Showing 93001 words to 96000 words out of 214110 words

Chapter 32 - Bakar Ta'ada Complete hausa novel

24 Aug 2024

11130

ba?
Kina kallon kayan miyan can da yawa sun lalace. Ya kike so na dinga yi ne? Idan na fita tun safe na dinga bulayin abin da zan yi na samu taro da sisi dan asirinmu ya rufu amma bazan dawo na tarar da kwanciyar hankali ba? Yini nake cikin zullumi da fargabar halin da kike ciki, da abin da zan dawo na tarar.
Me yasa bani da wata alfarma ne a wajen ki?"
Na zum'bura baki ainun.
Tsawon lokaci ban ce komai ba.
Ya numfasa ya ce "Pls Asiya na roke ki, mu zauna lafiya ki kwantar da hankalinki dan Allah".
Tsawon lokaci ya dauka yana rarrashi, akan na ce masa na yarda zan dinga yin girki.
Amma ban yarda na ce masa komai ba.
Ya harzuka ya ce "Allah kai ne shaida ta."
Ya tashi ya bar ni.
A hakan na cike sati biyu.
A wannan lokacin kuma aka fara zuwa mini lalle da kitso. Na rasa a inda zamu dinga zama. Domin tsakr gidan babu bishiya kuma babu rumfa.
Baranda kuma idan rana ta bude babu dadin zama.
Dakin da kayansa suke nan ne yafi dace wa ya zama dakin da zan dinga yin sana'a ta.
Dan haka na shiga na tattara masa kayansa gefe d'aya, na kunna turaren wuta a dalilin kayansa masu datti na zube a k'asan. Na ha'da na d'aure su waje guda.
Yini na yi ina lalle. Sai yamma ya dawo gidan da ledar abincin da ya siyo mini.
Kallonsa kawai na yi, na gane ya ji haushin cika masa daki da na yi da mata.
Ya ajiye abincin ya juya.
Sai dare ya dawo lokacin babu kowa. Tuni kuma na share dakin na kintsa shi tamkar ba'a ciki muka yi ba.
Fuskarsa a daure ya tarar da ni ya ce "Asiya Toro kada ki kuma shigar mini daki da nufin yin kitso ko lalle".
Na cuna baki na ce "Idan na kuma fa?"
Ya girgiza kai ya ce "To ki kuma din".
Washagari da hantsi sai ga Rafi'a ta shigo mini.
Da walwala na karbe ta.
Ta dinga fa'din "Amarya ashe haka kika iya kunshi da lalle?"
Da murmushi na ce "Ina koya dai, idan kina so sai ki zo na yi miki".
Da babbar muryarta ta ce "Ai kuwa na gode sosai".
Tijjani na fita na shiga d'akin muka fara yin kunshin.
Kafin na gama mata har mutum ukun sun zo.
Da azahar ya dawo gidan, ko d'ar ban ji ba, balle na yi fargabar na karya dokar sa.
Ga mamakina bai shigo ba, bare ya dauki matakin da nake son ya dauka.
Amma sai na ji ya bu'de murya yana kiran Rafi'a daga falon.
Ita kuma ta shiga da saurin ta.
Wani irin abu ya d'an mintsini zuciyata.
Amma na sanya jarumta na boye abin dana ji din.
Ina dan jiyo maganganunsu, har na fahimci sun saba dama tunda yayanta abokinsa ne.
Bansan me ya ce mata ba, na ga ta fito ta shiga kicin.
Abin ya sake buguna.
Ban ankara ba na ji ta fara jajjage.
Wata babbar mace da na gama sanya wa lallen.
Ta kalle ni babu alamun wargi ta ce "Je ki karbi hidimar mijinki a hannun waccar yarinyar tun baki janyo wa kanki sanadin bacin rai ba".
Na yi yak'e na ce "Ai tare muke da ita, k'anwarsa ce."
Ta saki gauron numfashi ta ce "Tau ya yi babu laifi, na dauka babu sidi bare sadada a tsananinku. Amma dai kada ki fara saka wani lallen, tashi ki je ki marabce shi, ki bashi ruwa sai ki dawo.
Ki kula da auren ki da kyau kin ji".
Ganin ta haife ni, dan na tabbatar tana da yaran da suka zarta ni.
Hakan ya sanya na tashi na yi tamkar na je wajensa, nan kuwa dakina na shiga na zauna bakin gado.
Tamkar mai jirana sai gashi ya shigo mini.
Ya kaurara murya ya ce "Asiya Toro ba ki ji kashedin da na yi miki ba akan shigar mini daki da mata ba ko?"
Na murguda baki na ce "Ban ji ba Tijjani! Ba kuma zan ji ba".
Ya ce "Shike nan"
Na riga shi barin dakin.
Ina kallon yadda ta shirya masa abincin a tray, cikin flask mafi kyau a kicin din.
