Showing 33001 words to 36000 words out of 122551 words

Chapter 12 - MATAR MAKAHO COMPLETE HAUSA NOVEL

07 Sep 2024

16745

Ina Mika Mata kudin



Ki bare Aunty mota za'a kawo a gidansu amarya zai d'auke kawaye



"Aikam yau a motar zaki,maza ki hanzarta Amma ki.karbi kudin Incase



Toh aunty sai na dawo,tace tana fita a d'akin



"Toh khadija Allah ya dawo dake lfy"



Ameen, khadija na fita a kofar shashen yayanta, duk Yan gidan suna zaune a tsakar gida daga maza har Mata,ido suka bita dashe kureeeee suna mamakin bakuwar nan Sam tun safe suke zaune Amma basuga wucewar taba,baki a tsake suka bi khadija da ido harta fita,



Khadija Kam duk tabi ta tsargu don Sam tunda take da wayonta Bata taba kwalliya irin na yau ba har kofar gida ta fita duk masu shaguna suka bita da ido suna mamakin Wannan kyakkyawar meya shigo da ita gidan Adara,

Amma wasu basa mamaki in sun tuna MATAR MAKAHO fa Yar manya ce Kamar yanda aka saigunta musu, Kuma sun rasa dalilin auren nan Basu mamaki yake,mutum talaka miskini,a d'auki lafiyayye ya abasa Kuma Yar masu kudi,masu kudin ma zuriyan shugaba,abin nan na mugun Basu mamaki,Amma Basu da halin sani



Khadija Kam ganin ido caaaa akanta yasa ta ruga gida da gudu ta koma kofar Sumayya



"Kee khadija lfy meya faru Naga kin shigo kofa Koh sallama Babu Kamar an koroki"



Aunty duk inda na wuce bina fa ake da ido,ni gaskiya tsoro nake ji



"Kai khadija akwai wauta,don ana kallonki saiki kame jikinki ki nuna musu kauyanci,ai dakewa zakiye kici bom"



"Koh gun kamu kikaje neman kujira zakiyi ki zauna abinki karki kuskura kicewa kowa kome Wanda ya gaidake ki amsa Wanda Bai Miki magana ba karki Masa kinji"



Toh Aunty,tace tana fita



Sai yanzun Yan gidan suka gane ta cikin mamaki Iro yace,buran uba muna d irin wannan kayan a gida Amma ace har yanzun banyi aure ba aradun Allah Naga Mata



Kutumar ubanka iro D'an iska watoh kaga kasa ya rufe idon uwarka shine bare ka karya alkawarin da mukayi akan auren ka da salame,watoh munafurcine kullum akace ka fitoh a muku aure,sai kace baka da kudi,

ah ah sai kayi gini ashe iskancine,baba lami tace



Kinga baba lami wallahih kibini a hankali Daman ni har yanzun haushin ku nakeji,

Aini ba shege bane dazan aure kanwar Wanda tayi sanadin mutuwar inno na ba,

Koh inno ne ta dawo nasan bazata yafe mini ba Inna aure yarki, iro yace



Kai karamin D'an Tasha wallahih karka kuskura, kace zaka zagarmin uwa inba haka ba naci ubanka a gidan nan, manu ya fada,babban yaron Inna asabe



Inka fasa shege kake,iro yace Yana huci



Ai Bai Gama rufe baki ba manu ya shakumosa suka hau dambe



Duk yanda matasan ke ta kokarin rabasu abin ya faskara abinka da tamben maza,

Mazan ma masu zuciya



Hatta iyayensu maza an Kira Amma duk sunki rabuwa sai an rabasu an Kama D'aya sai D'aya ya fizge ya shakumo D'aya Inka shiga tsakani duka ya sauka akan ka



Abin da yafi karfin Yan unguwan police aka Kira,suka zo suka kwashe su,inda sabo an Saba da ganin fiye da hakama agidan Adara







