Showing 45001 words to 48000 words out of 58156 words
nama abaki suna ta hirarsu da dariya.
Hauwa'u ta ce, "lallai bilki mai shiga tsakanin miji da mata yana tareda kunya.
Na ce, "wlhy kuwa hauwa'u, hannunta naja muka nufi d'akin sopy dan mugano muku halin da fareeda take ciki.
Saman gado muka tarar da ita, tana faman jan tsaki, na jin jina kai ina fad'in lallai wannan bata gajiba, dan na kula wani abu take k'ara shiryawa.
Hauwa'u ta ce, " 'yar wahala, ni kinga mutafi muma wajan mazajenmu karmu lalace anan.
WASHE GARI
sopy ta had'a break tsaf, ta gara gidan, saidai yau na kula kamar akwai abinda take k'ullawa, dan sai murmushi takeyi, tana shiga wanka fareeda ta fito tanufi kichin d'in.
Sopy suka gama shirinsu tsaf da uncle G! suka fito sunata zabga k'amshi, fareeda dake zaune afalon tun d'azu ta gaida uncle G!, suka gaisa da sopy, sannan suka nufi dini domin cin abinci, farida kuma saita nufi d'aki waizata d'akko abu.
Sopy tagama had'ama uncle G! abinci ta tura gabansa, yako ja ya hauci, sopy tatattare kulolin datai amfani dasu tanufi kichin, nayi dariya, dan nakula sopy ta kwashe abincin sune itada uncle G! acikin wata kula daban, saita bar wani a d'ayar kular, tayi alamu kamar an d'iba.
Tana dawowa ta tarar fareeda tafito, sai dai, sai kallon uncle G! take dayake cin abincinsa cikin kwanciyar han kali harma yana lumshe idanu.
Taja kula itama tazu, ko kallon inda take sopy batayiba taja abincin ta ta hauci.
Fareeda dai saicin abinci take tana matse idanu, gashi babu damar magana, tunda masu gidan basuce komaiba, saima hirarsu sukeyi, sai dai zuciyarta sai tunani take akan ya akayi basuji d'anbanzan sukarin data zuba a aciki abincin ba.
Da haka suka gama, uncle G! yafita, sopy ma tatafi d'akinsa dan ta gyara, fareeda taja abincin da uncle G! yarage taci, saitaji lafiyarshi lau, tarike kuguπ― tana fad'in wato matar nan boye musu abinci tayi kenan??.
Sopy dake lab'e tana kallonta tayi murmushi kawai.
Aka kwan kwasa k'ofa da sauri fareeda taje tabud'e azatonta uncle G! ne, amma saitaga su aunty Nafisa, da aunty hauwa'u, da aunty zainab yayarta, dakuma aunty Asiya matar uncle kabeer, cikin mamaki suke kallonta, itama dai cikin tsoro da fargaba take kallonsu.
Tofa masu karatu, koya zata kayane kuma, kukasance taredani danjin amsar tambayarku..........................βπ»
πBilyπ
ππMrs Abdus'salamπππ
πI LOVE YOU MY FAN'sππ
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 20~November~2016
π·πΉNI DA AMINIYATA!!!πΉπ·
NA BILKISA IBRAHIMπ
πΆπΈ4β£9β£πΈπΆ
..........Aunty zainab ta wankama fareeda mari, Wanda yasata zubewa awajan dafe da kumatu, cigaba tayi da dukanta tamkar uwarta, dak'yar su aunty Nafisa suka rik'eta, cikin matuk'ar b'acin rai aunty zainab ta ce, "kubarni naci uban wannan mara mutuncin, ita hartanada k'afafun zuwa gidan safiyya, saboda batada mutunci.
Sopy tafito da sauri dan jin hayaniya, yayunta tagani tsai tsaye da alama babu lafiya.
Aunty zainab ta tako har zuwa inda sopy take, tana fad'in wato sopy har kin farka daga magagin cin amana da yaudara irin na fareeda ko, tanuna fareeda da jini yake zuba ta hanci saboda dukan hancinta da aunty zainab d'in tayi, ta ce, "waccan dakike gani bom ce data tarwatsa rayuwarki abaya, kuma inada tabbacin yanzuma zata tarwatsa sabuwar rayuwar dakika kasance aciki, dan ita kaskace rab'u mai jini, data tsotse jinin jikinki saita barki da zallar ruwa, takama kafad'ar sopy ta girgiza tana kuka tana fad'in haba safiyya miyasa kika amince da wadda taci amanarki, miyasa kika amince da wadda tarabu da iyayenta akan d'ana miji, itace sanadin kamuwar mahaifinmu da ciyo mai muni, itace ta haddasa bak'in ciki a family namu wanda bazamu tab'a mantawa dashiba, itace tasa mutane sukema gidanmu kallon masu k'arancin tarbiya, miyasa kika yarda mak'iyyarki wadda bata sonki dan ALLAH, Aunty zainab ta durkushe awajen tana wani irin kuka mai ban tausayi, itama sopyn saita take mata baya, suka rungume juna suna kuka.
