Showing 3001 words to 6000 words out of 108527 words
makarantar cikin karyewar zuciya Yana jinjina rabasun dazaiyi yace"
Usman kaga amatu tafara girma akwai hadari abarta cikinku anan..
Kallonsa sukayi atare cikin rashin fahimta.
Gyara tsayuwa yayi yace zantafi da ita zan kaita gurin me 'dakina idan yaso Kai saika riqa zuwa Mana hutu.
Atare suka girgiza Kai itada Usman din suna kallon juna idanuwansu na cikowa da hawaye.
Nasan zaa rina yafada cikin ransa Yana kallonsu zuciya a karye.
Kamo hanun Usman yayi yajasa gefe ya fahimtar dashi sosai ta yanda zai gane Abinda yake nufi
Harya gane Yakuma amince sbd har abada bazaiso Abinda zai samu amatu ba.
Daga haka suka hakura sunaji suna gani suka rabu da juna kawu yatafi da su kafin daga baya Usman yadawo makarantar malam.
Tunda amatu tadawo gidan kawu Bata taba haduwa da tsangwama ba saidai Kuma babuwa wani janta ajiki da iyami tayi.
Basuda qarfi sai rufin asiri da haka malam yasakata primary school dinda yake gadi wadda tuni aka maidata 'yar maigadi.
Usman shekara daya yayi batareda itaba ya tattara karatun yadawo gidan kawu Yana kwana a soro komai tsananin sanyi da zafi kuwa.
A haka kawu yasamar Masa aikin tsaron gidan wanka da bahaya a Tasha har Shima yashiga primary 2
Yana shiga primary 5 ya tattara karatun ya ajiye sbd gwagwarmayar rayuwa.
Kawu da iyami sune gatansu na farko,
Kawu da iyami sune wainda suka cirosu daga bola suka basu sunanda ake kallonsu da daraja ayanzu.
Shekakarda tashiga js 2 a shekarar suka shiga wata sabuwar masifar da akayiwa kawu sharrin satar cire winduna da qofofin makaranta ya siyar.
Duk inda ake zuwa roqo da Kai kuka sunkai akan alamarin Amma Abu ya agagara qarshe dpo nunawa yayi sai idan ita amatu kokuma matar kawun zasu kwana dashi tukuna zai taimakesu.
Akaro na farko da amatu ta tsani maza da taimakonsu.
Ranar dukkaninsu kwana sukayi kukan baqin ciki sunaji suna gani akayi gidan yari da kawu hukuncin shekara biyu dama Kuma abin hadda gayya sbd Shima alqali yaso amatun tabasa hadin Kai sbd irin wankewa da jikinta yayi gashi fatarta Ashe me irin hasken Nan ce ga jikinta daya gama fitowa ana mace tsaf yanzu iyakaci qarasa balagewa ne dabatayiba a cikakkiyar mace.
Tunda akayi gidan yari da kawu alamarin duniya yasakosu gaba ko abincinda zasuci ya gagaresu dole Usman ne yanaji Yana gani yake fita gwagwarmaya Amma sai ahankali.
Wata bakwai da zuwan kawu gidan yari aka koresu daga gidan dasuke suka rasa gurin zuwa ga iyami Dan cikinsa take dauke dashi wahala tasaka ya bare ko kudin asibiti basuda.
Akaro na farko da Usman yakoma sata kenan arayuwarsa ya kama musu daki buyi a wani gidan haya me dakuna goma reras a jere kamar shaguna,
Gidanda ya hada mutane dabam dabam masu halaye dabam dabam.
#mamuh#
MIN QALB❤️
Mamuhgee
ZAFAFA BIAYAR
SIRADIN RAYUWA
safiyya huguma
MIN QALB
mamuhgee
YANKAN BAYA
billyn Abdul
KIBIYAR AJALI
Miss xoxo
ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA
hafsat rano
Pay @09033181070
Or 09032345899
[01/06, 8:50 AM] __*MAMUHGEE*__♥️🌹: *_MIN QALB 3_*
_mamuhgee_
_Min qalb Na kudine_
Daki 'daya ya dauka iyami da amatu suka dauka daya
Sabuwar rayuwa suka Fara a gidan inda ake zaman rashin nasiha da ragawa juna,
Sam gidan kowa ta kansa yakeyi Babu Mai ta6uwa kowa ka taba Babu sauki sai masifa.,
Hakan yasa suma ahankali rayuwa ta koya musu yanda take,
Sunaji suna gani itama amatu ta ajiye karatu suka fada gwagwarmayar neman abin rufawa Kai asiri,
Amatu da iyami suka bazama neman ayuka
Ita iyami tasamu aikin abincin wata makaranta amatu Kuma tasamu aiki bookshop din wata iyamura.
