Showing 24001 words to 27000 words out of 44320 words
roba.
Lumshe idan Laylah tayi tare da cewa.
“Kai my Aunty kinyi kyau, ƙamshin turarenki daɗi”.
Murmushin ta ɗanyi tare da jawo after dress ɗin da ta ciro Black blue ta ɗaura kan kaya, sai kuma ta ɗan sa hula, kana ta juyo ta kalli Laylah dake cewa.
“Aunty Garkuwa tace kizo ki kaiwa Uncle Taj dinner ɗinsa”.
Ɗan sunkuyowa tayi tare da riƙo kafaɗun Laylah cikin sanyi tace.
“Laylah ina son mu zauna muyi hira, zakiyi hira dani ko?”.
Da sauri ta gyaɗa kai tare da cewa.
“Eh sosai ma Aunty Ishmah”.
Murmushin mai haɗe da jin bacci tayi kana ta ɗan sumbaci goshin Laylah kana tace.
“Duk abinda na tambayeki
zaki gaya min gsky ko?”.
Da sauri ta kuma cewa.
“Eh”.
Sai kuma duk suka kalli Khadijah data shigo tana faɗin.
“Adda wai kije ki kaiwa Uncle Taj dinner, Aunty Amina tace kada a turo ɗan aike na uku fa”.
Cikin sanyi sauti tace.
“Uhmm wlh bacci nakeji”.
Sai kuma ta shafa kan Laylah tare da cewa.
“Yanzu dai jeki Sai gobe zamuyi hirar.”
Da sauri ta juya ta fita.
Ita kuwa Ishmah kamo hannun Khadija tayi suka zauna bakin gado cikin tsananin so da shaƙuwa na ƴan uwa cikin uwa da uba tace.
“Khadija ban gaya miki batun Hamisu da Rahama zasu dawo nan bako”.
Da sauri Khadijah tace.
“Adda Hamisu kuma harda Rahama, ai sunyi yawa karfa muyi rashin pulaku mu ɗaurawa bawan Allah abinda ba haƙƙinsa ba”.
Da sauri tace.
“A haba shi da kansafa ya faɗi haka, kuma ai zai iya ne”.
Cikin sanyi tace.
“Adda da kunya fa”.
Ɗan hararanta tayi tare da cewa.
“Ya dai keda nake zaton zaki tayani shawo kan Abba ya yarda, sai kuma inga ke ɗinma kina shirin ƙi”.
Da sauri tace.
“A'a wlh ba haka bane Adda, Amman dai naso a barmin Rahama ai mu koma Gombe da ita, ta fara GSU ai zaifi”.
Da sauri tace.
“To ko in kin ɗauki Rahama ni kuma zaku bani Maamah ko tazo mu zauna tare in haɗa da Laylah kinga na samu yan biyun da nake so”.
Cikin son juna tace.
“Toh Adda am, ai Maamah kam ɗiyarki ce nasan Abbansu bazai hanaba”.
Cikin yin hamma tace.
“Kina dai yimin daɗin baki”.
Dariya sukayi baki ɗaya jin Aunty Amina na cewa.
“To ga yar aike ta uku kam na shigo, Goggnku tace, duk wanda aka aika ya shigo kamar an aiki bawa garinsu, dan haka maza tashi kije ki kaiwa mijinki abinci”.
Ta ƙare maganar da miƙa mata basket ɗin data shigo dashi, wanda aka shirya komai a cikinsa.
Amsa tayi tare da juyawa ta fita.
Tana fita suma suka fito nan suka ci gaba da hirarsu.
A hankali ta ajiye basket ɗin akan Dinnin table ɗin,
Sai kuma ta dawo tsakiyar Parlour tare da ɗan tsayawa ido ta zuba wa wayarsa daketa Vibration.
Dr Abbas ta gani tana kai hannunta kiran na katsewa,
Sai kuma kiran Arfah ya shigo.
Hakanne yasa ta ɗauki wayar tare da nufar bedroom ɗinsa.
A hankali ta tura ƙofar bakinta ɗauke da sallama.
