Showing 60001 words to 63000 words out of 214110 words
da biro, ya yi rubutun magananun Jabir, da wanda su Baban Tsakiya suka yi da ya ji a harshen Dada.
Da irin manufar ba shi Yabi. Da yadda ake fatan ta tabbata cikin halin ni 'ya su.
Sai kuma ya je shafi na gaba sosai ya rubuta "Zan yi komai na halal dan na sauke nauyin da yake kaina.!
Allah ka sani ban sake aikata zina ba! Allah ka taimake ni ka cigaba da tsare ni.
Allah ka fahimtar da ni sarrafa mace ta yadda Yabi zata rayu cikin farin-ciki a hannuna.
Allah ka hore mini kofofin arziki ta yadda zan sauke nauyinta ba tare da tallafinta ba.
Na sani al'kawarin ka baya tashi, da kanka ka yi al'kawarin taimakon wanda ya k'udire niyyar aure saboda kai. Ga ni bawanka, Ibnu bawanka cikin kankan da kai, ka taimake ni, ka kubutar da ni kunyata a idonta da na dangimu. Allah ka hore mini lafiya, ka sanya mini hakuri akan sha'anin ta, sannan a mallaka mini zuciyarta da tunaninta." Sannan ya rubuta kwanan wata.
Ya rufe yana jin girman k'alubalen da yake gabansa.
Wani irin son ta da tausayinta yana sake bin dukkan jikinsa yana kutsawa.
Har yake jin anya akwai wanda ya so mace kamar yadda yake jin son Yabi ya sake shak'e shi a yanzu?
Domin shi son ta yake yi babu wani dalili na sha'awa ko na burge wa.
Na farko yafi son manyan mata masu manyan halittu. Yabi kuma yar mitsil mai k'ananun halittu, maimakon ya ga ba hakan yake so ta zo ba. Sai yake jin ko bata da komai na cikar mace yana sonta a hakan.
Na biyu yafi son mace mai sanyin hali, mai kawaici.
Amma daga ranar da aka jefa masa sonta shikenan ya ji da tsiwarta zai yi amfani wajen kutsawa dan ya sami kusanci a zuciyarta.
Ya sani ba zai yarda da rashin kunyar da ta wuce ka'ida ba.
Amma yana fatan a cikin rashin kunyarta ya dinga isar mata da sakwanni masu girma.
Na uku akan abin da aka yi mata na tirsasa Jabir auren Maijidda, da kuma yadda uwar Nasiba ta ture komai na zumunci ta fadi maganganu marasa dad'i a gaban mahaifiyarsa! Shike nan ya k'yamaci auren zumunci.
Amma a yanzu yadda yake jin Yabi zai iya yin komai dan ya same ta.
Ya gamsu tausayi da sonta sun masa rubdugu.
Ya rufe littafin ya mayar da shi ma'adaninsa.
Ya jima a zaune yana ta tunanin sana'ar da zai fara.
Ya saki gauron numfashi! A fili kuma sai ya ce "Allah ka hana Tijjani sanya Yabi kuka! Allah ka hana ni zaluntar ta. A hore mini ita ya Ubangiji".
Ya zabura ya mik'e yana ganin lokaci ya yi da zai daina buga buga ya samu tartibiyar sana'ar da zai dogara da ita tunda nauyi mai yawa ne zai hau kansa, wata'kila ma badi war hakan yana shirin zama Abba.
Murmushi da kunya suka subuce masa ya dinga sosa k'eyarsa tamkar yana gaban manya ne.
A fili ya furta wa ya ga "Yabi as uwa?"
Sai dariya ta sosai ta kama shi, har bacin ran da Jabir da Dada suka cusa masa ya yi sauki.
Ya fito ya nufi wajen Alh Tsoho magini dan ya ji ko zai masa hanyar samun aikin ginin.
Yana tafe sanye da yadi na wando da riga bata kai guiwar sa ba.
Kamar kullum a wanke suke amma fa babu guga.
Sannan ya saka hular sanyi ya rufe gashin kansa.
Domin tunda aka furta za'a bashi auren Yabi. Bai sake yarda an ganshi da gashin kansa ba, duk da ya ki aske wa.
Ba wanda yake jin kunyar ya ganshi da sumar irin Baban Marina. Domin ya sani baya so, ya sha tisa shi a gaba ya saka a masa askin akan dole.
