Showing 15001 words to 18000 words out of 45625 words

Chapter 6 - HAMDAH part 3 Complete hausa novel

RASHEEDA   

04 Oct 2024

12667

Allahu".
yayi maganar tare da buɗe tafukan hannunsa yasoma karanto Suratul (Khafi) aya goma na farkon surar haɗe da ayatul Qursi'yu ya tofa kana yashafamin a kan. cikin yar da da buwayar Allah naji ciwon kan na sauka.

Ko da muka shiga jahar plateau state, farkon shiga garin Jos NARKUTA. wasu zafafan kwalla ne suka gangaro kan fuskata tuno da Mama mai awara, da sauri nayi yinkurin yin magana a tsaya amma abun mamaki sai naji harshe na yayi min mugun nauyi gaba ɗaya jikina ya sake babu alamar karfi tattare da ni, abun da na fahimta tun lokacin da nayiwa Bappa maga shigar mu Bauchi zan kuma wata maganar naji na kasa, har kuma yanzu ina jin yanayin...
da daddare muka shiga Abuja, da kyar da taimakon Bappa na iya sauka cikin mota muka shiga ciki.
Inna wuro ta firgita da ganin yanayi na, ko da Bappa yayi mata bayanin abun da ya faru, hankalin ta yayi masifar tashi, yace ta taimaka min naje na kwanta, shikuma yafita can ya dawo da ɗan karamin ƙwarya da magani a ciki yabawa Inna wuro yace
"Kibata tasha babu komai insha Allah zata ware garin ne kwatakwata basa so tashiga sai dai tayi nesa da shi sun mance cewa Allah baya bacci".
Inna wuro tace "Ikon Allah wannan irin shiga sakani sai sakayyar Ubangiji".
ko da Inna wuro ta bani maganin inasha bada jimawaba bacci yaɗauke ni, ranar a kaina ta kwana, Fatu kuma tana tare da su Naseem a ɗaya ɗakin dake kusa da nawa.
washegari kuwa cikin yarda da buwayar Allah namike garau...
muna tare a parlour ni Inna wuro Fatu dan har lokacin basu koma side ɗin suba, labarin garuruwan da mukajejje narika basu ina washe baki da faɗin
"Allah Inna wuro bakuga abubuwan yan da sukayi kyau ba kai har da garin da ban taɓa zuwa ba".
nayi maganar ina washe baki, dariya suka rika min, nan
Bappa yashigo ganin jikina shima yazauna mukayi ta hira....

bayan kwana biyu

Mutane biyu daga cikin jagororin nan suka zo su da wasu mata guda biyar sukace na zama a cikin su wan da zasu rika yi min ai ki,
mata ne irin wan da suke karkashin paundation, irin waɗan da mazajensu suka sake su dakuma wan da mazajensu suka rasu, akan ɗauke su ai ki irin gidajen masu kuɗi ɗin nan, a cikin su na zaɓi guda uku dasukafi kwanciya min a rai, kana nace zan gwada ai ki da su.
ɗaya na ɗauke ta a matsayin mai kula da su Nasmah dakuma kula da tsaftar side ɗin,
na biyun kuma mai girka abibci, sai kuma ɗayar na turawasu Inna wuro ita zata rika kula da tsaftar side ɗin su dakuma girkin su.
nan suka kuma gabatar min da masu maza wan da nazo nasame su a cikin gidan, direba sai mai baiwa fulawa ruwa shi zai rika wanke mota, sai mai gadi dakuma mai kula da tsaftar farfajiyar gidan gaba ɗaya.
mun zauna da su na ɗan wani lokaci na fahimci mutane ne masu kirki da rukon amana.

Haka rayuwa tacigaba da tafi, tuni akayi bikin buɗe masana'antu da masallatan nan manyan shuwagabannin Nigeria sun halacci torurrukan sun kuma bada gudummawar su kwarai da gaske wajen ganin an ɗibi ma'aikata masu inganci.

Bayan wani lokaci

Tuni aka damkamin ragamar duk wasu kaddarori na ni nake bada umurnin ayi da kuma kar ayi, har kuma yanzu muna tare da jagororin nan su suke sanya ido kan ganin komai yatafi dai-dai.
tuni nasa aka baiwa Fatu uniform a ɗaya daga cikin makarantu na, dan dama acan rugar ma tana karatun ta tacigaba a nan.