Plate din na tangaran ta saka. Maimakon da ta kai ta fito, sai ta yi zamanta suna hirarsu.
A daddafe na kammala lallen. Dan da wata ta zo ma ha'kuri na bata, na ce ina da ayyuka mai yawa ga kuma maigidan na nan.
Wani irin makakin ba'kin ciki nake ji har cikin mak'oshina.
Duk da bana son Tijjani amma na ji zafin kiran Rafi'a da ya yi. Mussaman umarnin yi masa girki da ya bata.
Ina da eani irin kishi tun ina karama ta. Har ta kai Gwaggo kullum cikin yi mini addu'ar samun sassauci take yi.
K'asan zuciyata kuma ban yarda kishinsa nake yi ba. Tunda ba wai ina sonsa ba ne. Kawai wula'kanta ni da ya yi ne ya mini ciwo.🤣
Sai da ya gama ta fito da kwanukan abincin.
Da murmushi ta ce mini "Na gode sosai Amarya. Sai na sake shigo wa".
Ga mamakina na kasa yi mata ko da yak'e ne.
Murya a dakushe na ce "Madallah".
Da daddare ina falo, ina kallo ya dawo. Sai da ya yi wanka, sannan ya shigo ya zauna.
Cikin nutsuwa sosai ya ce "Asiya na ce kada ki kuma shiga mini daki da nufin yin lalle ko kitso amma baki ji ba ko?"
Yana rufe baki na ce "Tijjani ban ji ba, ba kuma zan ji ba, ka yi abin da zaka yi marar tsoron Allah kawai".
Ya yi mini k'uri ya ce "Me na yi miki na rashin tsoron Allah? Ni ban fa'di hakan akan ki ba, sai ke zaki fa'da mini hakan?"
Babu fargaba na ce "Ina da tabbacin bana aikata kaba'ira, kai kuwa kaba'irori nawa kake aikata wa? Tsabar shaharar da ka yi a BAKAKEN TA'ADODI har gidan auren ka ma bai tsira da sharholiyar ka ba".
Ransa ya baci. Amma da ya fahimci kishin Rafi'a ne ya k'ume ta, sai farin-ciki ya maye gurbin bakaken kalamanta. Da alamun da Rafi'a zai yi amfani ya dinga rama wula'kanta shi da take yi.
Ya girgiza kai ya ce "Sharri dai dan aike ne. Mussaman wanda aka ginasu akan zato da jita jita."
A kufule ainun na ce "Ba batun sharri a lamarinka. Iya karshen cuta an yi mini. Amma na barwa Allah al'amurana"
Na fa'da hawaye na subuce mini".
Ya kasa cevwa komai.
Tsawon lokaci mun yi jigum jigum! Sai hawaye da suke tsere a kan fuskata. Babu kuzari ya taso ya dawo kusa da ni sosai ya sassauta murya ya ce "Kinsan bana son kukan ki Asiya!
Na tari numfashin sa a zafafe na ce "A gidan uban waye baka son kukan nawa? Makaryaci, mugu, bunsuru..!
Ai ban karasa ba, na ji wani irin gigitaccen mari a fuskata. Wanda ya sanya na zunduma ihu a matu'kar ki'dime.
Cikin fishi mai yawa ya ce "Kin ci uwar karya kin kwana da yunwa Asiya. Kin yi ka'dan ki zagi ubana, ki wanye lafiya. Ashe togaciyar da na yi miki kwanaki a zauren gida baki ji ba?
Wallahi ki mutunta ta kan ki, ki kame bakinki daga zagina. Ni zaki ce wa a gidan uban wa? Ubana zaki zaga? Baki isa ba, rashin kunyar ki ya tsaya a kaina. Ni da kike ganina nasan mutuncin iyayena da gaske, ba wai yaudarar ina sonsu a baki ba, amma na kasa kare musu martabarsu a bayan idonsu ba."
Ya mike tsaye ya ri'ke kunnensa alamun gargadi.
Da kumfar baki ya ce "Billahillazi kika kuma yi mini lalle a daki sai na wula'kanta ki, ke da gayyar ta ki.
Sannan yau ne rana ta karshe da zaki yi gigin zagin iyayena. Ki bari, bana so! Idan kuma kin ki ji, lah shakka ba zaki k'i ga ni ba".
Ya tafi ya bar ni ina kuka mai tsananin gaske, domin ba k'aramin shigata marin ya yi ba.
Tunda ga wannan lokacin gaba ta k'ullu a tsakaninmu mai tsananin gaske.
Ya fita daga al'amarina gaba'daya. Baya bin ta kaina, yana dawowa daga sallar asuba zai fice tun gari bai yi haske ba. Ba zai dawo ba sai wajen Tara. Nan ma yana gama uzzirinsa zai sa kai ya fice. Ba zai dawo ba sai dare.
A hakan na fuskanci wajen gini yake zuwa. Fitar asubar ne bansan me yake yi ba. Zuciyata har kissima mini take yi lalata yake fita yi. Dan haka na sake wasarsa, na sake jin haushinsa.
