Showing 66001 words to 69000 words out of 122551 words

Chapter 23 - MATAR MAKAHO COMPLETE HAUSA NOVEL

07 Sep 2024

16767

da bincike ba menene hujjar ka? nace wa kamila ce taje da acid in, baban kamila ya tambayi Ammar



Ku tura d'aya daga cikin yaran ku officer aje a d'auko goran acid in Allah dai yasa sumayya baki taba bako?



"Eh yana nan ata gefen kitchen a kasa"



Ok aje a d'auko saiku saka a gwada yatsun hannun wanda aka gani a kai wannnan ma ai hujjane koh?



Wai kai a matsayinka nawaye har zakana bamu order kai waye?



Hannu Ammar yasa a Aljuhu ya zaro ID card nasa ya nuna



Ai da sauri duka police inda ke wajen suka kame tare da sara masa



A gaskiya station nan yana bukatar gyara tunda bakusan aikin kuba A matsayin ku na hukuma masu kare hakkin wa'inda aka zalunta shine zaku zamo masu tauye masu rauni ku aje hujja akan masu kudi, Ammar ya karasa maganar da tsantsan bacin rai



Don Allah sir kayi Hakuri wallahi kuskure aka samu Shiyasa kuma duba da irin rauni dake jikin ita yarinyar da aka ma dukan shiyasa muka d'auki matakin gaggawa officern ke magana cikin magiya



Mtwss Ammar yaja tsaki hade da rufesu da fad'a sosai, muje koh muhammad, yace yana kamo hannun Al'ameen



"Ina da magana yallaboi"



Wace magana kuma sumayya bayan an kashe case, Al'ameen ya karasa maganar da kamo hannun sumayya su tafi





Ah ah Al'ameen ka barta muji meke tafe da ita.



Ah ah Ammar mu tafi kawai yafi



Sumayya yi maganar ki, Ammar yace bai saurare Al'ameen ba



"Yauwa so nake Amana iyyaka da kamila Amata iyyaka da mijina Arubuta a ajiye don ban yarda da ita ba wanda yayi niyar zubama acid wata rana zai dabama wuka"



Keee ki iyye bakin ki yar tamu yar daba'ce? da zata daba miki wuka wallahi karki kuskura ki kara jefin yarmu da mummunan kazafi,



Kallon d'an sandar Ammar yayi



Da sauri yace an gama sir, ku kuma daga yau ku jama yarku kunne karta kuskura muji koh mu gani tsakanin ta da sumayya koh muhammad



Suna Fita a station in motar sa suka hau sumayya a baya Muhammad a gaba da Ammar



Don Allah kuyi hakuri da abinda ya faru sannan ke sumayya gaskiya banji dadin abinda ya faru ba yara irinsu kamila da basusan kwaba babu Alkhari rigima dasu .



"Gaskiya ne Ammar ni karan kaina danasan wannan fad'ar zata kai ga haka daban fara ma tanka kamila ba"



Allah ya kiyaye na gaba



"Ameen"



Al'ameen kam kala baice ba shuru ya musu fuskar nan a hade don yau sumayya ta kular dashi tunda yake police basu taba kamasa ba yau ta janyo har station ya shiga=ØÞ kad'an ya rage bai shiga cell ba



Suna isa kofar gidan Ammar yayi packing sumayya ce ta sauka tayi cikin gida abinta



Ammar kam maida kallonsa yayi akan Al'ameen dake kokarin sauka a motar, abokina kayi hakuri don Allah kasan halin mata kuma duk da bansan ainahin abinda yake tsakanin ku da kamila ba na fahimci kishine kawai ke damun sumayya, kuma koh wace mace iyya abinda zata kwatanta kenan



Ba kome Ammar amma wallahi naji haushi sosai yau innan gashi sumayya harda Ashar



Hakuri zakayi sai kuma ka mata fad'a a siyasa karkace zaka d'aga jijiyoyin wuya, mata sha'aninsu sai su



Ba kome Ammar nagode da taimakon ka gareni ashe kai police ne?



Eh muhammad



Amma babba koh naga suna baka girma



Eh, wani aiki kake ne muhammad? kullum nazo a gida nake samun ka badai bara kake bako irin yanda wasu keyi?



Ah ah ammar ina sana'a bana bara



Sana'ar me?



Mongoro, abakin titi



Amma meyasa kullum bana ganin ka a wajen sana'ar, inna zo?



