Showing 39001 words to 42000 words out of 44320 words
numberta ai sai ki biya kawai kafin kimin mgn. Tunda dai ga alamominshi da duk illar da yakeyi na faɗi in kina dashi faƙat in babu kada ki wani zo kice min bayani dan ko kinzo iya bayanin da zan miki kenan*
Alamomin infection sune kamar haka. Rashin sha'awa. Ƙaiƙayin gaba Kiji idan ya fara miki ƙaiƙayi kamar zakiyi hauka. Warin ko ƙarnin wurin. Fitar farin Ruwa mai fatsi-fatsi. Ƙurajen su ɗan fetso ƙananan ko ƴan manya, melewar fatar wurin, Tusan gaba. Bushewar gaba, Rashin ni'ima. Buɗewar gaba, domin har budurwa infection na iya buɗata. Ciwon mara ko ciki mai tsanani yayi al'ada, rashin haihuwa, domin har baƙin mahaifa take toshewa. Ko kirinƙajin wani abu na miki yawo ƙasan mara, ko jin zafi yayin yin fitsari, da kuma saduwa, da dai sauran abubudann ban lissafa. Sune manyan alamomin infection.
Shin kin kuwa san illar da infection keyi miki, amman kinajin ɗaya daga cikin alamominta kinyi bulum buƙui da ita a jikinki. To bari kiji illolin infection wato cutar sanyi.
Rashin haihuwa, ƙyara da hantara a wurin miji domin muddin kina tare da ita baki da wata daraja a idanu nai, sabida ƙyamas kike ba damshi bare wata ni'ima mai Taste, Kinga kenan shinfida ta lalace, in kuwa shinfiɗa ta lalace dole kiga sauyin fuska, domin su maza dole sunason wurin da kwaranya, zaki kasance baki da wani daɗi da ɗumin da mai gida ke buƙata. Kinga duk tsabtarki da kyanki da iya girkinki shinfidarki ta zama lami. Kiyiwa Allah ki nemawa kanki lafiya ki samawa mijinki da ke kanki nitsuwa.
KADA KUJI IYA WANNAN DOMIN AKWAI MUGUN INFECTION WANDA BAYA BAYYANA KANSA. Wanda kawai sai dai kijiki, kamar kwalta kin bushe ƙyamas ya dauke miki dukkan sinadaran ni'imomin ki, da sha'awarki, duk kayan matan da zakisha a wofi zadai kiji ƴan uwa da abokan arziƙi da ƙawayenki na yaba miki magunguna GARKUWAR MA'AURATA, amman ke in kinsha jiya I yau, duk nacin oga da yi miki wasannin bazaki ji sha'awa ba, toh wlh muguwar infection ce, wacce bata bayyana kanta har sai ta gama yi miki rugu-rugu. Ta lalata miki zaman aure. Lokacin da zata bayyana sai kiji Doctor's suna kira miki, ovarian cyst, ko kuma fibrod duk a cikin chronic infection ne yar uwa.
INFECTION set ɗinmu na kowa da kowane Mata, Maza, Bazawara, Budurwa, Maijego, Yara, Ke yar uwa Wlh har maiciki zatasha, bashi da matsalar komai Maganin na Gargajiya ne mai rakake INFECTION ya fito miki dashi, wlh duk nacin infection koda na cikin mahaifane bi'izinillahi ta'ala zaki rabu dashi, cutar infection cutace mai masifar naci, so yar uwa kana dole ki nace masa da maganin set ɗin na 10k ne kuma maganin kala biyarne nasha da kala uku na tsarki ɗaya na shafawa ɗaya. Yar uwa idan har kin saya to kiyi ƙoƙarin kisha da mijinki, in akwai abokiyar zama, kisa miji ya saya mata, domin ko kin rabu da shin dai ita tana dashi tofa kin kashe macijine baki cire kaiba, ma'ana zai sake dawo miki, idan kuna da yara suma a saya musu, domin tsoron kada ya riƙa a jikinsu musamman ya'ya mata ya buɗa miki ƴa tun tana ƙaramarta, ki aurar da ita miji na muku kallon lalatattun iyaye da baku iya bada tarbiyaba. Saboda yamayin garin yasa ina raba rabin set ɗin in sa miki komai rabi-rabi 4k amman set ɗin 8k ne. Idan kin san a shirye kike ga account number na nan 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, ki turo kuɗinki kafin kiyi min mgn ta WHATSAPP NUMBER'N na 08069423567 sai ki turo min shaidar biyanki, domin akwaishi Available ko yau kika tura kuɗinki, gobe kayanki zai taho, ina bada sari ko sayan ɗaɗɗaya. Farashin Sari da sauƙi daga kan mutum 3 ko 6 ko 12. Kai ko na mutum 24 kikeso in Sha Allah zaki samu. Please dan Allah in dai kinsan baki shirya sayaba kada kimin mgn ki bari sai kin shirya. Taku ce dai GARKUWAR MA'AURATA.
