Showing 63001 words to 66000 words out of 122551 words

Chapter 22 - MATAR MAKAHO COMPLETE HAUSA NOVEL

07 Sep 2024

16744

ya aje kulan hannun sa da plate da shukula, sai kuma gashi ya dawo dauke da flask da cups, ajewa yayi a hankali akan cafet ya zuzzuba doyan da kwai sai yaji a gefen plate ya tsiyaye tie a kofuna



Itakam sumayya sai ido kalala take kallonsa dashi"wai duk wannan kaika soya"?



Eh man bakin raina ni ba an gaya miki in mutum baida ido shikenan sai akace bazai iyya abinda masu ido keyi ba, ai harma yafi namasu ido muna iyyawa



"Ah ah kwadai kwatanta Amma badai yafi ba malam"



Au karya zan miki kenan?



"Bance ba,ina nawa doyan naga ka zuba plate d'aya"?



Eh namu ne yau tare zamuci a plate d'aya



Sumayya batayi magana ba sauka kawai tayi akan kujeran hannu kawai tasa ta fara cin doyan " kai maggi yayi yawa"



Kiji tsorin Allah fa sumayya



"Toh da tsoron ka zanji"



Amma dai k'wan nan babu maggin da yaji inba sharri ba



"Nikam naji, k'wan maggi ga Albasa doyan kuma bai soyu ba, tie in kuma sugar baiji ba"=ØÞ



Hannu yasa ya d'auke plate in gabanta da cup in tie in ya rike a hannunsa



"Yaya haka kuma"?



Ki miko mini kudi inje in sai miki abinci amma badai wannan zakici ba kowa ma ya hakura Almajiri zan kira na bawa, karasa maganar yayi yana shirin fita a d'akin



Da sauri sumayya ta biyosa hade da kamo rigansa"dan Allah yayan khadija ka aje abincin mana waikai bakasan wasa bane?wasa fa nake maka"



Wasa koh?toh ni da gaske nake kuma sakar min riga karki yaga



"Habba don Allah yaga riga sai kace wata mai farashunan mayu"



Toh waya sani



"Yasan me"?



Sakarmin riga hajiya



"Ayya ka bani abincin mana wallahi wasa nake doya yayi d'adi haka tie ma k'wai innan inda kasan dafin Turai"



Mika mata plate in yayi shima ya koma ya zauna abinci suka cigaba daci



Bayan sun kammala ci yaukam ita ta d'auki kwanuka, bayan ta kaisu waje brush tayi shikam Aswakin sa ya d'auka ya goge bakinsa d'akin suka koma kayan bacci sumayya ta saka rigane da wando cotton mai laushi da socks na sanyi a kafarta, jin an fara yayyafi yasa Al'ameen fita waje ya tattare musu ruwa

shima kayan baccin sa da sumayya ta sai masa ya yasa



Sumayya gado tahau iyafis ta d'auka ta jona da wayan ta ta manna a kunne tana kallon film a ciki



Shima bayan ya gama shiryawa d'akin ya rufe ya hau kan gadon, tattaba kan gadon yake har yaji ya tabota kwanciya yayi kusa da ita yasa hannu ya zame hular kanta



Hannu tasa ta cire kunne d'ayan ta makala masa a kunne



Kwanciya yayi akan filon da take gabaki d'aya ya nutsu yana sauraron abinda ke kunnensa, sai kuma yasa hannu ya taba sumayya hade da kiranta, sumayya!



"Na'am"



Uhmm Amma wannan indi'an film ne koh?



"Eh..ya akayi ka gane"?



Muryansu mana duk da Turanci suke magana amma dai sai kiji suna maganar sari koh bauta



"Gaskiya ne kasan sunan film in"?



Ah ah



"this is fate, watoh kaddarar Rayuwa na Arewa 24"



Oh film in karam koh?



"Eh shine ma ke magana yanzun"



Ai da sauri ya zare abin kunnesa tare da sa hannu ya zare na sumayya, kinsan Allah bazaki kalli film innan ba



"Ikon Allah akam me bazan kalla ba"?



Nidai kawai bazaki kalla bane.



"Toh me kakeso na gani"?



