Showing 57001 words to 60000 words out of 108527 words
Masa cikin mamaki yace"
Ya akayi yayi saurin ganowa Bayan kabada tabbacin aqalla har maganar taje court bazai gano inda takeba.??
Yanzu dai Bari na sanarda Andi saina kiraka kafin ka gansu.
Aje wayar yayi ya kalli Modibbo kafin ya kalli Andi cikin nutsuwa da girmamawa yace"
Andi khalilu ne yasamu gano inda take Yana bakin office din commissioner ma yanzu haka.
Dagowa yayi ya kalli alhaji qarami din da mamaki a fuskarsa kafin ya kalli Modibbo cikin bayyanarda mamakinsa yace"
Me Khalilu yakeson komawa ne akan mace????
Shiru Modibbo yayi Yana sauke Kai cikin takaici da mamakin Khalil din.
Sake bayyanarda mamaki da takaici Andi yayi Yana cewa''
Tabbas khalilu Yana buqatar hukuncindazai dawo dashi hankalinsa tunda yazabi wulaqanta hukuncina akan mace..
Dan gyara zama Modibbo yayi tareda gyaran murya cikin girmamawa yace"
Allah ya huci ranka Andi Amma sai Inaga tunda yariga yayi nisa duk wani hukunci sake tsaurara abin zaiyi tunda Babu wani a zabeera daya taba take hukuncin Manya sai akansa gashi yanzu kowa yafara ankarewa da hakan da azo ayi Abinda zaisa agano bijiewa yayi yayi watsi da hukuncinka asamu masu Goya Masa baya abun yayi yawa.
Shiru Andi yayi Yana sauraronsa cikin qoqarin son fahimtar zancensa
Ya dago ya kalli alhaji qarami dakeson Magana shima yace"
Kaikuma meye naka hasashen?
Gyara zama yayi Yana tausasa murya yace"
Inaga akashe maganar a idon duniya ma'ana a janye qarar amatsayin munduba maraicinta mun qyaleta idan yaso sai commissioner su saka kudin belin da Khalil din bazai iya biyaba idan yayi yayi Dole zai hkr kokuma ace za'a biya kudin belin Amma saiyayi alqawarin rabuwa da yarinyar
Hakan shine mafita a yanayin da ake yanzu sbd Khalil idan baa janye qararba zai iya dagewa qarshe ya aikata Abinda zai saka zabeera kunya.
Jinjina Kai Andi yayi Yana na'am da bayanin alhaji qaramin yace"
A aikata hakan Amma kafin Nan ayau nakeson Modibbo dukkanin Abinda Khalil ya mallaka na zabeera a karbe.
Kallonsa Modibbo yayi da sauri saikuma ya sauke Kai Yana jinjina hukuncin sbd kaf 'yayansa bama shikadaiba kusan duk yayan zabeera da arzikin Zabeera suke tinqaho MAHMOUD ZABEERA ne kawai Babu qwandalar zabeera acikin dukiyarsa da guminsa da wahalarsa yatara arzikinsa,
Idan akace akwace komai na Khalil to motarsa ta hawa da kudaden account dinsane kawai zai tsira dasu Dan kuwa ko asibitinsa dayake tinqaho da ita MAHMOUD ne ya Gina Masa ita amatsayin tayasa murnar zama cikakken likita.
Koda commissioner yabasu izinin shiga bai nuna musu komaiba suka gaisa kafin Khalil yafara Masa bayanin Abinda yakawosu Babu dogo musu yacewa Khalil din an janye qara belinta kawai zasuyi akan kudi naira miliyan daya sai kudin tarar bacin suna miliyan daya da rabi duba da yanayin gidan da akayiwa bacin sunan.
What?????"""Khalil yafada cikin tsananin mamaki da yiwa commissioner din kallon rashin hankali yace"
Beli ne wannan kokuwa hukuncin Rai da Raine wannan???
Murmushi commissioner yayi Yana gyara zama yace"
Dr khalil zabeera zaka iya Kiran lawyer dinka zamu basa komai a rubuce sbd samun qarin fahimta.
Kallon bakinsa kawu keyi cikin yanayin tsoron dayafi mamakinsa miliyan biyu kudin beli?gwarama su fito su fada musu bada itane bazasuyiba.