Tattausan murmushi mai cike da matsanancin jin daɗi ta watsa mishi, tare da ƙara sawa gareshi cikin sassarfa.
Buɗe idanunsa yayi da sauri lokacin da yaji ta Abka jikinsa, tayi mishi wani irin amintaccen ruƙumar dake nuna tsananin farin cikin da take ciki mara adadine.
Kar-kar haka jikinsa ya saki wani irin tsuma da ɓari da yasa shi ware hannunsa duka biyu yayi mata wani irin sahihin rugguma, tare da cusa kanshi tsakanin wuyanta da kafaɗarta.
Cikin Muryar dake bayyana samun salama, aminci, yaƙini, gamida nutsuwa mai tafe da tsananin farin ciki ta fara magana.
“Alhamdulillah Yah Sheykh na godewa Allah, ya tsarkake min kai ya nesantaka da kaidin magautanka, ya kare Laylah da mugun fatan, mun tsallake makircin makiran dake saƙa maka gadar zaren Allah ya warware mugun saƙansu.
Yah Sheykh Wallahi! Tallahi! Laylah tana nan da budurcinta, babu abinda ya sameta, kuma bata da ciki, namiji bai taɓa raɓar jikintaba she's varging Yah Sheykh ba abinda ya samu ƙuruciyarta bata da cikin da akace ma duk ƙarya ne”.
Rungume juna sukayi ƙam-ƙam tare da fara sakin numfarfashi a Jere a jere.
Ya ilahi ya mujibat da'awati yah hayyu ya ƙayyum bi rahamatika astagis.
Sune tasbihan da Taj ya fara jerowa a saman lips inshi, tare da ƙara matseta a ƙirjinsa tamkar zai maida ita jikinsa, sai wasu irin amintattun ajiyan zuciya da numfashi yake sauƙewa a jere a jere yadda kalaman Meymey na cewa Laylah nada ciki kuma shi yayi mata ciki suka gigitashi tare da fiddashi daga hayyacinsa da ɗimautashi da janye kuzarin sha'awarsa na komai a duniya.
A kuma lokaci ɗaya kalaman Ishmah suka dawo da mishi nutsuwarsa, lafiyarsa, tunaninsa, farin cikinsa, harma da kaso 60 cinin ɗari na sha'awarsa suka diro mishi in one second, sai ragowar kaso 40 da fushin Yah Abana da kewar Ummeeynshi ya danneshi.
Ethiopia
Cikin tsuke fuska da bayyana fushi da juya harshe ih zuwa bada umarni Malam ya kalli yaran nasa tare da yin gyaran murya yace.
“Na taraku ne, domin in gargaɗeku, in kuma baku umarnin ku gargaɗi fitsararrun ƴaƴanku more especially, Arfah da Imran da Hameedah kada wanda ya sake turo min hoto ko vidios ɗin Abban..”.
Sai kuma yayi saurin katse mgnar da zai ƙarashe da kiran sunan da yake kiran Taj dashi
Sai kuma ya ƙara tsuke fuska.
Jin Yah Hafiz na cewa.