Bana girki sai dai na saka almajiri ya siyo mini, abincin siyar wa tunda ana yi a makwabta.
Ina samun lalle da kitso. Ban kuma fasa yi a dakin nasa ba. Sai dai kafin ya dawo sun tafi, ni kuma zan gyara masa dakin, sai dai k'amshin muhallabiya ya kama dakin.
Bai ta'ba magana ba. Ban sani ba, ko dan bai dawo ya tarar da mu a ciki ba. Ko kuwa ya hakura ne?.
Cikin wannan yanayin da muke ciki na yi matu'kar rame wa. Na yi baki. Kullum cikin kuka da b'acin rai na ke.
A ranar da na cika wata guda a ranar Dada ta zo ganin dakina.
Bulkachuwa da kansa ya dauko ta a mashin ya kawo ta.
Ta dinga yaba tsarin dakunan.
Amma ta kasa gamsuwa da yanayinmu. A sanyaye ta ce "Mai sunan manya Yabi ta sake kankace wa, ta yi duhu, duk da ita fara ce kal.
Kai ma dube ka, babu wani annurin angwanci tare da kai."
Ga mamakina sai ya sassauta murya ya ce "Kowa da yadda yake fuskantar kalubalen duniyar nan ai.
Me nake da shi da zan jiyar da Asiya da'di bare na samu nutsuwa da ita. Na barwa Allah komai. Idan na mutu Dada na yafe miki wannan ha'din da kika jagoranci aka yi. Cike nake da fargabar kada auren namu ya sake d'aid'aita zumuncin gidan Marina."
Dada ta dauki salati tana fa'din "Ashe har yau baku shirya ba? Ashe ba kalau kuke zaune ba, shi yasa ka dinga zille wa idan na ce ka kawo ni gidan ka?".
A hankali ya ce "k'alau muke Dada."
Ta kalle shi ta ce "Tashi ka bamu wuri."
Bai yi musu ba, ya fita din.
Ta kalle ni ta ce "Haba Hajja Yabi. Me yasa ba zaki kwantar da hankalin ki ba? Mai sunan manya son ki yake irin son nan mai tsananin gaske. Ban ta'ba ganin abin da ya sanyaya shi irin lamarin ki ba.
Tun wanccan satin na je gidan Ubaida tana zaune k'alau da mijinta. Sai ke ce zaki kunyatamu?"
Na rushe da kuka sosai na ce "Ita mijinta ai baya wula'kanta ta, baya yi mata sanadin da zata kwana ta yini da yunwa. Mijinta mai kamun kai ne. Amma ni kuwa fa?"
Kuka ya ci k'arfina sosai.
Duk son kan da Dada ta wanzu tana yi a tsakaninmu da su Bulkachuwa a wannan ranar na ga damuwa mai yawa akan fuskarta. Na ga alhinin halin da ta gan ni a ciki a jikinta
Ta bu'de baki ta kira shi. Ya amsa ya shigo.
Ta ce "Me ka ke yiwa yarinyar nan haka? Ai farkon zaman bata birkice ba, tunda kowa ya zo sai ya ce Yabi tana zaune cikin walwala kamar ba ita ba. Me ya jefa ta cikin wannan tashin hankalin?"
Da rashin kuzari ya ce "Zagi irin na tsamar nama ta yi mini. Hakurina ya k'wace na mare ta. Shike nan fa! kuma yau zancen nan an kai sati biyu. Amma ta taurare ta k'i barin abin ya wuce."
Ya fa'da cikin damuwa mai yawa.
Dada ta ce "Ai baka rarrashe ta ba. Baka ha'diye fishin ka dan ka kawo masalaha ba."
Da sauri ya ce "To na yarda, na yi kuskure, taya ni bata hakuri. Bazan sake dukan ta ba, amma ita ma kada ta sake zagi na".
Tausayinsa ya cika Dada domin ta sake fahimtar ya fa'da matsanancin soyayyar Yabi.
Ta nisa ta ce "kin ji abin da ya ce Yabi. Ki yi ha'kuri, komai ya wuce ba zai sake ba.
Na cigaba da kuka sosai. Ina son na fa'da mata ni girkin da ya sanya aka aka yi masa ne, yafi nukurkusa ta fiye da marin. Amma bansan dalilin da ya sanya na kasa fadar wannan maganar ba.
Ta dinga rarrashina tamkar ba Dada da bata yi mini sassauci ba.
Sai da na yi shiru. Sannan ta kalle shi a zafafe take yi masa magana.
"Idan har ka kuma dukanta, to ka tabbatar zan aikawa uwarka ta zo, tunda ka nuna ban isa ba. Ai ba'a baka ita dan ka dinga gwada mata k'arfi ba. Duka duka ma nawa take ne Yabin? Ba zaka yi hakuri da kuruciyar ta ba?"
Ya yi shiru ya kasa bu'de baki ya fa'di abubuwan da nake yi masa.
Karshe ya buge da bata hakuri da al'kawarin zai canja.



Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki*
*Maganin sanyi*
*Saiwowin Tsumi*
*Saiwowin dahuwar kaza*
*Saiwowin dahuwar tattabaru*
*Gumba*
*Tsumin kwakwa*
*Y'aya'n gadali*
*Hadadden daka*.
*Tsugunno mai sa a matse*
*Goran tula*
*Goran tula syrup*
*Garin goran tula*.
*Maganin gyaran nono*.
*Zuma ta mussaman*.
*Tsumi*.
*Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*.
*Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*.
*Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya*
*08032773332*.
✍️
[9/27, 11:34 PM] Hauwa Galadima: *WANNAN LITTAFIN NA KUDI NE BIYA KUDIN KARATUN KI TA WANNAN ASUSUN DAN GUJE WA BAKAR TA'ADA!*
*REGULAR 500*
*VIP 1K*
*VIA*
*2384876855*
*SURAYYA IBRAHIM DAHIRU*
*ZENITH BANK*

*KO*
*7061488065*
*SURAYYA DAHIRU IBRAHIM*
*OPAY DIGITAL SERVICES.*

*TURA SHAIDAR BIYA TA WADANNAN LAMBABOBIN*
*08032773332*
*09069067488*.

*UMM NIHLA COLLECTIONS*
*Ta k'ware wajen kawo yadina masu kyau da sauki, cotton da silk, embroidered, Batik*
*A Malaysia take daga can kuma take turo su Kano direct. Dan haka kayanta akan farashi sari take bayarwa, daga guda daya har zuwa dari zaku samu*
*Kayan ta masu aminci da rahusa ne, ku tuntube ta Whatsapp dan ganin JERIN gwanon yadinanta da basa kode wa ko jeme wa*.
*07020695644*
*What's app only*.