Suma sauran sai matsar hawaye sukeyi, fareeda kam tana gefe tana jiyyar kanta, ahaka uncle G! yashigo yasamesu, ya tsaya turus yana kallonsu da mamaki.
Dak'yar ya iya furta tambayar waye ya mutu????.
Gaba d'ayansu suka d'ago kai suna kallonsa, sopy tazo da gudu ta shige jikinsa, ya rungemeta tsam yana lallashinta, bayan kamar minti biyar ya cirota daga jikinsa, ya ce, "Sopy miya farune wai??, ko wanine ya rasu??.
Sopy ta girgiza kai tana hawaye, yasa hannu yana share mata hawayen yana fad'in kukan ya isa haka, fad'amin miyake faruwa??.
Sopy ta nuna masa fareeda da hannu, fuska duk jini da alamun duka, kunsandai farin mutim, koyaya aka tab'ashi sai yanuna.
Uncle G! yadawo da kallonsa wajen su aunty zainab, har yanzu kuka takeyi, aunty Nafisa taje ta d'agota ta rungume, tana bata hak'uri.
Tsawon minti shabiyar, kowa ya nutsu, suna zazzaune a falo, harma Sopy tayi k'arfin halin kawo musu ruwa, fareeda kuma ta wanko fuskarta.
Uncle G! yay musu sallama suka amsa, sannan yad'ora da tambayar abinda yafaru.
Aunty Nafisa ce tasanar masa da komai, ta d'ora dafad'in, mukammu abin yabamu mamaki, dan bamuyi tunanin ganin fareeda ananba, dukda dai agida ana nemanta, saka makon mijinta yaje har gida yafad'ama iyayenmu cewa yasaketa har saki uku.
Uncle G! yaja numfashi sanna ya d'ora da fad'a musu yanda ya samo fareeda har zuwanta gidan da zamanta, dakuma hukuncin dasuka yanke na maidata gida, amma sopy ta ce, "tana jin tsoron hakan, dan bataso akasa fahimtarta, yaci gaba da fad"in amma ina mai baku hak'uri akan kubar fareeda domin tayi nadamar abinda ta aikata, Sopy ta ce, "azuciyarta zadai tayi nan gaba, dan mai hali baya canja halinsa uncle.
Uncle G! ya ce, "kutan bayi Safiyya tunda fareeda tazo gidannan bata tab'a aikata mana wani abu wanda bai daceba, dan haka ina rok'onku kuma ku yafe mata, kamar yanda Safiyya ta yafe mata, inada tabbacin hakan zai taimaka mata wajen k'ara samun gyaruwar halayenta, ku kuma zamo mana 'yan jagora wajen nema mata gafara gasu baba da mama.
Aunty zainab ta ce, "ban katsekaba yaya youseef, amma nasan har yanzu fareeda batayi nadama ba, wlhy nasan tana nan tana k'ulla wasu sababbin makirce2n nata, nasan fareeda sosai, tun muna k'anana nake fuskantar mugun halinta, nasan fareeda tafi shak'uwa da Sopy fiye da kowa acikinmu, amma nafi Sopy sanin halin fareeda, dan Sopy ta yarda da fareeda, kuma batada yawan saka idanu akan d'abi'un fareedar.
Aunty Nafisa ta ce, "A'a, zainab tunda ya ce, "tayi nadama bakuma ta tab'a aikata wani abu dazai shiga tsakaninsuba to yakamata muyafe mata, mukuma yimata addu'ar k'ara samun shiriya.
Nandai sukaita rok'on aunty zainab har ta sakko, ta yafema fareeda, dan saida fareedar ta gurfana agabansu tana neman afuwa, Na ce, "shegiya kamar har zuciyarta.
Yaudai anan suka wuni, Sopy tayi musu abinci mai dad'i da gamsarwa, sukasha hirarsu ta yaushe gamo, sopy ta ce, "aunty Asiya yaushe zaki haihu?, Aunty Asiya tayi murmushi ta ce, "sai watan gobe Safiyya.
