Showing 18001 words to 21000 words out of 108527 words

Chapter 7 - MIN QALB complete Hausa novel

MAMUGEE   

08 Apr 2025

8458

akai Mata akansu Wanda alhaji mande ne yabada bayajin
Shiyasa tasan tsaf amatun zatayi wannan aikin ba gashi indai akan kudi ne.


Zanje dake gidana zaki gabatarda kanki a matsayin wadda akayiwa fyade harda ciki ajikinki,
Ba shaidu,
Duk wasu manyan shaidu na tanadar Miki su tun daga Kan likitoci harzuwa Abinda zai biyo baya,
Aikinki na kammala na tanadar muku gida da sanaar yi a wani guri can nesa da Nan bazaku sake dawowa Nan ba shikenan kunyi bankwana da talauci da damuwa zaku samu damar Fara sabuwar rayuwa.


Duk iya yanda ta rude da Jin abubuwan dazata samu Bata taba kawo hajiyar batada isashiyar lafiya ba sai yanxu datai wannan maganar Amma Kuma bataga alamar hauka atareda ita ba,
Itadai yanxu matsalar dayace ko haj nada lafiya ko batada bazata mayar Mata da kudin nanba.

Yanda amatun ke kallonta yasa ta fahimci tunaninta ta 'dan qaqalo sakin fuska tace"

'dana ne nice na haifesa
Nasa kimin hakan ne sbd banason abawa 'yayana mulkinda zasu cutu Kuma Allah ya tambayesu ranar qiyama,
Mulkin zabeera akwai hadari,
Za'a iya hallakarmin da 'yaya sbd kwadayin mulki shiyasa nakeson kije amatsayin hakan Dan kada abawa 'yayana mulkin da zarar an nada wanda yakamata a nada zan kaiku inda zakuyi rayuwa cikin farin ciki da walwala.

Shiru amatu tayi tareda gyada Kai sbd soyayyarta da kudi yasa Kai tsaye tayi na'am da hakan Kai tsaye tunda daima ceton Rai ne zatayi koba komai Babu ruwansu da wani abin kunya tunda dai bayi tayiba tasan dai kawu ne bazai yadda da wannan tsarin ba bare iyami.


Kallon kudin tayi ta kalla hajiya aishan tace"

Kinada tsarin fadawa kawuna ya amince???
Dan nidai nariga na amince.

Murmushi umme tasaki tareda tayarda mota suka qarasa shiga layin gidansu amatun tace"

Kawunki bazaisan gskia ba sbd gudun samun matsala agaba,
Kidai saka aranki aikin kudine zakiyi domin samun ingantacciyar rayuwarsu kawai zan aiko a sanar dashi kinsamu aiki a zabeera tareda albashi me kyau zaki ringa zuwa duk sati kina ganinsu har tsawon wata biyar.

Kawu bazai yadda ba"tafada tana tunanin mafita.

Karki damu zai yadda idan wadda zanturo tazo saiki qara da dubarunki ta yadda zai yarda.

Kallonta amatu tayi kafin ta kalli kudin tsawon daqiqu tana nazari zuciyarta na son yin rawa a alamarin Amma burinta na hana hakan.

Rintse idanuwa tayi tareda sauke ajiyar zuciya me qarfi ta furta na amince saitazo nikuma Ina fatan wannan alqawarin yacika.

Gyada Kai kawai hajiya aishan tayi tareda nuna Mata qofa.

Fita tayi tareda kudin tabi motar hajiya aishan da kallo harta bace mata ta sauke ajiyar zuciya tana cewa'

Amatu wannan sa'a ce ko rashin sa'a???

Tana shiga gida Kai tsaye gurinsu kawu taje Allah yasa duk suna dakinsu kawun harda USI dayashigo yanashan magani kawu Kuma na gefe yanashan waqar 'dan indo,ta qaraso ciki tana sallama tareda qarasawa ta zauna gefen iyami dake ballowa usi magani ta ajiye Daurin kudaden tareda sauke boyayyan numfashin zancen dazata qirqiro.

Idon kawu na sauka kan kudin yatashi zaune da sauri daga kishingiden dayake Yana qarar radionsa Dan kada aji Abinda zai fada yace""kudi" Yana sake bude idonsa akansu.