Shuru Al'ameen yayi yanajin kamar ya fad'i gaskiya kamar karya fad'a, a hankali yace jarin nawane ya karye don mangoro yayi Araha yanzun ba ciniki shiyasa bana fita



Toh dame kake ciyar da iyalin kuma?



Had'a fuska Al'ameen yayi jin Ammar na masa tambaya kamar ya masa sata



Kayi hakuri muhammad ina ta tambayar ka Abinda bai maka dadi ba



Ah ah ba kome, daman ita ke kwalliya da lalle tana mana cefene da sauran abin bukata.



Gaskiya hakan bai dace ba Al'ameen ace kana namiji mace ke d'awainiya dakai ya kamata ka samu ka dogara da kanka, zan baka jari kamar na 300k sai ka kama shagon haya tunda azumi yazo kaga zama afi ciniki kayan narmari cikin azumi ga kankana ga lemo ga sweet milo harda dabino saika had'a, kana saidawa kaga saika kula da matar ka, ita kuma kudin da take samu saita kashewa kanta da kanwar taka hakan zaifi maka mutunci a wajen mace koh bata maka gori ba, koh bata nuna wani abinba Amma dai inka kasance kaike ciyar da ita kimarka daban yake a idon ta



Ammar ni......



Da sauri Ammar ya tare numfashin sa kaje kayi shawara da matar taka yanzun dai bana son jin kome bayan kwana biyu xan dawo inji Amsar ka eh koh Ah ah kawai nake bukata.



Shikenan nagode, Al'ameen yace yana fita a motar



Ta bangaren kamila kam da bacin rai iyayen ta suka shigo cikin clinic in tana kwance akan gado inda kasan wance tayi Accident haka ta koma gwanin tausayi sai kawarta dake gefe a zaune



Amma dai ke kamila bakijin bari ba saida namiki tsakani da yaron nan ba shine tsabar rashin zuciya kika ibi kafa kika tafi gidansa harda zuwa watsama matar sa acid kamila?



Nifa mama wallahi bani bace itace ta d'auko zata watsa mini



Uban me ya kaiki gidan ta?



Koyan kwalliya naje



Kwalliyar ubanki?dabani na haifeki ba sai ki gayamin wannan zance na d'auka yarinyar da bata jiran kanta.



Habba Rabi da wanne zataji ne da ciwon da ke cinta koh da fad'anki? babanta ya fad'a



Fita mamar kamila tayi,

Kamila tambayar baban ta tayi ya aka kare a station



Bai boye mata kome ba ya fad'a mata, tare da fita a d'akin



Kamila tun farko saida na fad'a miki karki fara abinda bazaki iyya ba matar Al'ameen ba wawuya bace kamar yanda kike zatoh mace mai shikara 26 koh 25 kema kinsan bazaki nuna mata tawaye ba shiyasa nace kibi abin ta bayan gida.



Wani banzan kallo kamila tama kawar ta, kinsan Allah sadika sai sumayya tayi dana sanin sanin muhammad saina dasa mata bakin cikin da yafi wanda nake ciki, muhammad kuma nawa ne tunda nayi aure nasan dadin abin kinga yanzun na gane ba kyau koh ido ne jin dadin aure ba keda kanki kinsan Al'ameen zaije duk inda ake so,

Don haka yanzun ma jira nake naji sauki mai gabaki d'aya zan musu.



Me kike nufi?



Uhmm ba sun mini iyyaka da su ba toh Malamai zan shi.............





<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß

08146017245 *hohoho wani Kaya Sai amale shin kunsan kayatattun magungunan Mata na maman haidar*

*Kayan maman haidar basuda matsala domin traditional medicine ne Kuma anahadasu da ingantattun itatuwa masu karfi da Basu da illah*



<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß



*1 Gumbar kankana da ayu* <Ø@ß<Ø@ß

2 *Gumbar ayu zallah* <Ø@ß<Ø@ß

3 *Gumbar Madara da kwakwa*<Ø@ß<Ø@ß

4 *Kaza mekwai* <Ø@ß<Ø@ß

5 *Zabo me zuma*<Ø@ß<Ø@ß

6 *Kaza me allurai<Ø@ß<Ø@ß sahihiyar mallaka ba boka ba malam*<Ø@ß<Ø@ß

7 *Kwallin idonka inadona*<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß

8 *Tauwadar mata*<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß

9 *ketar larabawa magani me kankarowa mace kima da daraja*

10 *Maganin sanyi me fatattakarsa duk kuwa nacinsa Koda bakya haihuwa indai matsalar sanyice gwada wnnn*