Sopy ta marairaice fuska ta ce, "dan ALLAH ki lallab'i uncle kabeer yabar uncle yakaini naga su inna, dan ya ce, "wai saikin haihu zan fara fita.
Aunty hauwa'u ta ce, "A'a bakin koma makarantaba??, Sopy ta zumb'uro baki gaba tana fad'in, to makarantar da ga ita ina nake zuwa,?.
Dariya sosai tabasu, Aunty zainab ta ce, "aii ko autar inna saidai kiyi hak'uri, dan muma duk haka akaimana, ta ce, "tab nikam wlhy nagaji, aii zama guri d'aya tsautsayi inji kifi, suka tun tsure da dariya suna tsokanarta.
Fareeda kuwa tana d'aki ta kume kanta, dan taji zafin dukan, zuciyarta ta ce, "karki damu fareeda dama abu mai daraja ba'a samunshi abanza, sai ansha wahala, inda zaki bini daki2 dana fad'a miki hanyoyin dazakibi ki mallaki uncle G!.
Na ce, "hummm naga wannan 'yar akuyar har yanzu bata san inda duniya ta nufaba.
Gani nai tana zuba murmushi, alamun karatun da zuciyar tata takaranta mata yayi mata dad'i, kuma ta karb'eshi hannu bibiyu.
Lallai idan zaka gina ramin mugunta tofa ka ginashi gajere, dan idan aka samu kus kure tofa kaizaka fad'a ciki.
saida akayi la'asar sannan suka tafi, tareda alkairi mai yawa daga uncle G!.
Bayan tafiyarsu Sopy ta shiga d'akin uncle G! Yana zaune yana duba wasu books, ta zauna gefensa, ya d'ago manyan idanunsa farare tas yana kallonta, tayi masa sassanyan murmushi, ya kanne mata ido d'aya shima yana mayar mata da murtanin murmushin nata.
Ya rufe littafin yajuyo gareta, ta ce, "hubbina ka daina karatunne??, ya jawota jikinsa yana fad'in ai idan kina guri sopyna banida lokacin komai sai naki, kin zamomin magana d'isun da kan kama zuciyata da matuk'ar sauri idan kika kusantota, idan kuma bak'ya kusa tofa zuciyata tana tareda ke, dan gangar jikina kaiwai kike barmini, yakama yatsun hannunta yana wasa dasu, yak'ara kashe murya ya ce, "Sopyna yaushe zaki bani magajinane??.
Sopy tasaka hannu ta rufe fuska dan kunyaπ.................βπ»
πBilyπ
ππMrs Abdus'salamπππ
π I LOVE YOU MY FAN'sππ
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 20~November~2016
π·πΉNI DA AMINIYATA!!!πΉπ·
NA BILKISA IBRAHIMπ
πΆπΈ5β£0β£πΈπΆ
...........Uncle G! Yay murmushi yana fad'in Sopy sarkin kunya, daga tambayar baby sai aji kunya..
Tayi k'ok'arin mik'ewa zata gudu uncle G! yakuma matseta, ta ce, hubbina aikifa zanje nayi, yaja hancinta yana fad'in ainanma aikin kikeyi, ta ce, "aikin mi nakeyi anan?, ya ce, "na bama youseef farin ciki mana.
Sopy tayi murmushi, ta ce, "uncle wai yaushe zamuje Gurum??.
ya ce, "kinaso mujene??.
ta ce, "emana inaso naje na gaida su gwaggona.
Yay murmushi to shikenan zamuje, amma kibari sainan gaba, dan su aunty hafsat sunce zasuzo ranar juma'a.
Cikin matuk'ar farin ciki ta k'an k'ameshi, ta ce, uncle dgsk kakeyi dan ALLAH?.
YA CE, dgsk Sopyna, sunce zasuzo suyimana kwana biyu, ta ce, harda Aysha?, ya ce, eh harda ita.
Kai wlhy naji dad'i sosai, tatashi tana fad'in bari kaga naje nafara shiri.
Ya bita da kallo yana murmushi, akullum tamkar k'ara masa son Sopy akeyi, yakanji kamar babu mata aduniya sai ita kad'ai, komai na yarinyar abin sone.
^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
Akwana atashi babu wuya gurun mai duka, komai yana tafiya yanda akeso, Sopy tana samun farin ciki awajen mijinta, takanji babu yashi a rayuwarta.