Iyami ma dakatawa tayi daga bude maganin ta kalli amatu da sauri,

USI ma kallon amatun yakeyi zaiyi magana ta rigasu da cewa"

Duk nasan tunani kukeyi dabam dabam
Iyami wlh tallahi ba kudin wasu bane na dauko,
Kawu aiki aka koreni sbd nayi kwanaki banje ba to, to ,to shine dama inawa wata babbar hajiya mama aiki a saloon dinmu shine tace ita zata daukeni aiki zata budemin gurin aiki irin fire fox me sassa dabam dabam wanda nice zanzama managan gurin Amma....

Amma me????iyami ta tambaya da sauri zuciyarta naqin gasgatuwa da zancen..

Amma Wai sai nashiga training dinda zaayiwa manyan ma'aikatansu a can inda aka kebe na tsawon wata biyar zuwa shida.

Tsit sukayi a dakin duka kowa na qoqarin fahimtar zancen saidai ta Yaya??

Kallonta USI yayi dakyau yaga itama shi take kallo yace"

Amah idan har cigabanki ne me kikeso yanxu to.

Kallon kawu da iyami tayi Shima kawun kallonta yake yace"

To wannan kudin fa???

Kai tsaye tace kudin albashinane aka bani na watannin Dan daukar nauyin Kai kafin mu fito training din.

Iyami ta kalla tace"

Wlh iyami aiki zanje Yi ba qarya nakeyiba na rantse Miki...

Duk shiru sukayi kafin kawu yace"

Naji kuje zanyi tunani akai.

Miqewa tayi ta fito usi ya biyo bayanta suna fitowa yafara watso Mata tambayoyi tajasa zuwa dakinta da sauri Dan kar kawu yajisu suka zauna tafara yimasa bayani komai Kai tsaye yace wlh bai amince ba.

Hayaniya suka Fara tayi saurin rufe qofa tana cewa"

Idan baka gaji da yawon cell ba ana maka dukan wulaqanci to ni nagaji da ganin hakan,
Rayuwa me kyau nakeson muyi kamar kowa Usman,
Idan har kanason farin cikina danasu kawu wannan maganar mungamata,
Banyi Dan Jin dadinaba sai Dan wainnan bayin Allan dasuka sadaukar da komai saboda mu,
Babu uqubar dabasu shigaba amma suka riqemu da Amana,
Kaima inason ganin kasamu ingantacciyar rayuwar sbd ka tallafesu a gaba Dan ni nasan rayuwata acikiku taqaitacciyace kobanaso nasan Dole wata Rana kawu saiyamin aure..

Usman mubar maganar Nan kawai qwarin gwiwarka nake nema.

Kallonta yayi idanuwansa na cikowa da hawaye yanajin inama ya mutu ya rage Mata 'dawaimiyar datake ganin itace akai,
Maimakon yazama jagora Amma yazama wani irin koma baya itace jagorar.

Ficewa yayi Yana share hawayen fuskarsa dasuka saka jikinta yayi sanyi matuqa Amma batajin zata fasa sbd tariga takai qarshe zasu bar Nan din sbd karatun Usman din.


Kwana biyu ana rigima sosai a tsakaninsu kafin iyami da Usin suka amince akan aikin nata bayan dattijuwar da aka aiko tayi zuwa kusan hudu tukuna.,

Kwana uku masu zuwa zata tafi Amma duk sai jikinsu su hudun hakanan ya mutu sosai suka shiga damuwar tafiyarta duk da dai Basu fadaba sai hakan yataba 'yan gidan Suma sbd su kawun dadu amah sune hayaniyar gidan dake qara Raya gidan shiyasa Suma duk sai sukaji ba Dadi,

Amatun ma hakanan takejin kamar zata rabu dasu kawun ne rabuwar har abada Wanda usi ne ma tadawo Yana qoqarin cire Mata damuwa,

Iyami da kantace ta hada mata duk wani abin buqata a 'yar Jakarta ta goyawa ranarda akazo tafiya da ita iyami duk hakurinta saidatayi hawayen rabuwa da amatun sbd zuciyarta takasa samun nutsuwa da tafiyar,
Kawuma kasa rakiyarta waje yayi saidai Usman ne aka tafi dashi Dan yaje yaga inda take.