Koda lawyer din Dr khalil ya iso aka miqa Masa takardun belin da aka bugo cikin qanqanin lokaci ya karanta yasake karantawa zuciyarsa na tafasa ko ba'a fada yasan shirine akayi Dan quntata Masa shida su Amatun,
Koma menene akayi Dan a cimma bazai taba rabuwa da Amatu ba,
Idan anyi ne Dan aga gazawarsa tabbas bazai taba gazawaba zaiyi komai iya iyawarsa zaikuma qwatar Mata mutuncinta da yancinta.
Dagowa yayi ya kalli kawu da idanuwansa sukai jajir sbd tashin hankali saiyaji zuciyarsa ta sake karyewa ya waiwayo ya kalli commissioner cikin yanayin na nuna rashin gazawa yace"
Ahada takardun belin su zama ready zuwa gobe zankawo kudin.
Kallonsa sukayi da sauri duk su duka commissioner na boye mamakinsa akan Khalil din yace"
Shikenan Dr khalil zabeera muna jiranka goben.
Miqewa yayi ya fice kawu da Barr Bashir na bayansa kowannensu cikin damuwa Yana Isa bakin mota ya tsaya ya juyo ya kalli Barr Bashir da idanuwansa dasukai jajir yabude busashen bakinsa yace"
Barr zankiraka gobe muhadu anan abasu kudin inshallah.
Kallonsa Barr yayi cikin kulawa da jimami Yana cewa''
Dr khalil kana ganin zamu karbi belin Nan ahaka?
Inaga muje can zabeera aroqi maganar tarar ajanye Mana ita zaifi....
Girgiza Kai yayi Yana qoqarin boye rauninsa yace"
Ba buqatar hakan zanhada kudin zuwa goben Inshallah.
Shikenan tunda zaka iya biya ba damuwa Allah yakaimu goben.
Suna Shiga mota yayi shiru cikin tsananin damuwa da tashin hankalin ta inda zai Fara hada kudin sbd dukkanin kudin account dinsa ya rabesu gurin case dinnan cikin kwanaki kadan
Duka duka abindake account dinsa baifi dubu dari bakwaiba Kuma gidan haya yayi niyar kamawa dasu ya ajiye Amatun.
Bayan kudin account dinsa da motarsa baida wata babbar kadara sai tsadaddun agogunansa da wayoyinsa,
Asibitin dayake tinqaho da ita bata cikin lissafi sbd tamkar alamar qaunarssuce me qarfi dake tsakaninsa da 'dan uwansa.
Kallonsa kawu yayi cikin tsananin damuwa da sarewa yace"
Khalilu kada ka takura kanka da hada wainnan kudaden daba haduwa zasuyiba,
Qaddarace wannan me girma ta samemu wadda Allah zai fitar damu inshallah.,
Zamuje muyita addua Allah yabamu ikon cinye jarabawa sbd koba komai munqara bambamce halaye irin na wasu masu arzikin Wanda bayan suna Babu Abinda suka damu dashi,
Farin cikin yayansu da walwalarsu bai damesuba kamar yanda sunansu da girman kansu ya damesu.
Ahankali yaja motar suka bar gurin suka kamo hanyar gida har lokacin bai iya cewa ko qala ba sbd nisa da yayi a tunani.
Koda suka Isa ajiye kawu yayi ya wuce zuwa zabeera.
Parking yayi daidai sashen Modibbo yafito ya nufi ciki jikinsa da zuciyarsa amatuqar sanyaye.
Sallama yayi palon yashiga cikin sa'a Modibbon na zaune shikadai Yana kallon labarai Koda yaga khalil din Saida yaji tausayinsa Amma bai nunaba sbd ya dauke Kai Yana cigaba da kallon labaransa.
Gabansa ya zube tareda sunkuyar dakai wasu irin hawaye masu zafi suka gangaro daga cikin idanuwansa akaro na farko daya nuna gazawa cikin wani irin sauti Mai tsananin sanyi yace"
Modibbo Ina roqon yafiyarku akan dukkanin Abinda yafaru Dan Allah ku sassautawa Amatu wlh batada laifi akan hakan kuskure ne da rashin sanin ciwon Kai wlh batayi Dan wata manufar Bata suna ko wani Abu ba dabam tayine kawai sbd kudi Wanda tsananin rayuwa yakaita ga hakan.,
Modibbo Dan Allah Ina roqon gafara da yafiyarku Dan Allah ku duba maraicinta kada ku tsaurara Mata.