Zaune nake a parlour ina dudduba jerin sunayen mata da matasan da nasa a ɗiba, a karkashin paudasion ɗina domin basu tallafin wasu kuɗaɗen da zai jamusu jari domin dogaro da kansu, matasa hamsin da kuma mata hamsin,na tura da kuɗaɗen tallafin izuwa asusun *HAM'NAS* paudasion.
a hankali na mike tsaye tare da yin mika haɗe da salati, wayoyina na tattara haɗe da sabuwar system ɗina, na haura sama,
kan bedside na ajiye su kana na haye gado dan bacci nake ji, ina so nayi baccin kafin su Naseem su shigo dan suna can side ɗin su Bappa.
har na kwanta na tuna da akwai maganar da nake so muyi da Bappa kan wani Company na murza karfe da ake gina shi a Lagos,
mikewa nayi na fita dan ina so muje ziyarar gani da ido acikin satin nan.
da gudu Nasmah ta shigo tana faɗin
"Mommy kin ga Naseem ko jai camin jiji".
Naseem shima dagudu yashigo yana binta da abun yana dariya, Fatu na biye da su tana dariya da faɗin "Naseem kabari kar ka sa mata".
da sauri nakarasa sauka kan step na rungumo Nasmah dake falfala gudu kamar zata kife kasa nace "K.......!★