To shima a b'anfarensa yakanji babu tankar Safiyyar, kullum burubsu su farantawa juba, takan tsara masa abinci mai gam sarwa dasaka nishad'i, kullum tana cikin kwalliya ta d'aukar hankali, ta bad'e gidanta da jikinta da k'amshi, kullum burunta tayaya zata farantawa mijinta.
Bata wasa da samo hanyoyin rik'e miji, dan haka bily ta sakata a groups masu dama, takan tsinci abubuwan k'aruwa acikin HAUSA NOVELs masu yawa, dan kowa da irin baiwar rubutun da ALLAH yabashi, idan dare yayi su kashe junansu da soyayya itada HUBBIN ta.
Uncle G! yana matuk'ar alfahari da ita.
Matsala d'aya take fuskanta, itace fareeda, dan yanzu fareedar tafito dawasu salo2 na rainin hankali, sai lokacin data fuskanci sun kusa dawowa saita ci kwalliya ta zauna a tsakar gida, da sun dawo itace zata bud'e musu get tana kwar kwasa, suna shigowa falo zatayi saurin kawoma uncle G! ruwa ko lemo, da daddare kuwa tana nane dasu a falo, har saitaga sun shiga sannan take tashi, takan k'ir k'iri dafa wani abu takawoma uncle G! wai yaci, idan suna hira, taringa wata kwar kwasa da kwantar da murya kamar tana kusada mijinta,ko sopy ta gwaleta tofa bata nuna jin haushinta, wani rainin hankali kuma data d'auka shine datayi isha'i saitayi shiri cikin kayan barci tazo ta zauna falo suna hira.
Wannan lamari yana k'ona zuciyar Safiyya.
Yauma suna falo suna hira, uncle G! yana kwance saman doguwar kujera, yayinda sopy take zaune a k'asa saitin kansa tana cin tuffa (Apple), fareeda kuma tana saman kujera tana satar kallon uncle G!, wandashi bama ta isheshi kalloba, sopy tana kula da ita.
Zuwa can sopy ta ce, "wayyo ALLAH hubbina??, uncle G! ya juyo da sauri yana kallonta, ya ce, "ya akayi Sopyna?, cikin shagwab'a ta ce, "jinayi kaina ya sara.
Ya tashi zaune yana fad'in zona yimiki kamu, dan bana son kisha magani, saboda gudun ganganci, bansaniba ko nayi ajiyar baby.
Sopy ta mike da nufin zama kusa dashi, amma saiya jawota saman cinyarsa, ta ce, "ngd hubbina.
Yayi murmushi yana fad'in wannan aikinane, addu'a yafara yi yana tofa mata, bayan ya gama tawani kanne masa ido d'aya tareda d'aga masa gira.
Aii sai jikin mutumin naku yasaki, kwata2 ya manta da wata fareeda afalon, saiya had'e bakinsa da nata, yashiga sumba tarta cikin nuna kwarewa, Sopy saita bada kai bori yahau, sunkai tsawon lokaci suna abu d'aya, zuwa can yashiga shafata.
Wani kududun bak'in ciki yatokare zuciya fareeda, ta had"iye wani mugun yawu wanda yasakata sark'ewa tafara tari.
Sai a sanna uncle G! yatuna akwai wata halitta fareeda a falon, suduka suka d'ago suna kallonta, sopy tayi wani murmushi mugunta, tad'aga yatsun hannunta biyu tama fareeda sorry, cikin wani murmushin rainin hankali ta ce, "sorry fareedana, munata soyayya agabanki, kinsan hubbina ya iya mantar dani duniyar dana ke ciki, wlhy nama manta kinanan, ta sumbaci hannun uncle G! sukaima juna murmushi.
Jin kalamun sopy na rainin wayo sai suka saka zuciyar fareeda kumburo wa, jita ke mar zata fashe, har fuskarta saida ta nuna alamun b'acinrai.
Sopy ta ce, "hubbina?
Uncle G' ya ce, "na'am sopyna.
Ta ce, "yakamata kasiyoma fareeda tv sai asaka mata a d'akina, dan bai kamata tana zama damu a falo muna tayar mata da hankaliba, kasan gwauro bai iya shiga matsalaba, gashi kuma babu mai taimaka mataππ.
Uncle G! ya sumbaci bakin sopy ya ce, "gsky ne sopyna, insha ALLAHU zanyi k'ok'arin hakan, dan nima nakula tana shiga damuwa da takura.
Fareeda tak'ara kumewa dajin kalamun sopy da uncle G!, ta kulama sun raina mata hankali, da sauri tatashi tana hawaye ta shige d'akin sopy.