Hummmmmm taja wani irin kasalallen numfashi mai gauraye da nataccen bacci.
A karo na biyu ta kuma jan numfashi saboda wani irin ni'imtaccen ƙanshin da sanyin da yasa baccinta gangarowa duk ya taho cikin idanunta.
A hankali ta buɗe idanunta tare da zubasu a kanshi, zaune yake a bakin gadon, system nashi na bisa cinyarsa da alamun abu yake sonyi Amman masifeffen baccin da yakejin ya hanashi ganin komai.
A hankali ya ɗago kanshi tare da zuba mata ido cikin sanyi suka kuma lunshe idan a tare.
Cikin sanyi murya ta sakeyin sallama.
Murya can ƙasan maƙoshinsa ya amsa mata sallamar tare da yafitota da hannunsa alamun tazo.
A hankali ta fara yin taku tana maijin sanyin tayis ɗin na ratsa tafin sawunta duk da safar da ta saka.
A hankali yasa hannunsa ya amshi wayar da take miƙa mishi, sai kuma ya nuna mata gefenshi tare da motsa lips inshi a hankali yace.
“Zauna”.
A hankali ta ɗan zauna gefenshi tare da ɗan yin gajeriyar miƙa, shi kuwa system ɗin ya rufe, ya ajiyeshi kan bedside drower.
Sai kuma ya ɗaura wayarsa saman system ɗin nasa.
A hankali ya ɗan ƙara matsowa gefentan murya can ƙasan maƙoshinsa yace.
“Babe bacci”. Yayi mgnar yana mai lumshe idanunsa tare da ɗan maida hannunsa duka biyu ta baya zuciyarsa na amintar da ruhinsa kasancewar Ishmah a gafenshi, a ƙasa ɗaya gari ɗaya gida ɗaya a ɗakin aurensu na Sunnan a matsayin ma'aurata.
Lumshe idanunsa yayi tare da fesar da sassayan numfashi, saboda nazarin zuciyarsa daya fayyacemishi yayi rashi da samu duk a cikin wata ɗaya, ya rasa iyayensa Allah ya samar masa Ishmah ya mallaka mishi ita, domin itace sanyin idaniyarsa mai sama mishi sauƙi da raɗaɗin zazzafar ƙaddarar data ritsa dashi Allah ya sani itace kaɗai zata iya tausasssa zuciyarsa a faɗin duniya shiyasa ya mallaka mishi ita cikin sauƙi.
Cikin kasalar da furar ta sakar musu tace.
“Nima baccin nakeji”.
A hankali ya ɗan juyo ya kalleta.
Cikin sanyi ya ɗan miƙe ganin idonta a lumshe, hannunsa yasa ya ɗan tattare jallabiyar jikinsa tare da murza robar boxer ɗinsa yayi ƙasa dashi.
Numfashi mai sanyi ya fesar lokacin da yayi ƙasa da Boxers ɗin nasa, saboda jin cinyoyinsa da Taj ɗinsa sun sake yadda yake muradi.
A hankali ya sunkuyo tare da zareshi duka.
Yana ɗagawo da Boxers ɗin a hannunsa tana buɗe idanunta, da sauri tayi ƙasa da kanta tare da maida idanunta ta lumshe shi kuwa Taj a hankali ya ida nade shi tare da cilla shi bisa kujerar dake gefensu.
Sai kuma ya zauna bakin gadon tare da hawar da sawunsa duka.
“Kinyi al'wala?”. Ya tambaya cikin murya kasala da bacci, kanta ta gyaɗa mishi.
Ganin haka ne yasa ya ɗan matsa gefe can kana ya jawo hannun ta, murya can ƙasan zuciyarsa yake faɗin.
“Zomu kwanta tare ko zan samu inyi bacci kamar jiya”.
Ya ƙare mgnar tare da tattare blanket ɗin kan gadon, da hannunsa ɗaya yayinda ɗaya hannun kuma ke jawota, kusa dashi.
Yana gyara mata pillow yace.
“Bismillah kwanta”.
