Showing 21001 words to 24000 words out of 108527 words

Chapter 8 - MIN QALB complete Hausa novel

MAMUGEE   

08 Apr 2025

8456

bazai bar umme ba hattasu yayanta sai haqqin MAHMOUD ya shafesu Dan haka bazai Bari tadau wannan alhakinba dazai ja Mata azaba gaban Allah hakama bazai Bari rayuwar 'dan uwansa ta lalace ba hakama amatu rayuwarta nacikin mugun hadari.....

Da sauri ya kalli usi yace"

Usman Yi sauri kabar Nan katafi gida namaka alqawarin dawo da amatu Babu Abinda zai sameta maza katafi karka fadawa kawu komai..

Da gudu ya nufi ciki yayi hanyar palon Yana adduar Allah yasa amatun Bata bude fuskartaba Yana Isa ya fada palon da qarfi daidai lokacinda amatun tariga ta bayyana fuskarta akace ta fada cikin waye ajikinta,meye alaqarsu dame cikin?¿

Bude baki tayi hannuwanta da qafafunta na rawa zuciyarta na harbawa da qarfi zatayi magana tana kallon inda MAHMOUD ke zaune har lokacin idanuwansa lumshe Kuma duk yana jin abindake faruwa kawai dai ba huruminsa bane shiyasa ko hankali bai badaba,
cikin wani irin sauri Dr khalil ya dako tsalle ya fado tsakiyar palon tareda cewa"

Allah ya taimaki Modibbo nine.

Wattttt????umme tafada da sauri tareda miqewa tsaye tareda haj Maryam
Nuratu ma da antynsa juwairiyya duk miqewa sukayi cikin tsananin firgici
Take palon yadauki hayaniya cikin rasa abin fada alhaji qarami yace kowa yatafi antashi meeting.

Hayaniya aka Fara saidai yanayin Modibbo yasa kowa yin tsit suka Fara sulalewa suna ficewa.

Kaf kowa ya fice Banda uwayensu maza da 'yannansu maza sai iyaye mata hatta MAHMOUD na gurin bai fitaba lokacinda yaji muryar khalil amatsayin me cikin yasashi bude Ido ahankali ya sauke Kan amatu dake gefen Khalil din tana kallonsa cikeda mamakin daga Inda ya fado.

Kallonsa takeyi tanason Kiran sunansa Amma ganin yanayinsa ta tana hango tsananin 6acin Rai da takaicinda yake ciki,

Idan har da khalil da MAHMOUD yayan hajiya mama ne kamar yanda tafada mata to acikinsu duk Wanda tace shine me cikin ta cecesa daga hawa mulkinda zaa salwantar da rayuwarsa to kenan duk dayane koba komai zatafi farin cikin kubutarda Dr khalil sbd kurkinsa akansu.

Da hanzari umme ta qaraso gabansa ta kalli cikin idanuwansa cikin 6acin Rai tace"

Me kake fada?
Maza maza fice wannan ba Abinda ya shafeka bane...ba magana nake maka ba""ta fada cikin tsawa da firgici.

Gyaran murya Modibbo yayi akaron farko bayan shock din daya samu na daqiqu ya kalli khalil tareda kallon amatu dake kallon Khalil din cikin rashin Jin Dadi qunci da bacin ran datake hangowa cikin idonsa.

Khalilu ta Yaya kazama uban cikin jikin yarinyar na???

Hadiye wani yawu me mugun daci yayi sbd dai gskia bazata faduba Dan idan yafada gski umminsa da amatu duk suna cikin hadari Dan umminsa har zamanta cikin zabeera saiya ware.

Rintse ido yayi ya budesu suna kadawa jajir take jijiyoyin kansa suka firfito sbd qarya ba halinsa bane bare wannan qaryar datafi kowace muni.

Muna sauraronka Khalil kafin fushinmu ya sauka akanka kayi bayani"cewar alhaji qarami.


Sauke Kai yayi daga kallonda Modibbo ya tsaresa dashi me girgiza jarumtarsa yace"

Mun jima muna qaunar juna tsawon shekaru uku
Nasan bazaa Bari na aurotaba shine mukaje wani guri aka daura Mana aure.....tassssssss

Umme tasakar Masa wani gigitaccen Marinda Saida ya zube Kan gwiwoyinsa tareda sauke Kai.

