Showing 72001 words to 75000 words out of 107151 words

Chapter 25 - KANA NAKA completed hausa novel

01 Oct 2025

29

fara harkan gabansa yana ta wasa da yar motan wasan yara na Mutsy da suka taho da shi Daga Abuja.
Hankalina ya tafi kan gugan da nake yi ban ji sallama ba,Kuma ko ma anyi in ba an matso kusa dani ba ne bana jin sallamr sai da naji an tabani na Juyo da Sauri har na Tsorata sai naga Tamadina da abokiyar zamanta Maman Isuhu suke kiranta.
Ai basan Lokacin da na watsar da gugan gabana ba na Daka Tsalle na Rumgume Tamadina ina murnar ganinta Cikin yanayin mganarta na Rikeni tana fadin"Faaa...Izzzaa..'
Sakin ta nayi na koma ina Dariya ina musu barka da zuwa,Ahmad ne motarsa ta makale jikin kujera sai ya fara kuka,Tamadina tayi Saurin zuwa ta Dauke sa,Ni kuma na kashe Soket din gugan da nake yi jikina na rawa Farinciki kamar ya sumar dani na nufi kitchen na Dauko musu ruwa na kawo musu ina gaishe su.
Sun sha ruwan Tamadina kuma wanda ta rage ta bama Ahmad kamar ya ganeta ya ko lafe a jikinta shi da ya ke da kiwuya.
Kafin ma na tambayesu daga Ina Mamar Isuhu ta ke shaidamin Matar yaron Uwargidan su ce ta haihu aiki akayi mata tana Asibitin katsina shine suka zo Dubata Tamadina tace su Biyo su yi sallah kafin su tafi.
Aiko naji Dadi,Dakina na kai su suka shiga bayi domin alwala ni kuma na fada Kitchen na fara kokarin sama musu abinci Jallop din Shinkafa na Dafa musu da bushasshan kifin da Yaya Asiya ta kawomin ina ta lallabawa Sauran sa kenan nayi takaicin rashin kudi ko Lemu ban da shi ballatana na siya musu kuma bani da kayan had'a Lemu ko daya ballatana na Had'a musu.
Har Daki na kai musu na iske sun Idar da Salla,Ahmad na kan jikim Tamadina yana ta wasan sa ta kalleni cikin mganarta tace"Suuuu...Saurrraaan...yarrran fa..?
Nace"Suna makaranta Tamadina sai yammah zasu dawo"
Ta gyada min kai Allah Sarki Uwa,uwa ce ko da akan bola take kwana,ita fa uwa ta gwammace tayi ma Abun da ta haifa ko da bazai rama mata wannan alherin ba.
Gyad'a Soyayyiya da Masara gashashiya ta kawo ma su Amir da gurjiya dafaffiya Maman Isuhu na Dariya tace abakin asibiti ta siya Masaran nan da gurjiya.
Ta turamin gabana tace na bama Yara sai hawaye suka kawomin cikin Idona na fara godiya Ahmad dai sai bare mai gurjiya take yi tana bashi yana Mamula da Hakoran sa guda Hudu Biyu a gaba biyu a kasa da suka fitomai.
Falo na koma har sai da suka gama cin abimcin,Sannan na koma naga suna shirin tafiya sai naji kamar kar su tafi ammh ba Dama Hijabi na Dauka muka fito ina Tunanin me nake da shi da zan basu..?
Na duba gabas da yammah ba ni da komai ballatana na basu haka muka tafi waje da su,ni nace su zo na kai su makota na da muke mutumci su gaisa.
Sa'adatu kadai muka samu Habiba bata nan taje gidan su daman yar katsina ce acikin gari.
Sa'adatu tana ganin Tamadina tace min"ga maman ku ko..?
Na gyada mata kai ta gaishe su cikin Ladabi daga jin yanayin mganar Tamadina basai ta nemi karin bayani ba tasan inda na gado Lalurata kenan.
Ita ta fitar dani kunya ta basu siga da yawa cikin wacce take saidawa bani da bakin da zan gode ma Sa'adatun tamin komai shiyasa mata mu daina kuskure domin mazajen mu sun hanamu huld'a da makotanmu sai mu Biye musu mu sani Annabi ma yayi Mgamar Hakkin makota sannan mutane Rahma ne duk yadda mutum yake shiga Jama'a yana da Bambamci da wanda ba ya shiga mutane sosai.
Har bakin Titi na rakasu suka samu Motar Dutsemah,Kunya naji da zasu tafi ban basu ko kudi ba Ahmad har da rigiman Tafiyar Tamadina nace Yaro yasan kakarsa.
Sai da suka wuce sannan na koma gida Ranar cikin Annushuwa na yini kamar an mun bushara da gidan Aljanmah sai dai ina ta kallon Tamadina ta kara ramewa nima tana ta kallona duk sanda na kalleta sai mun Had'a ido,Ina Kaunar Uwata a yadda take domin bani da makwafinta in kuma na rasata har Abada nayi maraici gaba da baya.
Haka kurum in na Tuna da kallon sai naji jikina yayi sanyi a raina nace kodai kallon karshe take yi mim..?
Tuna haka yasa sai da gabana ya amsa da Sauri nace a fili"A'a ba haka ba ne Insha Allahu ba yanzu zaki barmu ba Tamadina."
Da su Amir suka Dawo na basu tsaraban Tamadina suna ta murna sukace min waya siya musu ina Mirmishi nace"Kakar ku"
Sai Anum tace"Mama..?
Sai na kallesu nace'A'a mahaifiyata..Sunan ta Tamadina"
Anum tace"Umma bamu santa ba meyasa ba ma zuwa wajenta..?
Sai na kasa mgana nayi gefe da kaina araina ina auna yadda Ya Ishaq ya Rusamin rayuwata gabad'aya ace ya'yana ma basu san wacce ta Haifeni ba ?
sai kirjina ya karayin nauyi da Dubara na share hawayena na Lallab'e su da cewa zan kaisu su ganta Amir dai zai iya ganeta shima ba lalle ba.
A fili na furta"Na ga ta kaina ni Fa'iza wannan wata irin rayuwa nake yi haka..?



