalle baki da Fari kamar don ita ma akayi zanen Saboda yadda kunshin ya haskata kafarta da Takalmi daga ita har Ya Ishaq basu cire takalmansu ba har zuwa Tsakiyar Falon.
Kanta na kasa tana ma Musty wasa yana mata gauranci bata san da ni a Falon ba ni kuma kawai ita nake kallon Sakin Hannuna Anum tayi ta nufi Babanta tana fadin"Daada Umma"
Shima sai Lokacin ya Dago yana kallona ina ganin sanda Fara'arsa ta Dauke kamar yaga mutuwarsa hararata yake yi kasa kasa ni kuma Chanzawarsa nake gani yayi kiba kamar bashi ba Daga gani ya samu kwanciyar Hankali sosai.
Na kasa gaba ballatana baya sannan bakina yayi nauyi shine da yaga haka ya D'aga baki yana fadin"Haka ake tarban baki a karofi ko Fa'iza..?
Sai alokacin ta Dago kanta muka Hada ido hudu da ita ni dai a bangarena sai naji na muzanta ni bansan yanayinta a bagaranta ba sai dai ban gane yanayin da take ciki a Fuskarta ba.
Tayi saurin Shanye mamakin ganina ta kallesa tana fadin"Maman su Amir right..?
Tafada tana bin sa da wani irin kallon da Sai da na kauda kaina kai ya gyad'a mata yana fadin"Yes Fa'iza"
Dukkansu a tare suka sakarmin ido sai naji kafufuwana na rawa lojaci d'aya sun kasa D'aukana sai na bi ra'ayin su na Durkusa kaina na kasa cikin yanayina nake fadin"Sannun..Sannun ku da zuwa an zo lafiya..?
Bakina har rawa yakeyi Ta kalleni ta kara kallona sannan ta kallesa ya gyada mata kai Cikin Zakin muryanta da ta karye da Turanci tace"Hy Am Zainab Nice to mee u Fa'iza"
Tafad'a cikin wani irin Turancin da na kasa ma jinta ballatana na gane ina jin yana mata mgana kasa kasa ban ji me yace ba nadaj ji tace"Oh sorry Honey..Kiyi hakuri Fa'iza ban san bakyajin Turanci ba kina lafiya..?
Yasu Amir ina Ahmad ko shi ne a bayanki..?.honey goye kada kafafunsa sun lamkwashe ita kuma ta samu problem da kirjinta fa"
Duka alokaci daya ta fad'a,kunnina na kasa yasa naji wasu daga cikin mganar nata sannan na Dago kaina ina kallonsu jin nayi shuru yasa yace mata"Tun kafin mu taho na fada miki yanayin Fa'iza bebiya bataji sosai sai kin yi mgana da karfi sannan zataji jiki Honey"
Kwabe Fuska tayi kafin tace"Really..?
Kai ya gyad'a mata kafin yace"Yes bata ji ki ba sai kin d'aga murya"
Ta kalleni cikin Tausayawa kamar taga mai bara tace"Ayya am sorry"
Ni dai kaina na kasa ban ce komai ba kawai sai naji tace"Whta is bebiya Honey..? I did get u..?
Da Harshen Turanci naji yana mata bayani bana jin me yakefadi sai dai ina gani tana kallona tana d'an kwabe Fuska gani nayi bazan iya jure ganinsu ba yasa na mike da Hanzari zan koma Daki Ishaq ya Dakatar dani da Fadin"Kin ga Kwantomin Ahmad"
Ba musu na karisa na kwantomai na mikamai har ya fara barci su Anum kuma sun samu Chaculate basu ma bi ta kan mu ba.
Kallona yayi lokacin da yake karban Ahmad yace"Ki bude shashena ki kwashe kayan zeey da nawa zuwa chan"
Cikin rawan jiki na koma Daki na Dauko key din ina ganinta tana bina da kallo,ni dai na bude Dakin nazo na Rika daukan jakunkunan da suka zo dashi sai ta karshen ne zan Dauka tace"No.."
