Showing 9001 words to 12000 words out of 108527 words
aura Masa ita.
Ganin yanda ta taso din Dan kulawa yasa yadan tsaya tareda kallonta cikin Ido sosai Yana qoqarin Bata mahimmanci yace"
Ina buqatan light abinci Mara nauyi.
Murmushin qara ganin girmansa tasaki sbd yanda akoyaushe yake mutunta zamanta matarsa har kaqoranta suka bayyana ta matsosa sosai tareda kama hannun damansa ahankali ta riqe cikin nata ta dago ta kalli fuskarsa da ya juyo ya kalleta tace'"
Thank you MD ZABEERA.
Kallonta yayi yace"
Ina jira""ya haye saman tana binsa da kallon kauna fuskarta cikeda murmushi kafin tajuya ta nufi hanyar kicin tana cewa'"
Hafsat zo ki niqamun kayan Miya a blender.
**
Umme tunda Takoma palonta ta zauna tana sauke numfashi tanason saukar da zuciyarta ga wannan al'amarinda yake faruwa da ita ako yaushe.,
'yayanta kusan sune koma baya a cikin familyn ZABEERA,
Dukkanin 'yayan Modibbo matane su goma sha shida Khalil da Mahmud ne kawai maza Kuma sune dukkanin wani burin Modibbo ya Dora akansu sai gashi ita nata 'dan shine wani iri Sam ko kyashin 'dan uwansa bayayi duk da Shima Barr ne babba me zaman kansa Kuma yanada nasa arzikin daya Tara bana mahaifinsu ba Amma Sam bai kamo MAHMOUD ba Wanda duniya shi kowa yafi sani a familyn ZABEERA yanzu.
Burinta idan har MAHMOUD yafi Khalil ta wani bangaren to shi zai karbi zabeera na hudu ta yanda zai take MAHMOUD din ta fagen suna,arziki,mulki,dakuma martaba a idanun mutane saigashi Rana tsaka su Modibbo da zabeera sun zaba MAHMOUD Wanda Sam bazata yardaba.
Kamar daga sama taji daga bayanta ance"
Aisha wannan karon damar kice ta qarshe kisa Khalil yayi aure ko su Modibbo zasu sauya shawara su zabesa sbd shi wancan miskilin baya buqatar kujerar zabeera,
Duk wani suna ko arziki ko girmanda ake buqata ya samu abinsa da kansa amatsayinsa na Architecture MD ZABEERA so yanzu zabi ya rage naki na kisan yanda zakiyi.
MD bayada uwa a duniya bayada dangin uwa a duniya to kina tunanin idan yazamo zabeera na hudu waye zai nuna Miki iyakarki idanba zainab uwar matarsa ba wadda ko kadan kinsan Bata qaunarki.
Rintse ido ummen tayi tana jinjina 'dacin da zuciyarta keyi da zafi tace'"
Babu Abinda yakai ciwon hassada zafi a zuciya wlh Maryam,
Tun kafin MAHMOUD yazo duniya bandamu da uwarsa ba harta haifesa ga bar duniya bantaba kulawa dashiba duk da tsananin biyayyar dayakemin Amma tunda yafara zama wani abu a rayuwa Abu yazo ya dameni wannan masifa dame tayi Kama wlh zuciyata takasa samun nutsuwa shawon shekarun cigabansa
Amma wannan karon zanyi Abinda bantaba yiba.
Dawowa gabanta haj Maryam tayi tareda zama kusada kejerar dake kallonta tace'"
Me kenan???
Miqewa tayi tsaye tana takawa ahankali tace'"
A duniya Babu Abinda Modibbo da zabeera suka tsana irin cin Amana da zubarda mutunci,
Zansa su tsanesa tsana mafi Muni wadda zatasa sunansa yafita daga cikin zabeera bama zabeera kawaiba duk duniya ma saisunji yafita ransu sundaina ganin mutuncinsa.
Murmushin mamaki haj Maryam tasaki tana cewa'"
Wane laifi?
Wane cin Amana Kuma???
Laifin ciki
Da laifin zubarda mutunci ta hanyar aikata 6anna.
Wani murmushin haj Maryam tasaki tana cewa'"
To waye yayiwa cikin ni ki fahimtar Dani yanda zangane.
