Showing 81001 words to 84000 words out of 107151 words
mama bata aiko da kayan abincin ku ba ne..?
Ahmad na kallonsa ammh sai ya lafe ajikina ba irin zumudin daya saba yi mai a baya ni kuma ban kallesa ba nace"Wannan dankalin shi kad'ai garemu shima daga gidan haruna aka bani kyautarsa kayan abinci kuma ba'a kawo ba"
Daga haka na tsuke bakina daga alamu jikinsa yayi sanyi sai ya fara Fadan meyasa ban kirasa na gayamai ba cikin gajiya da korafinsa nace"A ina zan ganka ballatana na fad'a maka..?
Kai tsaye yace"Ina wayarki fa ?ko bata da amfani ne da bazaki kirani ba..?
Ina bama Ahmad Dankali nace"Bani da waya ta lalace tuntuni"
Sai kuma ya kasa mgana,Daganan ya shige bangaransa bansan ko ya kiran Maman ne me tace mai oho yadai fita sai chan kuma ga shi da Cefanen kayan abinci masu yawa wani Lokacin Ya Ishaq bai da matsala ta bangaran hakkin iyalansa da ya'yansa sai dai Mama itace tafi matssala ta wannan bangaran
Daga karshe yace na kwashe Dankalin nan na fitar mai dashi nace tab wlh bazan kwashe ba,Kafin yazo ai shine ya Rufamana asiri sai ya kasa mgana nasan yana ta mamakin yadda wannan karon nake iya maida masa mganarsa kai tsaye ni ko gani nayi tunda alfarma yake min nima sai na fara mai alfarma saboda ya'yan da suka hadamu tsakanina da shi ba Domin zumunci da baisan Darajansa ba.
Yaran ma da suka dawo ko da suka gansa ba su yi wani D'oki kamar baya ba, shine daya lura da haka ya rika jansu ajiki washegari kuma yace bazasu je hadda ba ya daukesu suka tafi yawo ya siyo musu kayan kwalama da duk abunda suke so,Daganan ya sauke su gidan Mama sai Dare suka dawo ashe sallama yazo yi ma su mama zasu tafi india inda Mahaifin zainab ya dauki nauyin su Saboda aduba lafiyar Farhan sai a daran da suka dawo ya fadamin ban san Dalili ba sai naji ban damu ba nayi masa fatan isa lafiya da kuma samun abunda akaje nema.
Washegari Litini ya koma ban ma sani ba ashe ya biya Haruna kudadensa har da na wata biyu anan gaba yana ta basa Hakuri,Harunan ya ke shaidamin washegarin talata da na rako su Amir kofar gida araina sai naji sanyi,in zan fadi gaskiya Yaya Ishaq baya so na ammh kuma yana son ya'yansa kuma bai hadasu da komai ba, sai dai sabon iyalansa sun Dauke masa hankali har akan yara sannan da karin muguntar Mama acikin lamarin tunda ita ake barin ma komai.
Ina nan bansan abunda ke faruwa ba Ba mai nema na kuma nima bani da Hanyar neman kowa ashe Tamadina bata da lafiya ta fito daga bandaki ta zame ta fad'i shikenan jikinta yayi nauyi tun tana gida har an kaita asibitin general na bakin asibiti,Har Yaya Asiya dake kano ta sani tazo ammh ni da nake kusa ban sani ba Goggo ganin ba'a samu inda zan ji ba sai ta Kira Mama a waya tace ta fadamin Lokacin Hafsatu suna Jarabawa,bata samun zama shiyasa ma Goggon tace bari ta kira Maman,Tunda Har Yaya mariya sai da tace tazo ta fad'amin tace ma Goggo sai dai tayi Hakuri bazata iya zuwa ba jin haka yasa Goggo bata matsa mata ba.
Ita kuma Mama da aka fad'amata washegari yamai ta tafi, diyar Kanwarta ta haihu,kuma abun bai Dameta ba shiyasa sai ta sha'afa.
Sai da jikin Tamadina ya kara rikicewa Goggo ta tada Ya Isa tace yazo ya fad'amin nazo in muna da Rabon ganawa da tamadina tana asibiti bata da lafiya.