*FA'IZA NA GODIYA TACE KU YI HAKURI KOWANI TSANANI SAUKI NA WAJEN ALLAH TACE MADALLA DA KU MADALLAH DA MASOYAN JANAFTY*






*Janafty**KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT 08066726866

Ni MMN MUJAHID Ina da kayn gyara kala kala na kasa da sama Ina Saida supplement da kayan mata kala kala cikin sauki Mai kama da kyauta

Hjy ta ki ajiye kunya kifitu kiyi bayani matsala ki abaki ABINDA yaddace Dake

Ina matan da ke FAMA da bushewa gaba

Ina maccen da take a bushe kamas ba niima miji sai yasa yawun sa ku BASILIN 😳

Ina matar da kishiya ta tayi mata zarra ga miji ke rasa Ina matsala take

Ina wadda mijinta kamar kurma baya nuna ya gamsu Dake Dan ku ayi ku abari duk dai suke dashi

Shin ke ku y'ar kuwa ga mijin ki baya Yi da sanbatu in kinji ana Fadi sai kece karya ce

Nazo muku da hadin Zuma wadda duk zata magance way'anga matsalolin cikin ikon Allah wanna Zuma ta samu yabo ga duban mutane Sha yanzu magani yanzu ce Banda haufi akanta wanna Zuma tana ta yadda sha'awa Kai tsaye ruba babba 2500 karama 700👌👌

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT MUNA SAKWATO DA KEBBI INA AIKAWA KU INA 08066726866

