Showing 186001 words to 189000 words out of 195514 words
ta shafa maka lalle ne uban yan sharri".
"Eh ai silar Kane kaita nufo dashi kasa ta ya'ba min ni meye hadina dashi nine ango ko kai fad'a min"?.
Kallon sa sosai Ajeeb yai sai kuma yasa dariya yana cewa "dama yau ba muyi ba tun safe na lura dakai kana takala ta fad'a ina share ka domin ni ango ne bazan biyewa tuzuru irinka ba shiyasa yanzu daga laifin daba nawa ba kake neman d'ora min dan ni akazo shafawa ya sameka a tunani na ai duk daya ne Asad babu bambanci tsakani na dakai kaine muke uwa daya uban daya dukkan yarda ta Asad tana gareka na amince dakai fiye da yadda kake tunani banida wani wanda ya kaika balle har na kalleshi naji dad'i a raina inai maka wani irin so wanda baki bazai iya musaltashi ba kuma zanci gaba da sonka matukar raina indai ina numfashi,.
'Dan dakatawa yai tare dayin shiru yana kallon Asad sai kuma ya ri'ko hannun sa batare da ya sake cewa komai ba suka zauna a bakin gado hannunsa na cikin nasa ya ri'ke sosai yaci gaba.
"Asad dan Allah komai zai faru gobe karka tada hankalinka ka d'auka cewa kaddara ce kuma kada kayi ba'kin ciki nasara tana tare dakai duk da zakaga abubuwa sa'banin fahimtar ka a matsayina na d'an uwanka ina gargad'in ka cewa kabi gaskiya Asad ka tsaya akan daidai dan Allah Asad gobe karka tada husuma a gidan nan ina fata zakayi min wannan alfarmar"? Ajeeb ya karasa maganar da serious face yana kallon Asad wanda shima shi yake kallo duk jikinsa ya saki da maganganun Ajeeb d'in saiya samu kansa cikin fargaba da shiga tunani iri iri meya faru meyasa Ajeeb yace masa haka a irin wannan lokacin shidai ya a iya sanin sa tunda suke dashi bai ta'ba fad'a masa magana irin haka ba sai yau meyasa? Katse masa tunani Ajeeb yai.
"Asad baka ce komai ba please 🗣️say something ️".
Kasa cewa komai Asad yai sai kallon Ajeeb da yake yana sake jujjuya maganar daya gama fad'a yanzu ya kasa gane me Ajeeb ke nufi ina ya dosa to meya kawo wadannan maganganun? Girgiza shi Ajeeb yai yana cewa "Asad are u ok? Kana lafiya kuwa"?.
Kai ya d'aga masa da'kyar yace "eh" kallon sa sosai Ajeeb yake yace "to amma ina ta magana kayi shiru kamar kurma meyasa naga ka canza yanayi daga yaune fa na final zaman karshe a bedroom tare ni dakai da sunan kwana saidai dan nishad'i shikenan gobe iwar haka bazaka ganni ba koda kud'i inacan kana nan".
Tabdijan wai tashin hankali wanda ba'a sa masa rana Asad ji yayi hankalin sa ya 'kara mugun tashi fiye da da hajijiya na d'ibansa kansa har ciwo yake ya d'au zafi sosai yake kallon Ajeeb da shikam harkar gabansa kawai yake kamar dai bai fad'i komai ba ganin zai sake magana yasa Asad cewa.
"Please Ajeeb maganar ta isa haka dan Allah na fahimce ka kayi shiru basai ka sake cewa komai ba" murmushi Ajeeb yai "shikenan Asad ni kwanciya ma zanyi na shiga kwana duk jikina ciwo yake good night" yana fadin haka ya haye gado tare da jan bargo Asad na zaune yai shiru cikin dagulewar lissafi ya kasa gane inda maganganun Ajeeb suka dosa balle ya fahimci abinda yake nufi saidai ya jira zuwa asuba idan sun dawo daga masallaci ya sake tambayarsa maybe lokacin ya sake dawowa cikin nutsuwar shi dan gani yake kamar baya cikin hayyacinsa yake masa magana d'azu, jin saukar numfashinsa yasa shi kallonsa har bacci ya d'auke shi fuskarsa ya zubawa ido ya kasa daukewa haka kawai ya gaza bambance wanne irin yanayi ya shiga meke damunsa haka ya 'bata lokaci a zaune yana tunane tunane iri iri har kusan karfe uku na dare ya kasa runtsawa karshe sai mi'kewa yai yayo alwala yazo ya fara nafilfilu bayan ya idarma zama yai yaci gaba dayi a gurin har akai kiran farko akai assalatu sannan ya tashi Ajeeb yayo alwala suka wuce masallaci bayan an idar tare suka dawo idanuwan Asad sunyi ja sakamakon rashin barcin da baiyi ba saboda baya son yawan tambaya yasa suna dawowa ya fad'a gado wanda Ajeeb ya kwanta a kusa dashi yana ja musu bedsheet.