“Afwan Malam kayi haƙuri ka gafarcesu, in sha Allah zamu ɗauki mataki a kansu”.
Juyowa yayi ya kalli Yah Aryan da yayi ƙasa da kansa cike da takaicin Arfah yace.
“Kai Aryan ka gayawa ɗanka Arfah ya goge Number ta a wayarsa tunda shi yafi kowa tsaurin ido da rashin kunya, har ni Arfah zai turawa video Afif harda cemin, in dai da ɗingon imani a zuciyarka dole kaji tausayin Uncle Taj kuma dole ka dawo dashi cikin ahlinka.
Aryan har ka haifi ɗan da zai nuna min cewa banida imani ko ɗigo kenan, shi ya haifa min Afif ɗin ne? Ko shi zai gaya min yadda Zan hukunta ƴaƴana in sunyi laifi, to Wallahi ka rabani da Arfah kafin in rabaka da kaina”.
Cikin tsoro Yah Aryan ya rinƙa girgiza kai tare da cewa.
“Afwan Malam in sha Allah haka bazata sake faruwa ba, zanyi maganin Arfah da yardar Allah.”
Sai kuma duk suka juyo suna kallon Yah Abduraham da suka ji shesh-sheƙan kukansa na tashi a hankali murya na rawa yace.
“Malam kayi min izini in tashi, in fita tunda ni dai bani da ɗa, ko ƴa kaga bana cikin masu laifin ko!? fatana kuyi min addu'o'in Allah ya bani ɗa mai kama da Afif mai irin halinsa da nagartasa da tarbiyarsa, zan soshi zan kusanta kaina dashi koda kuwa ace irin ƙaddarar sharrin data faru akan Afif ta faru a kansa sau uku ne, ni zan soshi bazan nesanta da shiba, tunda ni ƴaƴan basu dayawa bazan koreshi in nesan tani da shiba, dan ina jin ina da wasu kusa da niba. Yah Allah ka azurtani da ɗan kamar Afif, zan riƙeshi kamar yadda kace su ƴaƴan amanace ga iyayensu kuma ababen kiyayewa da tambaya ne”.
Wani irin murmushin mai haɗe da ruwan hawaye Yah Yusuf yayi sabida fahimtar Abduraham nayiwa mahaifinsu tunasarwa ne kana abinda yayiwa Taj dan yana ganin Allah ya bashi yara da yawa, ya kuma mance cewa suma ƴaƴa amanane akan iyaye, ya haɗe mgnar da nuna mishi ita ƙaddara ba'a guje mata.
Shi kuwa Malam ido ya zuba wa Abduraham har Saida ya dasa ayar ƙarshen mgnar kana yace.
“Ka gama!?”.
Cikin sanyin Yah Abduraham ya gyaɗa mishi kai alamun eh ya gama.
Numfashi mai zafi ya fesar kana yayi gyaran murya tare da tsuke fuska yace.
“Na fahimci cewa kai ke zuga Arfah da Imran da Hameeda yar Yusuf na fahimta ashe kaine ke ingizasu da tsara musu abinda zasu faɗa min kamar an sauƙo maka da wahayin maganar ba shakka Abduraham ka iya falsafa.”
Da sauri ya fara girgiza kai hawaye na zuba yace.
“Kayi hakuri ya kai mahaifina, wlh tun ranar da kace baka yafe mana muyi alaƙa da Afif ba, ko sunansa ban sake kira a saman lips ɗina ba, sai dai kayi haƙuri da aikin gafara, domin duk sanda nayi salla inayi mishi addu'o'in a cikin dukkan sallolina, tunda bakasa yi mishi addu'a a cikin sharaɗinka ba”.
Cikin tsuke fuska ya nuna mishi hanyar fita, da sauri ya miƙe tare da cewa.
“Ka gafarceni malam”.
Daga nan ya fita, su kuma sukaci gaba da zama suna jin gargaɗin mahaifin nasu Yah Hafiz kam sosai yaji daɗin kalaman Abduraham domin ko ba komai ya tunasar da mahaifin nasu cikin hikima.