IN BAKI SHIRYA BA KIBARI HAR KI TASHI SAYE 😀

          *🅿️14*

Tsakanin zuwan Tamadina da saukan su Ya ishaq da amaryan sa Zainab garin katsina kwana biyu ne,Ni bani da labarin suna tafe,Sai da yammah da suka iso gidan nagan su,Ashe wai Mama aka kawo ma Farhan ta gani shine suka zo gayya guda bayan kanwarta zuzu har da wata yarinya mai yi mata reno,sai Iyayanta Guda biyu,ban taba ganin inda iyaye ke rako ya'yansu ganin Dangin miji ba sai akan Amaryan Yaya ishaq na fara gani sai abun bai wani bani mamaki ba ya'yan yan boko ne da suka mallaki dukkan wani kawan duniya.
Shashen sa suka yada Zango dukkansu ni dai iyakata nayi D'awaniya da su kamar yadda na saba na abinci da shimfidar fuska wacce Hausawa sukace ta fi na tabarma.
Har shashen nasa na shiga suna ciki ita da kanwarta mai renon ne ke falo tana Fama da Farhan Yaya Ishaq kuma suna shigowa ya fice bansan ina zashi ba daga gani dai fitace mai muhimmanci.
Hannun mai renon sa na karb'esa ina kallon yaron yayi wani girma kamar dan wata biyar,Tsarki ya tabbata ga Allah nace acikin raina,Saboda ashe a Hoto ban ga komai na kyau da zatin yaron ba sai da na gansa a hannuna Jajir da shi kamar ka taba jininsa ya fito yafi kama da Yaya Ishaq sai dai Hancinsa irin na mamansa ne har da Idanuwan ma kuka yake ta yi yarinyar ta kasa lallashinsa na kalleta Lokaci daya ina fadin"me yasa ya ke kuka..?
Kamar zatayi kuka tace"Ni ma ban sani ba kuma ba yunwa yake ji ba yanzu na basa madaran sa"
Rikesa nayi a jikina ina kara Tattaba jikinsa naji zafi kad'an alamun yana Tare da zazzabi sai na kalleta lokaci daya ina fadin"Kamar da zazzabi a jikinsa bari nayi mai wanka sai a bashi mgani"
Kamar zatayi mgana sai kuma ta fasa ni kuma na fice da shi zuciya ta daya,Daman su Amir na makaranta basu dawo ba,kitchen na shiga na saka Ruwan zafi bayan na goyasa luf kuwa yayi shuru ruwan na zafi na juye a baho na shiga Dakina nayi mai wanka tas da ruwa masu dimi ina cikin yi mai wankan na fahimci Cibiyarsa ne ta dan kumbura ina da wani mgani da Goggo ta bani Tun Ahmad na karami da cibiyarsa ta fara kumbura ina fara shafamai ta koma ta daina ciwo kuma ta Daina kumburin,sai na Dauko daman ban cika banzarta da irin wadanan kayan ba tunda ina da yara na mulke mai Cibiyar da shi cikin kayan Ahmad da suka yi mai kad'an na saka mai riga da wando,na goyasa ram a bayana ba jimawa sai barci ya kwashe sa da shi a bayana na cigaba da Hidima ta Ahmad daman yayi barci ne yana tashi ya kafa rigiman sai na Sauke Farhan dake bayana na goyasa.
Ina Dariya shima na Sunkucesa na Saba a kafad'ana ina fadin"Haba babban mutum ka girma ka bar ma kaninka bambon mana"
Kuka ya fara min na fita da shi Falo na Zubomai abinci na zauna ina basa Shidda Saura sai ga yaran sun Dawo daga makaranta suna ganin goyo a baya suka fara tambayana Umma wa kika goya kamar ma Anum taji Labari.
Ina mirmishi nace"Sabon jaririn Anty ne"
Anum ta daka tsalle tana lekonsa ta bayana kafin tace"Umma waya zo da shi..?
Sai nace"Tare da Daadan ku suka zo da Antyn ku"
Anum ta fara tsalle tana oyoyo oyoyo Daada Musty na tayata Amir dai Dakin su ya shige ya Sauya kaya gudu ta kwaasa zuwa shashen baban nasu nace mata ya fita ta bari ta sauya kaya taci abinci in suka yi sallah sai ta shiga ta gaida Antyn nasu bata da yadda zatayi hakanan ta Hakura ni suka bari da kwashe takalma da jakunkunar su da suka watsar a tsakar Falon.
Anum dakina ta Shige Saboda na maidata da ita da kayanta tare dani,ina shigowa na iske ta watso kayanta kan gado da karfi nace"Anum ba na hanaki watso kaya ba..?
Cikin rigima tace"To umma ban ga wanda zan saka ba ne"
Riga da sikat na Dauko mata na bata ina Fadin"Duk na goge fa kayan nan ammh ji yadda kika wargazasu Anum"