Har gari ya waye sosai rana ta fito Ajeeb ya tashi haryai wanka amma Asad baya ko motsi bai tashe shiba bayan ya shirya ya fita zuwa 'bangaren mai martaba da gurin Mami dan ya gaishe dasu.
Kusan sha biyu na rana shiru Asad bai farka ba dawowar Ajeeb yazo yana d'an babbuga filon dayai matashin kai dashi yana kiran sunansa da'kyar Asad ya bud'e idonsa yayi ja ya kalli Ajeeb daya dafa kafarsa daya akan bed din daya tana kasan carpet da murya barci yace "lafiya meya faru"? Zama Ajeeb yai yana aje masa jakan dake hannunsa yace "lafiya kawai naga karfe sha biyu tayi kuma baka tashi ba kamar ka manta yau daurin aurena dana Ameer shiyasa na tashe ka" Asad baice komai ba yake shirin komawa ya kwanta cikin magiya Ajeeb yace.
"Please karka koma dan Allah"👏.
Dafe kai Asad yai jin har lokacin bai daina masa ciwo ba kuma rashin barcin da bai samu yayi da dare bane yasa gashi Ajeeb ya hana shi komawa yasan duk abinda zai fad'a masa yanzu bazai fahimce ba.
"Asad ka tashi man dan Allah yaufa ranar d'an uwanka Ajeeb ce ya kamata ka tashi ka taya ni d'iban nishad'i yau zanyi mata" Ajeeb ya karasa maganar yana murmushi kallon sa Asad yai kamar zaice wani abu ganin ya bud'a baki Ajeeb ya girgiza kai yana cewa "ga kaya nan wanda zaka sa idan zamuje wajen daurin auren ankon mune duka su Ameer da Annur duk iri d'aya ne baza'a bambance angon ba a cikin mu musamman nida kai tunda fuskan mu iri d'aya ka shirya a hankali akwai sauran lokaci sai 'karfe uku da rabi zamu tafi" kai Asad ya d'aga baiyi magana ba yayin da Ajeeb ya juya yana fita komawa Asad yai yana sake sabuwar kwanciya tare da sake jan bargo ya rufe idonsa dan gaskiya indai bai rama barcin nan ba tofa bazai iya samun nutsuwa ba a yau balle har yaje wani d'aurin aure.
'Karfe biyu daidai Ajeeb yazo ya matsa masa lamba dole ba yadda ya iya haka ya ha'kura ya tashi gashi ko breakfast bai ba amma wannan ba shine a gabansaba ba shine matsalar saba wanka kawai yayi ya shirya cikin manyan kayan hausawa shakwara da jamfa ga hula wai wai wai tabdijan sai kun ganshi FANS🤡 subahanallahi akwai dirarriyar halitta mai kyau anan abun baya fad'uwa fitowa yai sai nad'e babbar rigar yake ya wurga tanan ya jawota nan ya rasa yadda zaiyi yana shigowa falon Mami Aunty Fadilah ta kama dariya tana kallon sa cikin tsokana tace.
"Asad ya haka? Innalillahi ji yadda kake tu'kuikuye kayan zasuyi squeezing tun daga nan dan Allah kalli yadda ka wani soke hula a gaban goshi baka saba sawa bane ko kuma duk cikin style d'in ne😂"?.
Had'e rai yai yana d'an karkata kallonsa gurin Mami dake kallon sa itama tana murmushi tace "Asad kayi kyau sosai haka Fadilatinka ke nufi taga maradar kyau ta yaba" rufe baki Fadilah tai tana dariya tace "waye yaga madarar kyan? Uhm uhm nikam ban yaba ba jira nake ango Ajeeb ya shigo na saki gud'ar ban girma nai masa kirari yau ai bata Asad ake ba ana batun masu aure wayake sako tuzurai 😂" dariya Mami tai tana cewa "ayya saurin me kike lokaci ne shima wata rana zaiyi".