Mommyn Twins ce














5




"Kai Naseem me zaka sa mata kai ka bari zata faɗi fa kabari."
nayi maganar ina ɗago Nasmah cak na rungume ta a jikina, shiko dariyar yake yana matsowa in da muke ya ɗaga hannun sa sama tare da yin ɗagelgel da kafa, yana washe baki,
na ce "Idan ka zo nan sai na mare ka, zo kagani zo ka samata kagani,
dariya sosai yarika yana faɗin
"Mommy dan tamata ne dan ta mata wannan."
"To ka samata kagani sai na maka bulala."
kiran Talatu mai kula dasu nashiga yi ina faɗin
"Talatu zo ki kaishi wa ɗawisu ta cakwaɗe shi tun da dai shima sa mata jiji zaiyi."
Talatu ta iso da sauri tana faɗin
"Ayi hakuri Hajiya kar a kaishi wa ɗawisu zata cake shi, zo nan Naseem kada kasa mata ko, so kake a kaika wa ɗawisu ta cake ka,zo ko ɗan lele na mene ne zaka sawa Nasmah ɗin?."
ɗan karamin tafin hannunsa da ya dunkule ya buɗe kaɗan ya nuna mata kana ya kuma dun kulewa yana cigaba da dariya, "Lalala shine zaka sa mata?."
cewar Talatu tayi maganar haɗe da dariya, kai ya gyaɗa yana washe baki, duban Fatu nayi ina faɗin
"Wato Fatu keda Naseem kuke sawa Nasmah ta abin tsoro ko? to bazata sake wasa da ku ba."
dariya Fatu tayi tare da faɗin
"Allah Adda HAMDAH kin ga bansan in da yasamo ba kawai ganin sa nayi ya shigo da shi a hannunsa,malam buɗe takarda ne fa."
"Au malam buɗe takarda ne ya ɗauko shine yake so ya sa mata to bari yagani sai an kaishi wa ɗawisu shima, shine baki karɓa ba ko Fatu kika tayashi tsoratar da ita."
"Allah Adda HAMDAH binshi nake na karɓa shine yagudu."
Talatu ta ɗauke shi tabuɗe hannunsa taciro abun tana faɗin
"Kawo shi nan a yasar da shi kada ka saka mata kaga tana jin tsoro, kaima kada ka sake ɗauka a hannun ka."
tana rike da hannunsa tafita waje ta yasar da shi kana suka dawo ciki.
karaso wa cikin parlour nayi na zauna kan kujera tare da zaunar da Nasmah kan cinya ta, na dubi Fatu nace
"Fatu Bappa na ciki ne?."
tace "A'a yafita". sai kuma ta turo baki gaba tare da faɗin
"Adda HAMDAH nifa wannan sunan Fatun nace ki dai na faɗin shi, Fatun nan fa a can Ruga ne fa ake kiran Fatun nan tun da yanzu mutum yazo birni har yanzu ayi ta ce mishi wani Fatu, gaskiya Adda HAMDAH ni wlh na canza suna Fatu ai duk su Inna wuro ne suka wani lankwasa min suna yaya Mahmoud dake shi a birni yake ai Fatima yake cemin,haka jiya wata ƴar ajin mu tana ta min dariya wai ni Fatu, aradun Allah na canza suna ko a ajin mu ma na faɗa na canza suna".
dariya muka tuntsire da shi, Talatu tace
"To Fatu man yan gari me kike so ace miki kenan?".
"Ai sunana da yawa masu daɗi ma, Nana, Fatima, Faɗimatu, Faty Zarah duka gasunan masu daɗi sai a rika cewa mutum wani Fatu kamar rugo".
nace "To lallai kam kamar kin sani da ma kam wannan sunan bai dace da ke ba yanzu dai kawai Faty za'a rika ce miki."
tace "Yauwaaa Adda HAMDAH Faty wlh yama fi amma kuna ta cemin wani Fatu kamar rogo".
"Hhhhh Faty kenan Allah bakida dama".
tace "Yauwa Adda HAMDAH gashi kin iya faɗin sunan dai-dai mai daɗi".
kai kawai na girgiza ina dariyar ta.
tace "Zo muje muyi wasan mu o Nasmah."
nace "O'o kuje bazata biku ba kuje kusata kuka bazata biku ba kam kutafi ku."
"Allah bazan barshi yasa mata ba". fuskata na kawo dai-dai fuskar Nasmah nace
"Zaki bisu?". kai ta gyaɗa "To muje daga gun na duba ko Bappa ya dawo".
nafaɗa ina mikewa na direta kasa tare da ruko hannunta muka nufi side ɗin su Inna wuro.
a parlour muka tadda Inna wuro Bappa bai dawo ba sai na zauna muna ɗan taɓa hira da ita.
muna nan zaune har Bappa ya shigo yazauna muka cigaba da hirar da shi, acikin hirar nake yi masa maganar yace kwarai kuwa ya dace kam aje domin a ganewa ido, in yaso satin sama sai a je, duk da akwai idanu da yawa akan lamarin. nace "Toh Allah yakai mu."
muna zaune sai ganin Naseem mukayi ya kin kimo school bag ɗin Faty, a tsakiyar parlour'n ya zauna ya tuttuɗe littatafan cikin jakar kasa ya ɗauki littafi guda ya buɗe yana ta gwalaɓe wai shi yana karatu.
dariya duka muka saka, Faty ko da gudu ta mike taje ta tattari litattafan ta tana ta faɗin
"Kai kasan meye a ciki ka iya karatu ne".
Inna woro tace "To ai karatun yake baki gani ba".
cikin muryar dariya nace "Um karatu yake ko gwalaɓe har da wani mike kafa kamar mai karatun gaskiya."
"Ah to gaskiya za'a saku a makaran ta tun da har ka iya ɗauko littafi kazauna ka buɗe kana karatu".
cewar Bappa yana yi masa dariya.
"Wlh Bappa nima dama ina so a turasu makaranta amma a sona sai sun cika shekara uku da rabi, amma gashi nan bakin su ya buɗe kawai sutafi yanzu."
Bappa ya jinjina kai kana yace
"Kwarai kuwa ya kama ta kam tun yanzu, tun da ga bakin su nata kan buɗe wa a kai su makaranta yakarasa buɗewar a can"....


A cikin satin akayi musu komai da komai nashiga makaranta, sai dai wata makarantar daban badaga cikin nawa ba, dan *HAM'NAS* International School Of Science Of Technology. suna da nisa saka nin mu, duk da dai shima makarantar da aka sasun yana da ɗan nisa sai dai baikai su nisa ba,
Islamiyar da a kasasu kuma anan unguwar tamu yake.
ranar da zasu fara zuwa kuwa zo kaga murna wajen su, da misalin karfe 7 na safiya Talatu taga ma shirya su tsaf, Zulai kuma ta shirya musu lafiyayyen breakfast ɗin su.
ina rike da hannun su muka fito in da Talatu ke biye da mu rike da school bag ɗin su da baske, parking lot muka nufa, tun kan mukaraso Yakubu direba dake goge mota yayi hanzarin buɗe marfin motar, cike da ladabi yaɗan duka yana faɗin
"Barka da safiya Hajiya."
"Yauwa barka." nafaɗa cikin ɗan jin nauyin yan da suke yimin idan zasu gaida ni, duk kanin ma'aikatan gidan sun girme min nesa ba kusa ba wasu ma sun haife ni sun juya,nakan ji nauyi a duk san da sukayi min irin wannan gaisuwar.
Nasmah naɗaga nasaka ta cikin motar, Naseem kam cemin yayi shi da kan sa zai shi, Talatu tayi dariya tana saka musu school bag ɗin cikin mota tace
"Naseem iyayen rigima kai bazaka bari a saka ka ba da kan ka zaka shi ka girma ashe".
kai ya gyaɗa yana gyara zama tare da faɗin
"Eh nagima da kaina naciga."
tace "To babban zance ke kuma Nasmah yaushe zaki girma?". Nasmah ta cuno ɗan karamin bakin ta gaba tace "Gobe dan gima ai".
murmushi nayi tare da shafa gefen suskar ta nace
"Au ke sai gobe zakiyi girman naki?". kai ta gyaɗa tana murmushi, kansu na shafa dukansu nace
"To sai an dawo ayi karatu sosai kunji".
sukace to. direba yaja mota ina ɗaga musu hannu suma suna daga min
mai gadi yawangale get suka fita..