Ganin ban ji dadi ba yasa tace"Kiyi hakuri Umma"
Kanta na shafa ina fadin"Bakomai yar Umma muje aci abinnci"
Musty kuma Amir ya cire mai kayan makarantar ya sakamai, na gida suka fito falo na zubo musu abinci Farar shinkafa da miya,Sa'adatu ta aiko min da Kayan Miya itama daga gidansu aka aiko mata dashi kamar babanta aikin gwari yake yi.
Dukkansu waje daya na Hada musu kamar yadda na saba sun fara ci,Anum da Musty suka fara rigima kamar kullum nace su bari suka ki sai na kalle su ina fadin"Anum zan mai da ke cin abinci ke kad'ai tunda bakya jin mgana"
Jin haka yasa Da sauri Amir yace"Umma ki yi hakuri Musty ke Tsokananrta ki barta mu rika ci tare"
Sai na gyada kai ina fadin"Musty kana son Bulala ne..?
Na fada ina nuna masa hannun alamun duka kafada ya makale dariya nayi kafin nace"To ka daina tsonakar Yaya Anum in baka son duka"
Da sauri ya gyada min kai Lokaci daya yana fadin"To umma"
Cikin Salom mganarsa ,cin abinci suka cigaba da yi a natse ni kuma Farhan dake baya na ne ya motsa sai na mike ina Jijjigasa Daidai da Bude kofar falo da Shigowar Yaya Ishaq bayansa Jamal ne da manyan Ledoji,Nasan har ga Allah bai kalleni ba,ballatana ma yasan wanda na Goya Sannu da zuwan ma da nayi mai ban ji ya amsa ba Jamal ne yake kokarin Sauke Lodijin hannunsa a falon da Sauri ya Juyo yana fadin"Jamal bani Lodojin Hannunka"
Yafada daidai da yaran zasu tashi suna kiran Daada da karfi nace su koma su gama cin abincin su duk da ban kallesa ba nasan sai alokacin ya bini da kallo ni kuma sai na Dauke kaina ba domin ina jin Haushin sa ba sai domin nasan ba ni da wata Daraja a wajensa shiyasa nima na koyi kama kaina.
Jin abunda nace ne yasa ya kalli yaran yana fadin"Ku gama cin abincin ok.?
Atare suka gyada mai kai Jamal ya mika masa ledojin hannunsa ya shige Bangaransa sai da ya shige na Dawo da kallona wajen Jamal wanda ya zauna saman kujera su Amir na gaishesa ya amsa yana fadin"My Childreen how far"
Amir ne ya amsa mai da We are fine Uncle"Dariya yayi yana fadin"Daddy na ya fi kowa gane karatu a makaranta ko Amir..?
Anum ta tura baki tana fadin"Nifa Uncle"
Kallonta yayi kafin yace"Mommy nama tana ganewa itama"
Jin haka yasa ta washe baki Musty kuma ya tayata,Sai alokacin ya Dago muka gaisa,cikin yanayin mganata nace"Ya su Mama..?Daga ina haka da yammah nan..?
Yana sauke ajiyar zuciya na gajiya yace"Wlh Dad din Anty Zainab muka kai Masauki  sannan muka je Restaurant  muka yi oder abinci muka Biya gidan Mama muka kai mata kinsan Mom din Anty Zainab din wajen Mama ta sauka"
Na jinjina kai ban yi mgana ba ya cigaba da fadin"Shine duk najini a gajiye me kuka dafa ne..?
Kai tsaye nace"Farar shinkafa da miya ne a zubo maka ne..?
Kai ya girgizamin kafin yace"Bari mu yi sallah naji an fara kira ma"
Ina shirin mgana Yaya Ishaq ya fito Daga bangaransa, da Sauri bayan sa Zainab ne da kanwarta,Wacce ke jan Hannun yarinyar da suka zo da ita baiwar Allah tana ta kuka.
Ganin su hankali tashe yasa Jamal ya mike cikin wani yanayi yana fadin"Me ke faruwa ne..?
Zainab ne cikin rawar murya tace"Farhan..Ba mu ga farhan ba"
Sai abun ya bani mamaki suna nufin basu ga Farhan goye a bayana ba..?
Kafin na iya mgana Zuzu ta mari yarinyar nan Lokaci d'aya tana Hankadeta cikin fada tace"Ina Farhan.?wa kika bama shi..?
Yarinyar sai ta kasa mgana sai kuka Ya Ishaq ya fara fadin"To ku ina kuka shige ku bar ta dashi..?
Zainab ta fara fadin"Muna ciki ni da zuzu muna mgana mu ka bar Farhan hannun Shema'u"
Ganin abun nasu ya koma kan yarinyar har Ya Ishaq ya fara fada ita kuma sai ta kasa mgana ta Dago tana kallona kafin nayi mgana da Sauri Anum tace"Jaririn Anty..?ga shi nan Umma ta goyasa"