A yanzu kuwa wata irin kunyarsa yake ji ta sosai domin bayan kawunsa ne da yake yi masa adalci, yanzu shirin zama surukinsa yake yi.
Bulkachuwa da kansa ya yi amannar ba dan zuciyar Baban Marina irin ta daddako ba ce da ba za'a yi masa wannan k'arfin akan diyarsa ba. Ba dan alherinsa mai yawa ba ne, da ba zai ba shi aure ba, komai za'a yi kuwa.
Amma ya yi shahadar ba shi, babu dogon turanci. Yana tafe yana fa'din "Allah ka fitar da Tijjani kunyar Baban Marina".
Ya sha kwanar shiga cikin wani kwararo sai kawai ya fara jin k'amshin turaren da yake ji a jikin Yabi da kuma wanda yake shaka a jikin Jabir.
Ya shiga sai kuwa ya hangosu kowannensu jingine a garu.
Wani irin tashin hankali ya ziyarce shi.
Kishi mai tsananin gaske ya dabaibaye shi.
Tamkar ya juya sai kuma ya tsinci kansa da tunkararsu.
Ya zuba musu ido. Yabi na kuka sosai yayin da Jabir idonsa ya kad'a ainun.
Sau d'aya za'a kallesu a gane suna cikin tsananin soyayya da kuma halin cankacakare.
Ya kalli Jabir da yake tsab da shi cikin shadda ruwan toka ta sha guga. Farin gilass ya mak'ala.
Ga k'amshi mai da'di na tashi a jikinsa domin komin hassada baka isa ka ga wani abu na rashin tsabta ko gayu a tare da Jabir ba.
Yayin da Yabi take sanye da hijabanta har k'asa sai dai duk ya b'aci da hawaye har da ba'kin kwalli.
Kishi sosai ya turnike Bulkachuwa.
Har ji ya yi zukar numfashi na neman yi masa turjiya.
Amma a hakan ya motsa k'wanjinsa ta hanyar cewa "Jabir na tabbatar babu jahilci a tare da kai tunda ka yi zurfi a ilimummuka daban daban. Sai dai abin mamaki sanin naka bai amfana maka komai ba, tunda zaka iya tsayawa da wacce kwanaki kadan ya rage a daura mata aure a cikin lungu inda babu sawu.
Ni ba zan yi maka rashin adalci na yi maka kazafi irin yadda ka yi mini ba.
Sai dai na sha fa'da kai din azzalumi ne, ba masoyi ba. Ta ya ya an baka aure ka karba, dan kwadayin albarkar iyaye ita kuma ka dinga hure mata kunne da ga yiwa nata tsohon biyayya? Ban da ita din sakara ce har wanne kalami ne a bakinka da zaka tsara mata da yafi na ubanta da kannensa tasiri?".
Jabir ya sandare ya zuba wa Bulkachuwa ido, yana jin wata irin fargaba from no where tana shigarsa.
Yayin da ni kuma na dago ido jage jage da hawaye na watsa masa kallon kiyayya da raini na ce "Ba ruwan ka da ni Tijjani! Na saurare shi din, domin shi nake so, nake fatan kasance wa da shi".
Ga mamakina sai kawai ya ja kakkuran tsaki tare da ce wa "Ai ke din shasha ce! Kuma kin ji na saka maganata da ke?
Da shi na ke wanda na gamsu da hankalinsa da iliminsa, kawai adalcinsa ne bai gamshe ni ba. Amma ke da baki da hankali ina ruwana da ke?
Jiyan nan na gan shi da matarsa a asibiti yana ri'ke da ita. Yana faman tattalinta. Wai matar da ya aure ta ba dan yana so ba yake yiwa irin wannan son da adalcin, amma ke kullum yana cikin dama miki lissafi. Da yake ya mayar da ke shargalle marar tunani."
Ai kuwa yana rufe baki kuka ya k'wace mini sosai.
Jabir ya kasa magana domin ya tabbatar Bulkachuwa ya gansu a asibiti ba k'arya ya yi masa ba.
Bulkachuwa ya sake yin k'uta tare da nuna Jabir da yatsa ya ce "Neman aure cikin aure haram ne in ji ma'aiki (S.A.W).