Wani film banda wannan



"Uhmm nikam gaskiya shi nakeson kallo" tace hade da karban abinta ta mayar kunne



Da sauri ya fizgo abin gabaki d'aya ya had'a da system in yana kokarin sauka akan gadon



Da sauri sumayya ta cakumosa baya hade da kokarin karban system in



Duk yanda taso kwatar abinta abin yaci tura duk inda tayi saiya zillar da hannunsa karshe ma hakura tayi takoma gefe tana maida numfashi



Tashi yayi jin ta kwanta, zuwa yayi ya aje system in akan kujera, ya dawo ya kwanta abinsa



Ganin ya aje yasa ta saurin mikewa zaune cikin azarbabi take kokarin sauka ta gefen kadon a hankali, tana sauka saboda matsen d'akin yasa dole saita biyo ta bangarensa kafun taje kan kujera, a hankali take tafiya



Shikam tun tashinta zaune da saukarta duk a kunnensa shuru kawai yayi yana son ganin gudun ruwanta



Tazo daidai dashi har zata gifta a bazata kawai taji ya fisgota baya ta fad'a kansa



Kokarin tashi take, ya sake maidata, wai sumayya meyasa ne bakijin bari sam



"Me nayi kuma"?



Yanzun ina zaki?



"Waje zan fita"



Me zakiyi a wajen?



"Fitsari mana koh an hana fitane in aka kulle kofa"



Jin amsar da ta basa ya saka hannu ya mannata da jikinsa sosai kamar zai maidata ciki



Karan shagwaba ta sake da karfi"wayyo"



Ke menene haka saikin tara mini jama'ane



"Toh ba kaine ka matseni ba"



Toh ai ke ince bakiji koh kad'an kannan naki taurine dashi fa



Eh naji kaina taurine dashi kuma ni ka sakeni fit.........



Bai bari ta karasa ba kawai ya manna bakinsa da nata sosai yake kissing inta yana dad'a matsota garesa kamar zai maidata ciki



A hankali tasa hannu ta kama kansa da karfi ta danke gashin kansa masu yawa sosai, hade da ajiyar zuciya



Washhh ashhh kawai Al'ameen yace bayan ya zame bakinsa a nata, hannu yasa ya kamo hannunta data rike masa gashi ya d'aura a kirjinsa, da sauri ya maida bakinsa cikin nata



Sosai yau sumayya da Al'ameen suka farantawa junansu duk da tafiya tayi nisa sumayya ta copsa Shi kuma Al'ameen tsoro.



*RANAN MONDAY*

Yaune fa hajiya khadin Goggo zata makaranta jiya koh baccin kirki bata iyya ba, da sassafe ta tashi tayi wanke wanke shara kafun 6:00 har tayi wanka dumamen da goggo ta duma shi taci, uniform nata tasa fari kal wando da hijab harda riga duka farare ne socks ta saka fari ta d'aura bakin d'an kwali(kallabi)ta zura hijab, sandal inta da Aunty ta tasai mata kala biyu d'aya =Ø_Ü ne d'aya sandal, =Ø_Üin ta d'auka bakine shima don a dokar makarantar baki da fari suke so, tasa a kafarta sai agogo shima baki turare ta fisa fuskar nan washe kamar gonan Auduga takema goggo sallama hade da d'aukar school back nata shima baki mai kyau, ta fita a gidan



Sumayya da Al'ameen ne a kitchen suna girkin karyawa kamar kullum yauma hakan take watoh ana aiki ana fad'a



Assalamu Alaikum



"Wa'alaikumus sallam, yan makaranta"



Kai Aunty ina kwana?



"Lafiya khadija harkin shirya gaskiya ne Allah yasa hakan ya d'aure banda littin"



Ameen Aunty, ina kwana yaya?



Lafiya khadija harkin shirya?



Eh yaya na shirya



D'aki sumayya ta shiga naira 200 ta d'auko sai drinks d'aya da goran faro d'aya ta fitoh "ungo khadija wannan kudi yayanki ne ya bada na baki koda zaki zo ya fita ashe da rabon zaku hadu ma kihau keke sauran d'arin saiki rike a hannunki ga wannan kuma kisa a school back naki kinji, banda kawayen banza banda abota da maza kinga makaranta ne da Christian sukafi yawa sosai kuma benchi d'aya ake had'a maza da mata don haka babu ruwan ki da yaran Christian abinda ya kaiki shi zakiyi kinji ki maida hankalin ki akan abinda ya kaiki Allah ya tsare mana ke"



Hannu khadija tasa ta karbi kudin da drinks in hade dama sumayya godiya, yaya na tafi



Al'ameen kam ya rasa ma me zaice da sumayya sumayya Alkhari ce garesa matar rufin asiri, toh khadija saikin dawo kindaiji abinda Auntin ki tace miki koh?