Cikin sanyi da jin wani fitinenne kasalar bacci, ta ɗan kwanta tare da fuskantar alƙibla haka yasa ta bashi baya.
Nannauyan numfashi ta fesar, tana mai nazarto kasantuwarsu ma'aurata yana ƙara sa tsikar jikinta tashi.
A hankali ya warware naɗin da yayiwa blanket ɗin har zuwa saman ƙirjinsu,
Sai kuma ya gyara zamansa cike da kasala yayiwa kansa addu'a ya shafa, kana ya sake yin addu'a ya tofa a hannunsa.
A hankali ya juyo ya fuskanceta.
Hannunshi yasa ya jawo hannunta ya juyata rigingine.
Uhhhhmmmm shine sautin da suka saki a tare, lokacin da ya kife tafukan hannunsa kan lallausar fatar fuskantar,
A hankali ya fara yin ƙasa da hannunsa yana shafa mata addu'a ta ko wani sasan jikinta.
Shmmmmmm ya furta a hankali lokacin da ya dire hannunsa kan fatan wuyanta.
Sai kuma ya lumshe idanunsa a hankali a dai-dai lokacin da ya dire hannunsa ƙan ƙirjinta.
Da sauri ta rumtse idanunta da ɗan kare ƙarfi, saboda wani irin yam-yam da tsikar jikinta ya fara zubawa.
Shi kuwa Taj a hankali yaja wani kulafataccen numfashi, duk da kuma damuwar data Addanbi zuciya da ruhinsa bai hanasa jin wani baƙon yanayin ba, sai dai ƙarfin damuwar tayi nasarar tauye ta'azzarar mayatarsa ya duƙufar da kuzarinsa kaso 60 cikin ɗarin.
A hankali ya shafe mata dukkan jikinta, sai kuma duk suka sauƙe ajiyan zuciya a dai-dai lokacin daya konta gefentan gab da ita, har tana jin ɗumin numfashinsa.
Nigeria
A dai-dai lokacin kuma Dr ne kwance bisa kujerar a fili yake faɗin.
“Wannan Ustas ɗin ya watsa min shiri na, ya hargitse min duk maitar kwaɗayi na, nason jin irin ɗanɗanon ni'imar dake jikin Ishmah, wacce na tabbar zatayi min zaƙi fiye da duk matan da na sani”.
Sai kuma yaja dogon tsaki tare da miƙewa tsaye kayansa da dukiyar aurensa da Abba yasa Yah Abubakar ya dawo mishi dashi ya kalla cike da mamakin ganin tsinkensa basu taɓa ba. A fili yake faɗin.
“Duk da dai hakan ya zama sanadin kareni da yin dakon zunubin cutar da ita wurin raɓa mata HIV, Allah ne ya kareta, Afif ya zame mata Garkuwa Yah Allah ka bani dai-dai dani mai irin ciwona mu rufawa juna asiri.
Ethiopia.
Kwance take tayi lip ta rufe jikinta daga sama har ƙasa, wayartace a hannunta hotonshi dake fuskar wayar tata ta zubawa idanu babu ko kiftawa cikin murya mai cike da yanayin muradi tace.
“Kai wannan na mijine, cikekken namijin duniya, duk inda Namiji yake ya kai namijin da ko wacce mace take fatan mallakar irinsa Ya Allah kasa in samu na Habibina ma haka yake”.
Sai kuma ta fesar da numfashi tare da juyawa ta kwanta a kife cike da begen makusanci a gareta Allah ya sani ita macece mai muradi.
Doha Qatar.
a hankali ya ɗan yunƙuro kanta saboda jin yadda take sauƙe numfashi alamun bacci ya fara nasarar yin awon gaba da ita, kanshi ya ɗan ɗago matso da lips inshi yayi dai-dai kunnenta cikin raɗa yace.
“Babe! Babe!!”.
Sai kuma ya ɗan ƙara matsota cikin sanyi ya kuma kiranta yana mai ɗan ɗaura ƙafarsa ɗaya kan cinyoyinta.
“Hmmmmmm”. Tayi sauti alamun ta amsa.