Baiyiwa kowa cikiba Amma kudi zasusa ace yayi cikin.
Aisha kina tunanin akwai Wanda kudi zasusa tace MD yamata ciki karki manta MD mutuminda kowa ke mutuntawane wannan maganar bamai karbuwa bace mu canza shawara.
Maryam kudi duk inda kike tunanin su sun wuce Nan,
Akwai mutane birjik a duniyar Nan dazasuyi aikin komai sbd kudi musamman kudi irin wainda zan zubar akan wannan aikin.
##Mamuh##
#ZAFAFABIYAR##
[01/06, 8:51 AM] __*MAMUHGEE*__♥️🌹: *_MIN QALB 6_*
Wani 'dan murmushin mamaki haj Maryam tasaki tana miqewa tsaye bayan ta ajiye qaramin pillow din kujera data dauka ta Dora a cinyarta bayan zamanta,ta tsaya gaban umme din ta kelleta tanason Bata qarfin gwiwa da Abinda take Shirin yi tace'
Aisha Idan har wannan mafitar kike tunani zata bullar damu ga Abinda mukeso to haqiqa Ina taredake ako wane mataki dazamubi Wanda zai kaimu ga nasa,
Saidai Abu daya anan shine abin dubawar,shi Mahmud din tayaya zai zauna yana kallo ya karbi wannan false accusations din Wanda zaiyi tarnishing image dinsa a idon duniya.
Kallon haj Maryam umme tayi tareda sakin murmushin farko a ranar ta yau tace'"
Mune zamuji Masa ciwo Kuma mune zamu zuba Masa gishiri a ciwon Kuma mune zamu hanasa sosawa,
Abinda kenan wato shine Kinga Maryam narigada nasan weakness din MAHMOUD wato duk duniya rauninsa biyu ne wato mahaifinsa da Khalil,
As long as Modibbo zai zuciya akan wannan alamarin to tabbas MAHMOUD yagama yawo sbd duk wani cigabansa rushewa zaiyi.
To wani hanzari ba gudu ba ta Ina zamu Fara wannan Shirin?
Ma'ana ta Ina zamu Fara neman me wannan aikin? musamman fa Kinga aikine me tsananin hadari sbd 6atawa mutum kamar MAHMOUD suna a duniyarnan babban risk ne ataqaice ma kamar mutuwace kake kirawa rayuwarka sbd kamar yanda yake dinnan a natse zuciyarsa a bushe take,
Duk Wanda zaiyi Mana wannan aikin dole Muna buqatar Wanda zuciyarsa tagama mutuwa akan kudi.
Karuwa,,,,,,
Mene??? umme tafada da 'dan sauri tana kallon haj Maryam din sbd qyamar ma sunanda tafada.
Yes karuwa nace sbd karuwace kawai zata iyayin komai akan kudi,
Ita kadaice zata iya wasa da mutuwa akan kudin sbd sunanta matacciya daga lokacinda wannan alamarin ya lalace.
Dafe goshi umme tayi tana cewa'"
Maryam daina fadar sunan karuwa acikin zabeera sbd fadar sunanta kawai babban laifine a cikin ahalin Nan,
Kawo karuwa acikin zabeera shine laifi mafi Muni dazamuyi Wanda yafi Abinda muke Shirin aikatawa.
Aisha Idan har zamu iya qetare duk wata iyaka mu aikata irin wannan abin to inaga kawo karuwa ba komai bane,
Wannan zancen ma bai kamataba munayinsa acikin zabeera ki shirya gobe muje gyaran qafa zamu tattauna acan kafin Nan kin yanke shawara.
Ficewa tayi tana ayyanawa aranta dole Khalil yazama zabeera na hudu sbd 'yarta nuratu da ita su samu kyakkyawar gaba me kyau.