Cakumo amatu tayi cikin tsananin 6acin Rai tace"

Modibbo ba gskia yake fadaba Khalil bazai taba aikata wannan qazamin aikinba wannan ita zata fada ubanda ya Mata ciki Amma badai Khalil ba....hannu ta daga zata kaiwa amatun Modibbo ya daka Mata tsawa da cewa"

Aishatu ki dawo hankalinki ciki ne ajikinta kada hannunki ya sauka jikinta..

Ke matso fili ki fada Mana Abinda yafada gskia ne kokuwa??

Fitowa tayi daga bayan Khalil din tana kallon idanuwan umme dake fitowa da ruwa tace"
Eh gskia ya fada.

A Ina kuka hadu??

A asibitinsa.

Shekara nawa yanxu da auren??

Rawar murya tafara tana neman dufewa tace"

Daya.

Aikuwa take kowa yaqarin tsit cikin tashin hankali.
##mamuh#



______________
KUNA BUƘATAR A TALLATA MUKU KAYAN SANA'ARKU A PAGES ƊIN BOOKS ƊIN ZAFAFA BIYAR 2021?.

To kuzo ga dama ta samu💃🏻💃🏻.

        Ina ma'abota son a tallata musu hajojinsu a kafafen yanar gizo suke?.

Tofa kuzo dama ta samu, dan jerin gwanon haziƙan marubanku ƴan biyar sun fiddo muku da hanyar da kuma kasuwancinku zai zagaya lungu da saƙo ta dalilin shafukan littatafai.

Ga duk mai buƙatar a saka masa tallan kayan sana'arsa a shafin littatafan mu na zafafa biyar zai iya tuntuɓar waɗan nan Numbers 0903 234 5899 or 09033181070 ta vWhatsApp, idan har agama buks ɗin kana buƙata a sakamaka talla zamu saka maka akan farashi mai sauqi. Idan kuma wasu adadin pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓.

Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗.

______________________

#MIN QALB❤️
Mamuhgee

ZAFAFA BIAYAR

SIRADIN RAYUWA
safiyya huguma

MIN QALB
mamuhgee

YANKAN BAYA
billyn Abdul

KIBIYAR AJALI
Miss xoxo

ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA
hafsat rano

Pay @09033181070
Or 09032345899
[01/06, 8:53 AM] __*MAMUHGEE*__♥️🌹: *_MIN QALB 12_*
_Mamuhgee_



Kasa riqe hawayenta umme tayi suka gangaro Kan fuskarta ta shafa cikin firgici ta dago hannunta ta kalla taga tabbas hawayene,

Yau ni Aisha mezan gani ne??
Wace masiface wannan yarinyar na gayyatowa kaina ranar farko data sako kafarta gidana hawayenda na manta ya akeyinsu tun quruciya yau sune a fuskata,
Wlh shirina bazai lalace ba Koda kowama zai rasa saidai kowa ya rasa...

Juyawa tayi Kan khalil cikin tashin hankali da rudewa tace"

Khalil karkayiwa kanka haka ka 6ata rayuwarka kafada gaskia wannan yarinyar bakada alaqar komai da ita,

Rintse ido yayi Yana danne tsananin 'dacin da zuciyarsa ke Masa
Ummin ta girgizasa da qarfi tana sake Marin fuskarsa tace"

Kafada gaskia Khalil wlh bazan yadda a maqala maka cikin qaryaba wannan yarinyar 6arauni.....

Katseta Modibbo yayi da cewa"

Aishatu ki nutsu kisan a inda kike,

Shiru yayi Yana nazari cikin tsananin baqin cikin da takaicin Abinda ke faruwa ya dago ya kalli khalil
Khalil din yayi saurin sauke kansa
Yace"

Khalilu Abinda kayi a tunaninka meye shi??

Modibbo a musulunce shi aure idan har an daurashi Akan yanda sharuddan aure sukace to banyi laifi ba,
A tsakanina daku iyayena Kuma laifi ne sbd na boye Muku nayi bada izininku ba saidai nayine sbd girmamaku Dan inajin tsoron kawo muku zancen sbd tsoron bazaku Bari,
Dan haka na aikata laifi babba Kuma Ina neman yafiyarku dakuma amincewarku da amatun kodan Abindake cikinta baida laifin komai kada a hukuntasa ko mahaifiyarsa nine me laifin Kuma na dauka a shirye nake da dukkanin wani hukunci saidai Allah ya huci ran Modibbo ina fatan itama amatu abata adalcin datazo nema duk yanda akayi hukuncin zamu dauka.