*Littafin KANA NAKA book2,3.paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*
*Janafty*[6/23, 5:44 PM] +234 706 165 9686: *KANA NAKA..!*
*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
*TASTED & TRUSTED*
*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATUN SAIWOWIN MUTANAN CHADI DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZAR AMARE DA WADDA TAKE SON GYARA KANTA*.
*AN GWADA ANGA INGANCINSA SHIYASA NA KE TALLATA MUKU DA K'ARFIN GUIWATA*.
*ABIN BIRGEWA DA WANNAN SAIWAR ZAKI YI AMFANI DA ITA SAMA DA SAU DAYA.*
*AKWAI FULL PACKAGE, AKWAI RABI, TA YADDA KOWA ZAI IYA SIYA*.
*SANNAN BABU BAURI NA TASHIN HANKALI.*
*DA KANKI ZAKI DAFA ABAR KI, KOMAI ANA SAKA WA A CIKI*.
*SHIN KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR, KO KUWA KE CE KIKE SON GYARA KANKI?*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU*
*08032773332*
*DOMIN KARIN BAYANI, SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*..
*🅿️16*
Na gigice tare da Dimaucewa lokacin da Yaya Isa yake shaidamin Tamadina bata da lafiya ta kwana uku a asibiti bayan tayi sati a gida ba yadda take.
Sai naji na rasa hankalina na wani lokaci, na koma nayi yaraf saman d'aya daga cikin tsofaffin kujerun falona kamar wata kayan wanki.
Hawaye nan da nan suka fara sintiri a saman fuskana kamar an bud'e famfo sai yau na kara tabbatar da cewa Mama bata kauna ta kuma har abada baza ta taba so na ba,Uwa ai ta wuce wasa ace a fad'amata rashin lafiya ammh ta gagara aiko ko Badariya ta shaidamin sai da aka gaji da jirana akaji shuru Goggo ta tado mutum tun daga karofi akazo aka fad'amin, kawai tuna hakan da nayi sai naji raunina ya karu na Fashe da kuka Yaya Isa ya zauna gefena yana fadin"Ki daina kuka Fa'iza jikin da sauki sosai.."
Na dago idanuwana sharkaf da kuka ina fadin"Wa ke zama da ita..?
Kai tsaye yace"Mariya ce..Asiya tazo ta kwana biyu ta koma to bata ma nan aka kai ta asibitin ammh naji Goggo tana fad'amin itama gobe tana Hanya"
Jin haka sai na kara saka kuka ina fadin"Allah ya tada kafad'un ki Tamadina Allah ya baki lafiya"
Ya amsa min da Ameen yana fadin"Ki tashi ki shirya sai na sauke ki a asibitin"
Da sauri na mike jikina yana faman bari har na shiga d'aki na Sunkunci Ahmad dake barci na goya na zura Hijabi sai kamar an tuna min na tuna da su Amir sai jikina yayi sanyi na fito ina Raba ido na neman mafita yanzu in na tafi ina su Amir zasu zauna..?
Ko gidan su Sa'adatu zan ce su zauna kafin na dawo..?Sai dai akwai D'awainiya acikin lamarin yara ba d'aya ba,ba kuma biyu ba har guda Hudu ganin yadda jikina ya kara Sanyi ne yasa yace min"Muje ko..?
Ya fada Lokaci daya yana mikewa sai yaga kuma ban biyosa ba sai ya juyo yana kallona kafin yayi mgana na taresa da fadin"Ya Isa yara na..Su Amir bansan inda zasu zauna ba, in suka dawo daga makaranta ba"
Kai tsaye yace"Su zauna gidan kakaninsu mana"
Sai kawai na koma na zauna ina sharan kwallah Lokaci d'aya ina fadin"Ya isa kaje kawai sai gobe da Sassafe zan taho in sha Allahu"
Shima kansa nasan mamaki yaji da mganata saboda yadda ya ke kallona sai na sake sadda kaina ina jan majina.
Ajiyar zuciya ya sauke kafin yace"Shikenan ki tabbata goben kin taho kin ji ko..?
Yafad'a cikin alamun Tausayawa acikin lamarinsa na gyad'a mai kai sai ya kara kallona yana fadin"Kina da kudin mota ne..?
Sai na kasa mgana shi kuma ganin haka sai ya cire dubu uku yan Dubu Sabbi ya bani yace nayi na mota na karb'a ina godiya na mike shi kuma ya wuce da sauri nace"Wani ma asibiti kace..?
