Showing 180001 words to 183000 words out of 195514 words
abinda zata fad'a dan shima wani san baya abinda ba shine yayi ra'ayi ba tace.
"Dama batu ne akan tafiya gida naga mun shekara harda wani abu amma baka zancen muje mu ganosu dan Allah ina so muje ko bamu dad'e ba".
"Oh akan haka ne dama kikasa na daina wasa da yarona ashe shirme zaki fad'a min"?.
A shagwa'be Indo tace "Allah a'a yaya Dauda wannan ba shirme bane da gaske nake".
"Ok shikenan zamu je amma sai watan gobe kada kiyi magana domin ko tari kikai saina mayar dashi watan jibi kin gane" jin abinda yace yasa Indo rufe baki da hannu tana dariya qasa qasa dan tasan ba qaramin aikinsa bane yace sai watan jibin da tayi masa kuskure dole tayi taka tsantsan kada ta jawa kanta tana murnar zata gida ya qara jan tafiya.
🏙️KANO🏙️
_______Yau da gobe tafi qarfin wasa tun Amatu na shasshare Ajeeb idan ya kirata a waya har zuciyarta ta karkata kansa kamar bata ja masa aji ba sai tsintar kanta tayi dumu-dumu a cikin soyayyar sa kuma koda wasa bai ta'ba fad'a mata daga inda yake ba wai yace shi d'an sarki ne ko wani abu dazai nuna mata ainishin waye shi duk ya 6oye saida abu yayi nisa zuwansa ya yawaita Malam Habu ya sameta akan idan taji zuciyarta ta amince dashi zata iya zama dashi tayi masa magana yaga manyansa a gidan nan domin saurayin Aisha ma ya gama komai indai itama nata da gasken yake ya turo a had'a su ayi bikin kamar yadda akai na Asma'u da Jamila.
A ranar da Ajeeb yazo da dare ta fad'a masa kuma yayi mata alkawarin za'a daga gidansu domin shima yau da niyyar maganar data kawo shi gurinta kenan sai kuma ta rigashi furtawa amma tana ganin idan taga waye shi ko ya bayyana mata kansa zata amince ta aureshi ta nuna ko shakka babu mezai hana aishi take so ba komai ba.
Humm amma fa bayan wucewa kwanaki da mai girma Alhussain yazo su malam Habu sun girgiza kuma sun tsorata dama wannan saurayin dake zuwa dan sarki ne? Cafff gaskiya bazasu iya d'aukar 'ya suna matsayin talakawa a talakawan ma fakirai irinsu duk da yanxu alhamdulillah Allah yayi musu rufin asiri sosai domin har Jamila dake Canada tana turo musu da kud'i su sai abinci bangare guda ga Alhaji Musa gakuma uwa uba Malam Habu da baya son qasawa ko gazawa jajirtaccen mutum mai 'kwazo.
Abu d'aya ne ya tsaya a ran Malam Habu ganin mai girma Alhussain dayai ya tuna masa wancan had'uwar da akai karfa ace wannan d'an matashin ne da suka had'u a kofar shiga makaranta shekarun baya tun Amatu tana shekara shida harya bata kyautar rigarsa kodai da gaske abun daga Allah ne uhmmm bashi da ikon hanawa ko jayayya yabar za'bi a gurin mai duka domin kunyar mai girma Alhussain yasa dole ya kar'bi maganar baya da manyan mutane duk da sune suke nema a gurinsa itakam Amatu harda kukanta domin da tasan a masarauta yake bazata amince masa ba ita da ba jinin sarauta ba haka kawai taje ta cud'anya dasu gashi ta riga ta gama ji'kewa da soyayya dashi tayi zurfi a kansa haka ta gama kukanta ta share malam Habu yana kwantar mata da hankali cewa tayi fatan abinda zai zama alkairi a rayuwarta idan babu alkhairin a tsakanin su Allah ya raba abun ta ruwan sanyi amma yanada yaqinin afkuwar alkhairin domin abunda ya faru a baya.
GIDAN NURAIN
Su Mimih na zaune a parlor suka jiyo 'ka'karin amai daga part d'in Nafisa a guje suka mi'ke suna yin part d'in su ganewa idonsu miyake faruwa suna shiga suka tarar Nafisa dur'kushe tana she'ka amai duk ta 6ata jikinta zaro ido Mimih tai tana kallon ta tace .
