Showing 57001 words to 60000 words out of 107151 words

Chapter 20 - KANA NAKA completed hausa novel

01 Oct 2025

36

Rumgume hannunawana kawai na rasa mafita,kawai sai nace su dakata da zuwa makarantar sai an biya a baya duk Lalacewa yana biyan musu kudin makaranta akan Lokaci basai ta kai ga an koresu ba,ganin sun kwarari sati a agida ba bokon ba islamiyan sai dai nayi musu na Islamiyan agida,Sai suka fara Damuwa suna ta tambaya na Umma meyasa muka Daina zuwa makaranta..?Anum da Musty kenan Amir shi yafi su wayau da sanin me ake ciki,gabadaya na rasa mafita Kwana takwas da Faruwar haka Ranar da yammah sai ga Jamal yazo shima k'wallo suka zo yi anguwan ya shigo gidan ya iske su a bakin Anum yaji basa zuwa makaranta da ya ce meyasa yau basu je ba..?Shine daya tambayeni nace an koresu ne basu biyu kudin makaranta ba yana ta mamaki ya tambayeni ko na fadama Ya Ishaq sai nace mai A'a.
A gabana ya Daga waya ya Kirasa yana fadamai abunda ke faruwa duk da bana jin me yake fada nasan Fada yake yi kuma duk a kaina,Sai da suka gama mgana yace min Ya Ishaq yayi fada kan meyasa ban kirasa na fadamai ba..?
Har Jamal din na fadin"Anty Fa'iza kema da kin kirasa kin fadamai Halin da ake ciki.."
Kallonsa kawai nayi ban yi mgana me zan ce..?ko na fadamai ba ganewa zai yi ba shurun yafi alheri.
Labari har kunnen Mama da Anty Binta na kuma san nasha Zagi da cin mutumci washegari Jamal din yazo ya Dauke su ya kaisu makarantar ya biya komai,Sannan da yammah ya kawo min 20k a bama Haruna kafin ya Dawo na karba nayi godiya da Safe kuma da kaina na shiga na kai mai yana ta godiya nima inayi sai naga ai ni ce da Godiya domin ni yake yi ma alfarma.
Haka rayuwar ta cigaba da gangarawa masu jin dadi suna ji masu jin akasin haka ma sun cigaba da ji,Har azumi ya karato Ya Ishaq bai waiwayo mu ba abun na bani mamaki ace in shi ya manta damu su Mama ai basu manta yana da mata da ya'ya ba ammh sai naga suma basu damu ba kamar hakan ma yafi ye musu,Kayan abinci ko wani sako sai dai ta Hannun Mama ko Anty Binta batagwara,Ni bani da wata Daraja ko kima sai ta zaman ya'yansa kamar yadda yace din.
Tuni yara har sun saba tafiya makaranta ba biskit ba Lemo saboda babu Daga shinkafa sai taliya ake kawo min sai man girki da kayan maggi,duk abunda bazai zama Dole ba ba'a kawo mana shi,Nama ko mun manta rabon mu da shi,ni bana ma jin kaina yaran nake ji sun gaji da Rigima sun Hakura tunda babu sannan Tun suna Zencen Daada har suka hakura suka Dangana ni ce karfin gwiwan su shiyasa bana yarda na Sare ko Raunina ya bayyana agabansu
Ahaka muka fara azumin watan Ramadana,Har kuma muka fara shi muka sauke Ya ishaq bai zo ba,kuma bai taba nema na ba,Ni ma sai na kama kaina sai dai da watan nan mai albarka ban yi barci ba nayi addu'an Allah ya sama min mafita domin ya'yana domin goben su,Kayan sallar yara Sai ana gobe sallah Jamal ya kawo musu Amir da Musty shadda guda biyu sai yan kanti kowanne D'aya d'aya Ahmad ma shadda guda daya sai sauran yan kanti Anum kuma Atamfa da leshi dinkakku sai Doguwar riga guda daya,sai takalma su sai nawa kala daya jal na wata Bakar atamfa,ko araina ban ji zan sakaba sai dai in na zauna ba kaya ammh in dai suturan Ya ishaq ne na hakura da su har abada Tsoffin dai zan cigaba da sawa Tunda  bani da zabi ammh bayan ya jingine aure na dashi na cire ma raina kara Daura wani abu daya fito daga Hannunsa..