Eh yaya..



Adawo lfy



Bayan fitar khadija sumayya kam kitchen ta koma taci gaba da aikin ta Al'ameen na tayata



Assalamu Alaikum



"Wa'alaikumu salam" sumayya ta amsa tana fita a cikin kitchen in da sauri jin muryar wance ke sallamar



Aiko itace da mamaki sumayya ta bita da kallo,

Al'ameen ma da sauri ya fitoh a kitchen in jin muryar me sallamar



"Lafiya" sumayya ta tambaye ta



Eh lafiya daman n................







<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß *Albishirin ku Mata ku marmaso kuji sirrin,Koh kinsan mace sayanzunshi da gyara* =Ø Þ





<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß *Turare suna d'ayace Amma sun banbanta kowanne da ingancinsa kamshinsa da aikin sa*



<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß *Ina muku Albishir da UMSAD INCENSE Dan samun turaruka masu kamshi da* *gyara*



<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß *Tabbas Turare sirrine ga Koh wace mace*



<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß *Gamai bukatar turarukan UMSAD INCENSE*



<Ø@ß *Na tsunguno(habil)*

<Ø@ß *Na jiki (kwalaccam)* ( *khumra, black & white* )

<Ø@ß *Turaren turara jiki after birth* ,

<Ø@ß *Na d'aki(halud Al'oud)*



*UMSAD INCENSE suna kofar waika wajen Ado bayaro layout Kano State* =؃Ü<Øüß=؃Ü<Øüß



<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß *Suna bada d'aya Koh sare akan farashi Mai Rahusa*



<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß *Suna bada order kayansu Gamai bukata aduk jahar da yake a fadin Nigeria*



Contact them vie

>Ø€Þ08028827241 or 09033791049

IG @umsadincense



<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß<Ø@ß

>ØÑÝ
>Ø¯Ý *MATAR MAKAHO* =ØhÜ
>دÝ

~ Na ~



<ØCß *Rukayya* *Ibrahim* <ØCß



('Tsokaci wannan shine novel na farko Koh da za'a ga mistake Koh typing error Amin afuwa=ØLÜ

free book >Ø'Ý



*HAPPY INDEPENDENT DAY* <ØóÝ<ØìÝ



Page5ã 0ã &5ã 1ã

Lafiya daman nazo akan maganar make-up inne, naji shuru baki kirani ba inna kira ba'a picking call in.



"Ok toh ai na zaci koh kina da fahimta ne, ki gane me nake nufi"



Kamar ya sumayya ban gane ba?



"Ok toh kamila bara na miki gwari gwari, bazan koyar ba"



Akan me? bayan kince sai mijinki ya yarda kuma a gabanki yace ya Amince.



"Eh ya amince nima haka yace mini sai dai ni ban Amince dake ba har kizo gidana kina kare mini tanadi"



Kamar ya bangane ba me kike nufi?zanzo gidan ki in kare miki tanadi?ina ma gidan yake bare



"Hhhhh hayyeeee nanayeeee ashe gidan ba yanda yake akazo cin moriyan masu shi"



Ke sumayya nafiki rashin mutunci don naga baki dashi ya daga abin Arziki sai tsiya ya biyo baya matsalanka da matsiyaci kenan bai gaji arziki ba





"Ehhhhhh yariya tsiyama waje ya samu ki kalleni da kyau daga ni har mijina kinga Alamun yunwa a tare damu, kuma ki kallen sama da kasa koh uwar ubanki bataci arzikin da naci ba harta mutu ke uwarki data aure ubanki har yanzun bataci arzikin danake ciba.



A'uzu sumayya wani rin , zagine haka kar in sake jin kin tanka mata shige ki wuce d'aki, don Allah kamila kiyi hakuri



Kutt ni kike xagi? ai kamila super tayi da jakarta tayo kan sumayya da mugun sauri



"Sumayya da gudu tayi kitchen tabarya ta rarumo ta rike"don uwarki kizo yau saina rusa miki kai shegeya harni zakima bariki kizo mini da yaudara da sunan koyan kwalliya"



Ai da sauri kamila taja birki, in ba tsoro ba ki aje abinda ke hannunki yau saina nuna miki true colour na.