*******************

Bayan fitar khadija kwanciya nayi don yau dai naji na gaji da cin cimar mu tunda inada sauran 2k Kuma akwai kayan Miya da yawa,don haka yaudai zanci wani abin special



Duk abinda ke faruwa Ina kwance Ina jinsu sai dai.bansan ainahin abinda ya had'asu ba"garin kallon fad'a a kasheni a banxa " nace Ina gyara kwanciya na



sai kusan 5:30 Al'ameen ya koma gida kwata kwata naira 30 yayi ciniki Sam yau Kam sai a hankali,ya shigo gidan jiki a sanyaye hannunsa d'auke da kwandon kwanuka,bakinsa dauke da sallama



"Waalaikumu salam,sai yanzun"nace masa



Eh Sumayya yau inne ba kasuwa shiyasa ban dawo Koh da Rana ba



"Toh Allah ya bada kasuwa gobe"



Ameen yace Yana aje Kwanukan a mawanki,Mika Mata talatin in yayi



"Ka rike kawai agunka"



Ok yace,boket ya d'auka ya ibi ruwa, band'aki ya shiga yayi wanka Yana fitowa yayi Alwala,daidai lokacin aka Kira mangari ba, masallaci ya wuce



"Sallan mangariba,nayi wanka Nima zani na d'auka fille D'aya na had'a da t-shirt sai hulan bacci, Jin ana kukarin shiga sallan isha'i,

Ina da Alwala hijab kawai nasa na Tada sallah,



7:40 Al'ameen ya shigo d'akin bakinsa d'auke da sallama



Amsa Masa nayi"yauwa jiranka nake ka dawo daman"nace Ina mikewa



Toh Allah dai yasa lfy?yace



"Kasan inda ake Saida tsire"?



Tsire Kuma Sumayya?



Eh "tsire de"



Hmm eh na sani a tsallaken titi akwai Mai nama, kusa damai shayi



Yauwa karbi kudin nan 2k ne ka sai Mana tsiren 1500 sai Kuma ka sama Mana drinks Mai Dadi guda biyu yau Dadi zamuci gaskiya"

sai ka sai Madara bornviter da sugar in change ya rage kasai bread Nokia Ina da ruwan zafi a flasks,sai mu karya dashe gobe da safe"



A Ina Kika samu kudin nan? haka Sumayya don khadija tace mini ba kayanki Kika sayarba



Sosai naji Ina Kara kaunar Khadija yarinya Mai hankali hartasan ta rufa mini asiri agun D'an uwanta,

Amma ni bazan Masa karya ba"uhmm uhmm nidai gaskiya bazan maka karya ba Turarena na sayar"



Amma Sumayya banace ki daina Saida kayanki ba ,ni ban Kara Miki ba, Bai kamata in rage Miki ba



"Habba ya Ina da abinda Zan sayar na saka abakin salati saina zauna da yunwa tsakani da Allah fa, yau baka samu kome ba da haka Zan zauna tun safiya har warhaka banci kome ba kenan"na fada Ina Bata Rai



Ganin Kamar taji haushi sai ya sassauta murya,toh Yi hakuri kawo kudin naje na saya Miki



Mika Masa nayi bance kome Ba



Lalubar kudin yayi harya rike,ya fita



Baifi hour 1 ba ya dawo lokacin Ina kallo a d'aki



Shigowa yayi da sallama



Amsa Masa nayi,Ina karban laidodi Daya ke mika mini, karba nayi, na mike waje na fita na d'auko plates da cups harda flasks na shigo d'akin,

bude laidan tsiren na zuzzuba a plate,Goran pineapple juice in Mai sanyi na juye Mana a cup,d'aukan NASA nayi na Mika masa,"gashi naka"



karba yayi hade da Mata godiya,a hankali yasa hannunsa a cikin plate in ya dauki Naman da Bismillah yasaka a bakinsa

,lumshe ido yayi,rabonsa da yaci tsire tun lokacin da mahaifinsa kenan,bazai manta ba shike sayo musu duk dare, lokacin ma ba'a haifi Khadija ba