Bai juyo ba yace"Asibitin general da ke bakin asibiti Dutsenmah"
Na gyada kaina ina fadin"Ka gaisheta ka fad'ama Goggo gobe da Safe ina tafe..Allah ya tashi kafad'an Tamadina"
Ya amsa da Ameen ya fice bayan ya kare ma falon kallo lokaci da'ya yana girgiza kansa.
Komawa nayi na zauna in da na tashi na Rushe da kukan,kukan bakinciki da takaiici ace Tamadina ta kwanta jinya tafi sati ban sani ba to ni a wani bingire zan saka rayuwata ne..?
Ahmad da yaji ina kuka shima ya fara Rigimansa na kwantosa na Rumgumesa na cigaba da kuka sai kawai ya rika bi na da kallo.
Haka na yini cikin wani yanayi motsi kad'an sai na daga hannuna sama ina fadin"Ya Allah ga baiwarka chan tamadina kafini sanin Halin da take ciki..Allah ka bata lafiya ka tashi kafadarta"
Ko abinci da na kan yi ma yara da wuri ranar sai da suna gabda dawowa na dora musu farar taliya nace sa ci da mai da yaji,Domin bani da natsuwar yin wani abincin da zai bani wahala su kansu da suka Dawo sun ganni duk a sanyaye sannan fuskata da Idanuwana sun kumbura hatta Ahmad rigimamme yau bai yi min rigima ba kamar yasan bana cikin yanayi mai dadi.
Sun dawo suna murnan an basu resit a makaranta na shedar sun biya kudin makaranta har na Team biyu,Alfarma akayi musu saboda naje wajen sau biyu ina basu hakuri sai wannan lekowar tasa ne yaran suka mai mgana inaga yaje ya biya musu, ko kuma ya tura musu.
Ni dai da yake ba wannan ne a gabana ba ko duba Takardan ban yi ba,nace su adana cikin Littafansu.
Amir ne mai wayau cikin su shi ne ya tambayeni Umma baki da lafiya ne..?
Na kallesa cikin wani yanayi sai na kasa basa amsa,sai da daddare bayan mun idar da sallar Isha'i dukkanmu muna zaune sai na kallesu ina fad'in"Kowanne ku ya d'aga hannu ya ce Allah ka bama tamadina lafiya.."
Sai suka tsaya suna kallona Anum ce tace"Umma wace ce?
Da sauri nace"Ina wannan da ta taba kawo muku gyad'a da su masara har nace muku mamana ne kakarku.?
Suka gyad'amin gabad'ayan da sauri nace"To mahaifiyata ce, bata da lafiya ku yi mata addu'a in dai kuka yi sallah"
Fuskarsu ta nuna jimami Amir yace"Allah ya bata lafiya Umma"
Na amsa mai da Ameen atare muka daga hannu muka yi addu'a da Fatan Allah ya bama Tamadina lafiya.
Saboda tafiyata Dutsenma agobe da wuri nace su kwanta ko karatun Dare basu yi ba na kwana ina Tunanin inda zan kai su Amir su zauna kafin na Dawo na duba na hango ba su da inda yafi gidan Mama dole dai ko naki ko naso chan din zan ce Haruna ya kai su in suka dawo ban dawo ba.
Da asuba da na tashi ban koma ba ina gama shirya su na tafiya makaranta na Dafa musu abunda zasu tafi dashi makaranta,Tunda bani da komai sai nayi Tunanin na Dafa wani abu na tafin ma tamadina dashi,Shiyasa da kaina na saka Hijabi na raka su Amir kofar gida muka gaisa da Haruna na fad'amai zai kai su gidan Mama in suka Dawo da yammah ban dawo gida ba,Mahaifiyatace ba lafiya zan je na Dubata ya yi min Fatan Allah ya bata lafiya.
Na duka ina kallon yaran kafin nace"Zaku zauna gidan mama kafin na Dawo kun ji ko..?
Amir ne ya gyadamin kai Anum ce ta kwabe fuska tana fadin"Umma ki tafi dani"Na shafa kumatunta ina fadin"Zaku je Anum insha Allahu ku dai ku yi ta mata addu'an Allah ya bata lafiya"
Da haka na lallabasu suka tafi da Anum ta fara rigiman kayan sawan su ni kuma naga suna da kaya agidan mama bazasu rasa na sawa ba,Suna wucewa na shiga gidan Sa'adatu muka gaisa na gayamata abunda ke faruwa cikin tausayawa tace"Allah sarki wannan da kika kawo min ita muka gaisa ko..?