Shigowa Ajeeb yai shima ya d'au wankan ala tsine uwar me 'karya🙉 sai tashin 'kamshi yake fuskarsa da wadataccen murmushi ai kamar yadda Fadilah ta fad'a zazzafar gud'a ta sakar masa a satin kunne tana masa wata daddad'ar wa'kar ango cikin harshen larabci sauran suna tafi da salon wa'kar suna amsa mata Mami tace.
"Fadilah irin wannan bege haka"? Dariya aunty Fadilah tai tana nuna Ajeeb tace "ai dole mu kod'a ango mu yabeshi dan tuzurai suji haushi🤣 ko suma sa dage suyi" had'e rai Asad yai dan yasan dashi take kamar bazai tanka ba sai kuma yace "Aunty Fadilaty kin ganni nan ni Asad babu aure yanzu a tsarina bana tunani aikina kad'ai na sani kuma koda ma ace zanyi auren gaskiya ba kwana kusa ba me nisan kwana ne zai gani don sai nayi ritaya🙊" zaro ido Fadilaty tai "sai kayi ritaya kuma Asad subahanallahi gaskiya bamu amince ba sannan ai ka zama tsoro wazai aure ka"?.
"Mai sona"🙅 duk tsufa na ko na zama kwallafiya ne".
"Tabd'i wacce budurwar ce zata yarda ta aureka ka zama kwallafiya ka fara gigi".
"No aini ba irin wannan tsufan zanyi ba".
"Oh da gaske taya ka sani"? "Na sani mana alamar 'karfi"? Ya fad'a yana kallon ta rufe baki Fadilah tai tana dariya tace "tana ga mai 'kiba ai shikenan Allah yaja kwanan mu zuwa lokacin bikin tsofaffi ko ba haka ba" shiru Asad yai Ajeeb da suke tattaunawa da Mami daidai sun gama ya juyo yana cewa "Asad muje ko lokaci yayi" yana rufe baki kiran mai martaba ya shigo wayarsa da sauri ya d'aga cikin ladabi yace "hello Abba kayi hakuri gamu nan" sauke wayar yai yana kallon Asad yace "mu tafi Mami auntis mun tafi ku mana addu'ar dawowa lafiya".
"Ok Ajeeb sai kun dawo Allah ya tsare hanya ya sanya alkhairi" Amin yace suna fita daga part d'in Mami gabadaya gidan fal yake ya cika dam ta ko'ina da mutane manyan ba'ki masu mu'kami su hud'un duka mota daya suka shiga sakamakon Shaukiyyah da Ameer su na gida ne dukka sai aka bari a d'aura a guri d'aya idan anje na Ajeeb d'in.
Alhamdulillah Malam Habu ma yasha kwalliyar tsadaddiyar shaddarsa mai kyau sosai lokacin da suka je har an d'aura auren Aisha da Safwan sai su ake jira a d'aura na Amatun suna zuwa babu 6ata lokaci aka fara abubuwa da addu'o'i an d'aura auren Aliyu Alhassan Aliyudeen akan sadaki wanda ake neman albarkar aure uhmm Allah yayi Shaukiyyah Alhussain Aliyudeen yau buri ya cika itama an d'aura musu aure da Aliyu Alhassan Aliyudeen (Ameer) akan sadaki kai tsaya da wancan.
Bayan an kammala komai mai martaba suka gaisa da Malam Habu yayi masa godiya cikin mutuntawa sannan su Ajeeb suka shiga cikin gidansu Amatu gaisuwar iyaye kowa kallonsu yake su hud'u kaya iri d'aya biyu kama d'aya biyu ma kama d'aya 'ya'yan sarkin gari guda.
Sai bayan karfe biyar suka koma gida Asad yayi mugun gajiya ko part din Mami bai samu ya koma gurin su Aunty Fadilah ba suna parking ya wuce part d'insa bai tsaya huta ba ya shiga toilet yai wanka ya d'auro alwala domin lokaci kad'an ya rage a kira sallah saida ya shirya ya wuce masallaci da akai sallar magriba ma bai fita masallacin ba saida akai isha sannan ya koma part d'insa shifa a yau ma baici komai ba ko ruwa bai sha amma maimakon yayi kokarin cin abinci sai kawai ya zauna a parlonsa ya bud'e laptop ya fara aiki.