Qatar.
Kusan gaba ɗaya ido suka zuba wa Taj da yayi sujudushukur a Office ɗin Dr Abbas ɗin.
Murmushin Dr Amdaz yayi tare da zama bisa gadon dake can gefe.
Dr Abbas ɗin kuwa ɗaga Laylah yayi ya zaunar da ita gefen Dr Amdaz.
Dr Farida kuwa ido ta rumtse cike da kishi ganin yadda Taj ya kuma sake ruggume Ishmah tare da tallabe fuskantar da tafukan hannunsa duka biyu lips inshi ya manna kan goshinta tare da liƙa mata amintaccen kiss bisa goshinta.
Cikin Muryar dake nuna zafin so da ƙauna da matsayinta a rayuwarsa yace.
“Duk sanda na shiga duhu kece ke isowa inda nake duk tsananin duhu, sai kin iso gareni sannan ki haskaka min wurin, duk sanda na zubda hawaye kece ke shara minshi, ko a mafarki baki taɓa barin na zubda hawaye ba, in kin bani shawara ko yaya sai na samu al'khairi a cikinta, shiyasa koda a mafarki kika ban shawara sai na bita.
Ma'eeshah kin zame min Noor ala Noor. Laisa lee misluki abadan Hayateeh ana uhubbiki Hubban shadidan wa axeeman wa kabeeran Yah Hayateeh.
Duk ƙanƙamtar munin furuci ko suffa bakya kusantani dashi kinyi min yardar da har abada babu macen da zata yi min wannan yardar.
Tukucinki in soki ke kaɗai in killace ki a zuciyata ke ɗaya, in hana ko wacc mace kusantar zuciyata, Babey ni zanyi miki kishin kaina da kai na. I love You Every second every minute, of every day.
Sai kuma ya ɗan ƙara ruggume ta tare da kwantar da kanta ƙirjinsa cikin sanyi murya yace.
“Ma'eeshah kin min yardar da ko Ummeey wa Abeey basuyi min irinsa ba”.
A hankali ta ɗan fara janye jikinta saboda jin wani irin buga ƙofar da Dr Farida tayi bayan ta fita.
Shima saketan yayi tare da komawa ya zauna, kana ya nuna mata kujerar kusa dashi ta zauna.
Cikin sanyi yace.
“Maeesha ba mafarki nakeyi ba ko!?”.
Cikin yaƙini da sanin aiki da iyawa Dr Abbas yace.
“Ba bacci kakeyi ba, idonka biyu, kuma tabbas abinda kaji hakane Laylah bata san namiji ba, kuma bata da ciki”.
Cikin gamsuwa da mamaki yace.
“Toh Amman meyasa duk kamanninta suka sauya har amaifa takeyi, gashi tayi wani irin fari irin na masu ciki gashi sai ƙara girma takeyi”.
Cikin nutsuwa Dr Amdaz yace.
“A binciken da mukayi mun gano cewa,
Allurar sauya launin fata akayi mata shi yasa taketa ƙara zama kalar masu ciki.
Sai kuma allurar super appatite shine yake sata yawan bacci da kasalar, kuma ƙarfin da yayi mata Shiyasa take yawan amai dan shekarunta basu kai ɗauka ba, shiyasa madadin ta yawaita cin abinci sai yawan amai.
Amman Alhamdulillah yanzu duk anyi maganin matsalolin an haɗa mata maganin da zatayi tasha ya kauda ƙarfin alluran, sannan batun budurci ta kuma.
Duk inda za'aje a duniya a gwada amsa ɗaya zai baku so ba dalilin yin ciki”.
Ita kam Ishmah shiru tayi tana nazarin tabbas akwai lauje a cikin naɗi akan likitocin da sukayi ta gwada Laylah a Ethiopia.
Numfashi mai nauyi ta fesar tare da kamo hannun Laylah ta jawota jikinta a ranta take nazarto.