Ganin yadda ya kwarari wata Hudu bai zo ya ganmu ba nasan da gaske yake yi ya zabi Zainab a kaina sai ban ji komai ba sai dai naji Bakinciki har da ya'yan sa suma ya jingine su..?
Ban damu ba ni kawai Fafutaka nake yi har akayi azumi akaga gama bamu ci ko tsokar nama ba ballatana su Dankali da kwai sai tsurar abinci kawai nice nake Sarrafa nau'in abincin Tunda Allah yasa na iya sai Wahalan bata mana yawa sosai ba.
Naman Sa da naman kaza Jamal ya kawo min ranar idi da Safe na gyara na soya su Anum nata murna zasu ci Nama sai da nayi musu kwallah ina Tunanin tun yanzu kenan to nan gaba bansan wani Hali ni da ya'yana zamu shiga in dai na zauna ahaka ba,
Allah Sarki Goggo washegarin Sallah sai ga Hafsatu ta aiko da sakon Nama da Cincin da Cake,Naman soyayye da Danye,Sannan da sakon Hijabi Sabo da Anty mariya ta dinkamin da takalmi na karba na rumgume kayan ina kwallah Allah Sarki yan'uwana basu manta dani ba duk da ni ma ban manta da su ba yanayi ne yasa nayi nesa da su ba acikin son raina ba
Ta fadamin daga gidan Tamadina take jiya taje chan ta kwana ta kai mata kaya daga kano Anty Asiya ta aiko dashi sai naman sallah Daga Goggo sai na wajen Ya mariya naji dadin jin Tamadina tana lafiya,Naji takaici bani da abunda zan daga na bama mahaifiyata nima nema nake yi.
Zuwan Hafsah ne ya Debemin kewa Dani da yara Ranar sallah ta uku gidan Mama muka yini sai Dare Ya Ishaq ya sauka shi da Zainab,Anty Binta da Mama suka rasa ina zasu saka su saboda murna mun gaisa da ita sai mamakin ganin chanzawarta nake yi ta zama wata katuwa ta kara gogewa shima gogan ya Sauya kamar ba shi ba har da Tumbi ya sauke.
Darajan zainab yasa da ni da yara da Hafsah ya kwaso mu muka koma gida,Wannan karon ma Shashen sa ta sauka kuma ni na rika wahala da ita da shi,Dalilinta yasa yayo mana Cafane mai rai da lafiya Saboda sai abun take so ake ci acikin gidan,Da kuma zabinta ake amfani..
Hafsah ita kanta da take yarinya sai da ta ga abun bai dace ba ranar da zasu fita yace na shiga na gyara Bangaransa nasa,Suna fita ta kalleni kafin tace"Yanzu Anty Fa'iza bayan Girkin da kike musu har da gyaran inda suka kwana kamar wata yar aiki..?
Ban ce mata komai ba sai ma Dariya kawai da nayi to ai batayi karya ba kamar yar aiki nake agidan nan,Sati Daya suka yi mana suka koma inda suka fito,Hafsah dai ana jibi Tafiyarsu ta koma Karofi Saboda an koma makaranta..