"Ke aman uban me kike badai ciki ne dake ba"?.
Nafisa bata iya d'ago kanta ba balle harta bata amsa sai murd'e murd'e take ta'be baki Meelat tai tana cewa "kya tsaya tambayarta wai ciki ne da ita meye wannan inba cikin ba kalli fa yadda tayi wani fari kuma fuskarta ta kumbura kallo d'aya zaki Mata kisan wannan akuyar akwai ciki a jikinta".
Meelat na rufe baki mimih tace "tabdijan kan bala'i wallahi baki isa ki haifa mana baby a gidan nan ba familyn mu bazai ta'ba hada jini da bagidajiyar qauye irin ki ba".
Wata irin harara Meenah ta sakar mata na tsantsan 'baci ran ganinta da cikin wanda take so take fatan ya aureta ya'ki sauraron ta saboda Nafisan tace "Humm barni shegiyar Mimih saita haifi cikin nan a yanzu ko na 6arar dashi wai a haka iyayenta nada kud'i sune masu arzikin qauye".
Tsaki Mimah tai tana cewa "Matsiyatan qauye dai au wai dama a hakan ubanta nada kud'i aini duk zato na irin d'iban bolar nan yake da naga ya kawota dan rashin zuciya ba ko cokali babu tsabar rashin zuciya" Mimah ta karasa maganar tana d'aga waya ta Kira Zainab domin ta riga ta tafi hospital tana d'agawa Mimah tace.
"Hello Aunty zee ki dawo gida yanzu ba lafiya kiyi sauri dan Allah".
A rud'e Zainab tace "meya faru Mimah wani abun ne"?.
"Eh wani abu ne Aunty zee ki taho da allurar zubda ciki domin bamu ankara wannan banzar yarinyar ashe ciki gareta yanzun nan kin ganmu a kanta sai amai take".
Cike da kishi Zainab ta dafe 'kirji tana cewa "ciki kuma Mimah? ciki dai na haihuwa wanda na sani shi take dashi"?.
"Kwarai Aunty zee kiyi sauri kada tsautsayi yasa ya Nurain ya dawo komai ya 6aci".
Jiki na rawa Zainab tace "ok ku tsaya a kanta kada ku bar gurin karta kira my choice ta fad'a masa gani nan zuwa yanzu".
"Ok Aunty zee" Mimah ta fad'a tana sau'ke wayar.
Hankalin Nafisa in yayi dubu ya tashi jin suna neman zubar mata da cikin data 'kwallafa rai a kansa take murna su Bara'atu ma suke yi yau ta shiga uku idan suka rabata da cikin nan sun cuceta yun'kuwa tai da sauri batare dasun ankara ba ta fice dsgudu domin ta tsira daga hannunsu a guje suka rufa mata baya tana xuwa main parlor Zainab na bud'o kofa suka ritsata a tsakiya hannu ta d'ora aka tana fashewa da kuka wani irin kallo Mimih tai mata tana cewa.
''Oh da kike shirin guduwa gidan ubanki zaki tafi ko qauyen zaki tafi idan kin haihu kya dawo 'yar gidadawa".
Zainab da ranta ya riga ya gama tashi da ganin yanayin Nafisan tabbas cikine da ita domin ita likita ce tasan mace juna ranta na turiri tace "ku ri'ke min ita yau saikin gane kurenki".
Ri'kewa sukai tana ihu da qarfi Zainab tayi mata allura sannan tana huci tace "ku d'auke ta ku mayar da ita part d'inta ku samun ido a kanta lokaci zuwa lokaci har sanda cikin zai fita ku kirani a waya ku sanar min na koma hospital" tana fad'in haka ta dauki handbag d'inta ta fice.