Kwana uku kullum cikin ɗoki suke zuwa makarantar ranar na huɗu kuwa ɗoki tafara kare wa, ina kwance sai ga Nasmah ta shigo da gudu ɗaure da ɗan karamin towel ɗin wankan su tahaye gado ta ɓoye a baya na tana faɗin
"Ni bajan je school in ba."
zanyi magana sai ga Naseem shima da wandon uniform ajikin sa babu riga, sai muryar Talatu daga bakin kofa tana faɗin
"Kai Naseem kazo nakarasa saka maka kayan".
mikewa nayi zaune ina faɗin
"A'a yaya ne tsaya mana". ai kan kace me shima ya ɗale gadon
cikin cuno baki gaba Nasmah ta daɗa laɓewa jikina tana faɗin
"Ni Mommy bajan je School in ba".
ido na waro ina duban Naseem shima da yake faɗin
"Nima bayan jeba".
kai na langwaɓar gefe nace
"Oh yanzu wa School ɗin kuke gudu ne, bazaku je ba kuma, yaushe ne kuka fara zuwan da har zaku fara fashin sa?, kuna ji ko kuzo ku je makaranta".
kafaɗa suka make alamar o'o, rungumo su nayi dukan su ajikina ina murmushi kana nace
"Ina kallon da mukayi jiyan naaan na sojojin naaan, to waye meson zama irin su a cikin ku?".
da sauri Naseem ya mike a jikina yana washe baki tare da nuna kanshi yana faɗin
"Nine-nine". "Yau wa to har in kana son kazama soja to ko sai kaje makaranta, kaje makaranta kayi karatu sosai daga nan zaka zamo soja, in kuma baka so to kazauna kawai a gida ina baka so kazama sojan zauna abin ka kada kaje School".
kai yashiga girgizawa da sauri yace "A'a a'a Mommy ina so to danje School in nine toja".
"Yauwa to kada ka sake cewa bazakaje School ba dan soja baya fashin School, Nasmah ta kefa? baki son zama sojan ne?."
da sauri tace "Ina to." nace "To ke bama soja zaki zama ba Dr Nasmah ce a nan, ina kina so kizamo likita kirika yiwa mutane allura."
ta gyada kanta da sauri, nace "Yauwa kinga in kikaje makaranta kikayi karatu da yawa to zaki rika yiwa mutane allura".
kuma gyaɗa min kai tayi da sauri tun kan in karasa maganar, murmushi nayi ina shafa kansu.
kallon kofa nayi tare da ɗaga murya nace
"Talatu kawo musu uniform ɗin su saka".
daga can bakin kofar in da take tsaye ta waje ta amsa da to kana taturo kofar tare da sallam, nakarɓi uniform ɗin nafara sakawa Naseem rigar sa wan da shi dama ta saka masa wandon shine yagudu,gyara masa zamar rigar nake ina faɗin
"Um kaga soja wannan yaro zai iya rike bindiga in ya girma ya zama soja".
baki yarika washewa yana ɗaɗɗaga kafaɗa da faɗin "Nine toja ai nine toja". "Ai kam ga sojan gasken gaske".
a haka nagama kimsashi
kana nasakawa Nasmah ita ma inata faɗin mata itace Dr zata rika yiwa mutane allura.
nariko hannun su muka fito parlour nan muka iske Zulai da kayan break ɗin su, Talatu kuma ta ɗauko musu School bag ɗin su, muka nufi parking space, da murna suka shige cikin motar Naseem sai faɗi yake
nine toja, Nasmah kuwa ta dube ni tace "Mommy ni meye?". kumatun ta naja nace "Kece Dr me yiwa mutane allura".
sai washe baki suke cike da murna direba yaja motar suka tafi.