Sai ta juya tana fadin"Honey tok to her kasan ban iya mgana da Karfi ba..Tsaraban Kids d'ina ne"
Shi ya fadamin tace tsaraban yara ne sai na kalleta cikin yanayina ina fadin"Sun gode Allah ya saka da alheri"
Ta amsa da fadin"My pleasure"
Mganar abinci nayi yace sai sun yi wanka sun yi sallah tukunnah Jikin Ahmad dayaji zafi yasa yace min ba shi da lafiya ne na dagamai kai sai ya kalleni yana fadin"Meyasa baki fadamin ba.?ai da ko Jamal yazo kun je asibiti an dubasa".
Nidai ban ce komai ba itama kuma wayarta ta Dauko a wata karamar jaka mai kyau tana Dannawa kafin ta mike tana Fadin"Honey am Tired ina son nayi taking Shower'
Mikewa yayi yabi bayanta yana fadin"Me too duk a gajiye nake"
Ina kallon su suka shige suna rangaji Jikinsu na Dukan juna karamar jakar Hannun Zainab Ishaq ya amsa ya rike mata ita kuma sai lamkwashewa take yi tana Turancin da bana ganewa.
Su Amir kuma sun samu Chaculate basu lura ba na Dauki jakar da tace Tsaraban yara ne zuwa cikin Dakina na Bude naga kaya masu tsada Kala biyu biyu na Anum har da riga da wando da takalma ni ma har ni naga Doguwar riga da pakistan riga da wando sai naji kayan basu burgeni ba na Tattara na ijiyesu na fita nace su Amir su yi alwala an kira sallar mangariba.
Tare da yarana muka yi sallar mangariba muna zaune muna azkar Ishaq ya leko ya sauya kaya zuwa Jallabiya yace na kawo abinci,da Hijabin da nayi sallah na shiga Kitchen na Fara Daukan abincin nasu zuwa Shashen megidan basa Falon suna ciki na gama jera musu komai na Fice na koma D'aki duk da cikina na jin yunwa ammh na kasa cin komai a fatar bakina nake jin abinci bazai iya shiga ba sai kawai na sha Ruwa na koma ma kishingid'a ina kallon su Amir nata wasa Ahmad yayi barci,ina zaune a wajen har akayi sallar Isha'i sai na mike nace su bar wasa su sake yo alwala suzo muyi sallah
Bayan mun idar Anum nata rigiman zataje wajen Daada dakyar na lallasheta da yayi barci,kafin su kwanta sai da suka kara cin abinci sannan nayi musu shirin barci sai da sukayi addu'a na tayasu suka Tofa sannan na baro Dakin nasu na koma nawa Ko barayin Shashen Ya Ishaq ban kallah ba Tunda suka shiga Ciki ban kara jin motsin su ba.
Ni kuma na kasa barci da ya fara Fizgata sai na farka gajiya nayi da juyi na shiga tiolet nayo alwala nazo ina ta nafila sai wajen uku na Dare na kwanta shiyasa na makara sallar asuba rana ta farko da Ya Ishaq bai fito ya tara su Amir sun tafi masallaci ba Amir sai fadi yake yau Daada bai je masallaci ba ne Umma..?
Sai nace musu yaje yaga suna barci ya kyalesu har nayi musu shirin hadda nayi abun karyawa Haruna ya Dauke su ya kaisu basu fito ba yaran dakyar na janye su suka tafi batare da sun ce zasu je gaida Daadan nasu ba.
Suna tafiya nayi ma Ahmad wanka na shiryasa nima nayi wanka sai nasha Tea kad'an naji cikina ya Toshe Breakfast din Amarya da ango a kicthen na bar musu komai na shige D'akina araina nace me yasa zan damu..?Ai ya jingine auran mu alfarma yake min da nake zaune ma agidansa yana ci da ni.'