Jin karar doorbell yasa yad'au remote ya bud'e kofar duk zatonsa Aunty Fadilah ce amma sai yaga Ajeeb ya shigo yana kare masa kallo kafin yace.
"Asad wai kaci abincine a yau ko haka kake zaune"?.
"Mene damuwarka in naci in banci ba"?.
"Dole na damu saboda ni d'an uwanka ne kome zakai wai Asad dan jaraba baka gajiya da aiki kamar agogo"?.
Batare da Asad ya d'ago ba yace "to ko agogon ne"?.
"Oho waya sani amma da alama shi d'in ne tunda naga rashin hankalin naka yayi yawa ko agogon ma ai batir dinsa yana sanyi".
"Ajeeb fice min anan".
"Bazan fita ba kasa a fitar dani" daina aikin Asad yai ya d'ago yana kallon sa zaiyi magana wayarsa tai kara bai kulashi ya d'aga ganin kiran Mai martaba ne magana yai masa wanda kawai amsa ya bashi da cewa to sannan ya rufe laptop d'in ko inda Ajeeb yake bai kalla ba ya fice dariya Ajeeb yai yana bin bayansa yace "wato yaron nan ka gama raina ni ko? Humm zan kama kane" shidai Asad bai sake nuna dashi yake ba kawai suka wuce 6angaren mai martaba kamar yadda ya bukaci suje.
Shaukiyyah tana bedroom d'insu a zaune taci wanka tayi kyau sosai Khaldiyyah Makiyyah harda Khimiyyah suna gefenta da sauran yan Mata a dangin Sultana Shafi'ah da suka zo kallonta Khaldiyyah keyi tana daukar ta a photo cike da burgewa tace.
"Shaukiyyah na taya ki murna Allah ya sanya alkairi burinki ya cika kin auri prince Ameer nima Allah ya taimakeni ya karkato min da hankalin Annur kaina ko na daina shan wahalar soyayya".
Murmushi Shaukiyyah tai tana kallon ta tace ''karki damu Khaldiyyah kamar yau ne insha Allahu zaki auri prince Annur".
"To Allah yasa Shaukiyyah amma ni gabadaya na karaya da lamarinsa ne kullum kara nesanta kansa da soyayya yake saidai banace ba ko hakan wata manufar ce dabam amma nikam gaskiya maganar Allah ina matukar son prince Annur har cikin raina".
Sauke ajiyar zuciya Makiyyah tai tana cewa ",humm kefa Khaldiyyah kukan dad'i kike gara ke da sau'ki zaki iya tunkararsa kai tsaye batare dajin tsoro ba amma nifa wallahi Asad idan na ganshi gabana har fad'uwa yake tsabar kwarjininsa wallahi Nima shine za'bina".
Ta'be baki Khimiyyah tai tana kad'a kai domin ita kam yanzu babu komai tsakaninta da Asad sai d'aukar fansa ko sauraren maganar bata yi iya su kad'ai suke tattaunawa a junansu.
Da sallama Asad ya shiga fadar mai martaba ya tarar mai girma Alhussain yana can ga Mami sannan kuma shima gasu shida Ajeeb zama yai yana gaidasu tare da yi musu barka da dare amsawa mai martaba yai yana kallonsa kafin ya mayar da hankalin sa kan Ajeeb wanda yai shiri yana kallon Asad kamar mai tunani gyara zama Mai Martaba yayi sosai yana fuskantar Asad yace.
"Asad ka saurare ni da kyau cikin nutsuwa kaji abinda zan fad'a maka kasan cewa Allah ne keyin abu da ayi ko duk dabarar mutum bai isa yayi maka wani abu wanda Allah bai nufa ba Asad Ajeeb d'an uwanka ne uwarku d'aya sannan ubanku d'aya yaga ya isa dakai yana da iko dakai zai iya yai maka abu kansa tsaye batare daya nemi yardarka ko shawararka ba shiyasa lokaci mai d'an tsawo yazo min da wata magana yaga yarinya mai nutsuwa wacce yaga ta dace dakai zai wakilceka ya aura maka ita amma ya rokeni alfarmar kada na sanar dakai sai ranar da aka d'aura auren saboda gudun fitinarka Asad Ajeeb baiyi maka haka dan ya bata maka raiba a'a yayi haka domin samun farin ciki da walwalarka dan Allah Asad kada ka tada hankalin ka akan wannan al'amarin ka d'auka kaddara ce ka kar'bi auren nan da hannu biyu kayiwa Ajeeb godiya".