Da ku'din aurena akan ta, ko ba zaka yi mini kawaici irin na zumunci ba, to ka yiwa ka'idojin shari'a biyayya. Ka fita mini a harkar Asiya! Ubangiji ya baka Maijidda wacce ita ce mafi alheri a gare ka. Amma bar mini Asiya Toro domin ina da yakinin akwai babban al'amari a tsakanina da ita. Daga ranar da aka tabbatar mini an ba ni ita, na fara addu'ar na yi nisan kwana mai yawa dan na tabbatar ni kad'ai na mallake ta".
Still Jabir ya kasa magana domin gaba'daya almarin ba k'aramin bugunsa yake yi ba.
Kishin Bulkachuwa ya shak'e shi k'warai da gaske. Domin idan gaskiya zai fa'da ya ga son Yabi a idonsa irin wanda bai yi zaton Tijjani zai yi mata ba. Mussaman yadda bai dauki soyayya da muhimmanci ba. Mace tana bata masa rai zai juya mata baya duk yarda yake da ita kuwa.
Ina kuka, ina kallon Yaya J. Na sani dan na yi ba'kin ciki ya sanya Bulkachuwa sako maganar Maijidda. Ban da haka mene ne dan ya nuna kulawa akan matarsa ta aure?
Nan da nan zuciyata ta hassala cikin rawar murya na ce "Mene ne dan ya kula da lafiyar Iyalinsa? Tabbacin nima zai kula da ni ke nan tunda har ya yiwa wacce baya so adalci to ina kuma a ce ni ce da yake so? Kai sau nawa ana ganinka da tambadaddun matan banza?"
Take jikin Yaya J ya yi k'wari domin yasan yadda nake da kishi na gaske, maganar Bulkachuwa na iya tunzura ni na yi masa fishi. Dan haka ya dan murmusa. Sannan ya ce "Ko yanzu na mutu a sanadin rashinki ba ni da kaico tunda kin mini kyakkawar shaida Yabin J".
Da rawar murya na ce "Idan ka mutu, kuma ka bar ni da wa? Wanne irin ba'kin fata ne, akan me zaka mini fatan irin wannan asarar haka?"
Tijjani ya harzuka ya ce "Ba zaka mutu ba ka ga yadda Asiya Toro zata manta da al'amarinka ba Jabiru.
Ya sake sakin tsaki sannan ya ce "Idan kuwa har ka mutu ba wanda ya yi asara irin abin da yake cikin Maijidda, sai kuwa ita Maijiddan, da zata shiga takabar mijin da yake sonta yake gudun bacin ranta".
Na sake fasa kuka ina fa'din "Allah ga Tijjani nan ya takura ni, ya fitine ni haka siddan, ka sani bana sonsa, ka gaggauta cire mini shi a duniya ta".
Sai lokacin Yaya J ya ce "Yi hakuri kin ji Yabi! Ko zan mutu ba yanzu ba, da saura In sha Allah".
Na wuce na fara tafiya a hankali.
Bulkachuwa ya ja tsaki ya ce "k'aryar banza! Dan Allah ka mutu yanzu Jabir. Da an ga tsiya domin kuwa ana dawowa daga rufe ka zan lallaba na koma. Tamkar wanda zan yi maka addu'a. Nan kuwa fitsari zan tsula maka a kabarinka ta yadda sai ka shekara a kwance kafin addu'ar jama'a ta riskeka, mussaman ta Asiya Toro. Kai da addu'a ta riske ka sai damina ta zo. Idan na so k'eta ma, daminar na dauke wa na sake tsula maka wani. Kuma idan juninka tsiya ne Maijidda na haihuwa zan aure ta. Na ha'da su da Asiya Toro su yi ta faman buga competition a kaina".
Na juya da nufin na yi masa raddi ya nuna mini yatsa ya ce "Idan kika kuma tozarta ni sai na fasa miki bakin ki domin ban yi da ke ba, marar kishin kai".
Jabir ya yi hanzarin ce wa "Kar ki ce komai Yabi cikin yanayi na kad'uwa sosai.
Ya kalli Bulkachuwa ya ce "Har zaka iya yi mini fitsari a kabarina Bulkachuwa? Sannan ka ce "zaka auri matata akan idona?"
Wani irin murmushi Bulkachuwa ya yi mai dauke da nisha'di da ma'anoni.
Ya ce "In dai son Asiya ya zama ajalinka zan tabbatar na hana adduarta riskar ka.
Sannan dan na auri Maijidda ai rufa maka asiri na yi tunda tare da abin da ta haifa zan ha'da na rikesu. Idan kuwa kana kishinta kamar yadda yanayinka ya nuna har ka kasa ha'diye hakan a gaban wacce kake kirarin kana so. To kawai ka k'yale mini Asiyata.."
*Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
*Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntubi marubuciyar Halin yau dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa*.
*08032773332*
✍️
[9/25, 9:06 PM] Hauwa Galadima: *WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE BIYA KUDIN KARATUNKI TA WANNAN ASUSUN DAN GUJE WA BAKAR TA'ADA!*
*REGULAR 500*
*VIP 1K*
*VIA*
*2384876855*
*SURAYYA IBRAHIM DAHIRU*
*ZENITH BANK*
*KO*
*7061488065*
*SURAYYA DAHIRU IBRAHIM*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*TURA SHAIDAR BIYA TA WADANNAN LAMBABOBIN*
*08032773332*
*09069067488*.
*Annur food Delicious*
*Da k'arfin zuciya da guiwa na ke muku shunen inda zaku samu kayan da na zano a kasa cikin saukakkan farashi.*
*Shaida nake yiwa kayan annur domin dadinsu da ingancinsu ya kai kurewa*
*HANZARTA ki nemi kayansu dan ki gasgata batuna*
*Garin kunun tsamiya garin danwake, garin borkono, yajin daddawa, man shanu, nikekkakiyar gyada ta kunu da ta miya*
*08039183880*
*KUN TUNA MAI GYARAN GUDUYO?*
*INA NUFIN FASEELAT BABBAR DILA TA G.H.T.*
*KO WANNE NAU'IN KAYAN GHT TANA SIYAR DA SU AKAN FARASHI MAI RANGWAME*
*KAWAI KU TUNTUBE TA A WANNAN LAMBAR DAN GANIN JERIN KAYAN DA TAKE DA SU*
*TUN DAGA KAN SUPPLEMENT, SABULAI DA LIPTON*.
*MASANIYA CE AKAN KAMFANIN DOMIN TA SAMU KARRAMA WA DAGA KAMFANIN A BANA, HANZARTA KI TUNTUBETA DAN SIYA DAI DAI KO SARI.*
*IDAN KUWA KINA SON YIN RIGISTA DAN FARA KASUWANCIN DA G.H.T. KAWAI KI TUNTUBE TA DAN KUWA DA KYAKKWAR ZUCIYA ZATA MU'AMALANCE KI*
*07039269802*
Jin hakan ya sanya na sake kwasa a guje sosai, duk karancin shekaruna na ji kunyar Babah irin wacce ban ta'ba jin ta akan kowanne mahaluki ba. Dan hakan nake sake azamar gudun dan na kubuta da sake tsaya wa a gabanta.
Amma da yake hanzarin mace da namiji ba d'aya bane.
Sai gashi ya cimma ni da taimakon k'anwarsa Ihisan suka mayar da ni har falonta duk yadda nake tirje wa ina kuka, ina fa'din su sake ni suka ajiye ni a gabanta.
Bayan Bulkachuwa a zafafe ya ce "Nasir sake ta."
Nan da nan kuwa ya sake ni.
Na zauna ina ha'da kaina da guiwa ina kuka sosai.
Babah ta ce "Jira ni mu tafi tare. Ai ba zai yiwu na bar ki ki tafi ke ka'dai ba.
Yi shirunki, tashi ki je ki yi wanka ki ji sanyi a ranki.
Da kaina zan mayar da ke, na kuma roki Yaya a fasa wannan ha'din."
Kunyar maganarta ta sake rufe ni. Na sake k'ara wa kukana sauti.
Da k'yar na mike na nufi dakinta da zan wuce na dan kalli Bulkachuwa da yake zaune a kujerar kusa da dakin yana shan abu a kofi, idanuwan sa sun k'ada amma ya maze tamkar baya wajen, ko kwakkwaran motsi yak'i yi.
Hakan da ya yi ya sake bata mini rai.
Ba dan komai ba saboda jiya ya kare ni a gaban mahaifina, sannan ya dinga rarrashina, har kowa ya zaci matsanancin sona ya kama shi farat daya.
Amma anan ya yi kamar ma bai sanni ba, ashe dama maza ma sun iya makirci?
Ko yaushe ma ya zo garin?
Na wuce ina cigaba da kuka rurus.
Da taimakon Ihisan na yi wanka. Na sauya zuwa doguwar rigar da na zo da ita a leda.