Nima cin namana nake Ina korawa da drinks ba karamin Dadi naji ba kai.talauci ba kyau talaka sai yafi wata baici nama ba,

Ashe haka talakawa keji,tabbas badon jarabawar da Allah ya jarabceta ba bazata taba sanin rayuwan Talauci haka yake ba Alhamdulillah Alah kulli halim



Daga ni harshi duk nacin mu bamu iyya cinye namarnan ba, sai da muka rage wani,nikam har zafi hakorina naji yake mini kafun na aje Naman don yau cin yunwa na masa,sabanin da, da nake ma nama cin kwad'ayi kawai



Jin ta aje plate nata yasashe magana,sumy Wai harkin cinye ne ga nawa ki Kara wallahih na kasa cinye wa,



"Kutt bazanci sauran abinda kaci ba,Kuma nima ga nawa ban ciny.........



Bai bare ta Gama magana ba taji ya fizgota sosai suka zube akan gado kanta yahau cikin gaggawa ya hada bakin su waje D'aya y'awonsa ya juye Mata a baki



Ware ido nayi Jin y'awonsa cike a bakina so nake na zubar Amma ba Hali har lokacin bakin mu a hade,ji nayi kamar numfashina xai d'auke ai da sauri na had'iye Ina rumtsa idanuna



Jin ta had'iye yasa a hankali ya kamo harshen ta sosai yake tsotsarta cikin zafi zafi..



Fizge bakina nayi,"don Allah ka Bari banason abinda kake minin nan"na fada Ina ta kukarin turesa a kaina





Ni Kuma inaso,ya Bata Amsa,Yana Kai hannunsa, akan t-shirt nata Yana kokarin cirewa



Ai bansan lokacin da na Kama kokarin fizgo kaina ba ganin da gaske fa mutumin nan riga zai cire mini



Jin ta isheshe da fizge fizge shima ya biye Mata inya d'aga riga sai yaji ta jawo rigan kasa,inya cire hannu D'aya sai tasa d'ayan



Tambe muka fara sosai abin dariya abin haushi,daga ni harshi mun jikkata sosai Amma ba Wanda yayi niyar barwa Dan uwansa dama



ni naki yarda ya cire mini riga shi Kuma yaki yarda ya hakura,



Hannu yasa da karfi ya fizge zanin jikinta,



Gwalalo ido nayi jina ba zani,wani yunkuruwa nayi da karfin gaske Zan mike zaune



Cikin zafi nama ya maidata kwance Yana Kara Hawa kanta,





daidai lokacin mukaji sallama na muryoyin Yan Mata a kofar mu....,.....





<Ø>ß *Juma'at Mubarak* <Ø>ß







<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sai da kamshi da gyara* =Ø Þ





<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa*



<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara*



<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace*



<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE*



<Ø@ß *Na tsunguno(habil)*

<Ø@ß *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )

<Ø@ß *Turaren turara jiki after birth*

<Ø@ß *Na d'aki(halud Al'oud)*



*UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* =؃Ü<Øüß=؃Ü<Øüß



<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa*



<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria*



Contact them vie

>Ø€Þ08028827241 or 09033791049

IG @umsadincense



<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß

>ØÑÝ
>Ø¯Ý *MATAR MAKAHO* =ØhÜ
>دÝ

~ Na ~



<ØCß *Rukayya* *Ibrahim* <ØCß



('Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa=ØLÜ

free book >Ø'Ý



Page 2þã 6þã &2þã 7þã

Ba karamin Dadi naji ba,da saurina Amsa musu sallamar muryata na rawa"waalaikumu salam"nace Ina kallonsa ganin baiyi niyar sakeni ba,"toh ka tashi Mana naje naji suwa ke sallama"



Wayace kiyi magana?



"Au amsa sallaman ne,laifi"



Toh ai badon Allah kika.amsa ba ya fada Yana sauka a hankali ya kwanta a Gefen ta



Jin ya sauka akaina ai da sauri na mike zanina da ya yasar a kasa na tsunguna na d'auka,fita nayi a d'akin duk jikina sai rawa yake, na barsa a kwance akan

Gadon.