Umme kuwa kasa zama tayi palon ta wuce dakinta tana dafe kanta dake sarawa sbd damuwar data sawa kanta ga mafita na neman gagararta
Duk abinta bazata iya kawo karuwa ba a zabeera sbd sanin tsananin alada da Matsin dokoki irin nasu Wanda sune asalin zabeera da Abinda yasa suka fita dabam acikin mutane,
Familyn ZABEERA family ne dasukeda wani irin tsatsauran raayi da dokoki Wanda suka zame musu tamkar addini,
Basa auren bare,basa zama da bare,basa barin 'yayansu Mata suyi karatun jamiaa a qasar Nigeria saidai qasashen qetare na laraba sbd karsu barsu anan kowa yagama sanin 'yayansu wainda suke tamkar suna musu kulle ne sbd ko muamala basa barin yayansu suyi da mutane sosai,
Asalinsu Hausa Fulani ne saidai yanayinsu yasa ake musu kallon Fulani sbd yawancinsu farare ne masu 'yar doguwar fuska kalar Fulani,
Sarauta tasa dokokinsu da tsaurin raayinsu yin yawa saidai Kuma babban Abinda yasa suke buka mulki da iko shine Babu wani Dan ahalin daya taba karya doka ko qetareta,
Suna tsananin tsoro da bin umarnin manyansu musamman ZABEERA na daya acikin 'dakinsu asalin dahir zabeeran farko MUHAMMAD USMAN ZABEERA wanda suke Kira da ANDI,
Andi shine mahaifinsu Modibbo mahaifinsu MAHMOUD Wanda yake amatsayin zabeera na biyu Wanda yayi shekaru akai kafin yayi murabus ya sauka yabaro asalin zabeera dake cikin babban birninsu ya barwa qaninsa mulkin Wanda shine amatsayin zabeera na yanxu Kuma shine zabeera na uku Wanda ayanzu ne zaayi na hudu.
Andi shine shugaba mafi tsanani da duk zabeera ake tsoro ake Kuma gudun bacin ransa dagashi dai Modibbo daya kusan zartashi fiyeda komaima na tsananin zafi da dokoki,
Babu wani abu magi qyama agurinsu irin cin Amana da Abinda zai taba martabar ahalin,
Duk babban attajiri tareda manyan Yan siyasa abokanan hurdar familyn ZABEERA ne shiyasa ake matuqar giramamasu da mutuntasu,
Kaf familyn Babu wani sakewa atsakanin iyaye da 'yaya sai bin doka da oda sbd Sam basa Wasa ko sakewa 'yayansu shiyasa 'yayansu ke tsananin shakkar manyansu Dan kaf familyn Babu wani 'da dazaice yataba ganin dariyar manyansu iyaye maza saidai iyayensu Mata,
Modibbo keda Mata uku kowacce tanada Yara hudu Mata Banda mahaifiyar MAHMOUD wadda keda shi shikadai ta Haifa ta rasu tun yanada shekaru bakwai a duniya sai umme datake da Khalil bayan 'yaya Mata hudu,
Umme itace tafi kowacce mace zuba iko da Isa agurin Modibbo sbd zamanta uwargida itace Kuma uwar manyan 'yayansa da duk sunyi aure kusanma wasunsu sunkusa aurarwa Suma.
Umme Bata qaunar 'dan daba nataba saidai Kuma bazata iya cutatar dashiba 'yayanta su kadaine 'yayanta bayansu ba ruwanta da 'dan kowa Koda kuwa zataga masifa ta tunkarosa ne,
MAHMOUD shikadaine yataso a cikin iyalan Modibbo baida mahaifiya,
Yataso ne acikin wani irin kadaici ya rayu acikin kadaicin,
Tun Yana yaro baida Wanda yataba janza ajiki harya girma,
Shi kadai yake komai nasa na rayuwarsa iyakacinsa da mahaifinsa gaisuwa da bin umarnin baitaba jansa ya tambayesa Yaya rayuwarsa take tafiyaba tunda mahaifiyarsa ta rasu bama shi kadaiba kaf duniya baida Wanda yataba jansa ajiki yaji ya yake ba,
Baida kowa aganinsa,
Baitaba shiga cikin 'yan uwansa ba sbd basayi dashi,
Shi kadai yake kwana,
Shi kadai take tashi,
Ahaka yayi rayuwa ahaka harya girma,
Da kansa ya koyi faduwa da yanda zai tashi kansa,
Da kansa yasan yayiwa kansa fada ya tsaya ya nemi ilimi dan yin rayuwa dashi,
KHALIL shikadaine 'dan uwansa dayake dashi Wanda yake tsananin qaunarsa duk da yanda umme ke hanasa muamala dashi saidai Sam qaunarsa Khalil ke Masa Babu Mai iya kwabarsa akan shifa alamuransa,
Khalil na tsananin kaunarsa fiyeda wainda suke daki 'daya Wanda kowa yasan da hakan shiyasa tare sukai karatunsu tun primary har secondary saidai kasancewar Khalil din ba lafiyayye bane asthmatic ne Kuma irin chronic din Nan shiyasa daga secondary suka rabe MAHMOUD Modibbo ya turasa Sudan karatu shikuma umme taqi yarda yaje koina.