"Shegeya akan me zan aje nasan dame kikazo kizo kima mijina asara a banza "



Shammatar sumayya kamila tayi tana magana, da sauri tayi kanta gadan gadan da kwalba a hannu



Ai ji kawai tayi Al'ameeen ya hankad'ata gefe, don duk abinda suke hankalinsa na kansu, keee kamila kin isa kizo har gida kice zaki bugarmin mata kimin asara akan me? Ke kin kini na samu mai zama dani shine zaki bugeta



Wayyyo nashiga uku na lalace wayyo hannu na innalilahih kun kasheni, kamila ke ihun nan tana rike da hannunta wanda Acid ya zube mata akai



"Subahanallah daman abinda kike da niyar watsa mini kenan Algunguma shegeya, aikokin watsa min bashine yake nufin karewar auren mu ba tunda ba idone dashi ba bare yaga yanda na koma"



Sumayya meke faruwa ne haka meya sami hannun nata naji kina cewa zata zuba miki



Kamila kam ihu take kamar ranta zai fita



Ihun kamila shiya jawo da hankalin jama'ar gidan kofar su Al'ameen, da sauri daga maza har mata yara da manya suka nufi kofar donjin ba'asi



"Ruwan Acid tayi niyar watsa mini Allah yasa ka shureta shine ya zube a hannunta hannun sai d'ayewa yake"



Subahanallah Al'ameen yace yana nufar inda kamila take, kee kamila tashi muje asibiti tashi tashi yau an bonu





Kaiii karka kuskura ka taba ta kaji na fad'a maka, keee Kinsan su waye a gidan nan har kika iyya d'aukar Acid zaki zo ki zubawa mutum a cikin gidan Adara? kutumar uba iro yace yana nufar kamila



Salame ce ta Lailayo Ashar ta maka, Ci ubanta dan uwarta(wa'iyyazu billah) koh dabban gidan Adara bama bari aci zalinsa bare mutum



Ai kafun Al'ameen yace wani abu tuni iro ya fara wanke fuskar kamila da ruwan maruka ji kawai kake kauuu kauuuu kauuuu





Ihun kamila ke tashi yanda kasan ranta zai fita bugunta suke tana kokarin gudu wasu su kamo ta, Al'ameen karan kansa hankalin sa ya tashi da kukan ta kamila keyi duk yanda yaso kwatarta abin yaci tura karshe ma salman turesa yayi saura kad'an ya fad'i sumayya ta taro sa



Jama'ar kofar gida su suka shigo gidan jin kukar mace kamar me, shigowa sukayi ganin abinda ke faruwa yasa su rugawa a guje suka kwace kamila



Ai kamila na ganin ta tsira da wani irin matsifeffen gudu ta falla waje kamar walkiya ga hannu duk ya d'aye fatar



Bayan gudun kamila suwaiba ce ta d'auki jakar kamilar, Kai Allah ya mini ga jaka mai azaban kyau maybe ma harda cash a ciki, takara sa maganar da fita a kofar





Bayan fitar jama'a a kofar Al'ameen rai a bace ya fara magana sumayya yanzun kin kyauta fisabilillahi daga abin arziki saiki kama zagin yarinya



"Ok watoh laifina kake gani kenan na zagi budurwan ka koh"?



Waike sumayya meye haka duk wacece ummulkaba'isin wannan matsifar tun farko me yasa zaki zageta akan wani dalili yanzun mutuncin kine ashar koh zamanki a gidan nan ne kika koya, ni fad'a nake miki a matsayina na mijinki ba saurayin kamila ba, yana karasa maganar yayi d'aki ya barta tsayi kamar an dasa ta



Sai yanzun sumayya tayi data sanin biyewa kamila koh yaushe kamila tazo gidan saita had'ata fad'a da mijin ta ina bazai yuba, kitchen in ta shiga taci gaba da ayyukan ta, don batason basa hakuri yanzun ganin ransa ya baci sosai





Da misalin karfe 11:20 saiga yan koyan make-up inta sunzo a waje suka zauna ta shinfid'a musu taburma suka fara training don yau kwanan su biyu da fara koyo





Jin d'uriyar jiniyar motar yan sanda sukaji ya tsaya a kofar gida, ba'a wani jima ba saiga matan yan sanda sun shigo gidan har kofar su sumayya



Sallama dai...



"Yauwa sannunku da zuwa lfy"?



Lafiya ba lau ba don duk wanda yagan mu baiga lfy ba, wacece sumayya?



"Ikon Allah nice wani abinne ya faru"?



