Showing 36001 words to 39000 words out of 69565 words

Chapter 13 - 'Yan Abuja comeplat Hausa novel

HAERMEE   

13 May 2025

2227

ANA MUGUN TARE.ME LOVE U XOXO❤






Page 20:

















Alhj Kallah, Alhj Salihu, Oga Zaks, su ka dai na iya ganewa a qaton table din da yake kewaye da manyan Alhjzawa, wanda a qalla zasu kai ashirin , gaba dayan su da shigar tasu ta red and white, with a little black on it, kowa muzurai yake, irin nima wani shegen ne😎, Oga Zaks ne yai gyaran murya, ya ci gaba da magana" A a Salihu, wannan qorafin naku bai karbu ba, kun san qa'idar qungiya, an baku dama, ku kadai na bawa damar da ban ba kowa ba, saboda koba komai ana qaruwa da ku sosai, amma wannan karon, u guys disappointed me so much, that u have to pay for what u did, dan haka , nake baku imarni ba shawara ba, u go back and bring ur wives here, dole ne a yanki abinda ake buqata daga wajen su, ba dan komai ba kuwa sai dan cika sharuddan Dodo, dan haka na baku nan da kwana uku, kuje ku gama sallama da su ku kawo su" miqewa yai cikin izza yai hanyar waje, guards din shi na biye, Alhj Salihu ne ya kife kan shin a table, dan a qashin gaskiya ya fara son Suwaiba duk da wautar ta da gabuntar ta,Alhj Kalla na kula da shi, taba shi yai akan su tafi, miqewa yai da kyar, suka fice , ana ta yan gulmace2 , ko ina ba a raba mutane da gulma🙄bayan sin isa gidan Saudat ne, suka shiga inda suke tattauna matsala irin haka, suka zauna, Alhj Kalla ne ya fara magana, dan ya kula in bai ba Alhj Salihu ba zai ce uppan ba, " Salihu ni ban ga abin daga hankali a maganar nan ba fa, duk da ni kaina a yanzu haka na fara son yarinyar can,koba komai duk matan da muke hulda da su yaran nan na kula suna da na su sirrin daban a jikin su, ga yarin ta ga kyau, amma kasan bijirewa Oga Zaks na nufin qarewar arziqin mu, nikk dana talauce gwanda na aikata abinda yake so, mu kaisu kawai, nono ne kawai za a yanke, to meye? Naga dai ana ciwon cancer ma a yanke masu nan kuma su rayu" " bazaka gane ba abokina, in ba wajen a ina mutum zai na hutawa? Kai ni fa bari kaji ba zan iya bane kawai, duk sokoncin yarinyar nan ina son ta, dan in tare kk da ita ta bara maka wani haukan sai kaji kamar kaita zane ta shegiya, amma tayi akwai zuma, banjin zan iya rabuwa da ita, yanzu ni dai shawarata shinr suje gida kawai su ga gida na kwana daya ko biyu su dawo muga ya za ai, tinda kaga bai kamata har in ma mutuwa za sui tsohon su bai gan su ba, dan ta uwar su ita tajiyo bamda case da ita ni" " haka ne kayi gaskiya, to bari na fada masu kawai gobe su shirya zasu gida ko ya kace, dan da kaina zan hada mata kayan ta, amma ka tashi ka tafi gaskiya dan saina dana sosai kan ta tafi, bamu san ya abubuwam zasu kaya ba" dariya sukai suka tafa, " shegen sama nima ba ri na hanzarta" aiko hakan akai washe gari da asussuba suka dau hanya kowa da drivern ta dan wadata, ga wata mota nan shaqe da kayan arziqi na bin su, haka suka iso gida cike da doki da murna, suna shiga gidan, Salma suka hango kanta akan cinyar Mama Bilki tana mata kitso, a kwance, kamar wata jaririyar ta, " Kan ubancan, me nake gani haka ni Suwaiba? Yaushe gidan ya koma haka? Da jin muryar ta Salma ta miqe da gudun ta tai kansu, tana ihun murna," Goggo fito ga su Adda sun zo, Mama kinga su Adda sun zo, ina Abba? Abba fito ka ga ikon Allah su Addana ne a gidan yau" suma basawa sukai aka ci gaba da murna amma cikin ransu akwai tambayoyi sosai, dakin suka shige tana ta kwasar bacci, tashin ta sukai, ta miqe tana mittsika ido, aiki tana wartsakewa ta gansu, sai