Sai kallo ya koma kaina ni kuma sai na juya bayana suka ga Farhan goye a bayana,yana barcinsa cikin kwanciyar Hankali ina jin su suka Sauke ajiyar rai a tare Zainab tace"Thank god.."
Cikin yanayin mganata nace"Na shiga ne na iske yana ta kuka na karbesa ashe cibiyarsa ke ciwo shiyasa yake Rigima"
Kamar kiftawan ido nagansu a gabana,suna rige rigen kwancen goyen bayana ba Ya Ishaq ba,sannan ba Zainab ba kanwarta ba,zuzu ce ta kalleni tana fadin"So kike ya karye kafarsa..?ba'a fara goyasa ba"
Ni dai ban damu ba da Sauri na Sauko shi Tare suka karbesa ita da Zainab din Mamaki ya rufeni Lokacin da Ya Ishaq ya faramin fad'a meyasa ban yi mgana ba ina ji ana neman Farhan.
Na kallesa cikin yanayina Kafin nace"kayi hakuri na zata ka gansa a bayana"
Cikin Fusata yace"In da na gansa zaki ji muna neman sa..?
Kuma kada ki kara goyasa tunda bai saba ba,Ba irin yaran ki ba ne da kika Saba goyasu ba"
Kamar wata wawiya haka na bisa da kallon Zainab ta kara fadin"Honey kafarsa bata samu matsala ba ko..?
Tafada tana nuna masa suka Taru suna kallon kafarsa yaron suna Tattabasa kamar na shafamai mugun abu,Cibiyar Ta bude tana kallo Zuzu ta leka tana fadin"What is this..?
Wannan kayan fa..?
Tafad'a a wulakance,karbansa tayi Tun anan ta cire mai kayan da na sakamai,Ita da kanwarta suka koma ciki Shi kuma ya bisu,kamar wani bita zai zai,ni dai da kallo na bisu Jamal ne, ya koma zauna yana fadin Allah ya kyauta.
Yaran kuma duk sun yi wani iri,ganin abunda ya faru ni Dariya ma suka bani wai kafarsa zata samu matsala Saboda goye,Allah sarki rayuwa da goye na illa da tuni mu kan mu mun samu illah Tunda a baya kafin zamani ya zo da sauye sauye goyen aka sani ba wani gayu da feleke feleke irin na yan zamani masu nasaba da boko ya gama ratsasu ammh irin mu yan gargajiya ai goyen muka sani.
Daganan dakina na koma Dauke da Ahmad araina nace in na goya nawa ai ba mai cewa zan karya masa kafa,Amir da Musty tare da Babansu da Uncle suka tafi masallaci ni kuma muka yi namu ni da Anum.
Daganan ta tafi bangaran Baban nasu,Ta damu sai taje sai nace ta tafi,Su Amir kuma sai da suka yi Isha'i suka dawo suma ban kara ganin su ba Bangaran suka shige Jamal kadai ne afalo na zubo mai abinci yaci muna dan Taba Hira sama sama bai jima ba yayi min sallama ya tafi.
Daki na koma nayi wanka nayi ma Ahmad,na shiryasa nan da nan sai barci yau bai yi rigima ba sosai su Anum sai goma saura suka Dawo Daki  suna bani labarin sun ci nama da Ice Cream,Amir dai bana jin bakinsa sai bakin Anum da baya gajiya da mgana.
Washegari ba makarantar Boko sai Tahfeez tun safe nayi musu shiri suka wuce,Shinkafar jiya data rage na Dumama ma yara sukaci suka tafi,Sai Sauran Taliyan data rage na Dafa musu da miyar suka tafi da shi ni kaina Sauran Shinkafar naci bamu da dankali ba kwai ba komai na Kayan breakfast ballatana nayi  musu sai na kama kaina,ina gama abunda zan yi na koma daki bayan na tattara kayan yara da suka zubar afalo.
Dakin su na shiga nayi musu kaye kayen kayan da suka watsar sannan na koma nayi wanka na yi ma Ahmad daman na Dama mai kunninsa na dura masa yasha sai ya cigaba da Wasan sa,Ganin ban da wani abu da zan yi sai na dauko Qur'ani na fara karantawa ina cikin karatun ne naji Muryan Yaya Ishaq na kiran sunana sai da na kai karshen Ayan sannan na Tsaya Daga bakin kofa ya tsaya Ahmad na ganinsa ya fara tafiya wajensa yana Washe mai baki ya Dauke sa ya daga sama yana fadin"Ahmad ka zama kato yanzu"
Shi ko sai bangala Dariya yake yi.
Hijabin jikina na gyara sannan na kallesa ina fadin"Ina kwana.."
Ya amsa ba tare da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login