Showing 33001 words to 36000 words out of 107151 words
ni kadai,Nafi Sati bana ji na Daidai da taamakon Allah na Samu na Dawo cikin Hayyacina Tun kuma daga wannan Had'uwar tamu bai kara kallo na ba ko da yaushe ni ke mai Hidima ina rawan jiki a kansa shi kuma kalamansa Daya ne Hajiyar karofi da Baba sun cucesa har fadi yake yi tasan zata mutu ammh kafin hakan sai da ta jefa rayuwarsa a wani Hali sannan ta bar Duniya har yau bai taba gode musu ba ban kuma jin akwai ranar da zai gode musu.
Ashe wannan haduwar tamu itace sillar Zuwan Amir(Kabir) duniya ne Wata uku tsakani nayi ta ciwo a tsaye,Zazzabin Dare da amai kasala da yawan barci,Ya Ishaq baisan Rashin Lafiyata,baisan komai akaina ba ban da na girka mai abinci yaci yana ci yana bi na da mganganun kushe da Tozarci.
Fahimtar ma ban da lafiya girkin da na kasa yi ne yasa ya lekani ya ganni kwance Ba domin yaji Tausayina ba sai Domin Harshen Baba akansa yasa ya Daukeni ya kaini asibiti,Gwajin farko aka tabbatar da ina da shigar ciki dan watanni biyu da wani abu Bansan wani yanayi Ya Ishaq ya shiga ba, ammh nasan muna Hanyar komawa gida ya kalleni kafin yace"Ke haka kike daga tabaki sai ciki Fa'iza..?
Yaushe na tsara ma kaina aure ballatana har na haihu?
Ya manta Haihuwa na Allah ne,Bani na bama kaina ba Allah ya bani ammh da Gudummuwarsa,Cikin Amir ciki ne da nayi sa mai Laulayi na sha bakar Wahala acikin gida ni kadai,ina haka watarana Goggon Karofi ta zo ganina ita da Yaya mariya su suka iskeni ba yadda nake suka kwasheni sai asibiti dalilin kwanciyata a asibiti Cikina ya fallasa ga su Mama kowa yaji ina da ciki sai kowa mamaki ya kamasa.
Mama kuwa mamaki yasa ta kasa mgana,Anty Binta sai kallon Ya Ishaq take yi basu taba zaton zai iya kallona na da sunan auratayya ba.
Baba kuma sai murna yake yi shi ya Kira Ya Ishaq da kansa ya fadamai da yazo asibiti ga Halin da nake ciki Sanda yazo,Baba sai da ya Rumgumesa yana murna lokaci d'aya yana sakamai albarka.
Mama ta fad'a agaban kowa da kowa Bata kaunar hada zuru'a dani,Goggon Karofi tace Tunda Allah ya had'a ita bata isa ta raba ba,har sai da suka yi ta Hayaniya,naji jiki sai da nayi sati a asibiti likita nata fadan bana cin abinci sannan jinina yayi kasa Goggo kamar ta wuce dani karofi Baba ya Hana Akace gidan Mama tace ai har Abada na gama zaman gidanta Dole gidana aka maidani Goggon Ta zauna Dani tayi sati,Yaya Mariya ita kadai ta koma Karofi,A bakinta Ya Asiya taji tazo har Katsina ta Dubani bana ganin Tamadina bata taba zuwa gidana ba na Tambayi Goggo tace min tana gidanta ni nasan rayuwata cike take da abun Tausayi.
Har Amir yazo duniya ni Fa'iza babu abunda ya sauya gareni daga zuciyar,Ishaq a kaina na wahala wajen Haihuwa kamar bazan rayu ba sannan Amir yazo duniya wanda yaci sunan Baban katsina Kabir,lokacin da na Haihu Anty Binta na asibiti ana kawo musu abunda na haifa ta duba kunnensa ta Kira mama tace"Mama sai hakuri Dangin tsiya yaron ya Debo"
Nayi kuka sosai da wannan kalmar sai dai a kallah na samu wanda zai san zafina wani abu daya fito daga Tsatso na wanda kila shi zai kaunace batare da ya Duba yanayin Halitta na ba ko nakasun jina ba,An kai ruwa Rana kafin Ya Ishaq da su Mama su amince Goggo ta tafi dani karofi nayi jego shima sai da Baba ya saka baki,sannan ya amince a cewarsa wai Goggo sai tayi ta nuna yana zalunta ta na sannan baya so naje na had'u da su Yaya mariya wai ana zaginsa mganganu dai haka yayi ta yi kan yan'uwana da iyayena bani da tacewa.