Lallai an shirya wa makircin tunda anyi nasar sa Laylah tsoron Taj, har take bada tabbacin lallai ilaihin tabbas Taj yana zuwa ɗakinta ya kwanta.
Cikin sauƙe numfashi ta kalli Taj daya miƙe tsaye ruggume juna sukayi da Dr Amdaz kana ya ruggume Dr Abbas, sai kuma ya matso kusa dasu, shafa kan Laylah yayi wacce ta bishi da idanu cikin alamun tsoronshi ya fara ɗan raguwa a ranta, tun lokacin da aka shaida mata ciki da bayanan da Ishmah tayi mata,
Cikin tsananin farin ciki yace.
“Laylah ce Alhamdulillah”.
Cikin sanyi tace.
“Alhamdulillah Uncle Taj”.
sai kuma ya riƙo Ishmah kana yace.
“Mu tafi”.
Ya ƙare maganar yana ɗan murmushi.
Kusan a tare suka fito da rakiyar su Dr Abbas.
Suna fita Bilal na isowa, shiga motar sukayi kana yaja suka tafi gida.
Nigeria.
Abba ne zaune a Parlour'n sa Khalid da Mahamud da Minat ne zagaye dashi cikin jin daɗi Khalid yace.
“Abba Daddy'nmu ya yarda in na gama Secondary School zan koma wurin Mamey na, kuma yace ma, in an bamu hutun Ramadan zamuje”.
Murmushin Mahamud yayi tare da cewa.
“Yaro ana jirgaka yanzufa kusan wata shida ne ya rage Ramadan ɗin”.
Da sauri Minat tace.
“To ai zaizo kamar yau, wlh Daddy ya yarda yace zamu je”.
Cikin so da ƙaunar jikokin nasa yace.
“To Allah ya kaimu lokacin bisa rai da lfy, yau ma kwana zamuyi sai gobe ku koma ko?”.
Kai Minat ta jujjuya tare da cewa.
“To ai gobe Monday akwai school”.
Da sauri Khalid yace.
“To ai dukanmu sai 12:00 zamu tafi, zamu ƙara kwana da safe Uncle Hamisu yace zai maidamu”.
Kai Minat ta jujjuya tare da cewa.
“Amman kasan za'ayi mana faɗa mun ƙara kwana ɗaya kan ɗaya da aka bamu ko”.
Gyaran murya Abba yayi tare da cewa.
“Ba komai zan kira Daddyn naku in tambaya mana shi”.
Sai kuma duk suka kalli ƙofar shigowan jin Hamisu na cewa.
“Ai na tambayeshi ma, yace ba matsala da safe in maida su”.
Tsalle suka fara cikin jin daɗin, sai kuma Khalid ya tsuke fuska tare da cewa.
“Kuma tun da safe nake cewa ku kira min Mamey na baku kira min ita ba”.
Hannunshi Hamisu ya kamo tare da cewa.
“Zo mu tafi ball sai anjima in sake kiranta, na kirata sau biyu bata kusa”.
Daga nan suka fita.
Qatar.
Addawa ce ruggume dasu duka biyu Taj da Ishmah, cikin tsananin farin ciki, sai kuma ta sakesu tare da fuskantar alƙibla tayi sujudushukur, sai kuma ta tashi tare da fara ƴar rausayawa irin tasu ta tsoffi.
Kelƙelewa da dariya Laylah tayi harda riƙe ciki
Zulaihat ma dariyar takeyi.
“Alhamdulillah Allah kaine abin godiya, Ubangijin talikai maiyin yadda yaso a lokacin da yaso, mu dai yau haske yazo ya yaye duhun zuƙatanmu, nayi sujjadar godiya a gareka Allah ka ƙara amintar da gskya a cikin zuciyar bawanka Muhammad ya yarda dq nagartar ɗansa Tajuddeen”.
Cikin sanyi Ishmah tace.
“Amin Ya Allah”.
Sai kuma ta nufi Dinnin area da sauri tare da cewa.
“Ishmah ku taho kuci abinci, muyi farin ciki mu godewa Allah”.
