Showing 27001 words to 30000 words out of 45625 words

Chapter 10 - HAMDAH part 3 Complete hausa novel

RASHEEDA   

04 Oct 2024

12663

saka musu wasu daga cikin kayan su da yake bedroom ɗina, sai da na nagabatar da sallar azahar kana na janyo su muka sauka kasa.
dinning area muka zarce bayan munci abinci najasu muka tafi part ɗin su Inna wuro, nan muka tarar da Faty ita ma dawowar ta daga school kenan, nan muka yada zango mukata hira...
da yammacin ranar zaune nake a parlour'n sama na ɗago wayata na laluɓo number shugaban makarantar su Naseem.....!





Mommyn Twins ce







8





Nan nake shai da masa bukata ta nakan canza su Naseem makaranta.
shugaban makarantar nasu yace "To ba bubu da muwa amma dan Allah muna so musan dalilin da yasa ake son sauya musu makarantar ko kuma makarantar tamu babu koyo ne yan da ya kamata?".
nace "Ko kaɗan ba haka bane ba kawai dai ina so ne na canza musu makarantar ba wai kodun rashin koyo ba, ai ba za'a ce makarantar ku babu koyo ba, yara suna fahimta sosai, kawai dai yaɗan yi nisa ne."
yace "To in dai kuwa haka ne to dan Allah kada a ciresu a makarantar gaba ɗaya, akwai ɗaya makarantar mu dake wata unguwa mafi kusa da ku in dai kina so sai a maida su can ɗin, ranar Monday idan suka zo sai ayi transfer ɗin su can ɗin."
shiru na ɗan yi cike da nazarin maganar sa, sai kuma nace
"To shi kenan a mai dasu can ɗin."
har munyi sallama zan kashe wayar yayi saurin cewa
"Dan Allah Madam a daure a kawo su sai a kaisu wancan makarantar, idan akace an cire su gaba ɗaya kokon to zai shiga zukatan iyayen yara zasuyi zaton ko wani matsala ce mai girma aka samu cikin makarantar, tun da bawai barin garin zakuyi ba,
zamu iya samun dakilewar customer, adai duba lamarin da kyau Hajiya."
"Babu damuwa in sha Allah za'a kawo su sai a kai su wan can ɗin."
godiya yashiga yi min kana mukayi sallama na kashe wayar.

Ina sauke wayar number Ukhtee na kira yayi ta ringing ba'a ɗaga ba,nakuma mai da kiran shima har yakusa yanke wa kafin ta ɗaga, da sallama.
na amsa cikin harshen larabci nace
"Oh kai Ukhtee ina kika aje wayar haka ina ta kiranki baki ɗaga ba?, ko yanga kike min an ce miki ni saurayin kine."
dariya tayi tare da faɗin
"Saurayi kuma haba dai kedai wayar tana bedroom ne nikuma ina parlour, nama shigo ɗaukar abune cikin ɗakin naji wayar tana ring, ai da haka zaki ta kira ma ban sani ba, ya kuke ina yarana suke?."
"Lafiya lau duk muna lafiya, yaran ki suna can gurin Bappa sunki biyo ni suna can suna damin sa da surutu, ni nagaji da hirar ne nadawo side ɗina naɗan huta suna can."
larabcin nake ina ta haryaɗa shi.
dariya tayi jin yan da nake ta kwamusa larabcin, tace
"Oh kin dawo kasar ku yaren kasar ku yana so ya korar miki da yaren kasar muko?."
nima dariyar nayi tare da faɗin
"Ashe kin gane inata yi da kyar amma fa su Naseem sunanan da shi a bakin su domin makarantar isilamiyyar su larabci zalla ake, shi yasa yake nan zaune a bakin su."
tace "Kai naji daɗi wlh gara ai su zauna da larabcin a bakin su, ke kizauna da yaren kasar ku tun da shi kika zaɓa."
nace "To ya zanyi mahaifa ta dole naso yare na ke ma ba kina son yaren kiba?."
tace "Sosai ma."
"Oh to shine nima baki so naso nawa yaren."
mukayi dariya. hira kukayi tayi sosai da Ukhtee wani maganar idan nayi ita zata gyara min shi dan larabcin bai gama nuna baki na ba.
sai can da jinawa mukayi sallama.