Wani sati na gewayo wa muka fara shirin tafiya ziyarar gani da ido nan muka ɗauki hanyar zuwa Lagos,
sai dai wannan karon bantafi da su Nasmah ba saboda School, ni da Bappa da wasu jagorori biyu muka tafi, mun isa Lagos lafiya awani kayataccen hotel akayi mana masauki, mun isa yau washegari muka nufi Company da ake ta kan ginashi tamfatsetsen Company wan da girman sa ya kai ya kawo, an kai ni gurare da dama acikin sa an nunnuna min, masha Allah komai yayi saura kaɗan a kammala.
a gajiye muka koma masaukin mu kansan cewar da kafa akayi ta yawo damu acikin Company'n.
kayan jikina na tuɓe nashiga baya na watsa ruwa kana nafito na sauya kaya na haye gado dan na ɗan huta, waya ta na ɗauka na laluɓo lambar Talatu bugu ɗaya ana biyu ta ɗaga, da sallama bayan mun gaisa nace
"Ina mutanen naki?". tace "Gamu nan muna tare da su a parlour muna kallo, ungo Naseem karɓa ga Mommy tana magana."
tasaka masa wayar a kunne,
"Mommy da mu biki kijo jike da mu".
murmushi nayi jin muryar Naseem nace "To zan zo naje da ku, kuna karato sosai ko?".
kai ya gaɗa, Talatu tace "Ka amsa da baki ai bata ganin ka". yace "Eh." "To a dage sosai, bawa Nasmah wayar." ya mika mata Nasmah tace
"Mommy kina ina, damu biki kije da mu".
nace "Nasmah to zan dawo nazo naje da ku kinji."
"Mommy yaushe zaki jo?."
"Gobe zan dawo naje da ku kinji". to tace, haka sukayi ta zuba min surutu da gwalaɓen su ni ma ina biye misu kun kai minti 30 a haka daga bisani na kashe wayar.
na gyara kwanciya ta dan bacci nake ji.
kwanan mu uku a Lagos muka juya Abuja.

Yau asabar ba makaranta muna tare da ƴaƴana a parlour munata sharholiyar mu cikin farin ciki da jin daɗe, duban daular da nake ciki a rayuwa da nake yin ta yan zu nayi, Allah yabani duniya ya ɗaga ni ya ɗaukaka min daraja ta, a lokacin da duniyar ke kokarin suɓuce min a lokacin da rayuwa ta tazomo tamkar kwai a cikin tray, wan da yazamo baki-baki saura kiris ya suɓuce kasa ya tarwatse.
numfashi na sauke lokacin da tunanin Inna ta ya zomin, wasu zafafan kwalla ne suka zubo min,
Allah sarki Inna ta tabbas na yarda wani hanin ga Allah baiwa ce, ya ɗauke ta a lokacin da nake tsananin bukatar ta arayuwa ta, lokacin da duniya ta juya min baya lokacin da narasa madafar dafawa lokacin da na gwammaci mutuwa ta da rayuwa ta.
ya ɗaukaka darajata abayan bata nan ya azirtani da arziki mai tarin yawa, wa zai iyayin duk wannan in banda *RABBUSSAMAWATI WAL'ARDI*.
Allah sarki Inna ta Allah yakai haske kabarin ki ya sa mutuwa yazame miki hutu.
wasu kwallan nakuma sharewa lokacin da na kuma tunawa da wata uwar wato Mama mai awara, Allah sarki rayuwa
ta cito ni lokacin da duniya tafara wasan kwallo da ni, matar data jajirce wajen ganin an ceto rayuwa ta gun haihuwa, da awancan lokacin bata samo kuɗin da za'a min cs ba wata kila da yanzu na mutu da ni da su duka aciki, tarike ni tamkar ɗiyar da ta haifa a cikin ta. lokacin da tayi nisa wajen ceto rayuwa ta sai ta tsuɓuce min.
sai gashi yau Bappa yamaye gurbin su, yazame min uba kuma uwa,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login