Tsit sukayi suna kallon bakin Khalil din cikin girgizuwa da kalamansa,
Dukkanin Abinda yafada jin sukayi kalmomin na son tabasu,
Shi cikin babu ruwansa to meye mafita ga wannan alamarin?

Kallon mahaifiyar amatun Modibbo yayi yace"

Ina mahaifin yarinyar??

Ya rasu tun tana yarinya qarama.

Ina danginsa?

Daga maiduguri mukayo Nan munrasa kowa bamuda kowa nanma amatsayin 'yan gudun hijira muke har mahaifinta yasamu aikin sanaar Saida kayan Miya harya rasu daga Nan ne muka hadu da......sai tayi shiru tana satar kallon hajiya aisha sbd Abinda zata fada itama ba yanda ta iya Dole tabi tsarin yanda al'amarin ya juya kodan fita da ranta tace"

Daga Nan ne muka haduda likita shine yake taimaka Mana harya sanyata makaranta shine yakawo maganar son aurenta nikuma na amince saidai bai fada Mana cewar iyayensa Basu aminceba yakawo Mana wani amatsayin mahaifinsa aka daura auren yanzu shekara daya kenan,
Mu Kuma kusan wata biyu kenan bamu sake ganinsa ba munyita zuwa asibiti bama samun ganinsa saigashi ciki ya bayyana atareda ita
mutane harsun Fara binmu da gori da maganganu marasa Dadi shiyasa mukazo...

Faduwa ummi tayi Kan kujera tayi zaman 'yan bori tana kallon baba Jamila tayi wani kukan kura tayi kanta tana cewa''

Qarya takeyi Modibbo wlh taron maqaryata ne....

Saurin riqeta hajiya Maryam tayi cikin tashin hankali take itama tace"

Modibbo Sam wannan matar qarya takeyi wlh daga gani sharri ne zuke qullawa sbd kudi......kallonda Modibbo yayi Mata yasata yin shiru baqin cikin future din 'yarta dake Shirin lalacewa na cinta kamar ta rufe amatu da bugun mutuwa.

Khalilu duk Abinda tafada gskia ne kokuwa?

Gyada Kai yayi kansa na qasa Dan duk duniya bai ta6a Jin tsanar wani lokaci 'daya ba kamar baba Jamila.

Bsyan dogon nazari da tunanin irin rashin 'da'a da wulaqanta zabeera da Khalil din yayi take yafita ran Modibbo da kusan kowama a gurin kai tsaye cikin nuna qyamarsa ga khalil din da halayyarsa Modibbo yace"

Ban karbi wannan auren naka ba likita haka Kuma kaima na cireka daga iyalina ka dauki matarka kuje kibar Nan karka sake Kiran kanka da zabeera har abada,
Kuma kuje ga adalcin dakuke nema Nan anbaku,
Anbarwa 'yarki mijinta har abada duk ranarda qafarku ta tako zabeera aranar ne zakusan asalin hukunci da zafin Zabeera.........

Kuka ne qarfi umme ta fashe dashi tareda riqe Khalil din da idanuwansa suka qarasa rinewa jajir Yana Mata kallon kece Kika jawo..

Girgizasa tahauyi tana kuka Mai qarfi tace"

Dan Allah Khalil kafada musu gskia bakai bane
Wlh bazan yardaba nizan fada gskia..

Girgiza Mata Kai yayi tareda zamewa daga hannuwanta yayi qasa da murya cikin qunci Yana cewa'"

Ummi kema kisani idan har kina Sona da 'dan sauran farin cikin daya ragemin bazaki taba fadar gskia ba sbd zata saki keda amatu cikin hadari Wanda bazan iya daukaba,
Umme kece rayuwata gabaki 'daya amatu kuwa itace zuciyata
Meyasa zakiyi haka ummi....??

Mutuwar tsaye tayi tana kallonsa cikin tsananin tsoro da tashin hankalin Abinda yafada,
Me Khalil ke nufi?
Amatu zuciyarsa,
Dama sunsan juna da gske kokuwa ita yakeson rainawa hankali,
Amatu dama tasan 'danta shine ta karbi aikinta kenan ita take rainawa hankali tabbas zatasan tayi Wasa da wuta.