kukan dadi ya kamata, ta ko hau kukan murna suma sunayi, Abba ne ya lallashe su, nan fa aka hau gaishe gaishe" Ayyyuririri, kai shiyasa nake son Allah, akwai shi da biyan buqatar bawa, dubi yarana , san kowa baqin cikin marashi, ga kudi ga kyau, ga hutu, naji dadin zuwan ku yarannan, ya mazajen naku?" Cikin murmushi da dagun kai an gama kumbura masu kan suke amsawa" suna lfy suna gaida ku, ga abubuwan kayan abinci nan da kudade da suka aiko a baku ke da Abba" cikin murna kamar zata kifa ta dafe kudin dika har na Abban nasu, shi ko ko wajen bai kalla ba, ya masu godiya, Mama Bilki ce ta shigo dauke da ruwan Pure water a plate ta doro masu sanyi ta kawo masu, ajewa tai ta zauna a gaisa" wai ni shin gaisuwar nan dole ce ne, a bar yara su huta, kuma in banda abin talaka, duba fa wa zai sha wannan ruwan, dan Allah kije an yafe Allah ya bada lada" Goggo Sarai ke maganar nan, cikin shewa suka hada baki" Hahaiiiiii Casssss sai Goggo, ashe ana nan ana ci gaba da gashi, Allah sassaka to" dariya tai cikin isa tana wani daga hanci, Mama Bilki ce ta tashi ta ja hannun Ammar da ke son shigowa sukai gaba, Salma ma tashi tai rai bace ta fita" wai Goggo me ke faruwa ne me nake gan? Salma da waccan matar?" Abba ne ya basu labarin komai, nan da nan suka hau kokawa yar uwar su wahalar da ta sha, sannan ya qara masu da hukuncin da ta yanke, anan ne ransu ya baci sosai, suka kwala mata kira, bayan ta shigo ne suka balbale ta da fada kowa da abinda yake fada, sai da ta tabbatar sum gama ta miqe tai waje ba ta tanka ma kowa ba a cikin su, da bala'i Suwaiba zata bita ta daka Goggo ta hana ta, "aini yanzu na cire ta a Yarana nima, taje can ta qarata, ina da ku kun ishen rayuwa, kuma yanda kukai jan nan da alamar kuma kuna dauke da ciki, dan haka jika ne nake matuqar kwadayi yanzu a duniya fiye da komai, taje tai ta fama, ita ta sani, naku sun ishen zaman duniya dai ba na qiyama ba" kallo suka bi junan su da shi, take Saudat ta fada jikin Goggo tana kuka, Suwaiba ma idon ta ya cika da kwalla sosai, "Adda Suwaiba akwai abinda na si fada maki tin da na qi dan nasan halin ki tona mu zaki su kuma su kashe" cimin zaro ido Goggo tace" Suwa..... suwaye zasu kashen ku?" 😨" mazajen mu Goggo yan qungiyar shan jini ne,na gano hakan da jimawa, yanzu haka bamu da mahaifa da ni da Adda" wani mari taji guda biyu a fuskar ta, daya na suwaiba daya na Goggo" dan ubanki sharri kuma zaki masu, mutanen da suke kasuwanci a qasashe ko ta ina, arziqi ya wadata ya bunqasa shine zaki ce haka, so kk ki dawo kema ki xauna ki jamin asara, na haifi ya kamar ki da zan samu dukiya ki dankwafe kanki? To ki bude kunnen ki kiji, ko ya ake. Ciki gobe zaku koma va zan lamunci asara ba" cikin kuka ta rarrafa wajen Abban su," Abba ka yarda da ni, wallahi gaskiya na fada, yan shan jini ne, naji da kunne na" " na yara dake yata, dan baki taba fadan hakan ba kuma da dikkan alamu akwai gaskiya a zancen ki, wannan kudin nasu yayi yawa" " Abba ya zaka yarda da wannan maqaryaciyar ? Qayra ne fa kawai dan sun taba dukan mu sau biyu, shine fa ta qullaci abun take son ta gudu, to in ke bazaki koma ba ni xan kma dakina" " yauwa yar albarka, ai nasan in kowa zai juyan baya ke kin haifu" tashi akai inda kowa zuciya ba dadi, Saudat ta kafe bazata koma ba, inda Suwaiba tace ita zata koma, Salma kuma suna jiyo komai,hankalin ta ya tashi amma tasan bata da say a wannan kamarin,Mama Bilkince ta shawarce ta akan ta musu addua kawai, hakan akai kuwa ta kwantar da hankalin ta suka hau yankan farce bayan sun gama kitson.