“Babe zan rage Miki kayan nan sunyi miki yawa a jiki”.
Ya ƙare maganar yana zame mata hannunta cikin after dress ɗin.
“Hmmmmm”.
Ta sake faɗi Murmushin gefen baki yayi domin ganin yadda duk jikinta ya sake.
A hankali ya zare mata ɗaya hannun ma.
Ya zamana tana kwance ne kawai a samansa.
Komawa yayi ya kwanta tare da jawota jikinsa ya ɗaurata kan cikinsa ya manne kanta bisa ƙirjinsa.
Sai kuma yasa hannunsa ɗaya ya tattare after dress ɗin ya cilla shi can bisa kujera, blanket ɗin ya jawo ya rufe musu jiki, kana ya ɗaura tafukan hannunsa bisa bayanta yana ɗan shafawa a hankali yanayin sama da ƙasa dasu tare da ɗan mammatse wuyanta kamar maiyi mata tausa.
A hankali yaji idanunsa na lumshe,
ƙamshin jikinta ya kuma shaƙa a karo na barkatai tuni bacci yayi awon gaba dasu manne da juna.
Ethiopia
Washe gari da safe misalin ƙarfe tara.
Yah Aryan ne, zaune a Parlour Ummu Aryan ɗin, bisa alamu waya yakeyi da ɗansa Arfah cikin takaici yace.
“Wai ni Arfah anya kuwa ko ni ubanda da na haifeka kana sona kamar yadda kake son Afif wannan wanne irin nacin tsiyane da jarabar mayata shi yana can yana harkokinsa da karuwansa yama mance daku, kai ka buwayeni”.
Cikin takaici Arfah yace.
“Wlh Uncle Taj ba mazinaci bane, Dad ka daina faɗan haka”.
Cikin tsawa yace.
“To ubana yanzu dai saura ka rufeni da duka kawai ko. Maza gimtse wayar wlh in ka sake min mgnar Afif cin ubanka zanyi hegen yaron mai nacin jaraba”.
Jin haka ne yasa Arfah katse kiran kana yayiwa Imaran bayanin yadda sukayi da mahaifinsa ya ɗaura da cewa.
“Nifa gani nake kamar Abba na baya son Uncle Taj”.
Da sauri Imran yace.
“A'a Arfah kada ka faɗi haka, ya zaiyi ya ƙi ɗan uwansa yanzu bari in sake gwada kiran Uncle Taj ɗin”.
Ya ƙare maganar da kiran Taj ɗin, a hankali ya juyo ya kalli Arfah cikin sanyi yace.
“Layinsa baya shiga bari sai anjima in sake gwadawa”.
ranar dai haka sukayi ta gwadawa Amman bata shiga.
Qatar
Ƙarfe Goma dai-dai jirginsu Aunty Amina, Goggo Dija, Aunty Nana, Garkuwa, Khadija, Adam. Ya ɗaha daga Doha Qatar zuwa Abujan Nigeria.
Sai da suka ga tashinsu kafin, Taj da Ishmah suka fito Airport ɗin suka nufi gida.
Bayan sun dawo gida
Kwaɓe ta tsuke tare da tura baki, ɗan gajeren murmushin yayi tare da cewa.
“Afwan laifin me nayi ne wai?”.
Ya ƙare maganar yana ɗan zamewa ƙasa ya zauna gabanta bisa kujerar.
Murya can ƙasan cikin dishewa alamun tayi kukan tafiyarsu ta ɗan kalleshi kana tace.
“Shike nanfa sun tafi sun barni ni ɗaya, yanzu bani da kowa a ƙasar nan”.
Da sauri yace.
“Babe ba gani ba, Taj ɗinki fa, bakiji me Abba yaceba”.
Cikin sanyi tace.
“Naji”.
Miƙewa tsaye yayi tare da cewa.
To taso muje mu kwanta ki samu ladana Inyi bacci Kinga sai naji ɗimin jikinki nake iya bacci”.
Cikin ƙasa da murya tace.
“To Amman banda cire kaya”.
Hancinta ya ɗan lakace tare da cewa.