Gangarowa wasu sabbin hawayenta sukayi ta girgiza Kai tana cewa'"

Khalil wlh bazan iya gani na rabu dakaiba,
Ka saketa saki uku,
Cikin ma a zubar kabawa Modibbo hkr Amma Dan Allah Khalil kada katafi yaqarasa cikin kuka tana sake riqesa.....

Cikin tsawa wannan karon Modibbo yakira sunanta Yana kallon Khalil yace"

Ko bayan kabar Nan duk ranardaka saketa daga ranar zakasan ainihin fushin mahifinka,
Haka cikin dake jikinta.

Zubewa qasa umme tayi da sauri Yana cewa'"

Na roki Modibbo daya taimaka ya sassautawa Khalil wannan hukuncin.

Miqewa Modibbon yayi Yana cewa'"

Taro yaqare kowa ya tafi.

Kamar daga sama sukaji security din bakin qofar shigowa na bada sanarwar isowar Andi Wanda yasa kowa miqewa cikin tsananin firgici sbd Abinda andin yafi shekaru ashirin beyiba wato zuwa meeting palon.

Hajiya Maryam data yiwa amatu text din takira andin tafada Masa halinda ake ciki ta saki ajiyar zuciya tana riqo umme data miqe da sauri itama ganin Andi yau da kansa take ta shiga taitayinta tana shanye kukanta saidai hawayenta dasukaqi tsayawa ta kalli hajiya Maryam tace"

Kin kyautamin Maryam sbd Andi ne kawai zai iya ceton Khalil Dina yanxu.

Modibbo da kansa ya miqe yabawa mahaifinsa dake tattareda wata irin izzar mulki da cika Ido tareda razanarda mutane da kallo 'daya idan yayi maka Wanda kaf cikin zuriar zabeera mutum biyu ne suka 'daukosa sak alqasim zabeera mijin haj Maryam daya rasu sai MAHMOUD ZABEERA wanda beyi mulki ba Amma Yama wucesa a mugun miskilancin da kwarjini me ban tsoro.

Shigowar Andi tasake saka kowa cikin tsoro da firgici Saida yayi zaman minti biyar tsit bayan gama amsa gaisuwar kowa kafin ya bude muryarsa me amsa amo yace"

Khalilu da kanka zakayi bayanin abindake faruwa daga farko.

Ba inda inda Khalil yasake koro Masa bayanin komai tareda hukuncinda Modibbo ya yanke Masa ya 'dora da fadin"

Na aikata babban kuskure Kuma na amsa laifina nakuma karbi hukuncina Andi,
Zanyi nesa da Nan Kuma bazan taba Bari maganar ta fitaba bare sunan zabeera ya baci,
Nayi alqawarin daga lokacinda zan fita Nan zan aje sunan zabeera Dan kada gaba nayi Abinda zan kawo batanci gareku ba da......

Cikin firgici ummi tayi saurin zubewa qasa tana cewa'"

Allah ya taimaki Andi Dan Allah Andi ya tausaya a sauqaqawa Khalil tsaurin hukuncinsa kada arabasa da sunansa da zuriarsa indai akan laifin wannan yarinyar ne Andi abasa dama yayi Mata saki uku bayan ancire cikin.......

Maganar ummin yasa Andi dagowa ya kalli Modibbo
Modibbon yayi saurin qasa da Kai Yana cewa'"

Ayi Mata afuwa Andi uwa ce dake cikin firgicin rabuwa da 'danta.

Kallonsa andin yasake hakan yasashi yin shiru Yana cewa"

Allah ya huci zuciyar Andi da Abinda aishatu tafada.

Kallonta Andi yayi tareda kallon baba Jamila yace"

Aishatu matsayinki na mahaifiya kikeson a cutatarda 'yar wata sbd naki 'dan wannan ba adalcin Andi bane.