Yan matane zasu Kai su biyar gabaki D'aya bazasu wuce sa'o'in Khadija ba,"sunnunku da zuwa"



Sukam mamakine ya cikasu,wannan ne MATAR MAKAHO Mata Kamar balarabiya Aiko Mai kudi lafiyayye ba kowa bani yake sa'ar samun mace Mai kyaun Sumayya, yauwa,Ina wuni Aunty sumy? Suna had'a baki



"Lafiya Alhamdulillah bara na d'auko muku abin zama"



La ki barshi kawai Aunty,sauri muke ma dare yayi.



"Gaskiya Kam Kuna Mata yanzun ana neman 10 na dare fa,kuna waje"



Eh wallahih Aunty nasan bazaki ganemu ba,Daman mu kawayen Khadija ne,wata acikinsu tace





"Kawayen Khadija Kuma aini Khadija batace mini tanada kawaye ba bayan Asma'u"nace musu haka don na gane kawayen Amaryar ne,ganinsu da Anko



Eh Aunty dukan mu kawayen Khadijan ne harda Asma'u,



"Toh Allah dai yasa lfy ba wani abin bane ya faru"nace Ina zullumi kar wani abinne ya samu khadija





Eh Aunty yanzun ma gidan su khadija Muka fitoh akan ta rakamu wajen ki,shine tace Wai yayanta ya hanata fitan dare



"Gaskiya ne Bata fita bayan mangariba, Allah dai yasa lfy kuke son ganina"?



Eh lfy Daman mun tambaye tane akan inda tayi lalle da make-up jiya,

Shine tace Mana Wai agun matar yayanta,.

Shine mukazo mu tambaya Koh zamu samu lalle gobe,da kwalliya in Allah ya kaimu?





"Bazaku samuba" nace Ina zuyawa na shiga d'aki Koh bin ta kansu banyi ba, saboda sanin da na musu sune suka ma khadija rashin mutunci jiya agun Fulani Dance.



Ina shiga d'aki akan kujira na zauna, gaskiya Ina son yin lalle Koh don na samu na biyan bukata Amma bazan ma Yan iskan nan ba.





Sumayya meyasa bazaki musu lallen ba? Al'ameen ya tambaye ta



"Ina ruwanka watoh ka fara sa ido Koh"



Ina Naga idon bare na saka ni duhu nake gani,ya Bata Amsa



"Watoh kaima ka iyya bakar magana Koh"



Ai agunki na koya



"Badai aguna ba malam ehen"



Amma Sumayya dakin musu lallen ai.



"Bafa Zan musu ba Yan iskan yara bakasan me suka mini bane,"



Yaushe sukazo gidan nan har suka Miki Abu?



"Kai jama'a yaushe ka koma D'an jaridane ban sani ba"



Baimin magana ba mikewa Naga yayi Yana kokarin sauka a gadon ai ihu na saka na mike zanyi waje.



Wallahih Kika fita a d'akin nan saina Miki abinda bakiso



"Me kenan"?



Kin fini sani,yace Yana nufar kofa, waje ya fita yaje ya rufe shashen mu ya dawo ya rufe kofan d'aki



Ina dai zaune sai raba ido nake,ganin ya nufu kujiran,da nake yasa na mike a hankali na lallaba na chanja waje, zuwa gaban mirror na tsaya,



Jin motsen takunta yasa ya gane lallai tabar Kan kujiran..



Fara lalube yayi nidai sai chanja waje nake in ya nufi inda nake saina chanja waje,duk magiyar da yake min, kin tsayawa nayi.





Muna cikin zagaya d'akin kawai aka d'auke NEPA gashe ban San takamemmen inda na aje wayata ba.



Jin tsayawar fanka,yasa ya gane an d'auke NEPA ne, shiyasa ya fara tafiya a hankali Yana laluben ta sanin da yayi yanzun itama ba ganinsa zatanayi ba.