Zabura Asad yai yana cewa "Abba dawa aka d'aura aure dani fa? Haba wannan zance ne".
Da mamaki Mai Martaba yace "Asad nine zan fad'i magana kace zance ne"?.
Da sauri Asad ya d'an daidaita nutsuwarshi yana cewa "kayi hakuri abba abunne yazo min a bazata amma dai dan Allah Abba kace min da wasa kake taya Ajeeb zaiyi min aure kamar ubana"?.
Kai mae Martaba ya girgiza ''a'a Asad bada wasa bane da gaske ne dakai aka d'aura aure ba Ajeeb ba duk wani abu da kaga Ajeeb yana yi domin kane ni na amince masa domin bada ka yayi maka hakan ba saida ya nemi shawarata data d'an uwana sannan aka aura maka ita"....
Cafff mai martaba yana rufe baki Asad ya mi'ke tsaye a fusace yana kallon Ajeeb yace "dama nace maka kayi min aure ne nace maka Ina bu'katar aurene"?.
Wata uwar harara Ajeeb ya sakar masa yana cewa "dama saika bu'kata da nayi maka isa nai dakai shiyasa na nuna maka isar tawa a aikace ka gane"?.
Ajeeb na rufe baki Asad ya dam'keshi da dambe ransa a mugun 'bace idonsa ya gama rufewa har wata jijjiga da saiwa yake kamar wanda tsumunsa ya tashi mai martaba yana zaune yana kallon su ko kad'an baiyi motsi ba balle yayi magana mai girma Alhussain ke tayi da bakinsa amma ko jinsa basayi haka Asad ya shakewa Ajeeb wuya yana cewa.
"Ka bani amsar dana tambaye ka nace maka kayi min aure ne''?.
Fisgewa Ajeeb yai shima ransa a had'e sosai yana cewa "kuma dama sai kace nayi maka isa nayi shiyasa nayi maka d'in kuma babu yadda zakai dani zama da matar ya zama dol.....................
Tsalle Asad yai ya sake sha'karsa sukaci gaba da dambe wanda in kaga yadda suke kaiwa juna duka sai kayi tunanin irin ri'kakkun abokan gaban nan ne duk sun hargitsa parlon har kujeru Saida suka san ba lafiya ba table na glass kuwa sun fasa kusan uku har show glass saida suka ruguzashi ganin abun nasu yad'au zafi yasa Mai martaba cewa.
"Ku saki junanku kafin ku 6ata min rai Asad wannan abun ya isa haka sake shi kaima Ajeeb ka sake shi kun haukace ne kome tsabar rashi hankali".
Sakin Ajeeb Asad yai yana turashi baya da karfi yai yuuu zai fad'i da sauri Mai girma Alhussain ya tareshi yana cewa "subahanallahi Asad me kake haka kada ka fasa masa kai da wannan fasassun glass d'in".
Wani irin huci Asad keyi ji yake kamar ya sake fisgo Ajeeb d'in ya dokashi da qasa yabi ya take jin zuciya taxo masa har wuya yasa da qarfi ya jawo rigar Ajeeb wanda mai martaba yace.
"Asad sake shi nace".
Runtse ido Asad yai da qarfi yana sakin rigar Ajeeb d'in kafin ya juya da sauri a fice daga gurin yana shiga part d'insa a gigice ya fara tattara kayansa a take bai sake minti biyar cikin masarautar ba ya fice zuwa airport ya koma Marshall islands.
Hankalin Mami in yayi dubu ya tashi bawai fad'an da sukai bama Abinda yafi d'aga mata hankali shine jin wai duk wannan fafutukar da jajircewar da Ajeeb keyi dama saboda ya aurawa Asad yarinyar ne bayan ya riga ya fad'a masa bazaiyi aure ba sai yayi retire kai innalillahi wa Inna ilaihi raji'un kallon Mai martaba tai tana cewa.
"U're highness nifa ban gane komai ba wai dama shi Ajeeb d'in kunyi dashi ba a kansa zaiyi aure ba Asad zaiyi wa kai Ajeeb miyasa kayi masa haka bayan ya riga ya fad'a maka bazai aure yanxu