Su maman junior hadda rungumeta sukayi sunajin kewarta tun Bata tafiba.




****
Wayarta data gamayi ta kalla tareda kallon haj Maryam dasuke zaune a palon tace"

Su amah ne gasunan a hanya isowa zasukai mintuna ashirin kafin su iso zuwa lokacin an halarta gurin meeting din familyn ZABEERA daza'ayi yau
Yau komai zai qarewa MD ZABEERA.

Murmushi haj Maryam tasaki tana miqewa tsaye tace"

'yan jaridar Dana gayyatoma suna daga baya suna jiran kirana suzo ya sakarwa duniya wannan labarin da dumi duminsa.

Dariyar farin ciki suka saki atare daidai lokacinda nuratu tashiga cikin kyakkyawar adonta na wata Kuwait jallabiya datayiwa fatarta kyau sai qamshi takeyi tace"

Momy kusan kowa fa ya halarto dan gasu anty bahijja nacan sun iso taredasu anty juwairiyya dasu baba qarami.

MD ZABEERA ma Naga shigowarsa yanxu tareda ZARAH.

Kallon juna sukayi tareda cewa"

Shikenan muje.



***
_40 min later_

A bakin babban qaton gate din ZABEERA motarsu ta Parker Wanda akayi juyensu da ita zuwa wata matacciyar golf baqa.,

Akaro na farko ta 'dago hoton MAHMOUD ZABEERA da aka Bata bayan anmusu bayani wasu abubuwa akansa ta kalli hoton zuciyarta tayi wata irin bugawa akaro na farko...

Rintse ido tayi zuciyarta na wani irin tsalle tayi saurin rufe hoton tana dafe zuciyarta dake bugawa da qarfi tace"

Ya Salam..

Meyasa zuciyarta ke bugawa da ganinsa a hoto???

Kallon Babar dasuka Zo tare tayi tana qoqarin Hana zuciyarta bugawa Amma sai qara bugawa tayi tayi saurin miqa Mata hoton tana cewa'"

Ki riqe a hannunki nariga Naga hotonsa zan ganesa da kaina.

Kallonta baba Jamila tayi tana cewa'"

Ki nutsu fa.

Gyada Kai tayi tana yiwa qatoton gate din zabeeran kallon kwadayi da qauyanci.

Shima usi kalle kallen yakeyi baki abude sbd tsananin girma da kyan gate din kafin suka nufo gate din Babu dogon musu sbd babban security in charge yasan da zuwansu yasa aka Bari suka shigo suna kalle kallen baki asake
Amatu tace"

Usi kana ganin Abinda nake gani kuwa????

Kasa magana yayi yafarabin manyan motacindake harabar gidan da kallo Yana cewa'"

Wlh amatu wannan gidan aljannar duniya ce muka shigo.

Itama motacin tahau shafawa tana cewa'"
Aikuwa sa'a takawoni Nan ni amatu.
##mamuh##


______________
KUNA BUƘATAR A TALLATA MUKU KAYAN SANA'ARKU A PAGES ƊIN BOOKS ƊIN ZAFAFA BIYAR 2021?.

To kuzo ga dama ta samu💃🏻💃🏻.

        Ina ma'abota son a tallata musu hajojinsu a kafafen yanar gizo suke?.

Tofa kuzo dama ta samu, dan jerin gwanon haziƙan marubanku ƴan biyar sun fiddo muku da hanyar da kuma kasuwancinku zai zagaya lungu da saƙo ta dalilin shafukan littatafai.

Ga duk mai buƙatar a saka masa tallan kayan sana'arsa a shafin littatafan mu na zafafa biyar zai iya tuntuɓar waɗan nan Numbers 0903 234 5899 or 09033181070 ta vWhatsApp, idan har agama buks ɗin kana buƙata a sakamaka talla zamu saka maka akan farashi mai sauqi. Idan kuma wasu adadin pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓.

Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗.