A Sudan yaqara samun cikakkiyar rayuwar kadaici Wanda ta hade da rayuwar kadaicin daya baro sai hakan yazame Masa wata sababbiyar dabia wadda yazama rayuwarsa,
Baya fira sbd baida abokan fira,
Yayi gwagwarmayar karatun degree a Sudan na tsawon shekaru shikadai batareda yazo gida ba kokuma wani daga gidan yazo gurinsa,
Babu wani Wanda yataba kiransa yajisa tsawon shekarun bayan khalil sai Modibbo Wanda shine yake kiransa badai shi yakirasaba,
Baitaba damuwa da kadaicin rayuwarsaba da baida kowa sbd ahaka yataso
Hakan shiya kashe duk wani walwala ko muamalarsa da mutane sai kadaici yafi Masa Dadi da nutsuwa fiyeda komai,
Bayasan hayaniya ko shiga jamaa sosai sbd yafi samun nutsuwa a inda kadaici yake.,
Ahaka rayuwarsa ta nitsa inda yasamu nasarori bayan cikakkiyar gwagwarmayar rayuwa dayayi a cikin neman ilimi me zurfi,
Gwagwarmayarsa tazo da nasarori da dama wanda yasa yayi fice cikin manyan mutane da qusoshin qasa,
Zamtowarsa wani qusan Shima sai sunansa yaqarawa zabeera family suna da martaba sosai,
Ya mallaki abubuwan arziki da dama wanda kaf zabeera yanzu Babu abokin karawarsa idan ba Modibbo ko Andi ba wainda sukafi kowa dukiya,
Nasararsa tasa yanzu kusan kowa dangi binsa yakeyi saidai kasancewar bai Saba da a jasa ajikiba yasa baya sakewa da kowa ataqaicema baya iya rayuwa cikin mutane yafison zamansa a Sudan inda acan nasarorinsa suka Fara acan yafi samun nutsuwa idan ya kadaice abinsa
Yana daukar lokaci baidawoba Dan yanafin shekara wani lokacin kafin yazo Wanda duk zuwansa sbd Khalil ne kawai yake zuwa sai Modibbo Wanda yake matuqar giramamawa fiyeda komai arayuwarsa,
Ta bangaren 'yan uwansa kuwa sosai yake sake musu kudi duk da Babu wani sabo ko sakewa a tsakani Amma yakan Basu duk wani abu musamman umme dayake ganin qimarta sbd Khalil batareda yaduba yanda yataso ba sbd idan yace yaduba yanda yataso to zaitsani kowa arayuwarsa.
Ganin kamar MAHMOUD din yayi musu nisa sosai Wanda yanzu suke alfahari dashi amatsayin Dan zabeera sbd mutunci da girma tareda qimarda yake sake kawowa zuriar sai suka yanke shawarar nemar Masa auren 'yar qanin Modibbon Wanda yake kan kujerar zabeera ayanxu ZARAH,
Zarah ta auri MD ZABEERA cikeda alfahari da auren sbd samun miji yanxu kamarsa dibbin nasara ce arayuwa,
Tana tsananin qaunarsa saidai sanin yafi karfinta yasa ko a mafarki Bata tunanin aurensa saigashi Allah yayi shidin mijintane Wanda taqara haukacewa a tsananin qaunarsa,
Baya musu arayuwarsa sbd baisaba doguwar mgn ba ko ta fannin business dinsa ko deals dinsa Abune nayi ko bari bayasan dogon Bata lokaci shiyasa baibi wani dogon sawa Kai ciwon kaiba ya amince musamman da akayi saa zarah mace ce me tsananin nutsuwa da hkr ga biyayya da fahimtar Abu Sam Bata cusa kanta gurinsa tunda akayi auren
Rayuwa suke ta mutunta juna da kiyaye gudun shiga haqqi.,
Shi mutum ne marason damuwa da hayaniyar mutane akusa dashi shiyasa idan har yananan ko volume din tv bata sawa sosai sbd karta damesa,
Bata taba yin wani abu Dan damuwarsa ko sakasa ciwon Kai ba shiyasa yake respecting nutsuwarta musamman dayake dama baya shaawar mace arayuwarsa saidai sbd girman Modibbo da Andi dakuma qimarta yasa yake qoqarin bawa auren nasa haqqin.