Bata wani jima tana aiki gurinba saigashi Shima Usman aka kamasa aka rufe kusan wata biyu ga iyami ma tana fama da ciwon diabetes sai kawai tace Mata ta ajiye aikin abincin makarantar kada taji ciwo al'amarin yaqara lalace musu.
Hakan yasa nauyi yahau kanta na kulada iyami damuma nauyin ci da shansu.
Rayuwa da lokaci sune suka koyar da ita darussa da dama wanda ayanxu take musu kallon fahimta,
Tunda lalurar nauyin ahalinsu tadawo kanta Bata taba samun Wanda yadubeta da fuskar taimakawaba kowa da wata mummunar manufa yakeson taimaka mata,
Ansha niyar lalatar Mata da rayuwa tana tserata,
Ansha wulaqantata akan ana Mata kallon fandararriya Mara asali,
A ranarda wani yayi niyar lalatar Mata da rayuwa ta dole da niyar zai taimaka musu aranar ne zuciyarta ta gama qanqansewa da duk wani alamarin mutanen duniya
Shiyasa take Kiran kanta da furen kan juji.
Iyami ma hakan yasake busar Mata da zuciyar zata nemi kudi kota yayane Banda haram,
Babban Abinda ke qara kawo tabarbarewar zaman lafiyarmu shine hukunci akan Wanda hukuncin laifinsa bai Kai ba shike kawo sauyawar tunani da zuciya,
To kusan hakance tafaru da ahalin kawu,
Bayan fitowar Usman tuni zuciyarsa ta gama kangarewa sbd rufesan da akayi suncire Masa tsoron gidan yari Kuma,
Rayuwarsu tadawo sabuwa,
Burinsu shine kudi,
Farin cikinsu shine kudi,
Mafarkinsu shine kudi,
Mafarkinsu shine kudi
Idan har kudi suke Hana Dan Adam wulaqanta da tozarta tareda azabta Irin wadda suka taso suka rayu acikinta to tabbas sun shirya samun kudi Koda na wani ne.
Basu sake jinjinawa alamarin kudi ba Saida sukayi belin kawu da kudi naira dubu dari bayan yayi shekara daya da wata Tara gidan yari.
Babban al'amarinda ya shallake tunanin abokan zamansu na gidan hayan shine qarmashewar da zuciyar kawu tayi fiyeda ta kowa acikinsu game da kudi,
Yana fitowa gidan yari Abinda yafara fada afili shine'"
Idan har kudi sune maganin wulaqanci da toxarci tareda maganin wani baqin ciki to tabbas burina yanxu shine kudi,
Kudinma ba qananun ba manya nake buri.
Shekaru sunja sosai alamura sunyi haske sosai a rayuwarsu sbd kowa yanada hanyoyin samun kudinsa,
Acikin gidansu dake cike tab da 'yan haya to tabbas Babu me masifa da fitinar kawu,
Bayada sauki ko kadan Dan babu ubanda yake ragarwa a gidan ciki kuwa harda alhaji mande me gidan,
Duk masifaffun gidan suna shafawa kawu lafiya sbd fitinarsa Amma shikuma iyami ce kawai daidai dashi sbd ko atsakaninsu basawa juna nasiha ko sauqi.
Damuwa,kuka,kunci,baqin ciki,takaici,tuna baya
Wainnan duk wasu abubuwane dasuka binne a bayan rayuwarsu,
Sun koya su ciyar da kansu tun basusan kan nasuba,
Sun koya tsayawa da qafafunsu da junansu tun basusan meye duniyar ta qunsaba,
Sunyi yaqi da wahala da yunwa tareda azabta su kadai batareda wani ya tallafesuba,
Sun yakice tsoro tun basusan meye tsoronba
Dan haka su aduk yanda rayuwa tazo musu yanzu basuda damuwa da ita sbd sunsan babu wata gwagwarmayar data fi wannan din.