______________________

#MIN QALB❤️
Mamuhgee

ZAFAFA BIAYAR

SIRADIN RAYUWA
safiyya huguma

MIN QALB
mamuhgee

YANKAN BAYA
billyn Abdul

KIBIYAR AJALI
Miss xoxo

ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA
hafsat rano

Pay @09033181070
Or 09032345899


[01/06, 8:52 AM] __*MAMUHGEE*__♥️🌹: _*MIN QALB 11*_
_mamuhgee_



Babban palone na alafarma irin tsarin sarautar zamani daya dauke setin royal kushins hudu golden and red sbd girmansa ga kalar dasuka qara qawata palon,
Shine palon da dukkanin familyn ZABEERA ke meeting acikinsa qarshen kowane wata to wannan watan ma hakan ce tafaru dukkanin daukacin zabeeras dake jahar suna cikin palon kusan su sama da arbain kowanne yasamu guri ya zauna ana tsimayin fitowar me kankat wato Modibbo Wanda fitowarsa tayi daidai da tsit da gurin ya dauka sai gaisuwa kawai dake tashi Yana amsawa ta hanyar 'daga Kai batareda ya bude baki ba.

Zama yayi Yana bin kowa da kallon jinjinawa na riqe wannan al'adar dasukayi har idanuwansa suka sauka akan MD ZABEERA wanda ke zaune can bayani iyayensu dukkanin hankalinsa gabaki daya Yana Kan waya dayake karanta email din saqo daya shigosa,

Kallon zamansa Modibbo yayi har zuwa fuskarsa dake daukeda wani irin kwarjini da haiba ya jinjina Kai Yana cewa'

Tabbas Babu wani zabi daya wuce akan mulkin zabeera ayau taron naka ne.

ZARAH kuwa duk da ta shige cikin 'yan uwa da qawayenta 'yan uwanta Amma hankalinta na kansa akai akai take satar kallon gefen dayake sbd ganin yauma dai kamar ko yaushe arayuwarsa ya kebe ne daban duk da yanzu duk Wanda yashigo cikin qanne da tsaransa ma harma da wainda suka girmesa zuwa sukeyi suna gaidashi Wanda Shima yawanci daga Kai ne kawai bai cika bude bakinba Yana amsawa musamman sbd rashin sabo da Yan uwan duk wasu da dama baisansuba.

Khalil ne abokin zamansa akowane meeting tun quruciya Amma yau Khalil din baishigo da wuri ba Abinda baitabayiba ranar meeting wato latti.

Khalil kuwa yanacan ne hanyar gidansu amatu data Hana rayuwarsa da zuciyarsa sukuni,
Tsawon kwanakin Nan bayan haduwarsu da ita bincike yayi me kyau akanta sbd shigo da ita a rayuwarsa Dan sauya musu ingantacciyar rayuwa dakuma tunaninta daya kasa fita ransa da kansa,
Tabbas yasan babban laifine a zabeera neman aure a waje wanda bama ataba yiba asai yanzu dazai Fara shigo da tsarin karya dokar manya sbd bayajin zai iya hkr da maganar amatun a shirye yake daya tallefi yarinyarda zuciyarsa ta riqe a gani na farko Koda hakan na nufin barin zabeera ne barema yasan zai shawo kansu da taimakon MD.

Babban rashin sa'ar dayaci shine bayan isarsa kawu yayi Masa bayanin aiki tasamu ta tafi training Amma dai yabasa numbernta Dana usi din duk da shi Usin Rakata kawai yayi dawowa zaiyi.

Koda ya karba lambar agogo ya duba yaga yayi lattin meeting ga umme Bata gansa ba sai kiransa takeyi
sai bai tsaya Kiran numbrn ba yayi saving tareda dawowa zabeera cikin sauri sbd yasan zuwa yanzu anfara meeting din.

Yana qoqarin shiga gate din zabeera yaga motar 'yan jarida na tsayawa ta gate suna qoqarin gyara cameras dinsu ya Dan tsaya Yana kallonsu cikin mamakin meya kawosu musamman ma da zabeera basa muamala da duk Abinda zai hadasu da 'yan jarida sbd tsira da mutuncinsu da sunans ahalin,
Ganin yayi latti sauri yakeyi yasa bai tsayaba yashigowarsa,
Yanayin parking harabar gidan Kiran nuratu nashigowa wayarsa ya saki siririn tasaki Yana dafe kansa dake Masa ciwo sbd rashin bacci kwana biyun yayi rejecting kiran ko Ina bai tsayaba Kai tsaye ya nufi palonsu na meeting dasuke Kira da zabeera hall.