Sai da na koma karofi sannan Tamadina tazo ta ganni ta rike Amir gam a Hannunta kafin ta mikamin shi ta dafa kaina kawai tayi miirmishi na kalleta sai naji kuka duk ta lalace ta rame ta kara tsufa kamar ba ita ba,Bazan taba mantawa da Goggon Karofi ba domin ita ta kula dani ba,da kila sai da na Rub'e ni kadai ban san komai ba.
Ina yin arba'in ba Dadewa Goggo Karofi ta maidani gidana Ni da Amir mun yi bulbul duka duka sau biyu Ya ishaq yaje ya ganmu kamar Amir din ba D'ansa ba ne,Goggon Karofi da yan'uwana sun yi kokarin wajen gyarani ni kam ban ce musu komai ba, to ina zan fada musu sau daya tak Ya Ishaq ya taba hada jiki dani Rabon Amir ne..?
To kamar na Amir itama haka Rabon Saudatu(Anum) ya had'amu shima duka Duka Haduwar bai wuce sau uku ba ma na samu ciki Amir nada wata Goma sha hudu wannan karon Ishaq yafadamin sai dai a zubar da cikin ni kuma nace ban amince ba Karo na Farko da na taba kai karas gaban Baba Dalilim da yasa Baba Ya mari Ya Ishaq ya kuma nunasa da yatsa yace"Kada na kara jin wannan mganar a bakin ka..kasan baka son cikin ka yi sa..?
Ka kiyayi ranar da Fa'iza da ya'yanta zasu zame maka inuwa wacce zaka iya rab'ar ta ina jiye maka watan watarana kada kayi nadamar abunda ka aikata"
Wannan marin ya jamin abubuwa Dadama tsakani da Ya Ishaq,kamar ni na bama kaina cikin Dalilin Baba yasa Saudatu tazo duniya(Anum),Da kulawarsa na haifeta Lafiya ita ma kamar Amir ne Baka ce irina,Basu da yadda zasu yi su sauya wannan kaddaran tunda haka Allah ya Tsara Mama ta tsane ni ammh ta kasa Tsanar jokokinta Amir ma ita ta karbesa ta yayesa sai wahalan tamin Sauki,Goggon Karofi Sati daya tamin ta koma ni na mike na Rika kula da kaina har nayi arba'in din Anum.
Ya Ishaq baya barina fita ko'ina Sai gidan Mama ko gidan Anty Binta Su kuma har naje na Dawo bana samun kallon arziki,Karofi kuwa Tun da nayi jego ban kara komawa ba Har Haihuwa Ya mariya tayi ya Ishaq yace gulma zai kaini bazani ba.
Gidan Yaya Asiya kuwa tun bayan auranta kafata bai kara taka kano ba,Ya Ishaq ya rabani da kowa ciki har da mahaifiyata domin har Haihuwa tayi yaron bai zo da rai ba bai barni naje ba wai zan kwaso ma Anum Sanyi Baya sona ammh kuma yana kaunar ya'yan sosai yake kula dasu kamar yadda yake kula da kansa.
Anum na da wata Hudu watarana Baba ya fara rashin Lafiya anje asibiti an yi gwaje gwaje sai aka gano Hantarsa ce ta tabu ba'a sani ba,Ya kwanta asibiti yafi sau hudu duk Hankalin su Mama ya tashi ni kaina Hankalina baya kwance domin Baba shi kad'ai ne ya ragemin Saura gata na,Kwanciyarsa asibiti na Karshe an sallamosa Da ya ishaq zai fita yace na shirya naje na Dubasa Amir daman yana chan tun yaye bai Dawo ba.