Wannan shine rayuwarsu,
Rayuwar 'yancin Kai rayuwarda baduda burin komai cikinta saina suji Dadi su dawwama da juna acikinsa.
AMATULLAH yanxu rayuwarta takeyi cikin jin Dadi da walwala,
Babu Abinda ya dameta face taji dadin rayuwa tareda ahalinta data keda burin su samu duniya suji dadinsu,
Duk inda tasamu aiki Bata jimawa ake watsewa sbd halayenta na Babu Abinda ya dameta bayan shiririta da yin duk Abinda taga dama
Duk Wanda yayi gigin shiga huruminta kuwa Yara take sawa qanana su koyawa mutum hankali kokuma usi Wanda beda aikin yi yanxu sai yawon banza sai idan ansamu na sanfewa a sanfe.
Amatu kyakkyawar cikakkiyar budurwace yanxu wadda tagama hada komai musamman kyawun jiki da fuska.
Maza ko gigin zuwa nemanta basayi sbd a duniya idan akwai Abinda ta tsana fiyeda komai to mazane idan aka cire usi dinta da kawunta.
Kana cewa kana sonta zata saka ahada maka jini da majina Wanda usi ne me aikin shida wasu abokanansa.
Ayanxu Kam sunsan duniya sunkuma darassantu da iliminda tabasu shiyasa akoda yaushe ashirye suke da duk sabon darasinda zata kawo.
AMATULLAH K SALEH shine cikakken sunanta Wanda kawu yabata aranar da yafara kaita makaranta,
Usman K saleh 'dan uwantane da aduniya babu Abinda takeso da qauna sama dashi,
Zata iya sadaukarda rayuwarta data Bari wani abu ya samesa,
Hakama zata iya sadaukarda komai sbd shi sbd sunawa juna kallon uwa daya uba daya suke ko kawu baitaba sanin ba uwa daya uba dayane ya haifesuba duk da Shima bakowane yasan cewa bashine mahaifinsu ba musamman da kusan halayen amatu duk nasa ne na rashin hakuri ko kadan,
Acikin su hudu kuwa baasan waye yafi wani son kudi da abun duniyaba shiyasa ake musu laqabi da dangin tsamiya.
Arayuwarta tayi aiki kala dabam dabam zai Kai goma koma fiye Wanda takeyi yanxu a restaurant shine kusan na sha daya
Hakama kawu yayi sanaoin harya gaji Amma yaqi kudi shiyasa ya tattara ya watsar yakoma zaman saka ido da jiran Wanda tsautsayi zaisa ya tabasa yaga masifa tareda siyan radio yakoma Shan waqe waqen gargajiya wanda kowa naji ba halin mgn sbd Shima ubanda zai tanka dinyake nema Amma haka kowa ke dannewa sbd azauna lfy duk da gidan kullum cikin fada da hayaniya ake.
****
Qarar waqar sani sabulu ce ta _duniya wandon roba_ ta cika gidan ta karade wane daki da saqo na gidan sbd qarar muryar radio din da aka Kai qarshe gaba daya.
Hankalinsa kwance yake yana Shan waqarsa Yana sakace haqoransa da tsinke
Daka gansa zakasan babu Abinda ya damesa.
Dukkanin mutanen gidan 'dai 'dai suka ringa fitowa rayukansu a 'bace da takaicinsa na kullum Wanda inda sabo sun Saba da dabi'arsa ta tayardasu kullum da sautin radionsa da muryarsa Bata qasa
Gashi bamai ikon mgn 'yar gaban goshinsa da shaqiyin dansa suce ba Wanda ya isa
Amma rshin arzikinsu babu kalar Wanda basa fafatawa dashi wanda kallo daya zakayi musu kasan su din abin mamaki ne,
Rayuwarsu abin kallo ce sbd sudin abin mamakine.