Yau Monday kamar yan da nasa ba na rako su Nasmah gun mota, Yakubu dake goge motar yayi saurin buɗe motar nasaka su ciki,bayani na yiwa yakubu kamar yan da mukayi da shugaban makarantar su idan sun je za'a haɗa su da wani domin yayi musu jagora zuwa ɗaya makarantar.
ina tsaye ina ɗaga musu hannu har suka fita...

Kai tsaye Yakubu yaɗau hanyar makarantar, kamar koda yaushe hira yake da yaran yanata washewa da dariya kamar yan da suma suke ta washe baki.
suna isa bakin get ɗin makarantar yayi parking yafito, kana ya buɗe musu suka fito, suna fita suka shige cikin makarantar direct office suka nufa daga nan aka haɗa su da wani malami da zai kai su ɗaya makarantar, suka fito tare.
suna fita bakin get ɗin school ɗin,
wata lafiyayyi zazzafar mota tayi parking a gefe, tun kan motar ta kakarasa parking Naseem yafara murna yana faɗin
"Laa ga Daddy yazo laa ga Daddy yazo."
Nasmah ma kuwa ihun murna ta sake tare da sa gudu sukayi gurin motar.
da sauri ya buɗe motar ya fito yaware hannayen sa ai ko da gudu suka shige jikin sa ya rungume su, duk suka saki dariya har dashi, kana ya mike yashiga ɗaga su yana cillasu sama sai kya-kya ta dariya suke.
sai da yayi wa kowannen su haka har sau uku kana yadire su kasa,
Yakubu ya karaso in da suke yana washe baki da faɗin
"Ranka shi daɗi barka da war haka."
amsa wa yayi fuska a sake sai dai gaba ɗaya hankalin sa na kan su Nasnah da suke ta zuba masa surutu.
shima wannan malamin da aka haɗo su da shi ya karaso yana faɗin
"Barka da zuwa yellaɓoi."
yace "Yau wa, yaya ji da ɗaliban?."
malamin yawashe baki tare da faɗin
"Muna kai kam."
yace "Masha Allah."
malamin ne ya dubi yakubu da kuma yaran yace
"To muje ko."
yayi maganar yana duban motar su.
sai a lokacin Ahmad ya ɗago da kallon sa kan yaran yadawo da shi kan su Yakubu kana yace
"Ina kuma za'a je ba makaranta za'a shiga ba?".
yayi maganar yana shafa kan su Naseem.
malamin yace "A'a zamu tafi da sune ɗaya makarantar mu."
duban sa Ahmad ya kuma da alamun tabbayoyi ɗauke a fuskar sa,
kana yace "Wacce makarantar kuma?."
yace "Ɗaya daga cikin makarantar mu ne za'a mai da su."
da fuskantar mamaki Ahmad yace
"Har sun gama wannan makarantar ne da za'a tura su wata makarantar daban?."
kai malamin ya girgiza tare da faɗin
"A'a ai za'a sauya musu makarantar ne anyi musu transfer can ne."
ɗan shiru Ahmad yayi kana yace
"Malam ɗin yana ciki?."
kai malamin ya gyaɗa tare da faɗin
"Eh yana ciki." yace
"Okay to muna zuwa." yafaɗa tare da gyara rukon Naseem da Nasmah a kowani hannun sa guda, ya janyo su suka shige cikin makarantar.

Malamin ya dubi Yakubu dake ta washe baki yace
"Wai nikam da ma ƴaƴan Ahmad Tijjaji Sabil ne kake kawowa makaranta?."
Yakubu ya daɗa washe baki yace "A'a ƴaƴan me *HAM'NAS* Company ne fa."
"Au ƴaƴan mai *HAM'NAS* Company ne to shi Ahmad Sabil dangin su ne? lallai Allah mai yin yan da yaso yahaɗa family guda da tarin dukiya."
Yakubu yace "Eh ƴan uwa ne."
yafaɗi hakan ne kawai dan bashi da amsar bashi, dan shi kansa bai isa yace suna da dangan taka ko basu da shi ba, a matsayin sa na mai ai kin gidan ba lallai dole yasan dan gin gidan ba, san nan kuma baya so ya disga kan sa gaban malamin, ko ba komai shi ma za'a rika yi masa kallon wani...
suna nan tsaye
zuwa can Ahmad yafito shi kaɗai batare da yaran ba.
ido suka zuba masa ganin yafito shi kaɗai, yakaraso in da suke, duban malamin yayi tare da faɗin
"Ka koma kacigaba da koyar da ɗaliban ka, kai kuma ka koma gida ka dawo da wuri ka ɗau ke su."
yakara she maganar da duban Yakubu.
Yakubu yace
"Ranka shi daɗe hajiya tace na tsaya sai mun kai su kafin na komo gida."