Kallon Nafisa dake kwance tana kuka Mimih tai tace "kuka yanzu kika fara wallahi kuma bari kiji idan ya Nurain ya dawo tsautsayi yasa kikace mune sanadin zubewar cikin ki hummmm basai na karasa ba kinsan gamon mu dake baya miki dad'i" kallon sauran tai tana cewa ''ku jamin ita na kaita wawwaran part d'inta data gama lalatawa da qauyanci" ta fad'a tana firgar Nafisan har saida hannunta yai qara kuka Nafisa keyi suna janta kiiii a kasa saida sukai kaita har bedroom sannan suka barta suna ficewa rasa inda zata sanya kanta tayi ta shiga uku yanzu me zatacewa su Bara'atu bayan d'azun nan tayi musu albishir tana ciki gashi wadannan azzaluman yan matan sun zubar mata dashi haka ta wuni a daki tana kuka kamar ranta xai fita musamman yadda taga jini yana zuba a jikinta ta tabbata yanzu kam cikin ya fice daga jikinta har zazza'bin tashin hankalin ta yadda zata kare kanta idan Nurain ya dawo take yi tasan zasuyi mata sharrin itace ta zubar da kanta batasan wanne irin mataki zai d'auka a kanta ba.
🌃MARSHALL ISLANDS🌃
____"____Asad yana zaune tare da Isham yana fad'a masa zaije gida ne bikin 'yan uwansa Ameer da Ajeeb saidai bazai wuce kwana uku ba suna cikin magana Clarah taxo ta riski zancen nasu da sauri ta zauna tamkar wani zai rigata tana kallon Asad tace.
"Asad zan bika muje tare tunda ba dad'ewa zakai ba nima ina so na gano family d'inka su sanni na sansu kaga dama tunda nake ban ta'ba zuwa Nigeria ba saidai daga baya idan munyi aure zanje na fara shiri yanzu ko"?.
"No".
Shine abinda kawai yace mata batare daya kalli koda wajen inda take zaune ba kuma fuskarsa bataga alamar wasa ba dan kada tayi masa magiya amma sai tace.
"Asad meyasa baka so naje naga familyn ka wannan shine karo na uku Ina tambayar ka baka amincewa a tunani na akwai yarda mai karfi a tsakanin mu amma har yanzu gani nake kamar hankalin ka bai kwanta dani ba why Asad? dan Allah ka fahimci halin kad'aici da gararin da xuciya take fama a kanka ka tausaya mini kona samu salama".
Banza yayi da ita tamkar ba dashi take ba ganin haka yasa Clarah mayar da hankalinta kan Isham tana cewa.
"Isham ka taimaka min ka fahimtar da Asad ya gane cewa wallahi ina son shi shine matsala ta a yanzu wannan shariyar da yake min babbar ciwo ne ga zuciyata kace masa wani abu please".
Kai Isham ya girgiza yana cewa "Clarah ni a nawa ra'ayin ina ganin laifinki ne kece kika 'ki mayar da hankalinki guri d'aya ki fahimci Asad ba baya son kisan familyn sa bane a'a ya riga da kun gama magana tun da dad'ewa anyi yarjejeniya tsakanin ku kinsani ya sani yace miki zai aureki sai yayi retire to miyasa da kikasan hakan bazaki dauke kanki daga garesa ba ki mayar da hankalin ki kan aikinki kina kallo sabin d'auka ma nema suke su fiki 'kwazo da himma gaskiya Clarah kisa tunanin ki guri d'aya nayi mamaki ma yadda kike da wasan nan har Asad ya amince zai aureki Kinga kin ta'ki sa'a, na fad'a miki wani abu Asad ba ruwansa da mace ko wacece ita baya kula mace baya kallon mace baya had'a tafiya da mace idan baki sani ba ki sani shiyasa nake sake jajjada miki chance ur chance before chance, chance on you kiyi amfani da damarki kafin damar tayi amfani dake tunda Asad yace miki yasan da aurenki kija baki kiyi shiru kafin ki kaishi bango ya furta miki kalmar ya fasa duk ranar daya fad'i haka tofa ko mutuwa zakiyi bazai ta'ba aurenki ba nasan Asad nasan halinsa ba tun yanzu ba shi kaifi d'aya ne sannan baya magana biyu kin gane"?.
Shiru Clarah tayi tana kallon Asad jikinta a sanyaye itakam ta kad'e ta gama yawo ace mutum kana son sa kana nuna kulawarka garesa amma shi Sam baya takai da xata iya saita ha'kura dashi saidai batajin koda duk duniya zasu taru a kanta akan ta rabu da Asad bazata iya ba saidai idan numfashin ta ne ya yanke...................
"Zaki iya tafiya".