Raraba ido nake ta faman Yi banajin motsensa Sam sannan Banga wayata ba.matsawa nayi sosai jikin kujira na sunguna Zan duba wayata,ji kawai nayi ya rungumeni ta baya





"Wayyo Allah nikam ka sakeni wallahih banaso"



yanzun dai kema baki ganin kome kamarni.



"Allah ba kamar Kai bakam"



Koma yayane dai baki gani



"Nikam sakeni hai"



Naki yace Yana dagata



"Wayyo nashiga uku,ka saukeni"nace Ina ta faman mutsu mutsu



Kiye shuru Mana mu k'wanta



"Niki shurun nikam ka sakeni"



Kin saketa yayi duk yanda tayi ya saketa ki yayi



Ina ji Ina gani ya kwanta akan kujira d'aurani yayi akansa,tun Ina masifa harnayi shuru Jin ana iska da yayafi ,sanan aka kece da ruwan sama,

Baccine ya d'auke mu dukan mu biyu akan kujiran muka kwana





Da safe,shayi mukasha da bread,wanke wanke na fitar Ina wanke wa



Sanin da yayi Koh ya fita ba lallai bane yayi ciniki sai wani ikon Allah da safen nan, gashe mangoron duk sunyi labo labo.

Kayansa ya fitar Wanda Bai wuce kala hudu ba a igiyar bayan gida inda take Tara kayansa masu datti,d'aukar basket in kayan Sumayya yayi ya fitar dashe waje ya zuye a dakali,ibo ruwa yayi ya fara wanke musu kayan.



Ina wanke wanke,Yana wanki,dukan mu shuru Babu Mai magana



Assalamu alaikum, khadija ce tayi sallama hannunta d'auke da laida



"Waalaikumu salam khadija"



Ina kwana Yaya?



Lafiya khadin Goggo



Ina kwana Aunty,tace tana murmushi



"Lafiya khadija ya Goggo"



Tana gaisheki,tace tana zama a Gefen yayanta dake zaune abakin dakali da boket in ruwan kumfa



"Aiko Ina amsa wa"



Aunty kinsan me? Kai jiya Naga abin mamaki,tace d'auraye kayanda yayanta ke wankewa



"Me Kika gani haka"? Na tambaye ta



Aunty kinsan Allah Ina fita a gidan nan,na wuce gidansu Asma'u duk inda na wuce sai ayita kallona ,

Ina Isa na samu an kawo mototi sunkai ashirin,kinsan Aunty mijin Asma'u shima Mai kudine?



"Ina Zan sani khadija ai sai kin fad'amin"?



Ina isowa wajen mototi sun cika har ana kokarin tafiya,kawai saina nemi gefe na tsaya, kawai wani abokin Ango yazo kusa Dani,Wai hajiya baki samu mota bane?



Nace eh ban samu ba ku tafi kawai Zan hau machine,

Wai harda cewa Wai babban Dani ba girma na bane Hawa machine bara a sama mini wajen zama,

Kawai yaje ya fidda kawar amarya ya sani a motar



"Hhhhhh Kai habba dai khadija"nace Ina dariya



Yanzun abin dariyane agunki Sumayya an fidda wani Ansa wata,Koh ke zakiji d'adi a Miki haka, Al'ameen ya fada Yana Bata Rai



Khadija Kam tsoro ne ya kamata Sam ta manta da yayanta agun ta sake baki tana zuba



"Kasan me suka matane"?



Koma me suka Mata hakan Bai kamata ba cin fuska ne,



Fad'a Masa kome nayi akan abinda suka ma khadija



Koma me suka Mata banji Dadi ba



"Khadija tashi mu shiga ciki muye sirri"nace Mata Ina Kama hannunta Muka shiga d'aki



"Khadija karasa mini sai akayi yaya"na tambaye ta



Ai Aunty in gaya Miki kawai na Shiga abina kawayen fa Basu gagane niba sai da Muka Isa Taraba motel in da Muka fifita a motar,duk Saida suka Raina wankan su Aunty kaf insu harda Amarya Babu Wanda kwalliyar ta yayi kyau irin nawa,



Sai da nama Amarya magana kafun suka gane nice, wallahih Aunty baki ga yanda aka maida ni abin kallo ba masu vedion aure sai d'aukana suke harda hotuna,Kinga agun kawaye uku nayi yaran masu kudi,samari Kuma sai turawa suke Wai suna son magana Dani a waje.