*Littafin KANA NAKA book 2,paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*
*Janafty**KANA NAKA..!*
*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewa book:Jamilaumarjanafty*
MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT Y'A SKWATO__SAKINA HASSAN 08066726866
INA MATA Y'AN KWALISA MASU SON GYARAN JIKI MACCE DA TASAN KANTA KULLUM CIKIN GYARA TAKE
INA MATA MASU FAMA DA RAMA KU KINSA KAYA BASU KAMA JIKIN KI 😫
INA MATAR DA ADDA JIKI BAKI DA HIP BAKIDA BAYA IN KINYI DRESS BAYANKI A SHAFE
INA WADDA KE FAMA DA ZUBEWA NONO KU KE BAKI JIN DADIN GANIN SU KAMAR SILIFAS
KINYI TA GYARAN BRST HAR KIN GAJI HJY TA GYARAN BRST WAHALA GARESHI DUK WADDA TACE MIKI GA MAGANIN BRST DA SHA ZAIYI TO KARYA TAFADA MIKI GYARAN BRST YANA SON JUREWA DA DAGEWA IN KIN FARA BA'A TSAYAWA INSHA ALLAH SAI KIGA SUN ZAMA NORMAL
MUNA DA INGANTATA ZUMA BRST DA MUNKA SARRAFA DA KAYAN ORGANIC HERBAL SU MACA DASU AGUAJE WADDA INDAI KIN RIKE TA INSHA ALLAH ZAKI GA SUN CIKO SUNYI KOSHI RUBA 2 KU 3 SUN ISA YAZAMA MIKI YADDA KK SO 4K
MUNA DA GARIN HIP DA BRST YAKE GYARA DA GYARAN JIKI DA KARIN NIIMA YAKE YI 4K
MUNA DA INGANTATA ZUMA TA HIP ITA MA MUN SARRAFA TA DA KNGAN TATUN KAYAN ORGANIC HERBAL DA KE FIDDA MIKI HIP 6K
MUNA DA ZUMA KIBA WADDA ZAKIYI FRESH DA BULBUL ITAMA RUBA 2 KU 3 ZATA YIMIKI YADDA KK SO 2K
MUNA DA GARIN GYARAN BRST DA KARIN NIIMA SHIMA GUDA 2 KU 3 ZAKI SHA 2K
GASKIYA DA AMANA ITACE NASARAR.MU
MUNA AIKA KAYA KU INA CIKIN YARDA DA AMINCI
MMN MUJAHID __SAKINA HASSAN MUNA SOKOTO DA KEBBI 08066726866
*🅿️09*
Saboda barcin da ban samu jiya sosai da Daddare ba, ina zuwa shimfid'ar da Ahmad da ya yi barci nima sai na bingire barcin ya fara figata sama sama naji kamar ana kiran sunana a saman kaina Dishi dishi na bude ido na kafin naji ana tab'a kafata guda daya da sauri na mike zaune har wuyan rigana yana dan ja ya yage kada'n,Ido hudu muka yi da Yaya Ishaq da ke tsaye a kaina yana sanye da Riga da wando sauka'kku na zaman gida.
Mitsike ido nayi kafin na fara kokarin saukowa daga kan gadon Lokaci d'aya ina Fadin"Ina..ina kwanaa.."
Amsawa yayi da lafiya lau kafin yace"Ina abun karyawan mu fa..?
Ina kokarin gyara daurin D'ankwalina nace"Yana kitchen"
Juyawa yayi zai fita lokaci Daya yana Fadin"To fa'iza sai na fad'a miki abunda ya kamata ki yi..?
Da kika gama sai ki shigo mana da shi ciki ko..?
Daga haka ya fice nima sai na maramai baya shi ya koma Shashen sa ni kuma na fada kitchen na samu Babban Faranti na hada komai na nufi bangaransa yau ma ba kowa afalon sai dai duk sun yi kaca kaca da kwanukan da suka yi amfani da shi jiya Bayan nasauke na Hannuna ni na Duka ina tattara na jiya na kwashe na kai kitchen na Dawo Daukan jug da kananun kofina