Jin muryar Asad yasa a firgice ta dawo daga tunanin da take tana daidaita kanta tace "kayi hakuri dan Allah bazan sake ba".
Kalmar farko ya sake maimaita mata "zaki iya tafiya''.
Da mamaki tace "haba Asad ha'kuri fa nake baka ka saurare ni kafin na tafi....................
"Clarah get of my sight''.
Jin abinda yace yasa ta mi'ke tana sake kallon sa tare da jin zuciyarta kamar zata fito waje daga qirjinta tsabar zafi da turaruwar da take da zata iya ko tana da iko data fito masa da ita yaga yadda ta cika ta batse da soyayyarsa a kewaye take da muradin kasantuwa dashi tana fatan ranar da zata bud'e ido ta ganta tare da Asad matsayin couple💑 sauke ajiyar zuciya tai bata sake cewa komai ba ta fita a gurin da kallo Isham ya bita yana girgiza kai sannan ya mayar da hankalin sa kan Asad yana cewa.
"Ni kuwa Buddy ya batun abinda kake nema ka gano yarinyar ko har yanzu a'a"?.
Kai Asad ya d'aga masa ''ban ganota ba amma dai bincike ya nuna min 'yar Nigeria ce zuwa gidan da nayi tazo min a mafarki tayi min bayani sosai akan 'kungiyar kuma na yarda da abinda ta fad'a min domin dajin da suke ciki tabbas ba dajine wanda yake a bayan qasa ba dajine na siddabaru ba'a iya ganinsa kuma dole saida wata sar'ka ake iya shigarsa tace min akwai sar'kar a wuyan kowanne d'an 'kungiyar to amma Isham abinda na gagara fahimta har yau shine ita yarinyar mutum ce ko aljana idan mutum ce taya ta sani bayan tana karamar yarinya kuma ba wata babbar ma'aikaciya ba a cikin bincike na nagano bata da ala'ka da wani wanda yake neman 'kungiyar kuma batasan ana neman 'kungiyar ba sannan kullum suna cikin yi mata barazana duk ranar data fad'awa wani zasu hallaka ta amma haka bai bata tsoro ba a halin yanxu maganar da muke dakai mafi yawancin abubuwan da suke aikatawa ta sani d'ai-d'ai ne suka 6oye mata shi sai dai Isham nayi iya kokarina amma na gaza ganota na rasa inda take da kamar ace zanyi sa'a ta kunna location d'inta shine zansan inda take kai tsaye amma matukar mukaci gaba da tafiya a haka har abada bazan san komai ba".
Sauke numfashi Isham yai yana kallon sa yace "to yanzu mafita d'aya ce mezai hana kayi mata magana kace ta bud'e location d'in''?.
"No Isham link d'in shafinta baya aiki ai basu barta banza ba sun lalata mata komai ta yadda bazata iya tura sa'ko ko a turo mata ba shiyasa suke nuna mata komai sun san daga laptop d'inta babu inda zata iya share d'insa".
Kai Isham ya jinjina yana cewa "kai amma abun baiyi dad'i ba duk da haka Asad kada ka sare kaci gaba da jajircewa kamar yadda ka saba kullum insha Allahu zaka samota".
"To Amin Isham saidai bansan ta inda zan fara binciken ba"?.
"Tunda a Nigeria take acan ne idan kaje ya kamata ka tsaya ka bincika koda ace zaka dawo".
"Ok shikenan Isham zan jarraba".
"Yauwa Asad Allah ya bada sa'a Allah yasa ka samota a wannan karon" Amin yace masa ganin lokacin sallah yayi yasa suka mi'ke suna fita daga cikin babbar rumfar barrack d'in da suke.
🏕️QAUYE🏕️
________ Yau Dauda da Indo suka sauka uhm mamaki kowa keyi musamman wasu harda masu rantsuwa ba Indo bace saidai wata matar Dauda ya aura acan masu ganin 'kwa'kwaf saida suka zo suka tabbatarwa kansu Indo d'ince da gaske nan fa akaita gulmar abinka da qaramin gari ko'ina anji harda masu zuwa sannu da dawowa dan suga meke going.