Juyowa Modibbo yayi ya kallesa sosai ganin yanda babban namiji jajirtacce kamarsa ke kuka ya sauke ajiyar zuciya Yana cewa"
Khalilu zancenka ba'a hannuna yakeba Amma amtsayina na mahaifinka zanfada maka Abu daya,
Kada kayi Abinda zai kawo maka matsalarda bazaka iya tsayawa kaga wucewartaba,
Idan kanason yarinyar Nan tsakani da Allah Dan tallafawa maraicinta to tabbas na amince maka ka aureta sbd aurenta ne kawai zaisa Andi ya iya sassautowa tunda tariga tazama Zabeera Amma idan kasan tsakani da Allah yarinyar Nan batada nasaba to Ina baka shawara kayi gaggawar cireta daga rayuwarka shine kawai sauqi da mafita agareka..
Da jajayen idanuwansa ya dago ya kalli Modibbon Yana nazartar zancensa wani irin sanyin sassauci na shiga zuciyarsa sbd ya fahimci zancen mahaifin nasa take sabon qwarin gwiwa yasake shigarsa ya sunkuyar dakai cikin sanyi yace"
Nagode Modibbo Allah yaqara tsawon Rai.
Yana fitowa sashen ummensa ya nufa inda ya tararda ita zaune tayi tagumi kamar koyaushe cikin kwanakin tana ganinsa tayi saurin miqewa ya hanata ta hanyar mayarda ita zaune yana girgiza Mata Kai murya a mace yace"
Umme zanbar zabeera......
A firgice ta kallesa idonta na cikowa da hawaye zata fashe da kuka yace"
No umme karki manta kinmin alqawarin bazakiyi kukaba Kuma kinyi alqawarin bani support adukkanin Abinda Zan yanke.,
Umme albarkanki nake nema a rayuwar dazanyi wajen zabeera dan Allah umme kimin alqawarin bazaki saka kanki cikin damuwar dazata cutatar dakeba.
Kasa riqe kukanta tayi ta fashe dashi tana cewa''
Khalil Dan Allah kada kabar zabeera kabarni katafi Dani Nima
Wlh bazan iya zama baka nanba,
Katafi Dani duk inda zakaje zanzauna acikinku,
Zan zauna taredaku zanyi renon 'yayan dazaku haifa........
Kasa hkr yayi ya rungumeta Yana girgiza Mata Kai Yana cewa''
Umme Zaki zauna anan gidan aurenki sai mutuwace kawai zata fiddaki zabeera.
Aa khalil zanbika Dan Allah kada ka tafi kabarni.
Ganin yanda ta daga hankalinta yasashi zamewa da sauri ya fice Yana danne zuciyarsa dake neman fashewa yayi hanyar sashensa.
Kayansa ya diba a akwati tareda kwashe agogunansa da takalmansa masu tsada sosai da duk abubuwan dazai buqata ya saka cikin mota tareda dukkanin takardunsa yafito yaja motarsa yabar zabeera.
Daga zabeera gidan Ibrahim yaje yafara ajiye kayansa acikin dakin farkon Shiga ya rufe dakin da mukulli ya fito yarufe gidan ya wuce.
Tareda Ibrahim din sukaje gurin masu Saida agogo akayiwa agogunansa kudi kaf aka shiye suka hada kusan dubu dari uku daganan gurin Wanda zai siye motarsa suka nufa aka Fara cinikin saidai abin son Rai yayiwa mutane yawa Dan siyan wulaqanci sukaiwa motar har kusan mutum shida sukaiwa motar siyan wulaqanci qarshe Dole ya saidata miliyan daya da dubu dari suka karba ya hada hadda kudin account dinsa suka tashi 2.6.
Mashin yahau Abinda baitaba hawaba a rayuwarsa ya nufi gidansu kawu anan yafadawa kawu ya hada kudin daga iyami har kawu basusan lokacinda suka fashe da kuka ba.