Naje na dubasa yana kwance ne yana ganina sai da ya mike,Ya miko min Hannu na Kwanto Anum daga baya na mika masa ita yana ta mata wasa Baba yayi ta min Nasihan hakuri da kuma Umrtana da na zauna nayi Biyayyan aure zan rabauta Ranar gobe kiyama..
Ashe wasiyya yake barin mu yace na kula da ya'yana na basu tarbiya kada na Biye ma Ishaq,nayi hakuri dashi Sannan na kara hakuri da su Mama watarana dani da ya"yana duk sai mun zame musu Inuwar Rab'a,na dawo gida da Tunanin mganganun Baba ashe bazai kwana ba adaran Allah ya Dauki ransa.
Alokacin mutuwar Baba na kara yarda Tabbas ban da sa'a domin duka wada'nda nake gani agata na sun kare bani da kowa anan duniya da zan kallah nace Gata na ne duka sun tafi Na tabbata ko Mama bata kaini kukan mutuwan Baba,na fade lokaci d'aya nayi zuru zuru tabbas Mutuwar Baba ya sanyaya ma Ishaq zuciya sannan ya sa ya rage wasu abubuwan.
Rasuwar Baba ba'a rufe shekara ba Ya ishaq ya samu karin girma zuwa Abuja,chan ya koma aiki sai bayan Sati biyu yake zuwa katsina sai nauyin su Mama da su Jamal duk ya koma wuyansa abubuwa duk suka Tabarbare daman karfin zumumcin Baba ne to yana Rasuwa sai ahankali Hajiyar Dala ta matse kanta gefe itama Goggon Karofi sai ta kama kanta itama Daman basa shiri da Da Mama sai ta Dade bata zo katsina ba ba ita kadai ba Saboda Sanin Halin Ya Ishaq yasa ba mai son Rabata abu kadan yace munafunci ake yi shiyasa Dole dai su Mama ne bani da kowa a garin katsina sai su da ya'yana.
Samun karin girman Ya Ishaq yasa sai ya samu rufn asiri fiye da baya ya gyara ma Mama gida ya koma Fasalin na zamani shi kuma ya siya Fili ya fara gini a Anguwan layout,Jamal kuma ya shiga jami'a sai Badariya da ta zama yammata yanzu sai ni da ya'yansa wanda Darajan su yasa yake Ragamin shima ba wai don ya daina Tozartani ba ne A'a har yau har gobe ni Fa"iza ba kowa bace a wajen Ishaq kabir Karofi
Cikin mustapha ko ni bansan ina da shi ba sai da yakai wata Biyar Mama data ganni da ciki ta Dinga bala'in na zama kamar beran masar bani da aiki sai Haihuwa ta manta ba ni kad'ai nake samar da cikin ba har da Gudumuwar D'anta ammh bata ganin Laifinsa sai nawa,Na haifi Mustapah ba Dadewa muka tare a sabon gidan da Yaya Ishaq ya gina katon gida mai shashe biyu,Shashen farko mai 3Bedroom da Falo sai kichen,Nawa daya sai na yara sai guda d'aya na baki,Ya ishaq shi ya Zuba Sabbin kaya agidan komai bamu Dawo da Tsoho ba, Mama ta kwashe su ta kyautar ni ko da har nayi Tunanin na aika ma Tamadina da su Dakinta Sai leda ba kujeru ganin Mama tace akwai wacce zata bamawa ban yi mgana ba, Sanin Halinta.
Haihuwar Mustapah yazo da Budi sosai Ya Ishaq har motar hawa ya mllaka ya siya mama nata,Budi ta ko'ona sai hamdala da Godiya yana Dinkamin suturu daidai gwargwardo sai dai na yaransa Dabam suke,Ni wani Lokacin ko yayi niyar yimin Rantsatsun kaya sai kalaman Mama su Dishe niyyarsa tunda tasha fadin siyamin kaya na alfarma barnan kudi ne, Tunda ba kyau zasu yi min ba sannan bansan yadda ma ake gayun ba kuma gaskiya suka fada ba karya sukayi ba ban san komai na gayu ba.