***
Yau amatu Bata fita aikiba Saida tagama hutawarta a gida kafin tayi Shirin aikin ta fito tareda usi Dan dama kullum tare suke zuwa aikin
Suna Isa tun a harabar gurin suka fahimci da masu kudi a gurin saidai rashin saar dasukayi gefen VIP saloon dinsu sukaga motocin Wanda sunsan Babu rabonsu yau acikin aljihun masu wainnan motacin masu kama da tarwadar ruwa sbd sheqi.
Direct gefen restaurant suka nufa usi na cewa"
Juyawa zanyi amah zanje gurin insfector Garba naji uban me zaimin dayake nema na tun Daren jiya.
Tana shigewa tace' idanma ni yakeson katayasa lallashi kafada Masa duk yabari nayi Ido biyu dashi Aina sace Masa shegen cikinsa me kama da tayar motar Mai.
Juyawa yayi Yana cewa' nizan Fara nuna Masa kalar rashin mutuncina kawuma nacan Yana jiran ganinsa.
#mamuh#
______________________
KUNA BUƘATAR A TALLATA MUKU KAYAN SANA'ARKU A PAGES ƊIN BOOKS ƊIN ZAFAFA BIYAR 2021?.
To kuzo ga dama ta samu💃🏻💃🏻.
Ina ma'abota son a tallata musu hajojinsu a kafafen yanar gizo suke?.
Tofa kuzo dama ta samu, dan jerin gwanon haziƙan marubanku ƴan biyar sun fiddo muku da hanyar da kuma kasuwancinku zai zagaya lungu da saƙo ta dalilin shafukan littatafai.
Ga duk mai buƙatar a saka masa tallan kayan sana'arsa a shafin littatafan mu na zafafa biyar zai iya tuntuɓar waɗan nan Numbers 0903 234 5899 or 09033181070 ta vWhatsApp, idan har agama buks ɗin kana buƙata a sakamaka talla zamu saka maka akan farashi mai sauƙi. Idan kuma wasu adadin pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓.
Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗.
______________________
#MIN QALB❤️
Mamuhgee
ZAFAFA BIAYAR
SIRADIN RAYUWA
safiyya huguma
MIN QALB
mamuhgee
YANKAN BAYA
billyn Abdul
KIBIYAR AJALI
Miss xoxo
ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA
hafsat rano
Pay @09033181070
Or 09032345899
[01/06, 8:51 AM] __*MAMUHGEE*__♥️🌹: *_MIN QALB 7_*
_mamuhgee_
Kai tsaye change room dinsu ta nufa ta sauya kayanta zuwa na aiki ta fito tana gyara zaman qaramin Rolling dinta a wuya tana Dan yamutsa fuska tace,
Ni wannan aikinma harya Fara isata sbd wannan kayan aikin kullum mutum atakure bazan iyaba aje aikin zanyi na huta kafin daga baya zanda usi yasamomin wani yanzu dai kafin na ajiye zansamu kudinda zasu riqemu kafin asamo wani.
Tana isa reception dinsu manager dinsu na isowa
Shigowarsa kenan Yana waya yayi Mata hannu cewar ta tsaya yagama wayar
Wani harara tabisa dashi tana dauke Kai sbd manager dinnan nasu tafara gano take takensa akanta bazai shiga hankalinsaba sai ranar data sanfe duk wani arzikin dake aljihonsa,
'daga Masa qafa takeyi sbd kudaden datake sanfewa na restaurant Dan kullum saita diba son ranta take tafiya gida Bari tayi yaringa ji da 'daya Amma yakasa Kama kansa,
Kullum sai ayi rikici gun lissafin yanda kudi ke ba'ta Amma ankasa ganewa har so biyu ana sauya cashiers din aje kudin Amma 'yanda kasan 6era ne me satar ko clue bata bari bare amayi zargin mutum ne me satar.