Murmushi me ciwo kawai yasaki batareda yace komaiba anan yayi sallar ishai iyami tasashin tuwon Dole kafin yatashi yatafi.
Mashin yasake hawa yakoma gidan Ibrahim Yana Shiga Allah ya taimakesa ana kawo nepa Nan ya tube yayi wanka da ruwan rijiyar gidan da Ibrahim yacika Masa durum da kansa masu shegen tsananin sanyi Wanda Saida suka saka numfashinsa kusan daukewa daya watsasu.
Boxer da singlet kawai yasaka yadawo ya kwanta Kan sabuwar katifar da Ibrahim din yasiyo yau yakawo Masa.
Kiran salman ne keta shigowa wayarsa Yana qin dagawa sbd duk kwanakin ya tashe duk banyarda salaman zaishigo cikin Al'amarin sbd bazaiso laifin ko wani Abu yasamesaba kodan yanda Amatu ta daukesa kamar usinta.
Kiran MD ZABEERA ne yashigo wayar ya qurawa wayar Ido tsawon sakanni kafin ya dauka Yana boye damuwarsa Nan suka hau Maganar shi cikin sanyi MAHMOUD Kuma cikin nutsuwa da miskilanci.
Koda asuba tayi daqyar ya iya dafawa ya tashi zaune sbd tsananin sanyin daya Gama shigewa ya Kama dukkanin qasusuwansa.
Daqyar yayi sallah ya jingina da bango Yana makure jikinsa guri daya sbd kaf gidan gaba daya koina sanyi yake fitarwa sbd gaf suke kusada ruwa.
Daqyar yaga qarfe Tara na safe tayi ya miqe yasake zuwa bayi ya watso ruwan sanyin yafito jikinsa na Dan rawa yashigo daki ya shirya cikin qananan kaya masu Dan kauri ya bar gidan sbd Jin kamar zai iya suma da ciwonsa dake gaf da tashi.
A gidansu kawu yaci biredi da kunun tsamiya tareda waina da iyami tasiyo Masa me kyau ta shinkafa.
Kobai fadaba sungama gano halinda yake ciki sbd kada su qara Masa damuwa sukaqi yimasa maganar sai tattalinsa dasukeyi.
Qarfe goma da rabi a central tayi musu shida kawu suka zauna zaman jira har qarfe goma sha biyu commissioner bai buqaci ganinsuba sai daya da rabi Bayan anyi sallah anfito tukuna aka kirasu suka Shiga.
Barr Bashir ne yacire kudin beli da Tara ya bayar akayi rubuce rubucen daza'ayi aka gama kafin akace afiddo Amatun.
Lokacinda aka kawota suna ganinta kowannensu idanuwansa suka ciko da hawayen baqin cikin ganin halinda take ciki Amma ita ganinsu yasata qaqalo qarfin hali tana danne azabar cizon sauri da galabaituwar yunwa da dau'dar datake ciki Danma tunda tazo koda Wasa ba'a taba dukantaba Wanda umarnin Andi ne kada a daketa ko so daya.
Babu Wanda ya iya mgn acikinsu aka Bata gyalanta da takalmanta suka fito tana tafiya daqyar a galabaice.
Suna fitowa titi taga suna qoqarin taron adaidaita ta kalli Dr khalil din da mamaki Kan fuskarta saidai batayi maganaba suka tare adaidaita biyu ita dashi suka shiga daya kawu yashiga daya.
Ahankali ya juyo ya kalleta cikin tsananin kulawa da damuwa akan fuskarsa yace"
Are you ok?
Kallonsa takeyi tana mamakin sauyawar dayayi
Yayi duhu tayi Rama hakama kamar Wanda baida lafiya sai Nishi Nishi yakeyi kamar Wanda yayi aikin wahala.
Kai ta daga Masa ahankali tana lumshe ido a wahalce.
Koda suka iso gida tuni mutanen gidan suka rude da murna da yiwa Allah godiya take aka hada ruwan wanka masu zafi aka Kai Mata
Maman junior hadda tayata wanka kamar me haihuwa haka aka gasata tasamu 'dan qarfin jiki aka Bata abinci taci tareda magungunan da Dr Khalil din yasiyo Mata ta kwanta take baccin wahala ya dauketa.