Na gyada mai kai cikin wani yanayi cikin jimami ta yi min fatan Allah ya Tada Kafad'a,na amsa mata Daman Nama nake so na siya sai tace min sai karfe tara mai naman bakin titi yake fitowa, sai na zauna muka cigaba da Hira sama sama Ahmad na bayana yana barci,Taran nayi muka yi sallama Daga gidanta na gangara bakin titi daga cikin Dubu ukun da Yaya Isa ya bani na siya Naman dubu Daya na koma gida na Dora jallop din Shinkafa,da nama daman ina da Cabeji sai nayi amfani da shi kad'an sai da nagama komai,na samu wata Tsohuwar cooler dina na zuba abincin aciki,sannan na je nayi wanka nayi ma Ahmad muka shirya tare,Atamfa ta na saka wacce Yaya Asiya ta dinkamana mu hudu,na Zura Dogon Tsohon Hijabina da yasha ruwa,kan duk ya kod'e da Takalmina duk yaji duniya ya d'aga tun wani Takalmi da Anty Nasara ta taba bani ne, yafi shekara hudu ina moransa don ma ban cika yawan fita ba,ai da yanzu bani da nasawa.
Rufe get din nayi da key din gidam,Na rike Dubu biyun da suka yi saura da abincin da na Dafa na shiga nayi ma Sa'adatu sallama sha daya da wani na isa gidan Mama,adaidaita na hau na sallame shi na shiga gidan ba kowa ina ta sallama Ashe Mama na falo tana faman kirga kudi sai dai ta ganni na shigo kamar daga sama hankalinta yayi sama bata ji sallamata ba.
Tana ganina kamar taga mutuwarta ta wani zabura sannan ta saka kudin hannunta kasan cafet din datake zaune,Tana wani zare ido tun kafin na kariso ta tareni da fadin"Lafiya ke kuma daga ina yarkace yarkace kamar yar gudun hijira..?
Gabanta na Duka ina gaisheta ta amsa a gaggauce tana kara fadin"Lafiya..?
Kaina na kasa nace"Dama..dama zan je Dutsemah duba jikin Tamadina ne"
Sai Mama ta gyara zama tana fadin"To ashe jikin har yanzu..?ni Goggon taku ta kira ni tace a fad'a miki na sha'afa tafiya ta kamani zuwa Yamai"
Ina jinta ban ce komai ba sai ta cigaba da fadin"Allah ya bata lafiya"
Na amsa da Ameen shuru dai taga ban tashi ba sai ta fara fad'a tana fadin"Wai ni kam sintirman me kika zo kika min a gabana..?
Da Sauri nace"Dama ina so su Amir zasu zo nan su zauna ne in na Dawo da wuri to..inkuma naga jikin nata yayi tsanani zan kwana shine..Shine nace bari nazo na fad'a miki tunda Babansu baya nan"
Har na gama Mgana Mama na bina da wani kallon banza sai da na Dire sannan ta karbe da fad'in"Daman ai tunda na ganki nasan banza bata kawo ki..so kike bayan na gama wahala dake na kuma dawo na ya'yanki..?to baki isa ba malama kije ki Dubata la'asar nayi ki kamo Hanya,Gida ba kowa Badariya ta shiga makaranta Jamal baya garin nima yanzu da kika ganni Hajiya Barira nake jira zamu fita ban san da wa kike so su zauna ba..Kuma Allah na gani bazan soke fitata saboda ke ba"Ta karishe fada tana tabe baki daman ai nasan za'a rina sai kawai na mike ina yi mata sallama ta bi kulan Hannuna da kallo kafin tace"Ke ke..Wannan abun fa ina zaki kai shi..?
Sai nayi mata kamar ban ji ba kuma na jita naki juyowa ina ji tana fadin"Aikin kenan shiyasa kayan abinci ba sa wata suke karewa ga inda ake kwashewa ana kaiwa ashe "
Daganan na jita sauran mganganun nata ban ji ba Domin na fice daga Falon Idanuwana na kawo ruwa naji Nadaaman zuwa ma.
Sai dai na fita Hakkinsu daga ita har Yaya Ishaq din.