Yace "Kar ka damu kaje ka abin ka."
yace To. yashiga mota in da tuni malamin ma yakoma cikin makarantar.
shiko Ahmad a hankali ya isa jikin motar sa ya shige ciki...

Da misalin karfe 12
a hankali na mike na shige bayi wanka nayi haɗe da ɗauro al'wala nafito,nashirya cikin wani doguwar rigar atamfa pauda da man lip kawai na goga sai turare dana fesa a jikina,
a hankali na isa jikin window labulen window'n naɗan janye shi gefe tare da zuge glass.
ido na kurawa furannin da suke ta kaɗa wa gwanin ban shawa,
idanuna na sauke can bakin get jin karar buɗe get ɗin, da murmushi nake kallon kofar,
dan nasan su Naseem ne suka dawo, ɗan gimtse annurin fuska ta nayi ganin ba motar kai su makaranta bane wata motar ne daban ta shigo.
a sannu motar ta isa ta gyara parking a gefen farfajiyar gidan,
an ɗau tsawon minti 10 kafin aka buɗe motar,
ido na waro cikin tsananin mamaki da shiga shoc ganin wan da yafito daga cikin motar, cikin matukar kufula nake kallon sa yayin da yazaga ɗaya gefen ya buɗe, sai ganin Naseem da Nasmah nayi sun fito daga cikin motar suna ta washe ba ki.
"What! me nake gani haka, yaran da nasa a canza musu makaranta domin sa wai bin su yakuma yi?."
cikin matukar ɓacin rai nasaki labulen da sauri na juya nafita a ɗakin na nufi kasa,
da sauri na ke sauka har ina haɗa step cikin hanzari nakarasa sauka nayi waje da sauri.

Suna tsate jikin mota sai zuba masa surutu suke shiko sai binsu da murmushi mai haɗe da dariya yake,
tun kan na karaso in da suke nashiga faɗin
"Kai malam wai meye hakan ne, wai meye gamin ka da yaran nan ne kam?!."
dai-dai lokacin na iso in da suke, kugu na rike cikin masifa nacigaba da faɗin
"Meye da lilin ka na wani shishige musu da kake kana ta wani cusa musu
wani ra'ayi meye nufin ka da su?."
maganar nake a tsai-tsaiye kuma cikin ɗaga murya cikin masifa nakuma faɗin
"Bana bukatar wani ya raɓe su da manufa irin naka kagane ko malam?."
tun da na fara maganar ido kawai ya zuba min batare da yace komai ba, idanun sa kan lip ɗina, a sannu yaɗan yi baya ya jin gina bayan sa jikin mota hannayen sa ya sarkafe a kirjin sa, harshen sa yaɗan zuro waje yalashi pink lip ɗin sa,
har lokacin fuskar sa na ɗauke da murmushi wan da dimple suka daɗa kawata annurin fuskar sa.
cikin kuma ɗaga murya na dubi su Naseem nace
"Idan baku wuce kun shiga ciki ba na rantse sai na ɓaɓɓala yaro anan gurin ku wuce mutafi nace!."
nafaɗa ina nuna musu hanya.
Nasmah tace "Mommy ja mu jo."
ido na waro wato ma na jira su kenan sai sun gama abun da suke.
shiko wani murmuahi yakuma sakewa.
tsayuwar sa ya gyara tare da duban yaran kana ya mai da duban sa kai na sannan yafara magana
"Zaki ɓalla su?."
ya faɗa tare da kuma sakin wani murmushi kana ya ɗan sun kuya yarage tsawon sa dai-dai tsawon yaran ya dubi ko wannen su yace
"Kuje ciki ayi muku wanka kuci abinci ku kwanta ku huta kuyi bacci idan kun tashi kuyi karatu gobe zan tambaye ku karan tun da kukayi kun ji ko?."
kai suka gyaɗa masa suna faɗin
"Tom." yace "Yauwa to maza a je ciki."
Naseem yace "Daddy dakajo anjima?."
kai yagyaɗa yana mai cigaba da wannan murmishi wan da kamar da shi aka gina fuskar sa yace
"Sosai ma zan zo mana."