Da daddare kafin ya wuce Bayan yaci tuwon iyami cikin nutsuwa ya zayyanewa kawu duk halinda yake ciki yanxu tareda gabatarda buqatarsa na auren Amatun
Kawu ya sauke numfashi me sanyi yace"
Khalilu ko bakayi mgn ba nayi niyyar aura maka Amatu kobabu danginka ko daya sbd aduniya Babu Wanda ya cancanta yazama Dole yazama mijin Amatu idan bakaiba Dan haka wlh khalilu nabaka Amatu amatsayin Mata ka shirya nida kaina zanje masallacin juma'a nayi sanarwa ranar juma'ar Nan Inshallah za'a daura muku aure.
##Mamuh#
[01/06, 8:40 AM] __*MAMUHGEE*__♥️🌹: *_MQ 31_*
MAHMOUD ZABEERA ma yau dukkanin jarumta da qarfin ransa ji yayi Yana kakkaryewa daga zuciya har gangar jikinsa, tarota kawai yayi Amma shima Jin yake kamar faduwar zaiyi,
Dr Fatima tayo gurinsa da sauri tana hawaye ta tattaro Amatun jikinta tana Kiran nurses da duk asibitin jikin kowa da zuciyarsa tayi sanyi da rasuwar Dr khalil zabeera Wanda ya zamto cikakken mutum sbd kyawawan halayensa dasukeda wuyar samu acikin mutanen yanzu.
Dr ashir kuwa ganin dukkaninsu kowa neman zauce musu sbd tsananin tashin hankali da sauri ya dauko kujera yakawo wa Modibbo daya tare ummen data Suma,
Kiran wasu nurses yayi aka Kama umme itama akai ciki da ita aka kwantar gadan dake gefen Wanda aka kwantarda Amatu cikin sauri aka Fara Basu taimakon gaggawa dansu farfado tinda suma.
Su Modibbo kuwa zaunar dashi MAHMOUD yayi dukkanin jikinsa na rawa idanuwansa sunyi jajir ko mahaifin nasu yakasa kalla
Jin yanda jikinsa ke rawa sosai yasa Modibbo dagowa da jajayen idanuwansa ya kallesa tareda dange hannunsa Yana rintse ido tareda jinjina Masa Kai alamar sai hkr.
Dr salman zabeera kuwa kuka yakeyi sosai kamar mace sbd rasuwar Khalil din tamkar saukar tsawa sukajita kwatsam Babu Wanda yakawo tunani ko zancen mutuwa yanzu ba'a kansaba kosu Andi dasuke tsofi Basu kawo tunanin mutuwa akansuba.
MAHMOUD ne yayi qarfin hali da jarumtar karban wayar Modibbo yakira Andi dake zaune cikin tsakiyar Daren Yana salati sbd baccin dayaji haka kawai ya dauke daga idanuwansa Kiran farko na asuba dayaji anyi yasashi miqewa zaiyo alwala yafara ko nafilfili wayarsa tadauki haske alamar Kira.
Juyowa yayi ya kalli wayar yana mamakin Wanda ke iya kiransa a wannan lokacin saiyaga sunan Modibbo
ya sake shiga mamaki ya dauki wayar tareda dauka cikin nutsuwa yayi sallama.
Daga can asibiti Saida MAHMOUD ya tattaro qarfin halin iya bude bakinsa cikin rawar muryar dabai taba ba arayuwarsa yace"
Muna asibine taredasu Modibbo da umme Allah yakarbi Khalil cikin Daren Nan.
Tsit Andi yayi tsawon mintuna Yana qoqarin kakkamo zancen dazai fada yafara da Kiran"
Innalillahi-wainna ilaihirrajiun.
Kashe wayar yayi tareda ajiyewa yakoma bakin gadonsa ya zauna Yana sake maimata taslima Yana jinjinawa al'amarin ubangiji dayakeyin yanda yaso alokacin da yaso,
Ya dauke Khalil bayan cika masa burinsa na kwana daya tal,
Wannan shine cikakkiyar ikon ubangiji da Babu Wanda ya Isa ya sauya sbd yau da ace dukiya da mulkinsu nada iko meya hada Khalil da mutuwa a ranar yau da ko awa ashirin da hudu aurensa baiyiba.