Ni dai iyakata nayi wanka na shafa mai na saka kaya,Abaya telan su mama ke min dinki Mama ta koma ba wata mace saboda sai nace yana kamani ni kuma bana so kaya su kamani na fison a shatamin na rika yawo aciki,ya Mariya ko Ya Asiya ko da wani Lokaci suna kokarin gyarani ni ko bana jin su gani nake yi gyara da gayu na wajen mata masu kyau da gata ban da ni da bani da ko d'aya daga ciki Dalilin dayasa Ya Ishaq yake Biye ma Mama kenan in ta fadi mgana hakan take indai a kaina ne ballatana ba ran Baba ita ke tafiyar da komai.
Mama ta bada shawaran nayi Tsarin iyali sai dai bai karbeni ba wannan yar ashanan aka sakamin ya sakarmin jini Dole aka ciremin ana ko Ciremin ko wata Biyar ban yi ba na Samu Cikin Ahmad,na haife su kusa da kusa domin a shekara ta takwas da auran mu da Ya Ishaq duka na Haifesu haihuwan gwarne na rika yi don ma Allah yasa ina da jarumta daukan duka kwarmiyan yaran
Cikin ikon Allah cikin ya'yana ba wanda ya Dauko Lalurata sai na godema Allah Ammh wani ikon Allah susan Lalurata barin ma Anum da Amir susan bana ji sosai in zasu yi min mgana sai sun daga muryansu.
Allah ya bani yara masu kirniya,musty Da Amun basa jin mgana komai suka gani sai sun taba abunga ga wanda bai da karfin ji ina chan ina aiki su kuma suna Falo suna barna bana sani kuma Duk abunda suka Lalata sai Ya Ishaq ya dora komai akaina,Shiyasa ya dinga masifan na bari duk sun bata gidan sun bata kayan kallo sun bata in ji min wanki kuma Mama sai tace bazai kara siya ba, a kyaleni na wahala ai da gangan na bari suka bata komai.
Ni kuma bana cewa komai,Saboda bani da wani zabi,Har zuwa yanzu da girma ya kamani da ya'yana ban daina samun tozarcin Wajen Mama da Anty binta ba tun ba'a sani ba har kowa ya sani,Goggo karofi dai hakuri take bani,in ta kirani a waya sai dai fa ta wayan ammh Sai na shekara kafata bata taka Karofi ba Tunda nayi aure Sau Daya naje naga Tamadina Shima Haihuwan Mustapah ne da naje karofi da Ya Ishaq yaji Labari masifa ya farayi wai baya son ya'yansa suna zuwa gidan wasu suna Rabe rabe.
Haka nan nake daga ni sai ya'yana sai Danginsa alhalin yasan bana jin Dadin su ammh ni nawa yan'uwan sai dai zumunci ta waya ya rabani da kowa nawa.Hafsatu ce kawai tana ta da Kulafucin yan'uwana bai da yarda zai yi da ita in sun samu Hutu tana zuwa ta zauna dani hakan sai yasa na Shaku da ita fiye da su Yaya Asiya.
Nasan Tabbas Ya Ishaq zai kara aure watarana ban daukesa alokacin da najisa ba Nima abakin Anty Binta na farajin mganar auran sannan Mama ta Fadamin nasan bani da wata Daraja a wajen ya Ishaq ammh na Dauka zan ci albarkacin ya'ya ashe bani da wannan alfarman na Kunshi Bakinciki Tundaga ranar farko da na wayi gari agidan Ya Ishaq a matsayin matarsa,Na kunshi takaici a matsayina na Uwar ya'yansa na fuskanci Tozarci a matsayina na kanwarsa tun a baya to wani tozarci ne ni Fa'iza da ya rage ban gani ba..?