Kin zuwa nayi kawayen ma naki kulasu,ai Aunty badon Allah ba kenan suke Sona, tunda Basu Soni a khadija ta ba Saida suka ga nayi kyau,ta karasa maganar tana washe baki



"Gaskiya ne khadija bare ma insha Allah karatu zakiye insha Allah"nace Ina murmushi don tabbas khadija akwai kaifin tunani



Aunty jiya fa goshin mangariba na fitoh a Hall in Zan dawo gida Kinga yanda abokan Ango ke ribibin zasu kawoni gida,.

Amma naki,



"Gwara da Kika ki khadija yanzun mutum ake kiwo. Ba dabba kad'ai ba"



Wallahih kuwa Aunty kawai da dare saiga wani yazo gidan mu bansan ma waya nuna Masa ba Wai ana sallama dani,



"Lallai kanwata tayi goshi"



Allah Aunty kin fita nayi Goggo tayita fad'a



"Don me khadija wulakanci ba kyau fa dakin fitan ai"



Gaskiya ni Aunty banason Abu da masu kudi,

don mudi yace mini da babban mota yazo,Kinga masu kudin nan in Kika aure su wallahih Kina Yar talaka,basa ganin daraja. Yan uwanki



Ah ah khadija ba duka aka zama D'aya ba indai da kyakkyawan Niya akayi aure badon kyau Koh kwad'ayi ba,insha Allah ba abinda zai faru



Hakane Kam aunty,au Ashe fa na had'a da Aunty a magana ta am sorry (don tace auren masu kudi basa ganin darajan Yan uwan matan su,in talaka wa ne)



"Uhmm khadija kenan,ai Nima na zama talaka yanzun"



Amma ai gidan ku akwai kudi?



"Gidan mijina babu"



Aunty jiya wasu sunzo wajenki karfe kusan 10?



"Eh Khadija"



Nima jiya suka zo gidan mu Wai na fad'a musu Wanda tamin lalle,da Wanda tamin make-up



"Kawayen Amarya Koh"?



Eh Aunty sune,suka mini wulakanci agun Fulani Dance



"Aiko shiyasa nayi maganin su nace bazan musu lalle ba"



Meyasa Aunty



"Saboda kee kad'ai Zan ma kwalliya har Agama programs na auren Asma'u"



Kiye hakuri ki musu Aunty Zaki samu kudi sosai fa yau HENNA DAY, Kuma da yamma za'ayi Algaita



"Gaskiya khadija bazan musu ba "



Shikinan Aunty ga kayanki nan na dawo Miki dasu



"Habba khadija ki rike na bar miki"Daman kyauta na baki ba aro ba"



Aunty' ai yayi yawa



"Ki rike duka"



Allah ya..........



Bata karasaba mukaji sallama na muryar mace babba



Al'ameen dake zaune a waje ne, ya amsa



Sannu Ina kwana hajiya,yace Yana tsame hannunsa a wankin



Lafiya Alhamdulillah don Allah nan ne kofar MATAR MAKAHO?don ita Bata zata Al'ameen baya kallo ba



Kafun Al'ameen ya Bata Amsa Muka fitoh a d'akin dagani har khadija kallon matar muke hajiyace Kuma hamshakiya daga ganinta naira ya zauna



"Hajiya lfy" nace Ina kallon ta dajin haushin sunan da ta kirani Wai MATAR MAKAHO mtwss



yauwa wajenki nazo



"Ok Bismillah khadija d'auko Mata darduma" nace saboda d'akin mu D'ayane bazan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login