In munje station zakiji dalili, shige muje d'ayar yar sandan tace tana kokarin kama hannun sumayya



Da sauri sumayya ta fizge hannunta tare dama police in kallon banza, babu inda zani wallahi akan me banyi kome ba Awani ce za'a tafi dani





Babu wanda zai tafimin da mata ba tare da sanin laifinta ba, Al'ameen da yafitoh d'aki da sauri yake fad'a musu haka



Kai ka iyye bakinka fa kasan a gabansu wa kake babu ruwan mu da makantar ka wallahi koya maka hankali zamuyi.



Sannu uwar sa koya masa hankali na rantse kika tabamin miji ubanki za'a taba, station ne dai baza......



Bata karasa ba taji saukar mare tasss a fuska police in ta tsinketa dashi ai kafun ta sauke hannunta Al'ameen ya watsa mata rabonta itama duk da ba'a fuska ya saita ba amma ta maru kam



Kutturu hukuma ka mara yau daga kai har matar taka sai munga gatan ku a jala yau innan, waya tayi wasu mazan yan sanda biyu suka shigo aka rufuwa Al'ameen da sumayya da karfin cin tuwo za'ayi waje dasu Al'ameen kam anfa kasa tafiya dashi sai kokuwa suke, yau sunga ikon Allah kama MAKAHO ya gagare su sumayya kam an fita da ita waje bayan ta sanya hijab



Ammar ne yayi packing mota da sauri ganin yanda jama'a suka cika kofar gidan ga sumayya an tisata a gaba cikin sassarfa ya karaso wajen yana tambayar ba'asi ganinsa da daula yasa police in saura ransa suka masa bayanin sunzo kama sumayya ne Al'ameen ya mari police



Cikin gidan Ammar ya shiga da mamaki yake kallon Al'ameen dake ta fama da police da sauri ya karaso wajen hannun Al'ameen ya kama ya rike hade da kiran sunan sa



Tsayawa da kokuwar yayi, Ammar kaine?



Eh wai meke faruwa ne, meka musu?



Wallahi ba musan me muka musu ba daga zuwa wai zasu tafi da sumayya na tambayi dalili wai sai munje office insu kajifa.



Gaskiya ne Al'ameen ba'a fad'awa mutum laifinsa sai a station kazo muje ba abinda zai faru mundin kaine da gaskiya



Binsa Al'ameeen yayi police kam sai hararan Al'ameen suke da kitsima irin dukan da zaisha a hannunsu in ya shiga cell



Alfarma Ammar ya nema a barsu sumayya su shiga motar sa inyaso sai police shigo ciki



Bayan an isa station kenan officer ya had'asu da iyayen kamila a office insa sannan ya kalli sumayya, an kawo mana karanki kinyi kokarin zubawa wata Acid a fuska Allah ya kiyaye ta, ya zube a hannu bayan haka baki barta ba kika mata duka yanzun haka tana kwance a police clinic don haka zamu rikeki anan don iyyayenta zasu kai kara kotu



Amma dai yallaboi kafun a kamata ai sai an tambaye ita sumayyar ba'asi itama aji tata jawabin sannan kamila ta kawo shaida ku kuma saiku kamata ku rufe, Amma daga fad'a muku magana kuma sai ku rufe mutun ba bincike haka ake Hukunci?Ammar ne ke maganar yana nuna officer in



Toh kai kuma malam asuwa har zaka nuna mini abinda ya dace nayi koh kafini sanin doka ne?



Ban fika sani ba haka zalika bazan barka ka rufe baiwar Allah ba dalili ba akan me?



Kai malam dakata kasan a gaban wa kake kuwa? d'aya daga cikin police in yake Tambaya Ammar



Koma waye ne shi, nadai gama magana sumayya fad'a musu menene Ainahin abinda ya faru



Sumayya ba tsoro ta bayyana gaskiyar hakika nin abinda ya wanzu tsakaninsu da kamila



Kuna daiji koh asalima kamilar ce bata da gaskiya koh a hukunce wanda yazo ya sameka har cikin gidan ka kuma yajaka da fad'a kome akai masa shiya kai kansa, sannan a maganar nan ba ruwan sumayya haka zalika Al'ameen bada niya ya zubar da acid in a jikinta ba haka zalika itace take kokarin cutar masa da mata kunga kenan duka wannan abinda ya faru ba ruwan sumayya da Al'ameen duka, kuma jama'ar gidan ne suka mata basu ba ya karasa jawabin yana bin officer in da kallo





Kaima ai yanzun gashi ka yanke hukunci ba tare

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login