Yana ganin mutanen gidan sunfara fitowa ya sake dauke Kai sama Yana jiran yaji wani Mai shafaffun Mai akai ne zaiyi mgn ya sauke Masa masifar dake cinsa ta takaicin iyami daya kwana dashi na biya Masa bashin dabaiyi niyar biyaba yanzu da kudinda yaci burin canza radio dashi na AMATULLAH da USI.
Cikin bacci qarar radio din ke shigarta Yana damunta,
Juya kwanciyarta tayi tana toshe kunnuwanta da pillow Amma
Sam qarar Bata daina shiga kunnuwanta ba.
Tsoki tasaki ahankali tana cewa'
Kawuuuu.
Saidata sake rintsawa ta juya kwanciyarta tsawon minti goma Amma Sam baccin ya gagara sbd qarar radio din dole ta yaye lullubinta ta miqe zaune tana miqa tana cewa'
Allah yasa yanda natashi yau cikin qoshin lfy yasa yau ranar sa'atace,
Allah yasa yauma na hadu da irin hajiyar Dana hadu da ita jiya nayi mata kukan tausayi tabani kudinda zanyo......
Kasa qarasawa tayi tareda zaro ido sbd USI data tuno
Da sauri ta dauki hularta dake kan katifarta ta sanya akai tareda zura silifas cikin sauri tana fitowa kota kan kawun batabi ba sbd daga yanayin waqar dayake sha a radio din ta fahimci yau ba sauqi a qule yake Wanda zai saukewa haushin yake nema shiyasa ba Wanda yace Masa uffan gudun masifa.
Bokiti ta dauka ta nufi fanfon dake can kusada qofar shigowa cikin gidan
Tana zuwa ta tararda wani bokitin yakusa cika
Ta gefen ido ta kalli maman junior dake tsaye alamar natane take jiran yacika hancinta na asalin yorbawa sai cika yakeyi Yana fidda iska sbd ita kullum a shirye take da duk inda masifa zata fado ta hauyi.
Shahada tayi ta rintse ido cikin ranta tace'
Bayina bane Allah ne ya qaddaro bazanbi layin jiraba
Ta sunkucesa da gudu ta fada bayin gidan daidai salamatu zata fito bayin tsoron ganin mutum a fujajan yayo ciki yasa ta zame ta Fadi qofar bayin
Aikuwa itakam amah Bata tsaya wata wata ba ta rufo bayin tana cewa'
Haka Allah yaso anty salamatu bayina bane Allah ne ya qaddaro zaki Fadi,
Kema maman junior yi hkr Allah ne ya qaddara da ruwanki zanyi wanka bayina bane.
Cikin wani irin tsananin baqin ciki da takaici salamatu ke kallon kanta zaune cikin ruwan qazantar qofar bayin bayan tayo wanka.,
Wani irin tiririn masifa zuciyarta keyi ta miqe amatuqar zuciye daidai isowar maman junior itama jikinta harwani mazarin masifa yakeyi tana cewa'
Wlh yau gidan Nan saidai kowa alaji landlord yakore agidan Nan Amma sai anyi balain da ko kawu fatihu duk masifarsa bazai hanani yiwa yarinyar Nan dukan tashi Kisha ruwan gishiri ba.
Kallonta salamatu tayi a harziqe tana cewa'
Saiki sameta cikin bayin tunda akanki aka Fara sauke masifa duniya
Kinzo kina qaramin haushi
Idan ke duka zaki mata wlh ni yau saina dauko motar Yan Banga a gidan Nan kowa yaci ubansa tunda Nagano kowane shege a gidan Nan ya rainani tunda anga Ina zaman kaina.
Kota kanta maman junior batabi ba tahau dukan qofar bayin tana fadin'
Yau wlh zakisan halina dabaki saniba tun kafin kizo duniya nasan rashin arziki bazakizo ki rainawa kowa hankaliba kullum komai kikayi kina Kiran sunan qaddara ne daga Allah wlh yau Ina roqan Allah yahadaki da qaddarar Nan da kike kirawa mutane bayan nagama Miki dukan tuwon qasa.
Alhaji mande dake jiyo yanda ake buga qofar bayin gidansa da qarfi ba arziki ya zubo babbar riga yafito ya zagayo gidan tun a soron gidan yake jiyo qarar radion kawu fatihu yaja tsokin takaici ko sallama baiyiba ya fado gidan Yana cewa'
Uban waye zamansa ya qare a gidan Nan yau yake gyangyademin qofar bayi??