11 *Maganin nono. Sahihi*

12 *Maganin hips and bobbs*

13 *hodar. Ni I'ma koramar mata*

14 *nakasan Mara babban sirri*

15 *kafi jijjibi*

16 *daga Sha Sai wanka kasaitacce magani*

17 *Dan kwankwalati namata da mazajensu Kevin Mata*

18 *matsin kinfi budurwa dubu ko haihuwa nawa kikai Babu magana*





<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß

*Maman haidar Bata tsaya anan ba*

*takawomuku hadaddan sabulun gyaran jiki da hadin dilka Mesa sheki da laushin fata gaman kitso Wanda laraba ke amfani dashi inkin gwada saikin dawo kudai kunemeta awannan number* 08146017245

<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß



<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß

>ØÑÝ
>Ø¯Ý *MATAR MAKAHO* =ØhÜ
>دÝ

~ Na ~



<ØCß *Rukayya* *Ibrahim* <ØCß



('Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa=ØLÜ

free book >Ø'Ý



Page5ã 2ã &5ã 3ã

Malamai zan shiga, ke koh yawo tsirara zanyi don naga bayan sumayya sai nayi



Amma dai kamila baki da imani habba don Allah kin wulakanta bawan Allah ya fita a Rayuwan ki sannan yanzun kice zaki wargaxa masa farin ciki ai wannan baso bane



Wace farin cikin bayan nice farin cikin sa har gobe ina da gurbi a zuciyar sa



Hhh hayya lallai kamila kina da gurbi a zuciyarsa ya hankad'aki akan matar sa koh an gaya miki so na dauwa mane a zuciya? duk mai sonka muddin baka kyautata masa toh fa kamar fure ka shuka baka ban ruwa tum tana bushewa aje aje wata rana zata mutu



Kee sadika na fahimci daman ke yar hassada ce shiyasa kwata kwata tafiyyar mu bata kyau dake



Nidai gaskiya nake fad'a miki kamila kuma gaskiya d'aya ce da wannan haukar ai gwara kije garesa da soyayya koh xai dawo ku daidai ta kinga sai ayi na biyu dake



Ina ma yake fita kullun yana gida, naje inda akace min yana bude sana'a ma naje Amma shuru bantaba ganin sa ba, kuma ni nafi karfin kishi da sumayya sai dai ta fita tabar min shi



iii in kamila karkije kikai kanki a mahallaka wallahi wani rabon kashe ki zaiyi



Ya kashe ni mana indai akan Al'ameen ne kowa ma ya mutu



Wallahi badai kowa ba, nidai mai sonki ce zan fad'a miki gaskiya koh kinki koh kinso rabuwa da bayin Allah nan shiyafi miki mutunci Akasinsa kuma bismillah zaki ga.





Bakin ki ya sari d'anyen kashi ba abinda zan gani sai Alkhari



Ai baki neme Alkharin ba mutumin da keson kashe Auren wasu shine zaiga Alkhari?tace tana

Mikewa tayi ba tare da tajira Amsar kamila ba tayi mata sallama ta fita a asibitin





Sumayya na shiga cikin gidan kofar su ta wuce da mamaki take kallon kadija dake zaune tana rusa kuka"ke khadija lfy"?



Da gudu ta tashi zuwa wajen sumayya rungume ta tayi tana kuka'Aunty ina yaya? ina dawowa daga makaramta ake ce mini wai an tafi dake da yaya,.



"Babu inda akaje damu khadija yayan ki na waje shine kika kama kuka koh uniform baki cire ba kika zauna haka"



Toh ni Aunty fisabililah yazanyi na cire uniform yayana da Aunty na na station



"Toh gani na dawo ki ibi ruwa kiyi wanka na baki kaya kisa dai dai yayan naki ya shigo"



Toh kawai tace tana d'aukar boket, wanka tayi sumayya ta bata kayanta ta saka abincin da suka girka na karyawa daba su ciba shi ta ibawa khadija



Khadija na cikin cin abinci sai gashi ya shigo da sallama



Amsa wa khadija tayi hade da gaidashi, yaya sannu da zuwa



Yauwa khadija ya makarantar



Lafiya yau subject 6 aka mana a rana d'aya Assignment biyu



Masha Allah ki gama ci sai muyi assignment in





Hhh yaya ka iyya ne?



Toh khadija ba nayi secondary ba koh azatan ki duk abinda na koya ya gudu ne?