Astaghfirllah" yafara maimaita tawa Yana rintse idanuwansa ya sunkuyar dakai cikin tsananin jimamin rasa yaro me tsaftatacciyar zuciya da tausayi tareda tawakkali irin Khalil.
Allah yayi maka rahama yabaka hasken kabari da sakamakon gidan aljanna KHALIL.
Koda asuba tayi akai sallar asuba tuni rasuwar Khalil ta yada zabeera da familynta nako Ina da ko Ina tuni kuku ya sauka a zabeera sbd mutuwar ta girgiza kowa sbd Babu Wanda yayi tunanin mutuwa Kuma tasa adaren,
Koda gari yayi waye sosai tuni family suka Fara halarta zabeera tafara cika tun kafin akawo gawar tasa gida dama wainda sukazo biki Kuma dama Basu tafiba tunda a Daren jiyan aka kawo amarya Ashe basasu koma daga bikinsa ba saisunyi zaman makokinsa,
Duk Wanda ya iso saiyayi kukan wannan babban rashin na khalil zabeera sbd kowa Yana shaida kyawawan halayensa da nutsuwarsa wadda tasa yakeda jamaa ciki da wajen zabeera.
Ahankali tabude idanuwanta ta rufe tasake budewa tana qyaftasu
Da fuskar usi dake rungume da kanta tafaracin karo ta rufe idon ta bude taga shi din daine ta zabura da sauri ta tashi zaune har tana zamewa saura kadan ta fado qasan gadon iyami da maman junior da idanuwansu sukai jajir musamman iyami da har lokacin hawaye Basu dauke daga idanuwanta ba sukayi saurin tarota ta kallesu da manyan idanuwanta dasuka firfito sun bushe sai wani irin ja dasukayi tafara qoqarin miqewa qafafunta da hannunwanta tareda muryarta dasuke wata irin rawa tana cewa''
Ina...ina..Ina khalillll????
Sunkuyar dakai sukayi Banda iyami datayo kanta tana neman rungumeta tayi saurin qwacewa tana nufar qofar dakin asibitin USI dake kuka sosai yayi saurin tarota Yana kuka yace"
Amatu Ina zakije antafi dashi gida muke jira ki farko muma muke gidan.......
Zamewa tayi ta zube qasa tareda sakin wani irin gigitaccen kuka me qarfi dayasa asibitin suka qara daukar shiru kowa na sake rafka tagumin rashin Khalil din dakuma kuka da tashin hankali dazata shiga idan ta farka Wanda suka shirywa Sha dama.
Tsayawa sukayi kowannensu na nasa kukan me tsananin cikin tausayinta da Kuma zafin rashinsa Suma daya bugesu Babu Wanda yayi yunqurin hanata sbd kuka Kam yariga ya sameta abarta tayisa ko zataji sassucin radadin ZUCIYA.
Irin kukan datakeyi ne yasaka hankalin duk Wanda ke asibitin tashi sbd kukan nata taba zuciyoyinsu yakeyi Yana sake tuno musu da Dr khalil sbd rashinsa ne kawai yasa take wannan kukan Dan kuwa da Yana Raye Amatunsa bazatayi irin wannan kukan ba matuqar ba al'amari yafi qarfinsa bane.
MAHMOUD ne da kansa Modibbo yasashi yadawo asibiti yadaukosu Amatun tunda yashigo asibitin yaji tsit Yana Kama hanyar dakin datake yafara jiyo kukanta dayasashi tsayawa cak qafafunsa da zuciyarsa na qara daukar nauyin rashin Dan uwa mafi soyuwa garesa.
Jin kukan na kakkaryasa yasa yayi jarumtar qarasawa dakin ya tura ahankali yaci karo da ita zube bakin qofar tana kukan idanuwanta kamar zasu zazzago qasa.
Saurin juyawa yayi yacewa su iyami su kamota sutafi gida.
Daqyar suka tattarota suka saka mota suka nufi zabeera inda take cike tundaga farkon layin anguwar talakawane tako Ina bulbulowa sukeyi dukkaninsu yawanci mutanensa ne da taimako ya hadasu.
Ko a anguwarsu kawu jama'ar dasuka halarto dan jana'izarsa basa qirguwa
Hakama ko anguwar