Kallon qeyar kansa tayi tana sakin murmushin qeta tace"
Manager tashi aiki zakayi kwanan Nan...
Maganarsa ta kwasheta ta 'dago tana kallonsa tana 6oye murmushin gayyar datakeyi tace"
Barka da zuwa manager,
Kazo lafiya?
Washe haqora yayi Yana gyara zaman medical glass dinsa cikin son nuna shi wani ne yace"
Yawwa lfy klau amah
Dama sbd matsalolin damuke fuskanta na 6acewar kudi a bangaren restaurant namu yasa na yanke shawarar maidaki gefen saloon sbd zamu dauki mummanan mataki akan maakatan restaurant din banason asaki acikin Abinda baima shafekiba,
Dukkaninsu maganinsu zamuyi saisun fitar Mana da 6arawon cikinsu.
Kallon Wawa taqare Masa kafin tayi fuskar marayu taredayin qasa da Kai cikin nuna maraicinta tace"
Nagode da hakan Dan ni ko yanda alamarin kudi dake gudana agurin banma saniba,
Banmasan meke faruwa a gunba da azo adauki alhakina abatamin suna kawuna ransa ya baci ciwonsama na hawan jini zai iya tashi idan yaji hadda ni acikin wainda zaa tuhuma da sata Kai Allah dai ya tsareni ya rabamu kalmar sunan satama batada Dadi.
Sake washe baki yayi ganin kamar yayi Abinda ya burgeta taji Dadi ya sake gyara tsayuwa Yana katse Kiran dake shigowa wayarsa yace"
Ai dama shiyasa naga yakamata a sauyaki saga gun sbd kada sunanki ya baci gashima Kinga Ashe kawunmu zai iya samun damuwa.
Tana qaqalo murmushi tace'
Eh dama gashi Muna fama dashi yau ciwo gobe lafiya ko tashi zaune baya iyayi" yaqarasa fada tana soke kanta kasa.
Subhanallah Ashe dai alamarin sosai ne to Allah ya sawwaqa inshallah yau ko gobe idan nabar office zanje nadubasa.
Zakasan me ake nufi da asalin sunan sata idan kaje duba kawo ka laluba kaji usi ya sanfeka tass""tafada qasa qasa tana Masa kallon sakarai....
Me kikace????
Eh cewa nayi akaini inda aka sauyamin din manager.
Yawwa muje'' yafada yanayin gaba tana binsa abaya tana sake 6ata fuska sbd Sam ita Bata wani son wani canje canje ita dake Shirin barin aikin ake Mata wani yaje Jaye Amma dai bangaren saloon din idan taga yamata zata zata Dan jima Amma yanzu babbar damuwar shine kafin ta 'dan gama gane Nan bangaren harta Fara samun damar sanfesu za'a dauki lokaci qila gashi komai nasu yayi qasa na abinci iyami kasuwancinta na Saida garin 'dan wake baya tafiya da albashinta suka dogara yanzu sai Abinda tasamo ko usi yasamo.....
Katsewa tunaninta yayi daidai lokacinda suka iso bakin qofar saloon din dake cikin blue fox din sbd wasu manyan hamshaqan Mata data hango ta cikin glass,
Sake 'daga wuyanta tayi tana 'dan leqawa tasake hango wasu 'yan Mata daga dayan gefen take tasaki ranta tana cewa"
Yauma ranar sa'atace kenan
Nakusa zamowa shiyasa Allah yasa aka daukeni daga Inda mutane basa ajiye jakarsu Amma anan dole mutum ya ajiye jakarsa tunda aiki zaa Masa,
Numfashi ta aje tana cewa"
Inshallah usi nakusa samun kudin karatunka Dan Banda buri yanzu dayafi kayi karatu sbd Kaine namiji qarfinmu zaifi qarewa akan naka kawuma ga manyanci na rufarmasa.
Tana cikin tunanin taji muryar manager na cewa"
Shikenan amah kuje ga shugabarku Nan zata baki Abinda zaki ringa yi
Sai akula please amah.
Gyada Masa Kai kawai tayi sbd tuni