Yana shiga yaga har anyi nisa yayi saurin yin gefenda ya hango md zaune Ya lumshe fararen idanuwansa ya kwantarda kansa ta baya jikin kujerar dayake Yana sauraron Abinda ake fada cikin nutsuwa.

Qoqarin miqewa alhaji qarami yakeyi zaiyi mgn suka Fara jiyo hayaniya me 'dan qarfi tana tashi daga wajen qofa,
Sharewa sukayi alhaji qaramin yafara bayani Amma sai gaba hayaniyar keyi
Alhaji qarami ya kalli yakub babban 'dan alhaji qaramin yace"

Yakub dubo meke faruwa ne.

Miqewa yayi ya fita Dan dubowar sukuma suka cigaba da meeting din.

Mintuna biyu da fitar yakub sai gashi yadawo da sauri yazo gefen babansa yayi qasa da murya yafada Masa abin dake faruwa da sauri ya kallesa Yana cewa'"

Mene?

Kowa najin haka yayi tsit suna jiran jin abindake faruwa.

Je kashigo dasu""alhaji qarami yace Yana qoqarin cigaba da bayanin dayakeyi.


Sallama sukayi wadda tasa kowa juyawa hadda Shima dazaiyi maganar duk suka kalli qofar wadda ke seti tana kallon center inda Modibbo yake zaune Shima sbd ba'a taba barin wani shigowa ba idan suna taron yasashi dakowa ya kalli qofar.

Baba Jamila ce agaba amatu na bayanta fuskarta rufe da doguwar hijab dinda tasaka fuskarta da idanuwanta a kumbure sosai sunyi jajir tsabar aboniki dasuka Sha kamar wadda tayi wata biyu tana kuka.

Tsit sukayi kowa palon na aika musu da kallon mamaki da jiran bayani Amma sai qif qif baba Jamila keyi da idanuwanta tana sunkuyar da Kai.

Alhaji qarami ne ya kalleta tareda kallon amatun dake bayanta kafin ya kalli qafafunsu har zuwa zamansu ya gyara murya yace"

Malama Yaya dai??
Lafiya??
Daga Ina??

Saurin zubewa qasa tayi tareda sauke kanta qasa cikin rawar murya tanason fashewa da kuka tace"

Ranka ya Dade adalci nazo nemarwa 'yata...,

Kowa kallonta yayi wasu Kam Kai tsaye kallon mahaukaciya suke Mata mamakinsuma yanda akayi tashigo zabeera harta iso Nan din.

Cikin mamaki alhaji qarami ya miqe ya qaraso gurinta ya tsaya Yana cewa'"

Malama adalci kike nema ai banan ake zuwaba,
Mu Nan Kinga Muna wani taro ne me mahimmanci kinyi batan hanyane kije security zasu nuna Miki qofar fita......

Girgiza Kai tayi wannan karon tana fashewa da kuka Mai shiga zuciya tana bubbuga kanta.

Yanxu Kam mamakinsu yafara cirewa sai fargaba
Kamar daga sama taji saukar muryar dattijo me ran qarfe,
Muryar data saka 'yan hanjinta kadawa Dan tsoro da firgita da wani irin amo yace"

Idan da kanki a hayyacinki kikazo Nan kifadi Abinda yakawoki kokuma ki hadu da hukuncin kutse da datse mahimmin Abu acikin zabeera.

Jan hanci tayi tana shage hawayenta dasukaqi tsayawa murya na rawa tace"

Ranka ya dade 'yatace gatanan cikine a jikinta......

Cikin tsawa me qarfi alhaji qarami ya e"

To Nan asibitine ko gidan aurenta dazaki......

Uban cikin Yana Nan"""ta katsesa cikin rawar murya tana sake bulbulo da ruwan hawaye.

Atake gurin yayi tsit kamar ruwa ya cinyesu musamman Modibbo daya gyara zama Yana kallon matar da kyau kafin ya dago ya kalli amatu dake tsaye har lokacin tana matso hawaye cikin hijab.