Tsawon lokaci kafin su samu na yi shiru.
A kokarin Dada na son na warware sosai, sai ta fasa tafiyar ta ce ya yi tafiyarsa sai yamma ya dawo ya mayar da ita gida.
Ya fita, sai kuma ya bu'de baki ya ce"Asiya".
Na yi shiru kamar ban ji ba.
Dada ta sassauta ta ce "Kiran ki yake yi fa Yabi.
Ki na son ki k'one ne? Girman sa yawa ne da shi a wajen ki fa".
Na tashi bayan na cuna baki tamkar na buta.
Da fishi sosai na tsaya a gabansa.
A sanyaye kuma murya k'asa ya ce "Zan je na samo ko kifi ne, ki yi girki dan Allah".
Nan da nan na ce "Wallahi bazan dafa da kai ba".
Ya ce "Shike nan ki yi muku. Hakan ma na gode sosai".
Ya fita na bishi da harara. Ba'kin cikin yadda na takarkare na yi masa doya da k'wai ya k'i ci, ba k'aramin cizo na yake yi ba har yanzu.
Sannan girikin da ya sanya aka shigar mini kicin aka yi masa, sai ya gane ni ba irin matan da za'a yi musu hakan ba ne.
Bai wani jima ba, ya dawo. Sai da ya shiga kicin din sannan ya fito ya yi dakina.
Dada ta zuba mini ido alamun na tashi na bi shi.
Akan dole na je din.
Ya mik'o mini leda mai d'auke da sink'in sabulun wanka da kwalin TURAREN
Ismiyaki.
Na kar'ba galala.
Ya ce "Idan zata tafi sai ki bata".
Na gatsina baki na ajiye a bakin gadon ban ce komai ba, na fita na bar shi a tsaye, ya yi wani iri abin tausayi!.
Ya fito ya dan tsokani Dada sannan ya fice.
Zafi ya sanya na yiwa Dada shimfida a baranda.
Ta fito, muna hirarmu ina gyaran kayan miya.
Ina tunanin artabun da zan yi da attaruhu yayin greting. Don kuwa indai na murtsika attaruhu sai na kwana na yini hannuna na yin mini zugi.
Kwatsam aka kawo wuta. Cikin karambani da giggiwa na ha'da bilandar na fara markade.
Sai da na zuba shinkafa a dalilin ruwa ya tafaso.
Sannan na koma wajen Dada.
Da murmushi ta ce "Oh ashe dai da rabon za'a samu mai tu'amalli da injin markade na zamani a jikokina".
Na yi dariya tare da cewa "Dada kenan.
Bari na zauna ki d'ora mini karatu, ina kewar karatun ki."
Ta gyatta, na zauna kusa da ita.
Ta ce "Tunda Ubangiji ya sanya na ga auren ki har ga ni a gidan ki.
To zan 'dora miki karatun da har abada kin wuce yin boranci a idon namiji. Ban ta'ba koya wa kowa wannan addu'ar ba, saboda jarraba namiji ake yi da ita k'warai da gaske. Kema dan ina son ki tsare mijin ki, daga sharholiya ne!".
Ban ce komai ba.
Ta yi waiwaye dan ta sake samun tabbacin babu me jin abin da zata furta.
Ta matso kusa da ni ainun.
Murya k'asa kasa ta ce "A yayin da kuka shiga mayafin aure sai ki yi Bismillah ki ce "Allah daraja, MA'AIKIN Allah daraja a taimake ni akan aure. Zan jarraba y'an maza wane.. Ibnu wance.
Ki kamo ainihin sunan sa da sunan babar taku, sai ki tofo yawun bakinki akan yatsan sai ki yi matsi da wannan yawun addu'ar. Amma a zuci, zaki yi fa". Ta fa'da da dukkan zuciyar ta.
Duk da na saba jin karatun Dada wannan ya yi matu'kar sanya ni mamaki da dariya.
Amma na sanya jarumta na maze, na yi k'asa da kaina a zuwan kunya ce ta hana ni sukuni.
Ta kuwa dage ta ce "Ba kunya zaki ji ba Yabi! Na baki wannan fahamin ne dan na taimake ki, ku zauna lafiya. Amma fa kada ki yarda ki dinga jansa a k'asa. Domin k'arfin addu'ar yawa ne da shi tamkar yankar wuka take".
Na k'yal-k'yale da dariya saboda bilhakki take maganar zan jarabta shi da wannan karatun surkullen.
Sai da dariya ta tsagaita mini na ce "Allah ya bada lada Dada. Amma ni bazan yi a kansa ba. Baya sona, bana sonsa. Kowa harkar gabansa yake yi."
Ta dauki salati tana fa'din"Ashe har yau baku zama d'aya ba? Tisa ki yayi a gaba yake kallon ki kawai?
To idan na tafi zan fara tsayawa wajen Malam Nata'ala na ji ya ya matsayin aurenku.
Domin nasan duk ma'auratan da suka shafe kwanaki arba'in basu hadu ba, tabbas aure ya haranta. To ku kwanaki talatin da biyu da aurenku. Zan je na sake jin fatawar kada aje ko auren ya b'aci ba'a sani ba".
Na yi shiru domin na kasa gane bayanin na ta. Ban ce komai ba, domin kuwa ban ta'ba jin makancin hakan ba.
Ta numfasa ta ce "Yabi kin san duk macen da ta ki d'agawa mijin auren ta k'afa. Zata zama makamashi ne a cikin wutar jahimu?"
Na yi shiru tare da b'ata fuska. Ta sake ce wa "Wannan hukuncin lahira ne. A duniya kuwa babu ita babu ganin hasken rayuwa tunda malaiku dubu maitan ne zasu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login