Nayi Rayuwar aure shekaru Takwas da wani abu ammh Daidai da Rana d'aya ban Taba Danda'na yadda Dadin aure yake ba na dai yi shekaru Takwas ina Sanin yaya matsayin Tozarci da Gori yake sannan na kara zama Guilt akan kushen Hallita da kuma aibata Nakasa ta nayi rayuwa cikin Guilt din jin ban da sa'a na rayu cikin Guilt din Sannin ni bani da gata na zauna cikin Tunanin Mata ire ire na basu dace da suyi Farinciki ba.
Basu chanchanci miji mai kirki ba, basu chanchanci samun soyayyar ko wani Namiji ba,Sannan basu chanchanci Rayuwar Farimciki ba.
Mata ire irena Rayuwar kaskanci da Torzarci da Bauta ya dace damu,Ba kokarin mu goga kafad'a da kafad'a da mata masu kyau da gata ba shi yasa na Rayu cikin Tunanin kayan alfarma da shigar alfaarma da Kwalliya basu dace da ni ba, sun fi dacewa da mata masu kyau da Nagarta kamar yadda Ya Ishaq da mama ko Anty Binta ke yawan fadi akaina.
Tabbas na aminta da duka zencen su da Tunaninsu"
*Littafin KANA NAKA book 1 free ne book 2,3 paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*
*Janafty*[6/13, 12:28 PM] +234 808 711 8630: *KANA NAKA..!*
*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
*Book 1*
*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.
*🅿️06*
Filon da nake kwance akai sai da ya jike saboda hawayena,na kara birginawa ta b'arayin hannun haguna domin hannuna na dama yayi min Tsami sai naji kamar na Danne Gefen Kafafun Ahmad dake kwace gefena da Sauri na mike ina kara gyara mai kwanciyarsa barci yake yi hankalinsa kwance domin akwai haske acikin dakin ban riga na kashe ba ina kallonsa ne ammh a kasan zuciyata fad'i nake shi kam ya huta bai san duk wasu walhalhalun duniya da tashin Hankalin dake cikinta ba.
Hawayena har suna d'iga saman cikinsa nayi saurin matsawa ina sharesu da duka hannayena kafafuwna na zuro kasa kafin na dukar da kai na haka kurun nake jin kamar na yi ta rusa kuka da dukkan karfi na,na Dad'e ina so nayi kuka da karfi ammh bansan Kafad'an da kirjin da zan kwanta na rera kuka a lallasheni ba kawai sai na durkushe saman Dadad'den Cafet din dake cikin bedroom dina na fashe da wani marayan kuka hannayena duka biyu na tallafe fuskata da su wani irin kuka ne dake fitar da karar sauti cikin Yanayin da ni ke ciki.
Meyasa zan damu don Ya Ishaq yace zai jingine aure na dashi..?
Na dauki tsawon Lokaci daman ina jiran ranar da zai auro zab'insa na yi tunanin zan fuskanci tozarci ninki ba ninkin wanda nake karba a wajensa da wajen su Mama ammh bantab'a Tunanin zan fuskancin irin wannan cin Fuskar ba duk da nasan kalaman Baba sune suka yi ma wannan auran nawa tsakani da Ishaq sarka ba domin haka ba Tuni ban kawo lokacin nan acikin gidan sa ba.
Menene laifina domin na kasance a yadda Allah yake fatan ya ganni..?
Nayi kuka,kukan da ban taba irin sa ba Tun bayan da abubuwan suka fara zame min jiki sai dai wannan kukan nawa ya sha bambam da na kowani Lokaci na yau ina kukan yadda Rayuwata zata kare ne ni da ya'yana.
Kwarin gwiwa naji yana shigana irin wanda ban taba ji ba alokacin da wata zuciya ta tunasar dani ni uwace ina da ya'ya bai kamata na zama mai Rauni ba in na Raunana ya'yana suma zasu Raunana in na karfafa nima watarana ya'yana zasu zama karfafa.
Nasan Rad'ad'in maraici daga na uba har na uwa Tamadina tana raye ammh ban san Dad'inta ba,bayan Laluranta kaddara tazo ta raba tsakanimu da ita gwara ko wa dani Domin ni kam Ya ishaq ya rabani da kowa nawa ciki da har da uwar data Haifeni.
In