Bayan tafiyar su muka koma Gidan Jiya kamar yadda muka Saba dai,Allah ya taimake ni Matar Ya Isa wajen Goggo ta haihu,yan biyu Dalilin dayasa Mama tace na shirya aje suna Dani,Murna kamar an biyamun aikin Hajji,Dukkamu muka tafi har da Anty Mahma da Halisa da yara,Nima tare da su Amir muka tafi chan na hadu da Ya Mariya,Yaya asiya dai bata samu zuwa ba,naji dadin zuwana karofi Allah yasa kuma Lokacin Tamadina tazo gida na kai mata su Amir ta gansu sai mamakin girman su take yi shi da Anum,Koda wani Lokaci in naga Tamadina sai na tuna da Dan'uwan  ta da akace sun hada Uba,Wanda tunda mahaifiyarsa da Danginsa suka tafi dashi ba"a kara jin Labarinsu ba sai ina Tunanin ko yana Raye..?ina fatan yana Raye domin shi kadai ne shakikin Mahaifiyarmu.
Hajiyar Dala tazo anan take kara Fadin Bikin Diyarta Suwaiba nan da wata Daya,ban saka raina ba Saboda nasan ba barina ma za'ayi naje ba.
Kwananmu biyu muka Dawo gida Mama kuma Yamai tatafi kanwarta Hure mijinta ya rasu ta tafi gaisuwa ta jima tafi Sati biyu Sai Badariya ta Dawo gidana tana kwana in gari ya waye tayi wanka ta shiga makaranta in kuma tana gida mu shiga kitchen tare tana ganin girki Saboda bata iya Sosai ba Tunda bata zaman gidan.
Ita kanta sai da tayi mgana ganin Daga Shinkafa sai Taliya kawai muke da shi tace ban gayama Ya ishaq cefane ya kare ba ne. ?Sai nace ban fada masa ba ashe da ta koma gida Mama ta dawo sai ta fada mata shikenan Cibi ya zama kari wai ina yawo ina fadin Ishaq ya barni da yunwa Mama musamman tazo gidan Har Store ta shiga taga shinkafa ta fara Masifa tana zagina wai wannan abincin dake gidan gidan uban wa zan kai da zan ce ba kayan abinci..?
Har tana fadin nama samu ne mata dadama suna neman irin Damata basu samu ba,Har jamin kunnen tayi kan wai ina albuzuranci da kayan abinci,bai isa ace sun kare ba ko dai ina Saidawa ko kuma ina kyauta dashi Ina mata rantsuwa da abunda zai kasheni ban taba Saida abinci ko nayi kyauta da shi ba,Tace bata yarda dani ba ni bakar Munafukace ni.
Haka tatafi ta barni ina kuka kamar raina zai fita abun ya koma har da kazafin Satan abinci wlh ban taba ba,Ba Halina ba ne sai dai nasan ko zan shekara ina Rantsuwa Mama bazata yarda dani ba.
Sai nayi kuka na ni kad'ai na Share hawayena na riga na yardan ma kaina Allah kadai ke da mafita sannan garesa nake neman mafitana,Acikin wannan tsukin Bikin Diyar Hajiyar Dala ya taso har ga Allah ban sa araina zan je ba sai ga Mama ta aiko Badariya akan na shirya dani za'a tafi kano yara kuna gidan Anty Binta zasu zauna tare da Halisa suna Exams bazata samu zuwa ba.
Ashe ashe da walakin goro a miya,Hajiyar Dala tace azo dani Saboda aikin abinci Shiyasa Mama ta ce na shirya ana gobe biki muka tafi dani da Mama da Anty Binta da Badariya,Su Amir kuma na bar su wajen Halinsa.
Chan muka iske Goggo da Anty Nasara Da Hafsatu Yaya mariya sai adaran da muka isa ta iso,Yaya Asiya kuma ace ciki gareta har ya fito sai korafin na Rame na lalace suke yi  sannan na kara baki na zama kamar tsohuwa ni dai bana cewa komai Saboda bani da tacewa,Tunda muka isa Hajiyar Dala ta Turani Dakin girki,Da Goggo tayi mgana sai Mama tace Saboda na iya ne,kuma don na rika nuna ma ma'aikatan girkin yadda komai zai tafi ni ban damu ba Saboda ai wahala aikina ne.