Ni da naso naje tun da Wuri sai gashi sai azahar na isa Karofi chan na fara zuwa saboda ban san d'akin da suke ba,Ina ko zuwa na iske Yaya Isa zai kai su Goggo da matarsa da Anty Nasara Goggo na ganina tace"Ga ma Fa'izan nan ta iso..Sai mu rankaya muma asibitin zamu"
Sama sama muka gaisa na shiga Mota sai asibitin General na Bakin asibiti Tamadina na Female ward ne babban Dakin Yaya mariya muka iske a wajenta da Maman isuhu sai matan ya'yan su.
Muka gaggaisa da tambayan mai jiki sukace da sauki na Ubangiji.
Na kara rud'ewa da naga Tamadina kwance bata motsi numfashinta na sama sama alamun dai tana jin jiki na karisa gaban gadon na tsaya ina kallonta sai kuka na dafa Hannunta da ba karin ruwa ina fadin"Allah ya baki lafiya ta madina"
Goggo ce ta fara bani Hakuri sai na bar gaban gado nayi baya sai yau muka had'u da Yaya mariya tun bayan Tozarcin da Yaya ishaq yayi mata, kaina na kasa cikin jin nauyinta na gaisheta da Tambayan ya mai jiki tace da Sauki sai na sauke kulan Hannuna a gabanta ina fadin"Ga abinci"
Bata kalleni ba tace"Allah ya ba da Lada"
Bamu dade da zuwa ba Nurses suka zo suka fitar damu waje,muka fito baranda d'akin inda mutane ke zama masu jinya da masu Dubiya muma Tabarma Yaya mariya ta shimfida mana muka zauna Yaya Isa ya wuce wajen aikinsa.
Haka na zauna jugun jugum,sai da Yaya mariya tamin mganar salla,Sannan na tuna ban yi salla ba, na mike tace zata rakani masallaci Ahmad ya tashi Lokacin sai Maman Isuhu ta karbesa tace muje mu yi sallan mu dawo su za su yi nasu anan Tunda ga ruwa.
Yaya mariya ta dauko kwanukan da sukayi amfani da shi zataje chan ta wanke sai nayi saurin karb'a muka tafi ,Sallar muka fara yi sannan na yi wanke wanken,muka Dawo muka iske Maman Isuhu na bama Ahmad abinci Goggo ta kalleni tana Fad'in"Yaron nan naki rigimamme ne kuna tafiya ya fara mana rigima"
Ina dariya nace"Goggo har yaye fa kin masa..?
Goggo tace"Nasha rigima dai,don ma yana ganin idon Hafsatu ne. ita ai ya saba ganinta a gidan su"
Sai alokacin na tuna da Hafsah da na tambayeta sai Yaya mariya tace min sai ta taso makaranta zata zo.
Muna zaune ana ta hira sama sama duk rabin hiran na ciwon tamadina ne Maman isuhu tana fadin yadda ciwon ya fara daga zamewarta shikenan abu kamar wasa bata ko iya tashi komai sai an yi mata, suna mganar ni kuma ina faman share kwallah
Goggo tace"Abun ba dadi..Allah dai ya bata lafiya.."aka amsa da Ameen Goggo ke tambayana ashe Mama bata sanar dani ba..?nace bata gayamin ba Goggo ta jinjina kai kafin tace"Allah ya shirya Saudatu"
Yaya mariya na gefe tace"Itama karamar waya ya kamata a nema mata Goggo ace sai arika yin abubuwa mutum bai sani ba, yana chan shi kadai kamar wani mara gata da galihu"
Goggo tace"Haka Isa yace.bari dai komai ya daidaita bazai gagara ba"
Ana cikin tattaunawar ne sai ga Yaya Asiya ta diro ita da mijinta Dauke da kayan Dubiya katan din maltina da Ruwan gora,Ya duba jikin Tamadina bai jima ba ya bama Goggo dubu goma sannan yayi mana sallama ya tafi yana min tsiya da na gaishesa ya rike baki yana fadin"Wa nake gani kamar Fa'iza Asiya?
Tana dariya tace"Itace mana"
Sai kawai yace"Ke kan Fa'iza bakya zuwa ziyaran kano yaushe rabo na da ganinki..?
Goggo tace"Ai in dai Fa'iza ne haka take gidan kowa bata zuwa"
Bai tsawaita