Sai da ta ga na nutsu sannan ta bar ni, ta tafi Islamiya.
Sa'armu ce, ni na girmeta da watanni biyar.
Da la'asar Babah ta leko ta ce mini zasu shiga barka da taaziya mak'wabta.
Yanzu zata dawo na fito falo, na yi kallo.
Nasir yana d'aya dakin yana guga.
Na sani kuma dan ya mata gadina ne ta zaunar da shi tare da saka shi gugar kayanta da na Ihisan.
Ina jin yana kunkunin shi ba zai goge na Ihisan ba.
Yayin da Babah ta rantse sai ya goge.
Shi bai ga irin hidimar da take yi ba?
Kullum ita take girkinsu ya d'ebo ya ci babu godiya.
Sannan ita ce mai gyara dakunanta da falo ya zo ya zauna har ya bata wajen.
Shin shi ba zai dinga ji tausayin mace bane?
Ta sake cewa "idan baka ji tausayin mace ba me zaka yi mata Nasir?
Allah da kansa ya ce mata raunin su mai yawa ne.
Ka koyi kyautata mata, da jin tausayinta, sai ka ga idan an baka amanar mace ta hanyar aurenta baka musguna mata ba, domin dama ka saba. Mene ne dan kana mata wanki da guga?"
Bulkachuwa da yake zaune a kusa da shi, bai ce k'ala ba.
Domin yana wahalar gaske ta kula shi.
Amma shi da kansa ya sani magana mai harshen damo take yi.
Ta fita tana fa'din "sai mun dawo".
Tare suka ha'da baki wurin fa'din "Ku dawo lafiya"
Nima a hankali na ce "A dawo lafiya".
A zahiri kallon nake yi. Amma gaba'daya tunanina yana gida. Ko ya suke ciki?
Zuciyata ta harba da wanne idon zan kalli Gwaggo?
Ya ya Babanmu zai kalle ni?
Na dinga jin nadama tana kama ni.
Hawaye ya dinga zuba tamkar ba kwana na yi ina yi ba.
Haka dazun ma na yi kuka tamkar idona zai kafe.
Ba zato na ga Bulkachuwa zaune a kujerar da take fuskantar wacce nake zaune.
Murya babu amo ya ce "ya kamata ki yi kuka fiye da haka Asiya Toro".
Wani malolon ba'kin ciki ya makure ni, na ji zafin fa'din Asiya Toro fiye da koyaushe.
Ya sake yin k'asa da murya ya ce "na raina wayon ki Asiya! Jiya akan idona Baban Marina ya zane ki har nima fishin ya shafe ni. Da zan d'aga miki rigata da kin ga yadda bayana ya farfashe saboda kare ki da na yi.
Na dauka wannan bacin ran da kika sanya shi ya isa ki kwantar da hankalin ki, ki saki ran ki, ki yi masa biyayya, a gefe kuma ki yi ta addu'ar kada Allah ya k'addara miki aurena idan babu alheri. Amma sai kika kwaso jiki kika gudo wajen yar'uwar sa, kin kuma san k'anwa ce a wajensa idan har da tarbiya ba zata je gabansa ta yi inkarin hukuncinsa, ko ta goya miki baya ki bijire masa ba.
Amma dan baki da mutunci ki zo har gabanta kina fa'din ba kya sona! Ke ba ki ji a ranki sai maganar ta bugeta ba? Ba ki ji furucin zai iya janyo wa ta washe ki ba?
Tunanin ki bai fa'da miki ita ta kawo ni wannan duniyar ba, ko kuwa tsabar wula'kanci da rainin wayon ki ne ya kai k'ure wa?"
Duk tsiwata sai na kasa tanka masa domin idan har gaskiya zan bi, to zahirin gaskiya yake furzar wa.
Hawayen takaici da ba'kin ciki suka ci gaba da tsere a kumatuna.
Ya zarce da fa'din "k'iyayyar da kike yi mini ta saka kin manta da neman zabin Allah, ke dai ba kya so na, ke dai a kubutar da ke aurena.
Abin mamakin ni namiji ban yi irin wannan asaranci ba sai ke mace?
Ko kin ta'ba ganin wata alama da take nufin ina son ki?
Amma saboda tausayin ki da nake ji, saboda kimar Baban Marina sai na ajiye komai, na amince da ke, nake kuma yi miki tanadin alheri da gata."
Cikin kuka na ce "ka ri'ke