Ranar Daurin aure da Safe Bak'in Abuja suka Diro Ishaq da Zainab da kanwarta Zuzu wacce bata jin Hausa,ire iren kawayen Suwaibar Hajiyar Dala Hafsah dai da Badariya suna tare,Bamu hadu ba Saboda ina kitchen muna ta aikan abincin yan Daurin aure da ma'ikata,sai Dare na samu kaina ina Dakin da muka sauka nayi wanka kenan,na tada Sallar mangariba su Ya mariya suna Dakin ita da Anty Mahma da ta iso da Safe sai Hafsah,Sai ga Ya Ishaq ya shigo Dauke da Ahmad inaga Hannun Badariya ya karbesa.
Fuskarsa a gintse ganin Ya mariya Ita bata ma san yanayi ba Anty Mahma ce ke mai mgana ya fita ganin ina Sallah ba jimawa ya sake dawowa lokacin na Idar ina zaune ina azkar Tun zuwan su bai neme ni ba sai yanzu na zata ma Ahmad ke rigima ashe wai Girki zan yi amaryansa tace Faten dankalina kadai zata iya ci.,batare da nuna Damuwa ba na amsa masa ya fice Ya mariya ta hade rai ganin ina Ninke Hijabin da nayi salla a harzuke tace"Au ke ce ma baiwar Amaryan tasa kenan..?
Nayi shuru na kasa mgana Anty Mahma tace"Tunda umarnin mijinta ne ki barta taje tayi..Tashi kije Fa'iza"
Da Sauri na kama Hanya zan fice sai Naji Hafsah na fadin"Tab to ai ko achan gidan in yazo da ita..Itace komai nasu abincin su har da gyaran makwancin su"
Ya mariya ta gwalalo ido ni kuma sai na kasa fita na juya ina Harran Hafsah Saboda na jita ina kusa da ita Sanda ta fadi mganar..Anty mahma tace"Kin so ne Fa'iza gaskiya wannan karon ban goyi bayan ki ba..Har da gyaran inda kishiya ta kwanta da Mijina kayyasa.."
Ko da yake naga bakaramin so Ishaq ke mata ba..Ciki gareta naji Anty Binta na fadin shike wahalar da ita mama ai naji da wannan jikan nata Tun kafin ya Fito duniya.."
Ciki..!na nanata acikin raina kafin na girgiza kaina kawai na Fice Daga Dakin ina ji Ya mariya ta fara bala"i ban tsaya jinta ba Domin bazasu taba Sauya ma Tuwo suna ba har Abada yana nan a tuwonsa..
Adaran nan na tike nayi Faten Dankalin Turawa da Hanta,na kuma kai mata da kaina har Bedroom din Hajiyar Dala da ire iren mu bamu da Ikon shigansa.
Ita da kanwarta ne Zuzu,Na ganta duk tayi wani irin fari kamar zabiya tana kwance,Na gaisheta ta amsa tana Dagamin hannu ina ji suna mgana da kanwarta da wani yare shi dai ba Turanci ba kila bayanina take mata naga ta juyo tana min wani kallo ni dai na Fice ban kara kallon inda suke ba.
To bikin ma bai musu dadi ba washegari ya kwasheta suka koma Mama ke yawon fadin Laulayi ne ya sakata gaba mai wahalarwa yace ma ta bar zuwa bikin tace sai tazo Hajiyar Dala kanta ya kara fashewa ballatana da ta kawo kudi masu nauyi ta bata gummuwar Bikin ni duk sai Daga baya nake jin ma sun tafi ban ci Daraja ko arzikin ko sallama ya yi dani ba.
yaya Asiya bata mgana,yaya mariya ne bata iya shuru,Goggo kuma ke Tausanta to ba'a ma yi rabuwar arziki da Goggo karofi da Hajiyar Dala ba Ranar Litini suka koma karofi rayuka ba Dadi,Ba'a san me yahad'asu ba sun dai yi Hayaniya,Mu kuma sai ranar Talata muka koma katsina tsinke na abun Biki ba wanda ya bani ni kuma ban saka rai ba ammh su Mama sun yi guzarin Kayan fulawa da kalanda da jakunkunan rabo kaya dai niki niko ni ko Cincin kad'ai Ya Asiya ta bani na Riko ma su Amir.'