Indo tayi mamakin jin wai Dalah ta koma gidan babanta Balarabe gaskiya bata ji dad'i ba a fili qarara ta nuna rashin jin dad'inta da hakan Aliyah ta nuna Mata yanxu fa ba irin da bane Balarabe ya sauya Asabe bata da iko dashi ya dawo cikin hayyacinsa jin hakan datai yasa tad'an ji dama-dama amma duk da haka bata le'ka gidan ba a ranar sai washe gari da yake shigowar yamma sukai.
Tun safe taiwa Irfan wanka ta shirya shi itama tayi wankan bayan sun karya Dauda ya sa'ba d'ansa a kafad'a domin yanxu ya riga ya waye hakan ba komai bane suka tafi gaishe da Dalah suna shiga da sallama Dalah ta zaro ido waje tana cewa.
"Indo kune a gari"?.
Murmushi Indo tai tana kallon kofar d'akin Asabe batai magana ba ta karasa gurin Dalan sakamakon d'aki akwai zafi yasa ta d'auko musu tabarma waje zama sukai suna gaida ita fuskarta fal da fara'a ta amsa balle dama tun jiya yara suka zo suka yi mata albishir Indo ta dawo.
Kar'bar yaron tai tana kallon sa da murmushi a fuskarta tace "masha Allah Balah (Irfan) yayi girma lallai kun dad'e rabonku da gida ai jiya ina zaune Yusufa yaron gidan malam Hamza ya shigo da gudu ni harna yi zaton ko irin tsokanar nan ta yara yayo aka biyoshi na fara masa fad'an ya daina tsokanar kar wata rana ya tsokani wanda yafi karfin sa ya dakeshi sai yake cemin ba tsokana yayiba wai kune kuka dawo yazo ya fad'a min harda d'a um alhamdulillah Allah ya raya gashi babanki bai dad'e da fita waje ba ko kun had'u a hanya"?.
Kai Indo ta girgiza "a'a bamu had'u ba".
Dalah nayiwa Irfan rawa tace "to ta yuwu ko nisa yayi amma tunda anan zaki wuni harya dawo ku gaisa".
Tana rufe baki Balarabe yayi sallama da kaya a hannunsa ganin wadanda suke zaune yasa ya karaso yana cewa "Indo kece ko kuma ido nane"?.
Sauke ajiyar zuciya Indo tai itama tana kallon shi tace "nice baba ina kwana"?.
Zama Balarabe yai da fara'a yace "lafiya kalau fatan sun sauka lafiya"?.
Kaita d'aga ''lafiya alhamdulillah".
"To madallah" mayar da hankalin sa kan Dauda wanda ke gaidashi ya amsa yana cewa "Allah yayi maka albarka Dauda Allah ya baku zaman lafiya da zuriya dayyiba" Amin Dauda yace yana mi'kewa ya fita a gidan kar'bar d'an shima yayi sai kallonsa yake xuwa wani lokaci ya d'ago yana kallon Indo da suke zance da Dalah yace.
"Am Indo dan Allah kiyi ha'kuri ki yafe min kuskuren dana aikata miki a baya wallahi bansan meya sameni ba nake irin wadannan abubuwan na sani kinyi ha'kuri a gidan nan kin sha wahala amma yanzu ga ribar ha'kurin nan kina gani Allah ya miki babban arziki kina zaune lafiya a d'akin mijinki ido ba mudu ba amma yasan kima Indo ko ba'a fad'a ba ansan kinajin dad'i a hannun yaron nan Dauda ya rikeki da amana Allah ya baku zaman lafiya mai dorewa sannan bazan gajiya ba da neman gafararki ba dan Allah Indo ki yafe min kuskuren dana aikata miki a baya"?.
Kai Indo ta girgiza tana cewa "a'a baba bakai min komai ba na yafe maka albarkarka nake nema".
"Allah ya albarkaci rayuwar ki Indo" Amin tace cikin jin dad'i tana kallonsa rabon da ta zauna wai Balarabe ya fad'a mata magana mai kyau ta ruwan sanyi harta manta wannan lokacin.
Tashin Asabe kenan daga barci jin maganganu yasa ta fitowa ganin wadanda suke zaune ga Indo da gaske kamar yadda labari yazo mata cewa sun dawo harda d'a tayi ki'ba ta kara kyau Asabe batasan lokacin data sake murje ido ba ganin da gaske dai