Yi hakuri yayana



D'akin ya shiga sumayya kam daman tana kitchen



Bayan khadija taci abinci wanke uniform nata tayi ta shanya,school back nata ta d'auko ta bude Assingment ne aka busu na physics sai English, yaya na gama inzo muyi Assingment in?



Bara na fitoh khadija,



Toh yaya



Fitowa yayi suka zauna a dakali sumayya na kallon sa yana ma khadija bayanin assingment in yanda zata fahimta sannan yana fad'a mata Amsa tana rubutawa



Bayan sun kammala gida khadija ta tafi tabar uniform nata a shanye, mikewa yayi ya ibi ruwan wanka ya shiga yana fita yayi Alwala ya wuce masjid



Bayan fitarsa da ido sumayya ta bisa haka kawai yau taji tana jin shakkarsa sosai abinci ta juye a kula takai d'aki tayi sallah sanin baya dawowa sai bayan isha yasa tayin wanka d'akin ta shiga zani fille da T-shirt ta saka sai hulan bacci. TV ta kunna tana kallo gabaki d'aya yau ta rasa nutsuwar ta gabaki d'aya zuciyarta cike yake da tsoro



Bayan ya dawo sallah abinci ta gabatar masa baiyi magana ba kawai ya zauna ya fara ci



Itakam taji ba dadi koh fad'ane ya mata akan wannnan shariyan ba karamin damunta yake ba



Bayan sun kammala cin abincin wanke baki sukayi, Al'ameen kwanciya yayi a gadon yayi shuru baice mata kome ba



Sumayya dake kwance a gefensa hawaye ne ya cika a idanunta itakam ta shigesu da mutumin nan



Sunfi, minutes 30 a haka baice kome ba itama batayi magana ba Amma kowa yasan d'an uwansa baiyi bacci ba



A hankali sumayya ta matso garesa kwanciya tayi a gabansa sosai ta shige jikinsa



Al'ameen yana jinta kala baice mata na shuru kawai yayi don so yake ya mata horo ta ruwan sanyi yanda gobe baza tayi

Abinda bayaso ba.



Hannu tasa a hankali ta na cire botur in shirt insa nan ma baiyi magana ba



"Ni da wannan fushin ai gwara duka da wannan shariyan"



Kala baice mata ba sai kama hannunta dayayi wanda ke yawo a jikinsa



"Dan Allah ka kulani"



Kinsan Allah sumayya in baki rabu dani ba sai na sauka a gadon na koma kan kujera habba Ana dole ne?



"Kayi hakuri bazan kara bafa"



Sauka yayi niyar yi da sauri ta riko sa hade dasa ihu"wallahi nidai ban yarda ba kayi hakuri toh na tuba"



Fasa saukar yayi ya koma ya kwanta itama kwanciyar tayi a gabansa sosai ta mannu a jikinsa



Haka suka kwana tsakanin su babu shiri sumayya dai na makale da muhammad duk yanda yaso cireta a jikinsa taki



Washe gari haka suka tashi salam Al'ameen yasha mata mur sosai duk yanda tad'au abin da sauki abu fa ya wuce nan don da gaske muhammad yake



Bayan sun karya ta d'aga ido tana kallon sa"yayan khadija"



Na'am



"Daman maganar make-up inda zan ma yar kanwar Deputy ne saboda tsaro bazasu iyya zuwa ba shine wai naje na musu a gida har kwana biyar ana biki"



Saikin dawo kawai yace yana fita a d'akin



Sosai shariyan Al'ameen ya damu sumayya, haka dai ta lallaba ta shirya tad'au hijab nata ta saka rufe kofar tayi ta fita.



Bakin titi ta tsaya idonta ya sauka a kan Al'ameen ne zaune a bakin masallaci kusa da masu bara suna hira dasu, kara sowa tayi inda suke bakin ta d'auke da sallama, "Assalamu Alaikum"



Mutanen bakin masallacin gabaki d'aya suka zubawa sumayya ido suna mamakin ina zata, wa'alaikumu salam su Al'ameen suka had'a baki wajen Amsawa shikam cike da mamaki meya kawo sumayya gunsa bayam tace gidan deputy zata, tashi yayi ya matsa gefe



Binsa sumayya tayi inda ya tsayan ba mutane, itama tsayawar tayi batace kome ba



Lafiya?



"Lafiyar kenan koh laifine in nazo wajen ka"?



Babu laifi...