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.


*Janafty**KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT 08066726866

Ni MMN MUJAHID Ina da kayn gyara kala kala na kasa da sama Ina Saida supplement da kayan mata kala kala cikin sauki Mai kama da kyauta

Hjy ta ki ajiye kunya kifitu kiyi bayani matsala ki abaki ABINDA yaddace Dake

Ina matan da ke FAMA da bushewa gaba

Ina maccen da take a bushe kamas ba niima miji sai yasa yawun sa ku BASILIN 😳

Ina matar da kishiya ta tayi mata zarra ga miji ke rasa Ina matsala take

Ina wadda mijinta kamar kurma baya nuna ya gamsu Dake Dan ku ayi ku abari duk dai suke dashi

Shin ke ku y'ar kuwa ga mijin ki baya Yi da sanbatu in kinji ana Fadi sai kece karya ce

Nazo muku da hadin Zuma wadda duk zata magance way'anga matsalolin cikin ikon Allah wanna Zuma ta samu yabo ga duban mutane Sha yanzu magani yanzu ce Banda haufi akanta wanna Zuma tana ta yadda sha'awa Kai tsaye ruba babba 2500 karama 700👌👌

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT MUNA SAKWATO DA KEBBI INA AIKAWA KU INA 08066726866

IN BAKI SHIRYA BA KIBARI HAR KI TASHI SAYE 😀
 
       *🅿️11*

Ta gidan Anty Binta batagwarawa muka fara sauka saboda yara nan muka yi sallar mangariba da isha'i sannan nayi shirin tafiya ganin Mama bata da niyyar tafiya, ni kuma Saboda Dare sannan ga yara,Ganina cikin shirin tafiyasa yasa Mama tace na tsaya su Amir su ci abinci,kamar abun arziki na zauna suka ci abinci nima Halisa ta zubomin naci kad'an na kora da ruwa shuru shuru Mama taga na zauna ban tafi ba tagaji dai tamin mgana sai na fad'amata bani da kudi a hannuna ballatana mu yi na adaidaita zuwa gida.
Shikenan Mama ta fara fad'a ta inda take shiga bata nan take fita ba, ta kalleni tana fad'in"Ke kan Fa'iza ban ga amfanin ki ba..Tun da Ishaq ya aure ki bai Huta da wahalhalun ki ba..da an tabaki sai kice baki da ko asi ke ko irin Dubaran matan wannan zamanin baki iya ba? sai dai komai ki kwanta miji yayi miki tunda ya zama bawan ki"
Anty Binta na gefe ta karb'e da Fadi'n"Kuma Mama komai ne sai ka zauna miji ya baka..?,tsakani ga Allah yana ma kokari wlh,ammh duk da haka ba'a gani barin ma Yan'uwanta da Goggon Karofi,su yi ta korafi kuma in za'a duba tafi duka yan'uwanta jin Dadi ita Asiya ai malamin makaranta take aure ga abokiyar zama ita kuma Mariya d'an kasuwa ne mai karamin karfi ba wacce takai jin dad'in da Fa'iza take yi acikin su ammh kullum gani suke tana cikin Wahala'"
Mama ta ja tsaki kafin tace"To ai duk laifinta ne ita ke fad'a musu haka..Shiyasa nace miki Har ga Allah ban so hada zuru'a da Dangin Asiya da Sidi ba, domin nasan ba Dangin Alheri ba ne na tsiya ne kawai"
Ni dai ina zaune kaina a kasa na kanzil ban ce ba sai da suka gama cin zarafina sannan Mama ta zage jaka ta Dauko Dari biyar ta wurgomin tace sai na tashi na bar gabanta bata son ta kara ganina.
Jiki ba Karfi na mike nayi musu sallama yaran suna D'akin Halisa na Bisu na taho da su ko Tausayi na Mama bata ji ba ga goyon Ahmad ga Amir ga Anum ga Musty kuma na Tabbata Direban gidan zai kai Mama gida ni kuma Saboda k'iyayya bazata iya had'a Hanya dani ba.
Haka na fita ina Tare tare da su Allah ya taimake mu kafin mu isa Titi muka samu abun hawa zuwa gida.
Tunda daman dukkan mu a koshe muke sai shirin kwanciya kawai nayi musu,Tundaga Lokacin kuma Rayuwar mu ta cigaba da gudana yadda take tun farko ba chanji.
Ya Ishaq ko Labarin sa bana ji Wayar ma tawa ta Lalace inaga yara ne suka Y'ar  min ita a kasa ta bare biyu da na Had'a kuma nayi nayi ta kawo bata kawo ba sai na Hakura na tattara ta na ijiye ba mai nema na ni kuma ina gida

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login