Cikin hatsala haɗe da ɓacin ran ganin yau ma kamar na ranar da na same su tare da shi a kofar makarantar su, ina nayi musu magana sukayi kamar basu san ni ba,
sai shi da suke ta biye masa suna bashi amsar duk abun da yace musu,
bugu da karin bacin raina kiransa da sunan dana hane su a gabana.
cikin tsawa nace
"Kai Naseem me nace maka waye Daddy'n ka wato bakaji ba ko, ban ce muku kada ku kuma cewa wani Daddy ba, wato duk maganar da nake muku aban za bakwa ji ko, idan naji kasake cewa wani Daddy sai na fasa maka baki,wuce mutafi nace!."
ko da nake masifar harlau idanunsa a kai na, sai ya saki wani murmushin gefen baki yayin da gefen kumatun sa na dama ya lotsa, har kuma lokacin yana rike da kafaɗar su.
a sannu yaɗan sun kuyo yadubi Naseem kana yakuma dubi Nasmah kana yakuma sakin wani murmushin sannan yace
"Naseem Nasmah mene ne ma suna na?."
suka haɗa baki wajen cewa "Daddy Daddy tunan ka."
yace "Kai yaran nan to Allah yayi muku albar ka, to maza ku tafi ciki ayi muku wanka kuci abinci maza kuje."
ya faɗa yana tura keyar su.
ai ko da gudu suka yi ciki suna dariya, ganin rainin wayon nasu da yawa yake wato umurnin sa ma zasubi ba nawa ba. nadube shi tare da rike kugu nace
"Kai malam kana ji ko, kada ka sake zuwa in da yara na suke kada ka sake kasake zuwa in da suke, kada ka sake cusa musu ra'ayin cewa wai kai Daddy'n su ne, kai ba Daddy'n su bane basuma san ka ba, ni ban gayyaci wani acikin lamarin ƴaƴana ba,karabu da harkar yara na idan kuma ba haka ba wlh zan ɗauki tsatstsauran mataki a kanka, kada ka kuskura ka sake zuwa in da yara na suke, kada ka sake yi musu karya kan abun da ba haka bane, bana kara kan haka dan ƴaƴana nice kaɗai uwan su kuma uban su,
dan Allah malam kada ka sake cusawa ƴaƴana wannan gurguwar ra'ayin, ka gane ko?!."
na karashe maganar da nuna masa yatsa haɗe da murguɗa masa baki, na juya a hatsale ganin duk maganar da nake madadin ya shiga taitayin sa sai ma daɗa sakin wannan murmushin nashi yake.
tafiya na soma cikin fushi dan nalashi takwabin yau sai na zane yaran nan tun da har ni zasu gwadan wani yafi ni muhimmanci agurin su har zasu ji maganar sa akan nawa.
sai jin maganar sa nayi daf dani
"Kece uwan su kuma uban su to ya akayi kenan hakan ta faru, ke kika ba kan ki cikin kenan,faɗa min da ma a she mace tana bawa kanta ciki da kanta, dama a she uwa tana bawa kanta ciki ita kaɗai batare da uba ba??."
wani irin juyi nayi jin sautin sa kusa dani batare da zato ko sammani ba, maganar yashige ni tamkar shigar shoc cikin jini na, wani irin mugun kallo na watsa masa tare da jan dogon tsaki, najuya na nufi kofar side ɗina da sauri...
shiko bayana yabi da wannan murmushin kana ya juya yashige motar sa yaja yabar gidan.