Maman junior najin haka tayo gurinsa tana masifa tana zayyane Masa Abinda yafaru bakinta ta kumfar masifar customers dinta nata jiranta ruwan dafa musu doyane tazo diba.
Tanajinsu cikin bayin Amma ko ajikinta tayo wankan da sauri ta fito basuma ankaraba ta fada dakinta tahau shiri
cikin sauri ta shirya cikin doguwar riga baqa mara Fadi sosai ta sanya hijab iya wuyanta ash ta dauki Jakarta qarama ta rataya a wuya ta fice.
Gaban kawu tazo tana ciro qaramar wayarta jaka tace'
Kawu sannu da tashi.
Yi yayi kamar baijitaba Yana gyara zaman radionsa data ishi kowa gidan.
Qofar dakinsu ta kalla inda iyami ke zaune tana sakawa Koko sugar tace'
Iyami Ina kwana??
Lafiya kalau.''tace itama fuska a tsuke.
Murmushi tayi Wanda yasa kumatunta lotsawa haqoranta suka bayyana
Sbd tagano fadansune dai Wanda basa rabuwa dashi itada kawun Kuma ta tabbatarda akan kudi ne..
Dariya tayi tana juyawa tace'
Allah kasa muyi kudi kawu da iyami su daina fada.
Harta fito gidan alhaji mande da maman junior Basu daina fadaba sbd fadan tsakaninsu yakoma.
Titi ta nufa da sauri tana adduar samun kudinda zata bailing usi.
Tana isowa titin tasamu adaidaita ta tare ta fada cikin sauri tace'
Blue fox zaka kaini.
Tafiyar mintuna gomace takaisu gurin cikin sauri ta biyasa ta nufi harabar gurin dake tsareda security masu baqaqen uniform ta shiga
tana kallon wasu motoci biyu dasuka dauki hankalinta sbd tsananin kyawunsu da sheqin dasukeyi Dan har kanka kake gani ta jikinsu
ta kalli sama tace'
Ya Allah kasa muyi kudinda zamu mallaki irinsu nida usi mu Hana su kawu fada.
Ciki ta qarasa da sauri tana adduar Allah yasa yau tasamu sa'ar wani a cikin restaurant din.
Tana shiga ta nufi dakinsu na staffs din gurin inda suke sauya Kaya zuwa uniform din aikinsu.
Kayanta ta sauya izuwa uniform din aikin waitress dogon wando baqi da riga riga ash saita bar qaramin ash hijab dinta na iya wuya.
So takeyi ta tafi da wuri yau sbd gabaki daya hankalinta nakan usi.
Ta tabbatarda yanacan cikin wahala da damuwa duk da dai alqawarinsu ne bazasu taba saka kansu cikin damuwaba duk halinda zasu shiga sbd damuwa ciwo ce a ganinsu idan kasone zaka sakawa kanka damuwa a almarin duniya.
Amah!!!
Naam"ta karba tana juyowa daga jera drinks datakeyi a fridge.
Manager dinsune sanye cikin black Suit da medical glass a fuskarsa cikin tsuke fuska yace"
Ki hada black coffee dinda ake karbarwa _MD ZABEERA_ kullum ana kaimasa yau yazo da kansa zaisha anan,
And ki tabbatarda kinyisa yanda koyaushe ake hadawa kar asamu matsala amah.
Yaqe baki tayi da murmushin qarya tace'"
Bazaa samu matsalab inshallah manager.
Juyawa yayi ya fice Yana cewa' Allah yasa.
Kamar yanda tasan ana hadawa haka tafara hadawa cikin sauri sauri tana gama zubawa Yana sake shigowa yace"
Yawwa ki hada a tray ki Kai VIP 3 yagama Abinda zaiyi tafiya zaiyima.
Babu Abinda ta tsana kamar kai abinci a aikinnan nasu tafison abarta a hadawa suna dauka suna kaiwa sbd idan tana ganin masu kudi burinta sake hauhawa yakeyi.