Kallon baba Jamila yayi cikin sautin dayasata rudewa qafafunta suka hau rawa yace"

Kinxo neman adalci anbaki adalci
Kin aminta da auren 'yarki Dan haka 'yarki zatayi zaman sure bayan munyi bincike akan auren,

Zaki bar 'yarki anan Kuma zata zauna cikin gata da aminci
Zata raini cikinta a hannun matar 'dan uwansa MAHMOUD ZABEERA bayan haihuwarta anbawa mahaifiyarsa halak malak saimu sake daura musu aure,

Aishatu kinason kashe abindake cikin tun baizo duniyaba to kece zaki rainesa har girmansa bayan zuwansa duniya an mallaka Miki shi halak malak.

MUHAMMAD""fada sunan Yana 'daga sautinsa.

Sai alokacin MAHMOUD ya dauke idanuwansa daga Kan Khalil da amatu sbd jin a hannunsa yarinyar zatayi rainon cikinda bai gama yadda da akwaisaba sbd aduniya shine yafi kowa sanin wannan ba halin Khalil din bane ya kalli inda Andi yakira sunansa ya taso cikin nutsuwarsa dake qarawa Andi ganin kwarjininsa ya qaraso ya tsaya gaban andin tareda sauke kansa cikin girmamawa yace"

Allah yaqarawa Andi tsawon Rai.

Matar 'dan uwanka zata zauna a hannun matarka har tsawon lokacinda zata haihu,
Cinta da Shanta duk na hannunka,
Ciwonta da maganinta na damqasu hannunka Dana matarka,
Na damqa maka tsaron lafiyarta Dana Abindake cikinta sbd aishatu ta tabbatar Mana da AMATULLAH da abundake cikinta na cikin hadari a hannunsu Dan haka Kaine kawai Wanda na yarda dashi nabaka amanarsu a hannunka.

Shiru yayi bai motsaba sbd Abinda andin yafada yaxo da wani al'amarine da kansa yake kasa dauka,
6arauniya a gidansa?ta Yaya zai iya Bari wannan yarinyar ta zauna acikin inda yake rayuwa
Khalil dinma haryanxu yakasa yarda da shidin ne uban cikin wannan yarinyar
ahankali yadan dago ya kalli gefen datake tsaye riqeda rigar Khalil sbd zuwa lokacin tafara firgita da abindake faruwa Jin hukuncin da aka yankewa Khalil daga farko taji bazata iya Bari tazama sanadin batawarsa da rabuwa da iyayensaba saiga zuwan wannan Andin Wanda ganinsa kawai yasa taji tsoro da firgici ya kamata gashi ana maganar riqeta ta haihu
Ta Ina dakuma ta Yaya zata haihu
Kasa riqeta qafafunta sukayi tsabar rawa shiyasa ta boye bayan Khalil din.

Taro ya tashi kowa ya watse nagama magana abubukar a aika mahaifiyarsa gida tareda kayan abinci da jarin sana'a me kyau sbd itace kakar Zabeera na shida Inshallah.

Modibbo a qarqashinka zaa kula sosai matuqa da AMATULLAH Ina fatar Nanda watanni kadan za'a bani zabeera na shida a hannuna.

Kallon amatu yayi akaro na farko data saki fuska dukkaninsu Saida suka bude Ido sbd ganin murmushi akan fuskar tasa yace"

AMATULLAH ni Andi nine gatanki keda Abinda yake cikinki acikin zabeera nayi Miki alqawarin baki kyakkyawar rayuwa keda Abindake cikinki sbd zalincin da khalil yayi miki da Wanda mahaifiyarsa ke shirin Yi na cutatar dake da Abinda ke cikinki Dan haka na Miki alqawarin idan har Ina Raye Kika haihu indai namiji sai yayi mulkin zabeera wannan shine babban adalcin dazan baki,
Kece mace ta farko Kuma mutum ta farko data shigo zuriar zabeera a tarihi ki riqe wannan a ranki Dan haka karki Bari har abada Nasameki da illa ko laifin dazai sakani takaicin hukuncina sbd cin Amana,yaudara da qarya ba abubuwan da Andi ke yagewa bane.

Kai Kuma Khalil hukuncinka na ranardazan daura maka aure da ita.

Kowa yatafi nagama mgn.

Hannu umme take Shirin dorawa akai tasaki kukan baqin cikin wannan alamarin Modibbo ya aiko Mata da mugun kallo Haj maryam ma dake Shirin fasa ihu Andi ya nuna musu qofa sunaji suna gani suka hadiye cikinsu bame iya Jan wani suka fito Babu me ganin gabanta tsabar tashin hankali.