Koda na shiga banbi takan su Naseem ba dan nasan koda na yi musu hukuncin danayi niyyar ma bashi zai sa su dai na abun da na hanasun ba,
sai kawai nashige ɗaki nazube bakin gado, kamar an zabure ni kuma na mike na isa gaban mirror in da wayoyi na suke ajiye, number Yakubu na kira, nafara zazzage masa masifa
"Wato Yakubu dana ce kaje ka ɗauko su shine bakaje ba kabar wannan ɗan rainin wayon mutumin wai Ahmad yake ko wa yaje ya ɗau ko su ko?,
idan ka gaji ne kafaɗa sai a sallame ka."
da sauri yatari numfashi na da faɗin
"Dan Allah Hajiya kiyi hakuri wlh yanzu haka ina hanyar dadowa ne ina ma kokarin kiran ki kenan sanar miki sai ga kiran ki, naje makarantar aka ce min yazo ya ɗauke su, ai Hajiya baki sani bama ɗazu da zamu kai su sabon makarantar yazo ya mai da su cikin makarantar yace mutafi mu barsu anan."
ido na waro da ɗinbin mamaki mai haɗe da mugun ɓacin rai,
ban san san da na dakawa Yakubu tsawa ba nace
"Dalla malam ya isa ni da kai na nace ayi abu kan ƴaƴana sannan wani can daban yazo yace ba hakaba kai kuma ka yarda, umurnin sa kabi kenan? ok to ka wuce gidan sa daga nan kaje can yacigaba da baka umurnin!."
nakashe wayar rai ɓace,
"Lallai ma wato ashe ma ba'a kai su makarantar ba shike nan ya hana ko me?."

Afusace na danna number shugaban makarantar yana ɗagawa nace
"Malama ya zan ce ga abun da nake so sannan kuma wani yazo ya hana kuma ku amin ce, to gaskiya daga yau bazama su sake zuwa makarantar ba ma sun fita kenan."
da sauri yace
"Ranki shidaɗe mahaifin su ne yazo yace kada a canza musu makarantar bawai yin kan mu bane."
kashe wayar nayi jin raina yadaɗa ɓaci.
dogon tsaki naja tare da yin kwafa nama kasa cewa komai saboda sabar bakin ciki,sai dai naci alwashin daga yau baza su sake zuwa makarantar ba,
zan mai da su *HAM'NAS* International School Of Science And Technology.


After 1 week

Tsawon sati guda agida suka yishi ranar Lahadi nasa aka kawo musu uniform na *HAM'NAS* International School Of Science And Technology.
washegari Monday da misalin karfe 7 aka gama kimsa su tsaf,
muna tsaye a parking space, daga can na ɗagawa Faty hannu da fito war ta kenan daga side ɗin su, nayi mata alama da tayi sauri, ta Kara so da sauri, tace
"Ina kwana Adda HAMDAH." murmushi nayi tare da faɗin "Lafiya lau antashi lafiya."
"Lafiya lau." tafaɗa tare da
duban su Nasmah tace
"Yau yara sun koma School ɗin mu."
hannun ta Nasmah tarike taɗago kanta tana duban ta tace
"Aunty Faty School inku akwai lilo?."
Faty tace "Eh har da abun zame-zame da mota mai lilo da doki mai lilo."
tsalle Naseem ya tuma yana faɗin
"Yeee nine zan shiga moto in tuka ku."
dariya duk mukayi, na dubi Yakubu dake ta faman goge mota, nace
"Dan Allah kabar goge motar nan haka in ba halitta zaka sake masa ba, kutafi haka kada kasa su makara,kuma dai kaji abin da na faɗa maka wlh aka kuma samin wata matsalar duk wani hakuri da magiyar ka bazai maka amfani ba."
nayi maganar ne cikin jin haushin sa na rannan dan da kyar na hakura da hakurin da yayi ta bani.
da sauri ya bar goge motar yabuɗe marfin motar yana faɗin
"Zo ku shiga Naseem, wlh hajiya in sha Allahu baza a sake samin wata matsala ba, wancan rabar ma tsautsayi ne, dakuma ganin shi babban mutum ne a kasar nan shiyasa ban masa musu ba, dan gudun kada yasa a kwashe ni akai ni gidan maza,
dan musu da babban mutu awannan zamanin haɗari ne."
tsaki naja tare da faɗin
"Kabari zai kai ka karshen ɗauri kenan."
najuya naso ma tafiya ina ɗagawa su Nasmah hannu da cigaba da faɗin
"Kadai ji abun da na faɗa maka."
yace "Kwarai Hajiya, ai daga yau bazaki sake jin wata masala ba."
ban kuma bi ta kan sa ba nawuce part ɗin su Inna Wuro."

A parlour na tadda su Bappa suna breakfast na zauna nima bayan mun gaisa Inna Wuro tazubo min kayan breakfast ta turo min gabana, nan nashiga ci muna ɗan taɓa hira.
Bappa yace
"Mutanen sun tafi makaranta ko?."
nace "Eh sun tafi." Bappa yayi murmushi tare da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login