Kallon amatu yayi cikin wani irin amo yace"

Ke yarinya bude fuskarki kiyi bayaninda mahaifiyarki keson fada saidai duk Abinda zaki fada kifara tunanin a inda kike.

Qarar wayar Dr khalil ce ta katse maganar Modibbo wadda tasa kowa juyowa ya kallesa da sauri ya Danna wayar tareda miqewa ya fita da sauri Yana magana qasa qasa sbd daga asibitinsane ake Kiran wasu takardune da ake buqata emergency yace suzo su karba Nan gida.

Harabar gidan ya nufa gurin motarsa yana tareda budewa ya dauko takardun cikin Burnet din motar ya nufi bakin gate ya fita Dan miqawa Dr ashir.

Sama sama yayi Masa bayanin takardun sbd hankalinsa dake Kan 'yan jaridar da har lokacin suna gurin take yaji yakasa samun nutsuwa da hakan,

Meke Shirin faruwane?
'yan jarida a qofar zabeera,
Ga Kuma wasu baqi aciki suna maganar anyiwa 'yarta ciki.....

Da matsala yafada Yana sallamar Dr ashir ya juya ciki da sauri Yana tunanin Dole da akwai inda matsala take,
Me zaisa wannan matar su gayyato 'yan jarida??anshirya hakan ne Dan idan baa karbi cikin bane kokuma me??
Something is definitely fishy mezaisa tazo da masu jarida ita Bata damu da mutuncin 'yarta bane idan Yan jaridar suka watsa to kodai tanada wani manufa be??? Oh no.." yafada da sauri tareda yin ciki da sauri haryana hadawa da gudu gudu...

Karo yayi da mutum Wanda yasashi yin baya zai Fadi USI yayi saurin rikosa Yana cewa'"

Dr.

Da sauri Dr khalil din ya dago Ya kalli Usin mamakinsa a bayyane Dan komai nasa ya nuna mamakin cikin sauri yace"

Usman?
Kaine anan?
Me kakeyi anan??

Kallonsa Usman yayi Yace"

Aiki amatu tasamu anan......

Saurin gintse bakinsa yayi sbd shaf ya manta Abinda ya kawosun.,

Ya shafo kansa Yana waskewa yace"

Dr kaima me kakeyi anan din???

Kafa Masa Ido Dr khalil yayi ba Wasa a fuskarsa yace"

Wane aiki ne amatu tasamu anan din??
Ina amatun take????

Shiru yayi Yana shafa Kai Yana qoqarin hado qarya Dr khalil ya katsesa da cewa"

Ina amatun?

Rasa yanda zaiyi yayi yace"

Tana ciki tashiga da wata Mata.....

Wattt???
Yafada da qarfi cikin firgici da tashin hankali yace"

Meke faruwa?
Me sukaje yi?
Infact meya kawoku Nan din nakeson ji""zuwa lokacin yafara hasala yace"

Kuma wlh karka kuskura kamin qarya.

Kame kame usi yafara Yana neman yanda zaiyi saidai gskia zai fadawa Dr khalil idan yaso qila shi zai taimakesa ya shawo Masa Kan amatun kar tayi Abinda zatayin
Kallonsa yayi tareda jansa gefe yace"

Dr Dan Allah kayi alqawarin zaka taimaki amatu bazakayi Abinda zai jefata hadariba Dan Allah kayi wannan alqawarin.

Cikin zaquwa Dr khalil din yace"

Koba Dan alqawarinka ba bazan taba Bari amatu tashiga hadariba zan tsaya Mata ako Inane just tell me.

Cikin fargaba Usin yafada Masa yanda amatun tayi da hajiya aisha saidai ya boye Masa da yardar amatun nuna masa yayi kamar tursasata hajiyar tayi sbd amatun ta daukar Mata kudi.

Tsit yayi kamar ruwa ya cinyesa
Har wani duhu duhu idanuwansa ke gani sbd tsananin tsoro da firgicin zancen,
Ita umme ko tunanin hadarinda zata jefa 'yar mutane batayi da kantama tunda komai jimawa dai wataran gaskia zata fito,
Idan ita amatu hankalinta bai Kai ba ita meyasa zatayi hakan??
Qarin tashin hankalinsa MAHMOUD za'ayiwa wannan mummunar 6ata sunan
Haqqinsa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login