Sopy ta bita da kallo tana 'yar dariya, ta mik'e tana fad'in hubbina bari najiyo miye damuwar "AMINIYATA!!!!!;".
Uncle G yabita da kallo yana murmushi, yasani sarai bak'ak'en magan ganu sopyn tagawa fareeda.
A can kuwa sopy tana isa tabud'e d'akin ta shiga, agado ta tarar da fareeda tana kuka, sopy tad'an tab'e baki sannan ta k'arasa gaban gadon tana tafa hannuwa, ta ce, "fareeda kenan nakula ke har yanzu d'aukata kike amatsayin safiyya sakarai, fareeda!! Tabas abaya kinyi nasarar kwace Abdul daga hannuna, to ki d'auka awanna lokacin kece kikayi winning d'in game d'in, nikuma nasamu game over.
Amma saidaifa awannan karon ta canja zani, domin nima da shirina nazo fagen famar, kisa azuciyarki uncle G! nawane nikad'ai, babu wata kucakar mace data isa naraba son youseef da ita, karki d'auka wani ban k'aro k'irjinki da saka kayan barci kizauna agabansa zai ja hankalinsa a kanki, 'yammatan dasuka fiki ilimi da wayewa ma sunyi abinda yafi haka amma basuci nasaraba.
To kema inaso ki d'auka aranki bazaki tab'a yin nasaraba, tuni nasan kece kike zubamin gshiri, yaji, sukari acikin abinci, fareeda son gsky babu abinda yake rusashi, nida uncle G! son gsky mukema juna bana sha'awa ba, dan haka ki daina wahalar da kanki wajen hangen zaki iya rusa wannan soyayyar, bare harki samu damar mallakar mijina.
Sopy tayi wata 'yar dariyar k'eta, ta ce, "lallai yau nayarda da batun aunty zainab, datace ke kaskace rab'u mai jini, kuma ke bom ce, tofa saidai ki d'auka awannan karon remote d'in bom d'inki yana hannuna, idan nagadama saina danna ki tarwatse, dan haka ki dawo da han kalinki jikinki, tun kafin kiyi asararsa, ki daina biyema shed'aniyar zuciyarki datake d'ora miki karatun da babu fassara, inko ba hakaba kina gab dashiga makarantar dana sani.
Tana kaiwa nan tafice abinta.
Fareeda tana kwance kamar gunki, zuciyarta cike da mamakin kalam safiyya, wai yaushe sopyn ta waye?, ya akayima tagano sirrikan zuciyarta haka?, lallai yau sopy tagaya mata magan ganu masu ciwon gsk, irin wanda babu wani mahaluki daya tab'a gaya mata kwatan kwacinsu, ta dun k'ule hannu ta naushi iska, da sauri nafito ina tuntsura dariyaπππππ, dan karta maujeni nima, tabar mijina da jinya.
D'akin uncle G! na nufa, amma saina tarar sun rufe k'ofa, dan haka na nufi hanyar fita, dan bazan koma wajen fareeda 'yar mahakaciya ba ta bibbigeni abanza, gobe nakasa kawo muku rahotoππ......................βπ»
Assalamu alaikum, ina mik'o d'umbin gaisuwa ga dandazon makaranta littafin ""NI DA AMINIYATA!!!,"" ina muku fatan alkairi a duk inda kuke, ina kuma gdy da k'aunar da kuke nuna mini,, ALLAH yabarmu tare, ya had'amu a ALJANNARSA baki d'aya.
ππ»acigaba da gashiπ!!!!!!!!!!!!!!!!...ππ»
πBilyπ
ππMrs Abdus'salamπππ
πI LOVE YOU MY FAN'sππ
[12/19, 7:26 PM] mrs bilkisu: 21~November~2016
π·πΉNI DA AMINIYATA!!!πΉπ·
NA BILKISA IBRAHIMπ
πΆπΈ5β£1β£πΈπΆ
...........WASHE GARI. Fareeda kasa fitowa tayi, har sukayi break bata fitoba, Uncle G! ya ce, "Sopy yau kuwa lafiya naga fareeda bata fitoba??.
Sopy tad'an murmusa tareda fad'in lafiyarta k'alau, k'ila ta k'oshine.
Uncle G! yad'an tsura mata idanuwa, domin son gano wani abu, amma sai Sopy ta kauda kai tana dariya, shima saiyayi dariyar ya ce, "miya baki dariya sopyna?.
Sopy ta ce, "kaine kabani dariya, dan naga ka kafeni da kallo kamar