"so nake ka rakani"



Rakaki ina?da mamaki a fuskar sa



"Gidan da zanin mana"



Hala baki gani ne?



"Ah ah ina gani so nake ka rakani"



Bazani ba, yace yana tafiya



Ai da sauri sumayya ta riko rigansa



Keee menene haka? koh baki ganin a gaban mutane muke ne



"Toh sai me in a gaban mutane muke koh ba mijina na rike ba kuma wallahi in baka shige mun tafi ba saina rungume ka a gabansu"



Uhmm Allah ya kyauta shige mu tafi





Mutumin da ke saida ruwa kusa dasu Al'ameen ne ya dubi abokin sa, Kai Amma yariyar nan bata da kunya har masallaci zatabi miji bata maji kunyar idon mu ba muna zaune? wama yasan dalilin da yasa aka aura masa yarinya kamar wannan?



Gaskiya ne haruna daga gani idon yarinyar a tsatsaye yake..





Haka sumayya tasa muhammand a gaba har gidan kanwar deputy har falon baki aka kai Al'ameen aka had'asa da abin motsa baki sumayya kuma ta shiga falon matan gidan



Har yamma suna gidan sallah kawai ke d'aga Al'ameen yaje yayi ya dawo



Sai kusan 5:43 na yamma suka fitoh gida gaskiya sumayya ta yaba da karamcin y'an gidan don Take Away na abubuwan da aka shirya na biki aka iba mata" yanzun ina zamu"?



Sama jannati zamu, Al'ameen ya bata Amsa



"Ni kake fad'awa bakar magana"?



Eh an fad'a in ai nafi mai Ashar kuma bakar ma agunki na koya



"Badai aguna ba kuma in kayi tsiya saina gudu na barka ka bata"



Kanki kika ma Asara bani ba.



"Akan me xan ma kaina asara kuma"?



Aikan mijin da kike dambe mana



"Dambe ni banyi dambe akanka ba"



Au habba daman tabaryar ta burgane?



"Ai na razana tane, karka wani zata fad'a nake akanka"



Na nawa kuma.



"Allah ba wani"



Ke kika sabi dai mutum sai taurin kai



"Kamar kai"



Shuru ya mata don ya fahimci sumayya inya biye mata fuskar da ya d'aure bazai san lokacin da zai sake ba.



Keke suka hau suna isa gida ana kiran mangari ba masalaci ya shiga ita kuma ta wuce cikin gida



Bayan ya dawo sallah take Away in ta bude musu donut da kaza rabi sai drinks d'ayan take away in kuma fried rice ne da lafiyayyen naman shanu suna kammala ci, muhammad kam kwanciyan sa yayi



Sumayya TV ta kunna ta koma ta kwanta tana kallo a kwance"yayan khadija"ta kirasa tana kallonsa ganin ya natsu waje d'aya yana tunani, jin bai Amsa ba yasa ta dafa kafad'an sa



Da sauri yace Am Ammar kudin nan basuyi yawa ba, sai kuma da sauri ya fara kame kame don sam subutar baki ne abinda ke zuci shiya fitoh fili



"Wani kudi kuma Waye Ammar"?



Am ba kome.



Akan me zakace ba kome duk kabi kasa kanka a damuwa in ma bashi ake binka bazaka fad'amin na biya ba duk kudin da nake tarawa Wallahi tatali nake maka naga kudin yayi yawa sosai kafun na baka ka kama sana'a mai d'an kauri mu samu murufawa kan mu asiri, amma ina dalili ina dana rufin asiri kabar kanka a rikici"



Ba haka bane sumayya ba'a rikici zansa kaina ba wannan magana ne daban.



"Wace magana kenan?koh bankai naji damuwar kaba"?



Daman Ammar ne ya mini magana jiya zai bani jari dubu d'ari uku na kama shago kafun azumi tunda saura sati biyu ne ga kayan marmari a azumi akwai kasuwa.



"Bazai yuba wani ma Ammar inne d'aya? akan me zaice zai baka kudi tun da baisan zai Taimake kaba sai yanzun"



Sumayya bamu fa dade dashi ba kuma insha Allah ba abinda zai faru



"Gaskiya ban Amince ba ka bari inna gama had'a kudin saina baka kabar masa nasa"



Gaskiya sumayya gwara na karbi nasan kawai na gwada kasuwar tunda ba kyauta yace ba koh bashi saina tambaye sa in kyauta ne ni karan kaina bazan Amince ba Amma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login