“Jiyama ke da kanki kikace in cire miki, da izininki na cire Miki ai kuma ai ba kaya na cireba”.
Ya ƙare maganar da jan hannunta suka nufi Bedroom.
Alhamdulillah washe gari ranar Monday aka buɗe Al-AHLI AFISHA HOSPITAL, lfy duk Doctors and Nurse's da cliners sun fara aikinsu babu kama hannun yaro buɗe asibitin kuwa yazo da gagarumin nasarar da tasa duk Qatar aka san da asinitin saboda wata balarabiyar da aka cirewa yara tagwaye biyar reras uku maza biyu mata, kuma duk suna lfy.
Acan Nigeria ma Alhamdulillah sun isa lfy ko wacce ta koma gidanta sai Khadija da Goggo Dijan ne da suke ɗan ƙara huce gajia kafin su koma Gombe.
Bayan kwana uku, wanda ya kama yau kwanansu goma kenan da zuwa Qatar.
A Parlour suke shi da Ishmah da Addawa yayinda Zulaihat da Laylah suka fita suna can baya suna lilo.
Ido Addawa ta ɗan zuba mishi saboda ganin yadda ya zauna yayi tagumi da hannun biyu.
“Zuwa yanzu dai ya kamata ace, ka bar duk wannan damuwar tunda Ishmah dai tayi maka kekkyawar fahimta.”
Nannauyan numfashi ya sauƙe tare da cewa.
“Ya za'ayi hankali na ya kwanta bayan kuma ance Laylah nada ciki, kinga tana cikin matsala an cuceta anyi mata fyaɗa da ƙanan shekarunta, sannan ance tana da ciki”.
Cikin kaɗuwa da tsoro Ishmah ta ɗan zaro idanunta waje tare da cewa.
“Innalillahi ciki kuma Addawa, to wai wanne mara imanin ne yayi mata fyaɗen nan kuma ace harma da ciki?”.
Cikin sanyi Addawa tace.
“Abinda kenan har yau bamu ganoba, mun kasa gano ko binciko wanda yayi mata fyaɗen har ya narka mata ciki”.
Cikin tausayawa da ƙunan rai hawaye na cikowa Ishmah tace.
“Ba komai wlh na rantse da Allah in sha Allah sai na binciko wanda yayi mata cikin nan kuma sai an gano shi ya amshi hukuncinsa in sha Allah zan yi bicike kan lamarin”.
Ta ƙare maganar da yaƙini.
Addawa kuwa bayanin duk yadda abubuwan suka faru ta labartawa Ishmah sai dai bata faɗi mata sharaɗin Malam na cewa muddin Taj ya bari ya haɗu da wani dangi nasa ko yayi mu'amala da ahlinsa ba, a bakin auren Ummeeysa.
Tadai gaya mata yace ya ciresa a yaransa baya kuma bukatar sake ganinsa ya kuma ce ya raba sunansa da nasa kasake tayi tana jin Addawa cike da nazari da zurfin tunani a hankali tace.
“Tajj anya kuwa ka gwada Laylah da kanka? Anyama akwai wannan mgnar, nifa gani nake nakircine kawai da iya tsara gadar zaren kai kuma ka rubta ciki kuma ka rasa mai tayake warwarewa”.
Cikin sanyi yace.
“Ma'eesha kiga yadda Laylah ta sauyafa duk alamun ciki bayyana gareta”.
Cikin nazari tace.
“Hmmm Tajj kamar ba likitaba kawai sun haɗa ma zafi kan zafine da fushin Yah Abana shiyasa baka iya tuna komai ba.
Amman in sha Allah zan nazarci lamarin”.
Kiran salla Magrib da shigowar su Laylah ne yasa suka watse taron nasu.
Misalin ƙarfe tara na dare.
Zaune take a bakin gadonta yayinda Laylah ke gabanta cikin nitsuwa da kuma son kwantar da hankalin Laylah da son gane abinda ke ɓoye tace.
“Laylah tashi in aikeki wurin Uncle Taj.”
Da sauri ta zazzaro idanu tuni jikimta ya fara rawa murya a firgice tace.