Hannun Laylah Ishmah taja kana suka nufi Dinnin area.
Zama sukayi tare da jawo plate dan Allah ya sani yunwar sukeji dan basu karya ba suka fita.
Cikin kulawa ta kalli Taj dake zaune bisa kujerar 3 sitter bai tasoba.
“Yah Sheykh kazo muyi breakfasts”.
Kanshi ya ɗan jinjina tare da yi mata kallon aminci kana ya taso yazo.
Bayan sun ci abinci a hankali ya miƙe tare da kallonta kana ya kalli Laylah dake sauƙa daga kan steps ɗin cikin sanyinsa yace.
“Kinyi komai saura ki cire tsorona, a zuciyar Laylah ki tabbatar mata cewa ni matsayin uba nake a gareta, ni tamkar yata ta cikina nake jinta”.
Cikin jinjina kai tace.
“In sha Allah kuwa”.
Gefen fuskarta ya ɗan shafa tare da cewa.
“Zan shiga ciki in ɗan watsa ruwa in tafi masallaci, sai na dawo ki kai min tea”.
Kai ta gyaɗa tare da kallon time ɗin wayarta kana tace nima bari in shiga.
Daga nan ya haura ita kuma ta shiga bedroom ɗinta.
Wanka tayi tare da sauya shiga zuwa doguwar rigar atampa pink color da ɗan ratsin golding collar and white.
Ɗas rigar ta zauna a jikinta, hijabi tasa tayi salla bayan ta idar, ta ɗan ƙara turaruka a jikinta tare da mirza ɗaurin asetta.
Jin wayarta nata ringing ne yasata saurin ɗauka.
“Babeyyy!”.
Yayi mata kiran can ƙasan maƙoshinsa da wani irin salon da yasa tsikar jikinta amsawa cikin sanyi tace.
“Na'am”.
Gyara zansa yayi a kan carpet ɗin Parlour shi tare da cewa.
“Zan sha tea”.
Tana fitowa Parlour'n tace.
“To gani nan zuwa”.
Addawa kuwa tana shiga ɗakinta ko sallan bata yiba, saida ta kira Ummeey Taj tana ɗagawa tace.
“Alhamdulillah yau dai dole in nemeki kuma inyi miki maganar Afif tunda cikin sharaɗin mahaifinsa babu batun in kinyi mgnarsa dani akan aurenki”.
Cikin sanyi Ummeyy dake zaune kan salla tace.
“Ai dama kullum ina son tambayarsa fushikin nake tsoro na cewa kada in dameki da magarsa nake shiru yana lfy?”.
Cikin farin ciki Addawa tace.
“Toh Alhamdulillah, yana lfy matarsa na lfy. Laylah tana lfy nima ina lfya Zulaihat na lafiya, uwa Uba kuma yau a Asbitin suka wuni shida matarsa da Laylah, anyiwa Laylah duk gwajin da ya dace, wlh bata da ciki kuma ba'ayi mata fyaɗe ba”.
Tunda Addawa ta fara mgn tayi kasake sai jin kalaman Addawa na ƙarshene yasata faɗawa tayi sujudushukur tare da yiwa Allah kirari.
“Yah Allah masanin zahiri da baɗini, ya Allah kaine mafi ƙololuwar sani, kasan cewa ɗana tsarkakekke ne ya Rabbi kasan waɗanda suka shirya mishi wannan gadar zaren, ya hayyu ya ƙayyum bi rahamatika astagis Allah dan tsarkin Alkur'ani mai girma da nauyin kujerar al'arshinkan Allah ka hana duk wanda ya samu cikin wannan masifar samun farin cikin rayuwarsa, kasa ya tonawa kansa da kansa asiri ya rabbil izzati ka ƙara fidda gskyar mai gsky ka huci zuciyar mijina mahaifin Bawanka Tajuddeen ya yafe masa ya barni in kasance tare da ɗana kamar ko wacce uwa da ɗanta”.
Tunda ta fara jero addu'o'i da Amin Amin Addawa ke amsa mata cikin jin daɗi.
Tana