MAHMOUD ma ficewa yayi batareda yaqara ko second dayaba.
Baba Jamila da Sha Taranta ta arziki aka kaita gidanta inda suka tsara komai Koda anxo bincike.

ZARAH aka kirawo ita tazo aka damqa amatu hannunta wadda atake alokacin amatun tashiga ranta ta kalli amatun dake qara damqe rigar Khalil sbd hankalinta daya tashi gaba daya da alamarin sbd ita yanzu Tama rasa Ina aikin data zoyi yaje Sam sun rikita 'yar qaramar qwaqwalwarta.

Kallon Khalil tayi tana sake matsesa tana girgiza Kai tace"

Dr gida zani nafasa bana......

Hannu ya Dora a bakinta tareda girgiza Mata Kai Ya bude bakinsa daya gama nauyi muryarsa na nauyi a karye yace"

Kije kibi ZARAH komai zai daidaita bazan Bari komai ya sameki ba na Miki alqawari,
Kuma zansamu kawu nayi mgn dashi zan Masa bayani yanda zai fahimta Inshallah.

Qura Masa Ido sosai take kallonsa sbd yadda dashi datayi dari bisa dari kafin ta daga Masa Kai tasakesa ahankali tareda kallon zarah dake Mata murmushi suka wuce.

Bayan fitarsu Kai tsaye motar zarah din suka nufa suka shiga ta jazu sukabi ta bayan gefens Modibbo zuwa part dinsu dakeda nisa cikin zabeera din sbd kusan sune na qarshe.


Umme nashiga palonta ta zube qasa tareda Dora hannu akai zata saki ihu juwairiyya tayi saurin rungumeta tana Kiran sunanta itama muryarta na karyewa dason yin kuka.

Haj maryam ma kuka takeyi wiwiwi itada nuratu dake wani irin kuka tana kwantawa jikin momyn Tata sukam yau wace irin baqar ranace agaresu.
##mamuh#



______________
KUNA BUƘATAR A TALLATA MUKU KAYAN SANA'ARKU A PAGES ƊIN BOOKS ƊIN ZAFAFA BIYAR 2021?.

To kuzo ga dama ta samu💃🏻💃🏻.

        Ina ma'abota son a tallata musu hajojinsu a kafafen yanar gizo suke?.

Tofa kuzo dama ta samu, dan jerin gwanon haziƙan marubanku ƴan biyar sun fiddo muku da hanyar da kuma kasuwancinku zai zagaya lungu da saƙo ta dalilin shafukan littatafai.

Ga duk mai buƙatar a saka masa tallan kayan sana'arsa a shafin littatafan mu na zafafa biyar zai iya tuntuɓar waɗan nan Numbers 0903 234 5899 or 09033181070 ta vWhatsApp, idan har agama buks ɗin kana buƙata a sakamaka talla zamu saka maka akan farashi mai sauqi. Idan kuma wasu adadin pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓.

Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗.

______________________

#MIN QALB❤️
Mamuhgee

ZAFAFA BIAYAR

SIRADIN RAYUWA
safiyya huguma

MIN QALB
mamuhgee

YANKAN BAYA
billyn Abdul

KIBIYAR AJALI
Miss xoxo

ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA
hafsat rano

Pay @09033181070
Or 09032345899
[01/06, 8:53 AM] __*MAMUHGEE*__♥️🌹: *_MIN QALB 13_*
_mamuhgee_


ANNUR PERFUMES ANNUR PERFUMES!!!!!!

JAMA'A MA'ABOTA SON QAMSHI DAN SANYAYA ZUCIYA Ina kuke kuzo ga sabuwar duniyar turare sabon tashe ANNUR PERFUMES sunkawo muku,
Turarensu qarshene,
Qamshinsu na daban,
Kayansu tabbataccine,
Aikinsu ingantacce ne
shin kataba/kintaba amfani da ANNUR PERFUMES kuwa?
To maza qarzayo karki Bari ayi badakeba dankuwa kayansu lamba dayane Kuma amintaccine masu guarantee domin kuwa mun tabbatar.


ANNUR PERFUMES donjindadin customers munkawo muku dadadan turaruka na musamman masu nishadan tarda Amarya da uwar gida harma da angonta kamar haka turaren wuta humra kala daban daban kwalaccha Dana matsi na

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login