Tsaki tasaki ta dauke baki ta dauka tana tafe tana qananun tsoki tana Harare harare.
VIP dinsu Yana can sama Saida tagama tsinewa manager ko kafin takai saman daukeda tray din.
Saida ta tsaya ta huta kafin ta nufi VIP 3 din tana isa security din dake gurin ya tura mata qofar gurin yana washe mata baki sbd mutuniyarsace ba ruwanta lafiyayyan takeaway take Masa idan zasu tashi shiyasa kowa gurin yake yinta Dan babu ruwanta bayarwa takeyi shiyasa lissafin nasu yanxu gurin kullum cikin rudarwa yake tunda aka dauketa aiki gurin.
Tana shiga ta tsaya cak tareda lumshe ido tasaki wata irin ajiyar zuciya afili tace'"
Hummmmm masu kudi turarensu ma qamshinsa na dabam ne,
Ya Allah ga amah da usi.
Bude ido tayi ahankali daidai wayarsa na daukar ringin batareda ya juyoba ya sanya dogon hannunsa da fatarsa ke sheqin hutu da haske ya dauki wayar tareda miqewa ya nufi window ya Dora wayar a kunne batareda yace komaiba.
Zare idanuwanta dake neman rufewa su suma tayi tana girgiza kanta ahankali tace'"
Ya Allah.
Table ta nufa ta ajiye tray din idanuwanta suka sauka kan wallet dinsa dake ajiye da kudi acike acikinta batasan lokacinda tayi saurin dire tray din ta dauki wallet din ta bude taba zaro ido tace"
Yau ranar sa'atace ya Allah nagode maka.
Kudin ta zaro gabaki daya tana musu kallon qurilla fuskarta cikeda farin ciki tace'
Kayi hakuri Dan balarabe Amma nafika buqatan kudin Nan.
Aje wallet din tayi ta juya da sauri cikin farin ciki tana damqe kudin ta fice tana sauri Dan karya gama waya ya juyo yaga ba kudinsa ya biyota yace kudinsa zai qwata itakuma bazata bayarba.
Ta glass din window dayake tsaye yake kallonta cikeda tsananin mamaki da qyamar halinta daya sanyashi kasa juyowa akaro na farko dayaga mace da irin wannan halin mafi Muni agaresa Wanda hakan yasahi kashe wayar wadda tunda ya daga baice komai sai sauraren zancen da ake Masa tacan Wanda kusan hakan dabi'arsa ce.
#mamuh#
#MIN QALB❤️
Mamuhgee
ZAFAFA BIAYAR
SIRADIN RAYUWA
safiyya huguma
MIN QALB
mamuhgee
YANKAN BAYA
billyn Abdul
KIBIYAR AJALI
Miss xoxo
ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA
hafsat rano
Pay @09033181070
Or 09032345899
[01/06, 8:50 AM] __*MAMUHGEE*__♥️🌹: *_MIN QALB 4_*
_Mamuhgee_
#ZAFAFA BIYAR#PAY@+234 903 234 5899 OR 09033181070
Tana fitowa dakin ta washe baki tareda daga kudin ta kallesu tana fitar fuskarta dasu tace"
Hmmm amah zakiyi kudi ki mallaki uwayen wainnan kiyi rayuwa yanda kikeso ki juya Wanda kikeso hhhh.
Kallon hashimu me tsaron qofar tayi tareda sakar Masa murmushin iko na nuna Masa itace agabansa tunda ita ke riqeda kudi,
Sake juyasu tayi tareda zaro Yan naira dubu 'daya 'daya guda uku tabasa tana cewa'"
Kana fadar Abinda yafaru yanxu to sunan aurenka matacce dan wlh sainaje nasa anhana.
Damqar kudin yayi da sauri Yana turawa cikin aljihu tareda washe bakinsa har iyaka yace"
Haba Hajiya amah kema kinsan hakan bazaitaba faruwaba,
Ko bomb akamin belt dashi bazan fadaba.
Dariya tasaki cikin girmama alamari da mutunci irin na kudi Wanda yasa hashimu fadar haka akan dubu uku kacal ma,
Sake kallonsu tayi tana dagawa tace"
Allah sarki kudi,
Kudi muna sonku
Bama gane kowane yare sai