" Bbyna wai ni yaushe zaki gaida Mama ne kafin a zo ya zamana bazaki iya fita unguwa ba kuma, tinda ita tana abunnan na mutan da taqi zuwa dakin ki har yau" " hmmmm kaidai bari abunnan na min zafi ace wai uwa ba zata je dakin yar ta ta gani ba? Ba komai, xan je ko gobe ne naji dazu Nafee tace su Adda sun zo, kuma Salma ta dade a gida" " Eh haka ne, rand naje gaida su ma na ganta ai, Allah ya kaimu goben..........❤




Na gode maku da nuna kulawar ku akaina masoyan YAN ABUJA naji dadi sosai da yanda novel dinnan ya samu karbuwa a zuqatan jama'a masu tarin yawan da ban san iyakar su ba, ina roqon ku da ku qoqarta ku sa na samu ladan abinnan, ta hanyar aiki da abinda kuka karanta na amfani , in da kukaji nai kuskure ku yafen ku nemamin gafarar Allah, wanda yaji dadin novel dina kuma ya mafana da abinda ke ciki ya min adduar samun biyan buqatuna na alkairi. Tanx Love u all❤
[11/26, 12:35 PM] Hermeebrah: 💅🏼 ' YAN ABUJA 💅🏼





BY HAERMEEBRAERH





Dan Allah masu tambayar novel daga farko ina qara baku hakuri da cewar, na kusa kammalawa inshaa Allah, so ina ganin it will be better and easy for me inna kammala nai document sai mai so ya same shi. Na gode. Love u xoxo❤





Page 21:






To day is a busy day for Juwairah,amma dik da haka ta kafe yau take son ta je gida dan su gaida da yan uwanta dika, da farko Jabeer yaso hana ta ta bari sai jibi tace sam zata iya ba wani gajiyar da zatai, haka ya hakura, tana idar da sallar asuba azkar din ta dik a hanyar kitchen take yin shi, fitowa tai dan yi ma Jabeer abinda zai samu ya tafi da shi Abuja wajen interwie da aka kira su na wani aiki da ya nema a NNPC, dubawa tai taga basu da wasu kayan abinci sosai as usual, ragowar Flour da ba zata wuce gwangwani hudu ba ta dakko da dan kifin da ta siyo a jiyan, na dari, da kayan miya albasa ta yanka mai ganye sosai ta daka attaruhun ta hada da dan kifin nan, ta soya sama2, nan take ta hada flour tai meatpie cikin mintina qalilan( da ace akwai wadatar a cikin meatpie dinnan zata iya amfani da nama ko kifin ya fi wannan da veges masu yawa a ciki in ta hada sai ta soya sama2 dika amma a yanzu tinda Juwairiyyar mu na da dabara sai ta cika albasa dan ya tada kifin) bayan ta kammala me ta dakko kamun su tai mai koko, ta hada mai shi ta kai mashi, daki kafin ta gama shima yana ta shirin tafiyar, jakar shi da komai ta hada mai dama, komawa tai ta samu zobon ta da ta dafa da yamma jiya ya sha kayan qamshi ta tace ta hada mai shi, ba qaramin dadi yai ba, ta samo wata yar robar ta cika mai da ita ta daure yanda ba zai zuba ba, ta debar mashi meatpie ta rage ma surukan su da zasu zo anjima wajen neman auren Nafeesa, sannan ta koma daki, qarasa tayashi hada komai tai, dai dai da brush din shi bata manta da saka mai a jaka ba, bayan ya gama cin abincin ne ya gama komai ya janyo ta jikin shi" My princess ba abinda zan ce maki sai dai nai maki fatan shiga aljanna, tin da ance sai miji ya yarje wa matar shi shiga aljanna zata shiga My Juwairiyyah na yarje maki shiga madaukakiyar aljanna da izinin Allah, ke macen kwarai ce, macen nunawa kowa ba tare dana kunyata ba, Allah ya sauke ki lfy, ya shiryar min dake , Allah ya qara miki imani, kinga ga wannan ba yawa kwama biyu zan kamar yanda na sanar dake, ki ta tayani addua inna samu aikin nan xamu samu hutu sosai, zan jiyar da ke dadin da baki taba zato mace zata iya samu wajen mijin ta ba, Juwaireren Mama ina son ki" ba abinda take zabgawa in ba murmushi ba, amma yana cewa Juwaireren mama ta turo baki tana buga qafa," Ni dai Yah Jabeer bana so, taso ka tafi kar ka makara, Allah ya karen kai mijina kaje lfy ka dawo lfy, Allah ya bada sa'a a abinda aka tafi nema, inshaa Allahu kai me nasara ne akan komai na alkairi da ka sa a gaba, dan haka don't feel nervours, u will do just fine, u can do it, saboda kai din na daban ne a cikin mazaje,karka manta da karanta lahaula wala quwwata....... da hasbunallahu wa ni'imal wakeel, Allah will be at ur aid, he will guid and protect u, ina son ka Jabeerun Baba" ta fada tare da miqewa da sauri tana dariya bin ta yai ya cafko ta ya hade ta da gini, " maimaita me kk ce" turo baki tai tace " yo ni me nace, dan dai kawai an ga yau mijina zai tafiya sai kuma a ce za a min yar qure a ci zalina, dan irin wannan kallon da kk min ji nake kamar na dawwama da kai a haka a tsaye ba tare da duniyar ta juya ba" ta fada cikin qasa da muryar ta, wani irin farin ciki ke ziyartar zuqatan su, a cikin ran su kowa na yaba kyau irin na dan uwan shi, bakin shi ya kai saman nata, ya shiga sarrafa lips din su, cikin salon da dikkan su zuciyoyin su sai da ta narke, biye mai tai sosai suke jin dadin hakan, aka kace musu da sallama, Nafeesa ce tai sallama ta taho dan Juwairah tace ta zo sui komai da wuri zata gida yau, janye jikin shi yai a kasalance, ya riqe hannun ta ita kuma ta kwantar da kanta a jikin shi, fita sukai tare idon ta taf hawaye, yau je ranar farko da zai tafiya tin auren su,kuma har zai kwana biyu baya nan, saurin maida kwallar tai kar ya gani hankalin shi ya tashi, amma ta makara" Haba my Queen, ki kwantar da hankalin ki mana, inshaa Allah jibi da yamma kina maqale a qirjina,daga wannan tafiyar ko ina ban sake zuwa na barki qafa ta qafar ki kinji" ai kamar ya zuga ta ta bare baki irin na yaran nan ta fara kuka, rungume ta yai tai kukan sosai sannan tai shiru ta sake mai addua, ya suka fita har Nafee suka raka shi, Innar mu ke tsokanar ta" to kukan rabuwa da maso yi aka shaaaaa Hoh yan zamani, to dakko mayafi ki bishi" da gudu Juwairah ta tafi tana dariya, suma dariyar suke, sai da taje baqin qofar shiga wajen su ta juya, dan tsuke bakin shi taga yayi alamar kiss, ta waro ido ta kalli su Baba Balarabe dake gefe zasu raka shi qofar gida, rufe baki tai da hannun ta ta fada wajen nasu tana dariya, " Allah sarki mijina,kaje lfy ka dawo lfy cikin sa'a da nasara, tare da kariyar Allah" Nafee ce tace " Ameen masoyan asali" murmushi sukai suka shiga kitchen, lokacin takwas da rabi tayi, masarar da aka barza suka dakko nan da nan suka je suka tsinko zogalen da Juwairah ce ta shuka da hannun ta, da alayyahu, sai albasar su mai lawashi, gyarawa sukai suka dake gyada, da kayan qamshi attaruhu da maggi gishiri suka saka yanda zai isa yai dadi suka saka suka dora a wuta, nan da. Nan sai ga dambun masara mai dadi ya hadu, mai s Juwairah ta soya dayaji albasa, hadawa sukai a flask wannan zobon juye ragowar tai a wani babban jug nata sannan ta dakko meatpie dinnan ta aje Nafeesa ta ji dadi sosai tana taima yar uwar ta kuma matar yayan nata godiya har saida ta ba Juwairah haushi, godiyar tai yawa, ajewa sukai a gefe Juwairah ta sa Nafee debo wani alayyahun da albasar mai ganye, ta sa ta gyara, ta daka kayan miya wanna karon harda timatir, jelop rice mai dadi tayi wadda ta yayyanka dan naman d suka tafasa tin jiya, saboda bai da yawa yasa Juwairah tace bari su yanka qanana sai a soya sama2 su saka a abincin, har da dan carrot din su, nan da nan sai ga girkin da su suke ganin anyi a talauce ce amma wani gidan masu akwai din ma matat gidan ba zata zage tai hakan ba, wanka ta tafi tayi ta sa Nafee taya ta gyara gidan, dan bata son fita ta bar gida da datti in ta dawo ranta baya dadi, ganin dattin, sannan kuma ga gajiya, ( wasu matan taqamar fita za tai unguwa sai ta bar gidan kamar bola ta tsallake,na farko in kk dawo zaki iya baqin kunya gida kaca2, ko kuma ki dawo a gajiye,ga shi maybe miji ya kusa dawowa, shima ya dawo yaga yanda ya fita haka ya tarar wataqila harda qarin dattin ma, amma in kk gyara gidan ki fes in da haki kikai girki, da kij dawo wanka zaki fada ki fito tsaf dake,maybe sai bacci ma tinda baki da aiki, mata mu kula👂🏻) bayan ta fito ne abincin ta da zata ci yanzu ta dauka taci ta aje na daren da ta diba ta rufe kitchen din bayan ta wanke plate din data ci abinci,kmawa tai ta shirya ta fito, bangaren Innar mu taje ta mata sallama ta dau hanyar gida cike da zumudi da doki.










Sallama tai a cikin gidan, inda ta isko ana ta daru, ita Saudat tace bazata koma ba, Suwaiba ta shirya tsaf da shirin tafiya,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login