“Afwan Aunty Ishmah ina tsoro, ni bazan jeba”.
Cikin tsareta da ido tace.
“To Laylah me kike tsoro wai? Uncle Taj ɗinkin nefa, me zai Miki?”.
Cikin rawan murya da jiki ta ƙara matsowa jikin Ishmah cike da tsoro tace.
“Ni dai ina tsoronsa tunda yake cemin zai yankani in ban bari yayi min cikiba”.
Ya Salam shine abinda Ishmah ta faɗa cike da ɗimuwa da mamaki gami da firgici tace.
“Laylah Uncle Taj ɗin naki ne yake cewa zai yankaki in baki bari yayi miki cikiba, cike da gskya da gskya tace.
“Wallahi shine tunda mukaje Nigeria muka dawo, duk randa ya dawo Ethiopia a ɗakina yake kwana kuma sai yace in nayi ihu zai kasheni kuma in bari yayi min ciki, wai kuma kar in gayawa Aunty Meymey”.
Far-far jikin Ishmah ke rawa da tsuma, da sauri tasa hannunta duka biyu ta riƙe kanta saboda zafi da raɗaɗin kalaman Laylah yasa kan nata fara sarawa da ƙarfi, sai kuma ta buɗe bakinta da ta samu numfashi ya dai-dai saboda jin numfashinta na cizga.
“Yah Salam wannan makircine aka ƙullawa Tajj aka ɓatashi a gaban ƴar da yakeji shi ya haifa” .
Ta ƙare maganar zuci tana mai rumtse idanunta saboda jiri data fara gani.
Ita kuwa Laylah cikin Tsananin kukan rauni da ruɗu taci gaba da cewa.
“Har bindiga yake nuna min, yace min in cire kayana”.
Da sauri Ishmah ta riƙo hannun Laylah cikin son gano gskyr da takejin tsoron in ya tabbata cewa anyiwa Laylah fyaɗe nan tabbas zuciyarta zata buga domin tasan har abada yarinyar bazata yarda ba shi bane.
Murya na karkarwa tace.
“So sorry Laylah, kiyi haƙuri daina kuka, gaya min gsky tsakanin ki da Allah Uncle Taj ɗin ne, yake miki haka kin ganshi da kyau da haske lokacin da yake shiga?”.
Cikin shesh-sheƙan kuka ta fara gyara murya cikin gskyar lamarin da fahimtar yarintarta tace.
“Eh ko na kashe wutama, yana shiga yake kunna wuta, ya cire kayansa yace nima na tuɓe, kuma ya kwanta kan g...”
Da sauri tayi shiru ba tare da ta ƙarasa mgnar ba, saboda jin Yadda Ishmah ta saki wani irin.....
*Littafin INDA RAI na kiɗine ki biya ki karanta cikin aminci da salama 1k ne rak 0661110170 GTBank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidar biyanki ta wannan number 09097853276 mutanen Niger kuma 1000fc ne jaka ɗaya kenan rak zaku biya ta wurin Mommy +22790899076 idan kika karanta min littafina baki biyaba wannan ke da Allah*
By
*GARKUWAR MARUBUTA*
[4/30, 10:43 PM] +234 706 616 8286: 📝🕋💉🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*INDA RAI*
*BOOK 2 PAGE 6*
*AYASHA ALIYU GARKUWA*
*Bononza! Bononza!! Bononza!!! Kayan Mata na musamman. Kuɗi nake nema wuri janjau yaseen saboda inada abin yi dasu!!! Yoh ace min turo account no ma kaɗai yana sani farin ciki, inaga kuma inga alerts na zubowa kamar ruwan sama, toh wannan shine sirrin rashin raina Customers ɗina, ina yinku ina ganin girman yardar da kuke min saboda wasu ko mgna bata taɓa haɗani da suba sai kawai su turi dubban juɗaɗensu kafin ma suzo suce min ga abinda suke, wlh hakan kan sani jin in mutuntasu sabida ai yardace ta kawo haka, yinku ina sonku domin kuna sani